Showing 21001 words to 24000 words out of 77913 words
santsi da shekin baki ,ya dauki mayukan gashi ya shafa
Shi da kansa yake nanade kansa ya saka macaji ya daidaita shi yana jin haushin saurin taruwar gashin kansa kawai sai ya aske ya huta, kuma sai ya fito
Cikin nutsuwa yayi shirinsa ya gama ya dauko kayan , yana dagawa yaga manyan kaya ne gari da yar ciki da hula sun sha wani mahaukacin zubi a jikinsu hular kanta wani irin aiki ne aka yi mata sosai ta hadu , abinka da mai son manyan kaya , yayi murmushi a fili ya ce " Maman Mubasshir Kenan
Su Idriss na suna ta labari suna dariya su uku daidai suma sun sha manyan kayan su sai anuri suke abinka da ranar fito na fito
Mubasshir ya sauko cikin takun kasaita tamkar dan Sarki daidai da takalmin kafarsa na shadar nan ne haka agogonsa mai zubi ya sha hularsa , yana ganin su ya saki murmushi
Nura ya ce " waouh , waouh , waouh , wata miyar sai a makota , wai dan Allah kaine kuwa?
Mubasshir ya Mika musu hanu daya bayan daya suna gaisawa sanan cikin murmushi ya ce " angoncewa ce
Idriss ya sha kunu ya ce " kai kasan gaban manya fa kake
Mubasshir ya ce " meye manya? Yana wata yatsina
Ramadan ya ce " ya ilahi sirikinka ne fa
Mubasshir ya mike yana fadin " kunga mu yanzu mun zama masu iyali ku tashi mu nufi gidan iyayena na gaisar da kakata sai iyayen matata a al'adar chadi
Suka Mike suna murmushi , fitowarsu keda wuya wanan mawakiyar ta larabawa ta kwasa sai koda Mubasshir take , dago kansa da zai yi ya hango gimbiya Mubinah yar gidan sarkin Makah cikin shiga ta alfarma ta zuba zinari da wani mahaukacin lesh fari gata fara sai daukan ido take ,
Suna fitowa ta mike ta nufo Mubasshir Wanda sai da gabansa ya fadi a ransa ya ce " ya akayi mai martaba ya BArTA ta biyo su mai girma Barhan?
Tana isowa ta rungume shi irin gaisuwar larabawan nan sanan daidai kunan sa ta rada masa " na zo na raka mijina gidan amaryarsa da tayi min shigar wuri kafin na shigo
Mubasshir ya dan saketa ya lakaci habarta yayi murmushi sanan ya juya wajen iyayensa yayi Saurin tsugunawa yana gaisar da su
Hajiya ta taso ta kama hanunsa ta daidaita masa hularsa ta ce " Alhamdulilah yarona ya girma , Allah ya kade baki ( kunsan larabawa suna mugun gudun baki shi yasa daga sunyi magana sai kaji sun ce Masha Allah , 😁 )
Haka sukayi ta saka masa Albarka sanan suka juya inda wasu motoci kwaya hudu a jere farare tas sai sheki suke , yau yau aka fitar da su da ka gani ka san an cashi kudi a nan ,
Karar tafiyar doki naji na waiga wani ne ya taho da dokina biyu yana jaye da su da irin runfar nan ana jaye da su , sai karar kacaukacau suke sun mahaukacin sha ado na zinari sai kara suke
Mubasshir ya juya ya sauke idanuwansa saman Mubinah dan kuwa ya san wanan aikinta ne ya gala mata harara dan ta sani sarai ya tsani hawa doki KO a can su biyu suke hawa KO da ita KO da wani a gefen sa ,
Tayi murmushi cikin harshen larabci ta ce" kar a yada al'ada ka sani sarai da a can ka yarda kayi aurenka da sai ka zaga gari a saman doki dan haka ya sa na shirya wanan KO ba komai ka girmama al'adar mai martaba uba a wajenka
Da haushi haushi ya taka ya hau itama aka kama mata ta dare tamkar itace amaryar ,motocin nan suka saka su a tsakiya , mai girma Barhan ya karaso ya rufa masa alkyaba aka cire masa hular aka rufa masa ta alkyabar nan dan kuwa haka al'adarsu take
