Showing 54001 words to 57000 words out of 77913 words
ya kuma dagowa ya kara kalon ta a ransa ya ce " Ai fa ni ba dadin zamanta nake so ba, dan kuwa na sani Sahla ta FITA dan ta FITA kama kai,duk da haka ga yanda na same ta ballatana Wace ta waye a harkar? Ni kawai hutu na aura sai kuma ina dan tausaya mata,
Hajiya Hawau ta ce" ka bani amsa, shin zaka iya kular min da yarinyata? "
Mubasshir ya danyi murmushi ya ce " ai KO da ban sanki ba girman ki ya isa na girmama abinda kika hango ballatana na yarda da zabin ki, insha Allah zan yi kokarin adalci a tsakaninsu
Hajiya Hawau ta amsa sa cikin farin cikin girmamata da darajata da Dan Aljannah yayi
Bayan ta salamce salar walahar ta ta juyo a nitse ta karasa inda Gajiya Fadimatu ke zaune da abinci a cikin assiete tana jiran ta gama sallar, tsugunnawa tayi har kassa fuskarta da dan murmushi ta ce" Mamana ina kwana, an tashi lafiya? "
Wani sanyin dadi ne ya ratsa zuciyar Hajiya Fadimatu ta ajiye plat din abincin ta kamo Yar Mahaukaciya ta zaunar da ita saman bed din tana kalon ta, can ta ce" jiya kinyi baci baki ci abinci ba Yar Fadimatu,"
Yar Mahaukaciya tayi murmushi ta ce" kawai sai da na farka na ganni ina baci kuma sai tsoro ya Hanna ni FITA na debo abinci, "
Hajiya Fadimatu ta ce" Tsoron mai?"
Yar Mahaukaciya tayi gagawar dukar da kanta ta ce " ba komai mama"
Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta dago habar Yar Mahaukaciya ta ce" idan na ga auren nan cutuwa ne a gare ki believe me ba inda zai da izinin Allah, sanan a yanzu haka idan kika kafe kan bakya so zai sawake miki duk da shi din yana so"
Yar Mahaukaciya ta zaro idannuwanta bata san sanda ta ce " Yana so?
Hajiya Fadimatu ta ce " Yes, yana so"
Yar Mahaukaciya ta dan sadda kanta da matsanaiciyar kunya tana tir da wanan baki nata, a zuciyarta kuwa tasan wacece ita harda AA Mubasshir zai so auren ta? (Haka)
Mikewa Hajiya Fadimatu tayi ta bude werdrob din Yar Mahaukaciya ta ciro wata doguwar riga ta atamfa, rigar taji dinki daga sama ta matse sai ta bude daga kasa, da dan tsaga tsaga a sama daidai kirjin rigar sannan zub din bai hau har sama ba, hanun rigar daya dogo ne daya gajere , jar atamfa ce mai ratsin baki baki kalar fararen fata 😅🤷🏻♀,
Ta mikowa Yar Mahaukaciya dake zaune sannan ta ciro mata dan kwalin rigar ta miko mata ta ce" tashi Yar Fadimatu ki shirya mu tafi amsar kaya na nadiya nan makota,"
Yar Mahaukaciya ta dago atamfar, dinki ya hadu iya haduwa sai dai kunyar dinki ta saka ta kasa sakawa, sai dai a yanzu bazata taba iya musantawa Hajiya Fadimatu ba , Hakan ya sa ta dauka ta nufi gaban mirror dan ta dan gyara fuskar ta dan Hajiya bata son ta FITA bata saka kwali ba ,
