Showing 36001 words to 39000 words out of 77913 words
toh kuma a wajen ina suke?
Yayi murmushi ganin yanda bata iya boye damuwarta ya ce " ai ki gama cin abincin sai mu tafi ki Gansu KO?
Sahla ta ce " ba damuwa
To fa Sahla shin kin sans abinda mijinki ke tanadar miki? ..........'
[
*'YAR 👧🏻*
*MAHAUKACIYA👹*
*_Na SAJIDA_*
42
Bayan ta gama cin abincinta yana zaune saman baban kujerar tsakar falon yana kalon TV ta fito da wandon nata da rigar ta ce " mu tafi husby
Mubasshir ya dago kansa yana kalonta shi bai san ana konbo da rama ba sai a kan Sahla ya girgiza kansa ya mike ya dauko mata abaya baka da mayafinta ta karba ta saka tana yatsina suka kama hanya , ita dai burinta ta ga su waye a cikin gidanta
Tafiya ta kai ta minti goma da suka yi a tsakar gidan sanan suka ISO wani wajen mai shegen kyau , abinda ya bata mamaki yanayin ginin wajen ya fi nata kyau , haka dai ta zuba ido tana biye da shi har ya tura ya shiga da salama , ta biyo bayansa itama tana wara idanuwanta
Wata irin zabura tayi abinda idanuwanta suka gane mata , wasu tsafi ne yangom a zaune a saman cafet suna cin abinci wata tsanwar miya mai warin dadawa ta doki hancinta idanuwanta suka sauka a saman miyar gogo wace sam ba hakora a bakinta abincin ma sai ta dame shi sanan take iya hadiyewa ga bakin nata gaba daya ta jamula shi da miyar wata irin tashin zuciyar ba gyaira ba dalili ta tasowa Sahla da sauri ta saka hanunta ta toshe bakinta da hancinta ta zaro ido ganin Mubasshir ya saka hanu yana sakawa wata tsohuwar abinci a bakinta sanan ya juyo ya nuno mata sahla , Abinka da tsafi aikuwa ta Mike da kyar tana fadin Yau ga matar Yaron mu har cikin gidan mu
Sahla ta shiga baya baya dan ta lura dukan su fama suke su taba mata jiki , bata Ankara ba taji wata ta taba ta tana juyowa ta ga Gogo ce ai bata san lokacin da ta saki ihu ba ta juya da gudu ta nufi bangarenta tana rusa kuka wiwi
Mubasshir ya zaro ido ya san a rina aman bai taba tinanin abin zai kai haka ba , wai a nan ta tardo su an kimtsa su ne , da irin kafin ya tafi aiki da yake biyowan nan ne da ta suma ma dan a lokacin suka farka wasu har kashi a nan suke yin kayansu dan kuwa tsafi ne sosai ya tara yake ciyarwa da shayarwa bisa yardar hukuma da saka hanunta harma masu gatan dan kuwa irin kulawar da yake basu tafi wace zasu samu a gidan nasu
Sai da ya zazaunar da su yayi Kiran masu kula da su sanan ya juya ya nufi bangarensa
Yana shiga kakarin amai ya fara ji ya girgiza kansa ya nufi dakinsa yayi konciyarsa ya dauki waya yayi Kiran mahaifiyarsa
Daidai lokacin suna zaune Hajiya Fadimatu na gyarawa Yar Mahaukaciya gashinta dan gobe zata fara zuwa makaranta wayar dakin tayi ringin
Yar Magaukaciya ta mike ta dauko dan wayar jikinta da doguwar waya Wace za'a iya janta
Hajiya Fadimatu ta ce" daga maga mu ji kowaye?
Yar Lahaukaciya ta daga ta yi salama
Daga dayan bangaren Mubasshir ya ja wani dogon nunfashi ya kasa amsa salamar muryar nan duk da sanin mahinmancin salama haka kawai ya tsinci kansa da wani irin yaunin baki
Yar Mahaukaciya ta ce " hello , heloooooooo?