Cikin nutsuwa suka kama hanyar gidan su Sahla
Hajiya Hawau ta sha dinkinta na shada ta hade harda kafa daurin dan kwalinta sun malaya manyan tabarmi a tsakar gidansu da kawayenta tsofafi sai labari ake ana shan fura mai cukui sai kanshi take ga dadi abinka da tsohuwar da ta san darajar baki duk Wanda ya shigo Yar Mahaukaciya da kawarta Fati sai su zuba furar a cikin kwarya da ludayi su Mika masa , suma sun sha dinkinsu na shada duk da ba wata kwaliya suka yi ba dalilin ainkin da suke yi
Suna tsaka da shan dariyarsu suka jiyo karar ganga da kuma muryar mace tana ta ISO da larabci tana wakarta , ga Wanda ya iya ya san dan gata ake wakewa ga Wanda bai iya ba kuwa sai dai ya gyada kai dan dadin wakar
Fati ta kama hanun Yar Mahaukaciya ta ce" kawata ai angwaye ne
Yar mahaukaciya ta ce" mai ya kawo angwaye nan kuma a yanzu?
Fati ta ce " oho o mu dai mu shirya tarban su
Hajiya Hawau ta fado kincin din ta ce" Ramatutu ai ga Dan Aljannah nan ya ISO da tawagarsa kinga wa'incan kwaryoyin masu zane su za'a dauko a zuba musu furar , aman ai ke kinsan yanda ake dama ta dan Aljannah dan haka a dauko duka cukuii din da nonon a dame musu yi maza yar Aljannah
Yar Magaukaciya tayi murmushi Ganin irin yanda Hajiya ta rikice ta ce " Hajiya ai na dame ta tun dazu Idriss ya ce a aa zuwan su duk da nayi zaton ko wasa yake mun dai dame kuma yanda kike sonta , aman ciki zasu shigo kinga baza a bar Dan Aljannahn ki a wajeba KO?
Hajiya ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Allah yayi miki Albarka bara na sauke su a baban falon , ku kuwa ku jera furar ku kawo musu
Ta juya tana kara daure dunkunkumin dan kwalin da ta dunkuma
Yar Mahaukaciya haka kawai ta tsinci kanta da tsoron hada ido da Dan Aljannah a wanan ranar , mutun a ranar da ba ta aurensa ba ma yana mugun daukan ido bare a yau?
Fati ta ce" Malama Hajiya garin kidima har kofina take ambato 😁
Yar Mahaukaciya ta ce" Dole Hajiya ta rikice dan kuwa dan gatanta ne
Haka suka dauko kwaryoyin suka kara darwaye su , gasu kananuwa masu shegen kyau da ludayinsu masu kyan gaske suka jere a saman wani baban faranti na silba mai shekin gaske , sanan suka ringa zuba furar nan suna saka ludayin a ciki , sai da suka gama
Yar Mahaukaciya ta ce " plz my kawali ki dauko na Dan Aljannah dan Allah
Fati ta zaro ido ta ce " mai kike nufi da hakan? Yayanki ne fa kuma kin sani sarai kar na fita na zubar garin kalonsa
Yar Mahaukaciya ta san sarai zata aika hakan yasa ta dauko wani farantin dan madaidaici ta zuba furar a wata kwaryar mai murfi sanan ta dauko ludayi ta dora a gefe ta dauko mushoir ( hankici ) sabo fil fari kar ta dora shima a gefe ta gyara komai
Fati dake kalonta ta ce" gaskiya al'adar Hajiyar gidan nan na mugun birgeni , koman ta daban ne sanan ta koyawa yar Jikanlen ta
Yar Mahaukaciya tayi dariya tana dora farantin Dan aljannah a gefen sauran furar ta ce " kama mu tafi malama kar suyi tafiyarsu
Suka kamo suka fito suna tafiya cikin nutsuwarsu suna fitowa kanshin ya daki hancinsu daga fatin Har Yar Mahaukaciya suka dago suka zubawa bakin dakin kalo
Idriss da dan Aljannah sun saka Hajiya a tsakiya ita kuwa sai washe hakora take daga gefe guda kuwa Mubinnah ce sai fifitu ake yi mata ta sha kyau har ta gaji, sai su Ramadan da Nurah a wata kujerar abin gwanin ban sha'awa