Zama tayi ta yi dan adonta iya lips dinta da idanuwanta ta Mike ta dauki bras dinta ta saka ta saka pant dinta sannan ta dauko rigar har wani kara karan zub din take dan KO tafiya kake zub din na motsi suna Jan hankalin mutun, , cikin nutsuwa ta saka ta ja zub din sannan ta dauko dan abin hannunta baki siriri ta saka , ta dauko dan kwalinta zata daura Hajiya Fadimatu ta shigo tana fadin " Yar Fadimatu ki fito sai su dauko miki wa'inan bol din , hajiya Karima ce ta ce a zo mata da su saboda wajen mijin Nadiya gidan sarauta ne ita kuwa bata tanadi wanan ba , dan haka bara nayi gaba sai ki biyo ni da sauran
Yar Mahaukaciya ta ce " To mamana , ki bata kar ta manta"
Hajiya Fadimatu ta ajiye ta karbi bakin ribom din ta tatara gashin kan Yar Mahaukaciya ta hade waje guda ta saka mata ribom din sai gaba daya ya zubo ya rufe mata wajen da rigar bata rufe ba daga baya sanan ta dauko bololin ta nufi hanyar gidan Hajiya Karima makociyar su,
Bayan ta gama shiryawa ta dauko tirarukan dake saman table din dakin ta yiwa jikinta barin sa ta bude wajen takalman ta ta dauko wani plat mai igiya baki ta daura a kafafuwanta sannan ta fito cikin nutsuwa da mayafinta baki mai shara shara irin mai dan duwatsun nan tamkar sange ,
Cikin nutsuwa ta sauko direct ta nufi kicin tana kwalawa ma'aikatan gidan kira dan ta ga an fitar da kayan ita kawai suke jira
Da ido ya bita sauran kadan ya kware , yana waya da Sahla tana ta magiyar ya amsata yayi mata shiru , cikin sarkewar murya ya ce" Sahla ina zuwa ,"
Kafin ta bashi amsa ya katse Kiran ta kali mahaifiyarta dake zaune tana sauraron labarin nasu ta ce " Mama kinji fa ya kashe, ni gaskiya sai na kara kwana biyu na kara hutawa dan wly so yake ya kashe ni sam bai san gajiya ba a rayuwarsa "
Hajiya Marhaba ta ce " ai shiyasa na amso miki magungunan nan sai kiyi ta anfani da su yanzu haka Wanda kika matsan nan kinga dubu hamsin na siyo shi dan karfi ne da shi, sai dai yayi ya gama har ya gaji ba dai ke ki gaji da shi ba "
Sahla ta dan yatsina fuska dan tunda ta matsa maganin nan cikinta ke yi mata wani irin ciwo kokari ne dai kawai take dan Mahaifiyarta ta fada mata anfannin maganin yawa ne da shi , ita fa a gaskiya a yanzu tsoron mazan ma take tun karfinta cause Mubasshir tamkar machine yake shi dai burinsa ya ji sa a birnin nan Wanda jirgin sa mai wuyar sauka ne (😲). " tayi kwafa kasa kasa ta ce" Ashe dai ana gajiya da ita"
Fitowa ta kuma yi da wata Babar leda a hanunta tana kokarin gyara rikonta kwalabe ne a ciki na shan ruwa masu nauyin tsiya ga tsada ga kyau , sam bata lura da mutun a falon ba tana juyowa ta gamshi zaune yana kalonta , gabanta yayi wani mugun faduwa bata san lokacin da ta saki ledar ta fada mata a kafa ba ,
Ido suka rintse a tare dan kuwa yanda ta ji azabar faduwar wanan kofofin haka ya ji a jikin sa , , wani ihu ta saki na azaba da firgici domin ta firgita kwarai da ganin ba zatan da tayi masa a falo ga kuma faduwar wanan abubuwa masu masifar nauyi murafen su masu dan kaifi har daya ya yanke ta, wani wahalalan kuka ta saki gaba daya jikinta na rawa ..