Ta mikawa Hajiya Fadimatu tana fadin Mama ai ba'a magana KO an datse Kiran ne ban sani ba ?
Hajiya Fadimatu ta karbi wayar daga hanun Yar Mahaukaciya ta kara a kunanta tayi salama
Daga dayan bangaren Mubasshir ya amsa salamar a kasalance sanan ya ce " Maman Mubsshir ina yini
Hajiya Fadimatu ta saki murmushi dan ta gane ya kasa amsa salamar ne jin muryar Rahma , ta amsa gaisuwar sa sanan ta ce " lafiya nake jin muryar taka kamar maran lafiya?
Mubasshir ya shiga kame kame ya ce" am daman aa baci ne nake ji shine nayi kira nayi miki sai da safe
Hajiya Fadimatu ta ce " To Allah ya tashe mu lafiya , am daman insha Allah tomorrow yarinyata zata fara zuwa makarantar islamiyar fa
Mubasshir ya danyi Jim sanan ya ce " Maman mubasshir plz a kula da tsaronta direba ya ringa kaita yana jira har ta fito ya daukota ya dawo da ita saboda kinga ba'a so a san inda take , sanan malaman nasu mata ne kadai?
Hajiya Fadimatu ta ce " da mata da maza ne
Yayi Jim sanan ya ce " To maman Mubasshir plz ta kula
Hajiya Fadimatu ta ce " kai ni fa na haifeka zakana kokarin koyar da ni yanda zan kula da yata? Aman ai batayi baci ba KO na baka ita kayi mata hudubar?
Da Sauri ya ce " no maman Mubasshir kiyi hakuri ba haka nake nufi ba , love u , good night
Hajiya Fadimatu tayi Murmushi a ranta ta ce zama kayi nufin hakanan din aman a fili ta ce " ohk by a gaishe min da Sahlan ta datse Kiran
Mikewa yayi zaune daga koncen da yayi ya shiga kikifta idanuwa ya ce " Maman Mubasshir plz da hakuri kika yi KO wani irin malami take da bukata sai na dauko ya ringa koyar da ita saboda kar aje rana ta baci ldriss ya hadu da ita alura ta tono garma ( to fa ka tabatar dan haka kake gudun fitarta? )
Haka yayi ta tinane tinane hardai ya yanke shawarar da shi kadai ya san kayansa ya gyara konciyarsa yana adu'ar baci ya lumshe ido yana fatan zakara ya bashi sa'a 🤔
Karfe bakwai ta gama abinda ta saba sanan ta shiga wanka tana fitowa ta zauna ta shafa mai ta daga kayan makarantar tata ta islamiya doguwar riga ce har kasa sanan hijabi shima har kasa da nikaf na matan aure da budurwar dake bukatar saka shi
Ta saka rigar Kenan tana kokarin konce hijabin dan an daure shi ne da wata yar igiya wayar dakinta tayi kara ta matsa a hankali ta daga tare da salama
Hajiya fadimatu ta ce " yar Fadimatu sauko ina jiranki yanzu
Yar Mahaukaciya ta ce" to mama
Ta ajiye wayar ta sauko da hijabin dan Hajiya Fadimatu ta konce mata daurin tana zuwa ta tarar da Hajiya Fadimatun zaune tana zuba abinci cikin faranti , ta duka tana gaisheta
Hajiya Fadimatu ta amsa tana murmushi daidai nan aka turo kofar falon aka shigo
AA ne cikin wata dakakiyar shada fara kar sai zuba kamshi yake ya shigo da salamarsa
Hajiya Fadimatu ta zaro ido ta ce " lafiya da safiyarnan? Mai ya fito da kai yau? Ka manta al'adar mu ne?
Mubasshir ya karaso yana murmushi ya kama hanayen mahaifiyarsa ya ce" Maman mubasshir i really miss u , kinga abokina ya gayaceni yau shine na biyo na ganki kafin na fice
Hajiya Fadimatu ta ce " Kenan ka karya dokar?