Fati ta juyo ta kali Yar Mahaukaciya Wace itama kamar ta fadi dan yanayin Mubasshir ya kidimata harda Idriss abin ya mugun haduwa kawai sai taji eh lale tana iya yin soyaya da shi dan kuwa ya mugun birgeta a yau
Fati kuwa ta kidime ta haukace ta ce" kawata kina ganin zinaria ce fa a jikinsu dan Allah ki duba ki ga irin yanda AA ya zama uwa Kwaï dan daukan ido
Yar Mahaukaciya cikin rada ta ce " ki nutsu mu basu juya tun kafin na kife a nan
Su duka suka dan saki murmushi sanan sukayi salama
Hajiya Hawau ta dago kanta ta amsa haka sauran jama'ar wajen
Cikin nutsuwa su Yar Mahaukaciya suka ajiye wanan farantin a saman table din dake ajiye a tsakar dakin sanan suka shiga dauka suna mikawa mutanen dakin , har sai sun duka har kasa su Mika musu hakan ba karamin birge hajiya Hawau da kuma su idriss yayi ba
🙆🏿
[10/3, 13:50] Umar Dalha: 🇳🇪Belles écrivaines du Niger
*'YAR 👧🏻*
*MAHAUKACIYA👹*
*_Na SAJIDA_*
29
Fati ta dauko ta nufi Mubinnah tana isowa ta dan risina ta Mika mata da Sauri mai yi mata fifitar nan zata karba Mubasshir ya daka mata tsawa " cikin harshen larabci ya ce" idan anzo waje ana anfani da al'adar su ce sanan nan gidan sirikai na kuma iyayena ne dan haka kar a kawo min batanci kin gane ?
Da sauri ta risina tana fadin Allah ya huci ran Dan Gattahn Mai Martaba mafi soyuwa ga gimbiya Mubinnah
Mubinnah duk da bata ji dadin yanda ya sacewa kuyangarta gwuiwa aman bacin ransa yafi komai daga mata hankali hakan yasa ta mika hanu ta karbin wanan kwabin da bata san KO na menene ba ta dan gyara zamanta tana shawara da zuciyarta shin zata sha ne KO aa
Su dai KO a ransu , Yar Mahaukaciya ta dauko farantin Mubasshir har a lokacin bata gama yi masa kalo ba tayi niyar bazata yarda tayi masa kalon kurula ba ,
A nitse ta nufi wajen da tafi jin kanshin sa , itama Fati ta dauko na Idriss ta nufe shi
Yar Mahaukaciya na isawa ta tsuguna har Kasa ta dago hanayenta ta mikawa Mubasshir dan farantin mai kyan gaske
Mubasshir ya zuba mata ido dan gashinta daga gaba ya dan leko kadan sanan bakinta sai sheki yake na mai mai maski da ta dan goga ,
Maganar idriss ya dawo da shi inda yake fadin" Malan kaga Karka wahalarmin da mata mana ka karba plz karka rama a kanta
Firgogit yayi dan kuwa ya fada wata duniyar tinani ya Mika hanunsa wajen karba sai da hanayensu suka gogi juna , ita kuwa Allah Allah take ta bar wajen dan jikinta har karkarwa yake jin baranbaramar da Idriss ya afka mata a gaban Hajiya harda bakin kunya sai ma da taji Muryar Ramadan na fadin" au kace kaima taka a gidan take , gaskiya kunyi mana wayo , wanan wayo har ina ? Gaskiya muma a san yanda za'ayi da mu
Da Sauri Yar Mahaukaciya ta janye hanunta ta Mike da gudu tayi dakinta tana haki
Mubasshir da Idriss gaba dayansu da ido suka bita , Mubasshir yayi dan daman bai rike hanunta ba , ji irin yanda take gudu ana kalonta ( inada tambaya , ina ruwanka hon)
Shi kuwa Idriss wata irin faduwar gaba ce ta ziyarce shi ta haka kawai a ransa ya ce " wai a nan a cikin zulumbuwar riga take lale akoy aiki a gabana ( to kaji 😏 )
Hajiya ta katse dan shirun da ya gilma ta hanyar fadin " tayi maka kyau idrissu , nace tayi maka kyau ka firgita min ya
Yayi murmushi ya ce " haba kakus ya zamu zo ki hada mû da fura ?