Mikewa yayi cikin zafin nama ya isa wajen ta , yayi gagawar janye ledar ya cire Wanda ya dan yankun mata , yanda jikinta ke rawa haka NASA ke yi, cikin dauriya ya Mika hanu ya daukota cimak ya nufi Babar kujerar dake tsakar falon ya shinfida ta , sai wani kakauda kai yake
Wayarsa ya janyo yayi Kiran Umairah docter matar général kadre makociyarsu dan yanda take karkarwa sai yake jin tamkar wani abin ne ya shige mata kafar,
Minti sha biyar tsakani sai gata ta shigo ta karaso tana fadin "Oh yar gidan momynta ce ba lafiya? Oya cuta baki yi mana adalci ba "
Mubasshir ya dan Mike yana fada mata ga abinda ya faru,
Umairah tayi murmushi ta kama kafar ta Yar Mahaukaciya tana dubawa ba karaya ba gocewa , jin ciwon nan dai ne , hakan ya sa ta dauko compress ta goge mata da alcool ta rubuta mata amoxi ta mikawa AA sanan ta juya ta tafi ,
Mikewa tayi a hankali tana dan rintse idanuwanta ta mika hannu zata kuma daukar ledar ta je ta kaiwa Hajiya Fadimatu ,
Mubasshir ya zubawa kirjinta ido ta tsagogin dinkin nan, gabansa ya fadi yayi gagawar hadiyar wani yawu mai wuya , ya kuma zubawa dogon wuyanta da bayanta ido ba shiri ya kawar da kansa tun kafin ya bada kansa, cikin muryar tasa ta yana hanu ya ce" ina zaki je?"
Gaban Yar mahaukaciya ya Fadi ta dago tana kalonsa cikin gargadar murya ta ce" am daman mamana ce ta ce na kai mata wa'inan wajen amsan kayan Nadiya"
Ya juyo yayi mata kalon kinyi kadan ki fita sanan ya mike a nutse ya nufo ta,
Takunsa take ji sai ji tayi ya kure mata waje, a hankali ya Mika hanunsa daya ya dan rankwafa daidai wuyanta har lumfashin sa na sauka a saman wuyan ta ya kama zub dinta ya ....... ......................... ................ ........(😅😅 oh my Hawee kinyi shiru ki ji yayi mai da zub din KO? Har kin diro, to alhana bazan fada ba 😲🤒🤒🤒🤒💃💃💃💃)
🇳🇪BELLES écrivaines Nigériennes
👹 YAR MAHAUKACIYA👹 na SAJIDA
59
Lumfashinsa na sauka a saman wuyan ta, da gangan ya kara jawota kadan hakan ya Sakata jin bugawar zuciyarsa da Sauri da Sauri, Zip din ya kama da niyar ya ja shi ya rufe sauran wajen da bai rufe bayanta ba , hakan ya baiwa hancinsa damar sauke numfashinsa a kunnanta ,
Jin wanan bakon al'amarin ya saka jikin Yar Mahaukaciya mutuwa, gaba daya jikinta ya saka ta furta " *Wayo Allahna* " tayi luuuu zata fadi
Cikin mutuwar jikin shima ya tarota suka fada saman Babar kujerar, da Sauri ya mike yana kakabe jikinsa ya dan gyara tsayuwarsa ya saita muryarsa ya ce " Kai Bariki, idan mutun ya saba da abu hakane, na tabo miki wajen dake miki kaikayi KO? Yayi kwafa ya dan duko cikin rada rada ya ce " i'm sorry da na katse miki jin dadin ki dan ba kyau bin maza a waje may be ni kadai zan iya gamsar da ke , aman da alama sai nayi da gaske dan kin fiya zalama" yana gama fadar haka ya juya yana taka mattatakalar dakin ya nufi dakin mahaifiyarsa
Da kalo ta bi bayan sa har ya shige, nanauyar ajiyar zuciya ta sauke , tabas da da ne bazata damu da maganganunsa ba , a lokacin da idan ya yi su ma bata san inda suka dosa ba , sanan da a shekaran jiya ne ma ba zasu wani mugun damun ta ba cos ba'a fada mata cewar miji yake a gareta ba , aman a yau sai ta ji ba dadi, gaba daya sai ta ji ta muzanta, shin ina laifinta dan ta wayi gari ta tsinci kanta a bola? Menene laifinta dan ta rayu a cikin bola? Ta rintse ido a fili ta furta " *Shin mijina yana yi min kalon fasika ne?* ,
Lami dake tsugune tana maganna ta ce" na'am hajiya?
Yar Mahaukaciya tayi gagawar kallon ta , sannan ta ce" Au Lami kin fito?, kinga bara na saka hijab dina mu tafi mu kaiwa mamana nassan tana ta jira"
Lami ta ce" Ai hajiya Elhaj ya ce a fada miki karki fita, mu mu tafi mu kai kayan"
Yar Mahaukaciya ta ji zancen wani iri ta dago ta ce" Elhajin ne ya fadi haka?"