Mubsshir ya ce " Maman Mubasshir Al'ada ba adini ba , kinfi kowa sani , so please ki bar maganar nan kiyi murnar ganina
Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta ce" to sanunka da zuwa
Yar Mahaukaciya dake tsugune ta ce" barka da safiya yaya
Mubasshir ya juyo ya zuba mata ido ba wata kwaliya tayi ba aman har wani fizga yanayinta yake, ya ce " Barkan ki
Yar Mahaukaciya ta Mike ta mikawa Hajiya Fadimatu hijabin na hanunta ta ce " Mama na kasa kunce wanan daurin gashi lokaci ya kusan yi
Mubasshir bai san ta ina maganar ta fito ba saï ji yayi bakinsa na fadin" halan wanan rigar da ita zaki tafi makarantar ?
Hajiya Fadimatu da Yar Mahaukaciya suka kale shi a tare , da tambaya a fuskar su
Sai a lokacin ya gane cewar yana fa son ya kwafsa kansa hakan yasa cikin basarwa ya dana wayarsa yana kalon kofa ya ce" am naga kamar tayi kadan ne , am manta ,
Ya mike yana fadin Maman Mubasshir tayi sauri dan hanyata ne na sauke ta sai na fice yayi waje yana karasa zancen
To fa Malan yayadai???????
[
*'YAR 👧🏻*
*MAHAUKACIYA👹*
*_Na SAJIDA_*
43
Ya kai minti ashirin a zaune cikin mota yana jira , abinda bai taba yi ba a rayuwarsa wato zaman jiran mutun ya fito koma waye dan koda mahaifiyarsa zai fita ta san halinsa bata barin sa zaman jira dan kuwa yanzu zai fara shiga yana fita yana takurata da Maman Mubasshir ki fito plz, aman wai yau shine zaune yana jiran fitowar wanan yarinyar da ba komansa bace , haka kawai ya ja tsaki a fili ya ce " dan na kula da amanar da na daukowa kaina ne da ba dan hakan ba da ba Wanda zai fito da ni a yau daga gidana ,
Yana tsaka da mita ya hango fitowarta ya tsura mata ido nan da nan ya ji wani sanyin dadi na ratsa shi ganin hijabinta har kasa sai dai fuskarta a bude kuma da alama da nikaf a hanunta ,
Horn ya dana hakan ya sa ta nufi motar dan kuwa ita a tinaninta ai yayi tafiyarsa tana isa ta Buda baya ta shiga tana furta barka da warhaka Musa direba
Maganar ta tsaya mata a makogwaro sanadiyar hada idanuwa da suka yi ita da Dan Aljannah
Ido ta zaro tayi Saurin dora hanunta a saman bakinta tana kikifta ido ta ce " yaya yaya kayi hakuri nayi tinanin Musa ne yake yi min horn i'm sorry ta karasa tana kokarin bude motar ta fita sai karkarwa hanunta yake sanan motar taki buduwa
Sai da ya gama kalonta a yanayin tsoro son ransa sanan cikin dakakiyar mirya ya ce " ba'a tsayar da ni jira , wanan ya zama na farko kuma na karshe cos hakan na bata min rai ba kadan ba , ki dawo gaba dan ni ba Musa direba bane
Wani iri yake saukan mata a jiki yanayin maganarsa gaba daya tamkar tayi tsere haka take jin zuciyarta nayi mata lugude da kyar ta samu ta bude motar ta fito tana ta adu'a ta bude gidan gaba ta shiga kanta a kasa sanan ta kama yar karamar yatsarta tana ta murzawa da karfi tamkar ita tayi mata wani laifin