Ta ce " to dan nema ita ce da ni ehe 😏
Mubasshir ya ce " kyale shi hajiyata ni kadai na san darajar wanan dan haka kowama kar ya sha idan yana so
Haka sukayi ta barkoncinsu har dai Sahla ta gaji da Kiran mamanta tana fadan sun shiga wajen tsohuwar nan sun makale kar ayi mata abinda ba shi ba
Sahla ta ce " mom kiyi Kiran Yaya Idriss plz
Hakan kuwa akayi ta dana kiransa daidai zasu shigo falon nata ,
Salamarsu ta saka ta katse kiran jama'ar dakin na amsawa
Marokiyar ta rangada guda ta kwashi kirari da kuma isowar angon auta wato Sahla
Cikin nutsuwa suka tsuguna gaba dayansu kasa suka shiga gaisar da Su Hajiya Marhaba da kawayenta
Hajiya Marhaba murna kamar mai ,
Suna tsaka da gaisawa wayarta ta fara ringin
Ta dauka sai taga sunan bokanta ne inda ta rubuta hajiya bokatu ,
Tayi murmushi ta Mike ta dan matsa kadan ta daga
Daga dayan bangaran ya ce " na gama aikinki na aikawa mijinki yanzu yanzu zai aikata abinda na saka shi tunda kince kina so a cikin jama'a yanda kowa zai ganta a rana yanda ba Wanda zai so ta rabe shi KO?
Hajiya Sahla ta ce " kwarai kuwa boka yanzu ne daidai dan kuwa gaba dayan mutanen da nake so su ganta a tozarce suna wajen nan so kawai ayi aiki na cika
Boka ya ce " karfa ki manta kudin ki mai yawa ne
Ta ce " kar ka manta aikinka mai kyau ne idan har yayi kyau din ai kuwa abinda zaka samu har sai ya fi wanan
Ya bushe da wata mahaukaciyar dariya ya e " to bunsura sai na jiki , ya datse Kiran
To fa , kaka kara kaka , shin waye za'a tozarta a cikin mutane? Waye za'a wulakanta har ma kowa ya gujeta? 🤷🏿♀🤷🏿♀🤷🏿♀🤷🏿♀🤷🏿♀🤷🏿♀ taku har kulun yar mutan Niger 😘😘😘😘
🇳🇪Belles écrivaines du Niger
*'YAR 👧🏻*
*MAHAUKACIYA👹*
*_Na SAJIDA_*
30
*Jiki Alhamdulilah sisters na gode da adu'ar ku gareni love u*
Cikin takunta tamkar ba ita ce ta gama wayar ba ta juyo ta zauna , tana zama idanuwanta suka sauka kan Mubinnah Wace ita har ga Allah da farko bata ganta ba , gabanta taji ya fadi abinka da mai sakin magana idan ta raya mata ta kali Mubasshir wanda ya kagauta su tashi su bar dakin irin yanda matan nan kowace ta zuba musu ido ga uban surutu an cika su da shi ga wasu hotuna uwa Wanda aka gayace su gidan TV shi kam duk a takure yake
Hajiya Marhaba ta ce" Mubasshir wanan fa? Ban Santa ba
Mubasshir ya kara sada kansa kasa dan kuwa KO bai dago ba ya san da Wace ake magana
Idriss ya kaleta ya ce" Mom Wanan fa itace Mubinnah daya daga cikin yayan sarki
Hajiya Marhabah ta ce" wani sarkin?