Lami ta amsata cikin biyaya
Yar Mahaukaciya ta ce " ohk tohm ki dauka ku kai mata , aman kar ku ce shi ya hana ni zuwa kunji? "
Lami ta ce" to Hajiyata a huta lafiya" suka dauki kayan suka tafi abinsu
Birgima take tana ihun cikinta , fitowa tayi daga bayi ta nufota da Sauri tana fadin Sahla ke kam akoy ragwonci , matsin maganin matan ne kike yiwa wanan ihun? To da a gabansa ne sai ya san abinda kika matsa KO? "
Sahla dake rusar kuka ta cusa hannunta kasanta ta shafo lemar da take ji na binta ta dagowa Hajiya Marhaba dan kuwa bakinta ya kasa magana bale har ta furta kalmar jinnin dake binta
Idannuwa Hajiya Marhaba ta zaro sannan ta juya da gudu tana ihun a zo a taimake ta dan ta kai Sahla Asibiti. ,
Bayan kamar awa uku likitici biyu maza suka fito da nurses sun hada gumi sosai , Hajiya Marhaba ta mike tana karkarwa ta nufe su ta ce" Ya jikin y'a ta docter?
Docter Aliyu yayi gagawar fadin ki biyo ni office dina , yayi gaba inda docter Usman ya bishi da kalo yana jin haushin wanan halaya na docter Aliyu Wanda a da bai san shi da su ba ,
Suna shiga ya ja kujera ya zauna inda Hajiya Marhaba ma ta nemi waje ta zauna tana sauraron sa cikin bugawar zuciya ,
Docter Aliyu ya ce" wa ya zubar mata? "
Hajiya Marhaba ta dago tana kalonsa da alamar tambaya ta ce" ban gane inda ka dosa bâ?"
Docter Aliyu yayi murmushin rainin hankali ya ce" cikin jikinta wa ya zubar mata?"
Hajiya Marhaba ta zabura tana dafe kirjinta ta ce " ci.....ciki????? Inalilahi wa'ina ilaihi raj'une, ciki ne da Sahla ? Kuma ya zube?"
Gaba daya cikin firgici take da tashin hankali dan KO an fada mata ba zata yarda cewar Sahla har ta dauko ciki ba , abinda suke nema tamkar ransu gashi sun samu kuma sun barar da shi garin a kara mata kokarin juriyar yawan sha'awar sa , wannan ai shine kaga samu ka ga rashi, ta kuma rushewa da kuka
Docter Aliyu yayi zuru yana son sanin kukan na mainene , can ya nisa ya ce " tana da aure ne?"
Hajiya Marhaba cikin share Hawaye ta ce" da aurenta mana"
Docter Aliyu cikin jin haushin Kenan ba zai samu kudin da ya hango ba zai samu ba ya ce" Toh dole sai mijinta ya zo wajen nan dan kuwa cikin mun gano cewar matsa wani abin ne akayi dan a zubar da shi, dan haka sai ya zo KO an kawo mana takardun da likita ya saka ayi hakan saboda lafiyarta"
Hajiya Marhaba ta zaro ido ta ce" uban mai mijinta zai yi a nan? Tap KO daya ai KO mai za'ayi ayi shi iya nan docter"
Docter Aliyu ya zuba mata ido shi daman da ganinta ya san ba gaskiya a al'amuran ta shi ya sa ya gano ci a tare da ita hakan ya sa ya gabatar mata da uzurin sa inda Hajiya Marhaba cikin karkarwar jiki ta biya masa muradinsa ta baro offishin sa cike da jin haushin kanta na asarorin da suka sameta a dan kankanin lokutan nan ( wannan Kenan)
Cikin bacinta take jiyo waya na ringin ta Mika hanu ta kashe kafin ta maida hannunta ta kuma kwasan kuka hakan ya sa ta Mike tana murza idannuwanta ta nufi kofa dan bude kofar shigowar,
Tana budewa idannuwanta suka sauka kan fuskar mutanen dake Dana cl din shigowa falon nasu , kirjinta ta dafe ta kurma ihu daidai da daukewar nunfashinta tayi baya yim ta fadi kass inda suka nufota cikin kidima da tashin hankali.................'''