Tafiyar kurame ne suke domin ba Wanda ke cewa dan uwansa ufan sanan KO saukar numfashin su ba mai ji sai yatsarta da ta koma jajawur dan azabar murzata da take tunda suka fito tsawon tafiyar minti arba'in Kenan dalilin gosulo , suna isowa makarantar ya shiga direct har cikin kofar baban office din malamin mai suna ustaz Mu'azu ya faka
Cikin nutsuwa ta dago kanta sai taji ya ce " ina zuwa
Fita yayi ya shiga office din bai wani jima ba sai gashi ya fito da wata malama a bayansa ta karaso wajen Yar Mahaukaciya ta bude motar ta fito
Tana fitowa ta tsuguna ta gaisar da ita , ita kuwa sai washe hakora take ta kamata ta mike sanan ta ce " muje madame
Sai da ta sada Yar Mahaukaciya da ajinta sanan ta dawo wajen Mubasshir AA
Tana zuwa ta ce " an gwada mata kuma insha Allah za'a kiyaye , aman fa dalilin bazata zaman jiran malaman mu maza ba zatana sauka a lokaci daban daban dan haka dole mu dauki nimber wayar ka idan ta tashi da wuri muyi kira kazo ko ka turo a mayar da ita gida
Mubasshir ya ce" wanan duka ba damuwa idan dai har za'a kiyaye wanan , sanan komai akeda bukata ni za'a kira ba ita ba so ya mika mata takarda ya ce ganumberna personnel koda yaushe kika kira zan daga
Malamar mai suna Husnah ta karba tana godiya ya juya ya shige motarsa yana hamdallah a cikin zuciyarsa
Tafiya yake wayarsa ta fara ringin sai da tayi har sau uku sanan ya mika hanu ya dauko dan ganin KO waye ke kiransa da safe haka
Number Hajiya Marhaba ya gani hakan ya sa ya nemi waje yayi parking ya daga tare da salama
Hajiya Marhaba dake haki ko tsayawa amsa salamarsa bata yi ba ta ce " Mubasshir ina gidanka ina jiranka yanzu
Mubasshir ya ce " am Hajiya Gidana kuma? Ni ai ina gidan Maman Mubasshir fa
Hajiya Marhaba ta ce " ohk mu hadu a can din
Kafin ya bata amsa har ta datse kiran a hankali ya furta ya Salam sanan ya tada motarsa ya juya kanta ya nufi gidan mahaifiyarsa
😘😘😘😘😘😘😘😘😘
*'YAR 👧🏻*
*MAHAUKACIYA👹*
*_Na SAJIDA_*
45
Kamar yanda suka zo haka suka koma tafiyar kurame suna isowa ta kama kofar zata bude ta fita
Mubasshir da ya kasa hana kansa magana ya ce ji mana
Yar Mahaukaciya ta jiyo tana kalon kasa dan koda wasa bata iya kalonsa cikin ido
Mubasshir ya mika hanunsa ya karbi nikaf din dake hanunta ya daga yaga eh lale nikaf din ne
Ya ce " mai yasa ke bakya saka shi ne?
Yar Mahaukaciya ta dago ta kale shi , idan bata manta ba wataran ta taba riskar hirar su da Hajiya Hawau yana fada mata cewar ya tsani yan matan nan masu saka nikaf din munafurci dan abinda suke aikatawa gonda gagarumar karuwa da su yawancinsu aman yau kuma ya tambayeta mai yasa ita bata saka ba?
Tambayarki nake , Muryar Mubasshir ta dawo da ita daga duniyar da ta fada ta ce " Am daman ance na matan aure ne , yan mata sai idan mutun yana da ra'ayi ne zai saka idan kuwa baka ra'ayi to karka saka
Mubasshir yana sauraronta sam bai so maganar ta tsaya daga nan ba ya lumshe ido ya ce " aman ai zawarawa ma na iya sakawa KO?
Yar Mahaukaciya ta dago idonta suka yi ido hudu ta kawar da kanta ta ce " eh
Ya Mika mata ya ce " toh ki ringa rakawa duk inda zaki je tunda zawarawa ma na iya sakawa kinga kina layi KO?