Idriss ya ce" na Makkah mana mom
Hajiya Marhaba ta washe hakora ta shiga yiwa Mubinnah barka da zuwa jama'ar dakin ma haka , sanan kasa kasa sai surutu suke suna tambayar Kenan harda iyalan sarkin sun zo? Gaskiya Hajiya Marhaba ita tayi dace ,
Wani irin ihu suka jiyo , gaba dayansu suka yi tsit , suka kuma jiyo wani ihun da Sauri suka Mike Idriss ya ce " a nan ne
Mubasshirr ya kama hanyar fita shi da Idriss inda matan suka yi cirko cirko suna raraba ido dan kuwa kowanen su tsoron FITA yake ayi ba shi
Suna fitowa suke jin ihun daga wajen bangaren Hajiya Hawau ne Harda Alamar koke koke
Idriss ya sha gaban Mubasshir ya ce cikin haki" Malan dakata , mu fara Kiran yan sanda kafin mu shiga cikin gidan nan wa ya san Abinda ke faruwa a ciki, idan fa yan boko haram ne?
Mubasshir ya gala masa harara ya ture hanunsa ya ce" KO yan a rayu haram ne Allah ya jikana ya juya ya nufi cikin gidan
Da shigarsa abin mamaki ya tarar Wanda ya kasa gaskatawa idanuwansa abinda suke gani , haka kunuwansa suka kasa yarje masa abinda suke jiyowa, nan da nan wata nadama da dana sani suka darsu a zuciyarsa domin wanan ba halin datako bane, sam wanan abin datijon kirki ba zai aikata shi ba
Cikin sauri ya FITA ya saka akayi gida da Mubinnah domin idan ta ga wanan abin shi aka tonawa asiri ba kowa ba ,
Cikin mutuwar jiki ya juyo ya dawo inda wajen ya zamana tamkar ana kida dan kuwa har dan gewaye su aka yi ana kalo , ba kowa bane face *Elhaj Ilyass* sai Jan kafar *Yar Mahaukaciya* yake yana mugayen kalamai a kanta kamar haka
*Ashe Hajiya Mahaukaciya ce kika tare min a gida? Ashe kortuwa ce yarinyar nan ? Idan ka ganta luplup tamkar mutunuyar arziki ashe ita kuwa munafuka ce?*
Hajiya hawau cikin tashin hankali da kuka tana Jan Yar Mahaukaciya , Elhaj Ilyas na jan ta ta ce" Haba , haba Ilyasu dan girman Allah ka cika min yarinya ka cikata mu bar maka gidan ka domin wanan yarinyar ni shaida ce kan mutuniyar kirki ce , KO wa ya fada maka abinda ya fada maka karya ne domin wanan yarinyar marainiya ce sanan ni ni na daukota lokacin da danta ya rasu harma akayi masa sitira a nan , Haba Ilyasu wanan wulakanci har ina, ya kake so nayi da raina ne?
Elhaj Ilyass ya ce" Hajiya wly kinji na rantse ba inda zaki sanan yarinyar nan a yau yau din nan zata bar min gidana domin ni ba mazinaci bane sanan ba zan lamunci ta bata min suna ba da sunan iyalina , ke kuwa ni kika Haïfa ba ita ba dan haka ita kadai zata bar min gidana
Hajiya Hawau ta juya wajen kawayenta tsofafin dake tsaye suna al'ajabin wanan lamarin da hanu daya ta fara rokon a taimaketa a tafin mata da Yar Mahaukaciya kafin danta ya gane yayi kuskure ta maidota
Aman ina kowa sai ya silale domin da ace ma jinin hajiyar ce aman