Shin su wa Yar Mahaukaciya ta gani????????????????????????????????
🇳🇪Belles écrivaines du Niger
*'YAR 👧🏻*
*MAHAUKACIYA👹*
*Na*
*Sajida*
70
Adu'a suke tun karfin su, aman jikinsa sai kara daukan zafi yake,
Hajiya Fadimatu ta daga hannunsa ta saki hannun wani irin nauyi, tayi saurin kawar da kanta ta rintse idannuwanta gabanta na mugun faduwa
Yar mahaukaciya ta ce" mama Lafiya ? Ba alamun sauki ?
Hajiya Fadimatu ta tataro dukan KOkarinta ta ce" ba komai y'ar Fadimatu,
Yar Mahaukaciya ta ce" KO na Kira Yaya Idriss ne ?
Hajiya Rafi'at ta Gyada mata kai, hakan yasa ta ajiye kansa à hankali ta nufi wayar falon ta danawa ofice dinsa Kira domin ta san kawai yana ofice
Jin abinda ke faruwa ya saka shi barin Ofice dinsa ya kwaso yan kayan aikinsa ya nufi gidan su abokinsa domin ceto ransa
Yana zuwa ya tarar still sun dukufa sai adu'a suke masa zuwa lokacin Yar Mahaukaciya kam ta fara zubar da hawaye domin hannun sa baya KO karyuwa
Yana zuwa ya shiga tambayar abinda ya faru, inda hajiya Fadimatu ta fada masa komai na idan yayi irin haka harda na Karshe da yayi bai kai hakan ba
Idriss ya ce" Mama na karshen da yayi mai akai masa yaki yin nisa ?
saï à lokacin suka tuno jawabin mahaifin Fadimatul islam (Yar Mahaukaciya) kan idan hakan ta faru à tabatar da an saka shi à ruwan kankara sosai cikin ikon ALLAH zai kawo hankali
Nan ta kwashe ta fada masa yanda Elhaj Muhammad ya fada,
Idriss ya ce" to wankan za'a yi masa ai mama
Hajiya Fadimatu, Aunty Habiba, Hajiya Rafi'at da Islam gaba daya suka zuba masa ido suna kalon sa
Hajiya Fadimatu tayi karfin hali ta ce" wankan KO ? To ya zamu iya kai shi dakin ?
Idriss ya Mike gannin yanda duk suka wani tsure ya nufi kofa yayi Kiran securitiesn suka taho suka cicibi AA suka yi dakin Yar Mahaukaciya da shi inda ta Mike ta bi bayan su domin hada ruwan wankan
Baban bokici ta cika da kankara ta shiga bayin ta zagine tana sauyewa à cikin bahon wankan Daidai nan Hajiya Fadimatu ta shigo ta kama mata suka juye kankarar,
Suna gamawa su Idriss suka shigo da shi à talafe da dan gajeren Wando à jikinsa Yar Mahaukaciya tayi gagawar lafewa à bayan Hajiya Fadimatu , suka saka shi à cikin bahon ruwan da yayi mahaukacin sanyi
Suna saka shi securities suka juya suka fita inda su Hajiya Fadimatu ma suka yi niyar fitar dan barin Idriss da AA ya zuba masa ruwan à jikin sa
Idriss ya ce" Mama ku dakata ku matso mu yi masa tare
cikin sagewar gwuiwa suka juyo islam na biye da ita tamkar jela kanta à kasa suka shiga daban ruwan suna zuba masa har à cikin sumar kansa
Basu dau wani lokaci suna hakan ba ya ja wani dogon numfashi ya bude idanuwansa tamkar gauta dan ja à fuskar mahaifiyarsa domin ita kawai ya fara tozali
ido ya rintse yana Jin yanda kankarar nan ke ratsa masa jijiyoyin jikinsa, kokarin zama yake aman sulbin abin wankan ya