Yar Mahaukaciya ta karba ta daura a fuskarta idanuwanta kadai ake gani ba'a ganin sauran fuskarta , ta dago ta sauke idanuwanta cikin nasa ,
Wani irin yar yaji a jikinsa harma yayi nadamar Sakata daura nikaf din , dan da ta daura kawai sai kyan idanuwanta suka fito ba kadan ba har wani walkiya suke balatana na tsakiyar nan mai kama da na mage , Saurin kawar da kansa yayi yana fadin kina iya tafiya
Yar Mahaukaciya ta kama ta bude kafin ta fita a hankali ta ce " Allah ya saka da mafificin alkhairi sanan ta fice tana tafiyarta da ta saba
Ba shi ya bar wajen ba sai da yaga eh lale ta shiga falon sanan ya ja yayi gaba yana mai jin haushin kansa irin yanda yake mantawa da ayukansa masu mahinmanci wajen tinanin gyara rayiwar yarinyar nan , dan ba dan ya daukarwa kansa alkawarin kulawa da ita da bazai tsaya batawa kansa lokaci a kanta ba , aman insha Allah zai nema mata miji Wanda ya san zai kula da ita domin Allah a daura musu aure KO yayi abinda zai fishe shi ( toh fa )
Tana shiga Hajiya Fadimatu na amsa waya ta zauna sai da ta gama ta gaishe ta
Cikin murmushi take amsawa ta ce" ah Yar Fadimatu ya akayi kika saka nikaf din?
Yar Mahaukaciya tana cirewa ta ce" Mama ai yaya ne yace na saka kar na kuma fita babu shi
Hajiya Fadimatu a ranta ta ce toh kaji shi da ya tsani saka nikaf yau kuma shine da kansa yake cewa a saka ? Lale yau kam ta gama yarda da abinda take zargi aman zata gwada shi tayi murmushi ta ce " toh ki ke kiyi wanka sai ki sauko mu ci abinci
Yar Mahaukaciya ta amsa tana mikewa ta nufi dakinta
Konci tashi har Hutun su Yar Mahaukaciya ya kare sun koma makaranta inda wanan karin da wani irin gata take tafiya wanda wataran direba ya kaita wataran Maman Mubasshir kanta kawai sai ta shirya wai rakiya zata yi mata har cikin makarantar ba wanda bai Santa ba sanan yanzu idan bata son zuwa ta ci abinci har inda take ake kawo mata cikin mutuntawa
Yau ta tashi a lati dan kuwa mura ta hanata baci sai daidai asuba ta samu ta rintsa jikinta zafi rau da zazabi
Hajiya Fadimatu ta fito karfe bakwai da rabi ta zauna tana jiran saukowar Yar Mahaukaciya abin mamaki har karfe takwas tayi bata sauko ba , a fili ta ce" lafiyar Yata kuwa? KO ta tafi ne? No bazata tafi bata sanar da ni ba dan ba dabi'arta bace
Hakan yasa ta mike ta nufi dakin Yar Mahaukaciya tana fatan Allah yasa lafiyarta lau
Tana shiga ta hangota konce lulube cikin bargo tana karkarwa , Da sauri ta karasa ta dan yaye mata bargon tana fadin Yar Fadimatu lafiya?
Yar Mahaukaciya dake barin sanyi har hakoranta haduwa suke da kyar ta iya furta mama can cikin kasan makoshinta sanan ta maida idanuwanta ta rufe
Ai da gudu Hajiya Fadimatu ta juya tana rarumar wayarta ta danawa doctern su kira ta fada masa yarinyarta ba lafiya kuma sosai ne jikinta yayi zafi sosai
Doctern ya ce " To Hajiya Zan karaso nan da Awa biyu dan makocina ya rasu muna wajen jana'iza
Hajiya Fadimatu ta ce " Eyah Allah ya jikansa ta datse Kiran ta shiga neman lambar Mubasshir dan kuwa bazata iya zubawa yarta ido a haka ba har tsawon wani lokacin
Lambarsa ta wajen aiki take kira dan tasan a wanan lokacin yana office aman secreteria dinsa ta