Showing 51001 words to 54000 words out of 77913 words
Abdallah ne
Yar Mahaukaciya ta sine kai ta mike ba tare da ta amsawa Hajiya Fadimatu ba dan wani irin nauyinta da take ji, ta nufi kofa
Tana FITA Hajiya Fadimatu ta sauke ajiyar zuciya a fili ta ce" astaghfrullah ya Allah ka yafe min wanan abin da nayi , Allah ka san abinda ke zuciyata Allah ka shige min gaba, sanan ta kama hanyar dakinta
Tana shiga dakinta ta tarar da Mubasshir yana zaune saman darduma yana Jan carbi , a nitse ta nufi windown dakin ta bude madubin tana lekawa
Mubasshir dake zaune yana hailala yana neman sauki wajen Ubangijin sa yayi fatiya ya juyo yana kalon Mahaifiyarsa ya ce "Maman Mubasshir ina yini? "
Hajiya Fadimatu ta juyo da murmushinta ta ce " Lafiya lau Dan Fadimatu, kaga Mamarka da tsegumi KO? Ina kalon yata ne "
Mubasshir ya ce "Yarki?"
Hajiya Fadimatu ta ce" yes zance ake kaga yanda ta ja gefe tamkar Wanda take tsoron saurayin"
Mubasshir ya zaro ido bai san sanda ya ce" What? Zance ? Kuma ita da wa?
Hajiya Fadimatu tayi masa kalon lafiyarka? Domin tambayoyin nasa a jere sanan ya mike lokaci guda har mazari jikinsa yake ,
Da Sauri ya juya ya fada bayi yana tari ya kuna pampo ya sha ruwa da kyar tarin ya sake shi ya juyo ya fito, yana fitowa ya tarar da Hajiya Fadimatu tsaye hankalinta tashe ta ce" Son jikin ne?"
AA ya girgiza kansa da yake Sara masa ya nufi bed ya konta yana rinrintse ido
Hajiya Fadimatu ta bi bayansa ta dafa shi ta ce" KO mu tafi asibitin ne? "
Mubasshir ya girgiza kai sanan da kyar ya ce" maman Mubasshir ba komai karki damu"
Zata yi magana taji ana konkwasa dakin ta taso ta bude a tinaninta Yar Mahaukaciya ce sai ta ga Hajiya Hawau
Murmushi ta saki tana fadin" Hajiya barka da warhaka , sanan ta bata guri ta shige cikin dakin
Hajiya Hawau ta kali Hajiya Fadimatu ta ce" Hajiya da wa yar tawa ke zance ? KO dai shine sirikin namu?
Hajiya Fadimatu ta ce" shine kina gani sai wani kawar da kai take," ta karashe tana kokarin kawar da fuskarta gefe dan kar ya dagota
Hajiya Hawau ta ce" ai kuwa idan ya shirya ai sai ya fito kawai ayi da shi"
Mubasshir dake sauraron zancen su a ransa ya ce" tazo ganina ne KO tazo ta karasa ni, ? A fili kuwa da kyar ya samu ya tashi ya juyo yana kalon su ya ce" Barka da zuwa Hajaju"
Hajiya Hawau ta karasa tayi tamkar yanzu ta Ganshi ta ce" Dan Aljannah ya jikin?
Mubasshir ya ce" Jiki yayi sauki Alhamdulilah, daman ina son zuwa wajen ki sai gaki kin zo"
Hajiya Hawau ta gyara zama ta ce" toh bani na sha"
Ya dan furzar da iskar bakinsa cikin kawar da kai ya ce" *Abdul ya sameni kan zancen nazo na sameki ki fadan inda Rahma take yana son aurenta , plz ki taimaka ki fada masa na yarda da son da yake mata* "
Hajiya Hawau ta kali Hajiya Fadimatu itama ta kale ta irin kalon aikin banza din nan sanan ta ce" *Ai yata anyi mata miji sai dai kuyi hakuri* "
Irin kwaruwar ta dazu ya kuma yi wanan Karin yama kasa tashi balatana ya shiga bayin ya samu sasaucin kwaruwar da yayi ta hanyar shan ruwa,
Wasa wasa tari ya tirnike shi tun yana rike daidai zuciyarsa har ya saka yana kokarin faduwa,
Da gudu Hajiya Hawau tayi bayi ta dibo ruwa inda Hajiya Fadimatu ta zauna tana rike da shi suka bashi ruwan ya sha, suka kuma bashi ya sha yana ta ajiyar zuciya
Hajiya Fadimatu ta dora kansa saman cinyarta tana shafa bayansa a hankali ta kali Hajiya Hawau da ido tayi mata maganar da su kadai suka gane abinda suke nufi sanan cikin muryar nutsuwa da kontarwa mai sauraro hankali ta ce" *Ya zakayi kokarin boyewa Wanda ta dauki cikinka ta raine ka ta shayar da kai ta juri rigimarka ta ga girman ka damuwarka? Ya zakayi kokarin yin gardama da abinda na hango a kwayar idanuwanka? Shin ka manta alkawarin mu na bazaka boye min sirinka ba?* "
Mubasshir cikin Mutuwar jiki ya dago da kansa daga cinyar Hajiya Fadimatu gabansa na ci gaba da faduwa a ransa ya ce" Kardai Maman Mubasshir ta rigayi Mubasshir sanin abinda ke zuciyarsa? Kar dai Maman Mubasshir ta gane cewar Mubasshir ya kamu da son Yar Gidan Fadimatu? Son da yake kokarin zautar da shi? Kaunar da tayi masa shigar bazata?
Hajiya Fadimatu tayi murmushi ta kawar da kanta ta ce" *Idanuwanka sun nuna tsantsar tsoro da fargabar abinda na karanta a tare da kai* "
Ta Juyo ta kama kafadunsa ta ce " *YA KAKE KOKARIN KASHE KANKA KAN HALALIN KA , IYALINKA, MATARKA? SHE IS UR WIFE MUBASSHIR* "
wani irin dum dum dum maganar ke yiwa Mubasshir a kunansa , wasu tambayoyi ya juyo yayi min Wanda nima nace AO🤷🏻♀
Tambaya yake shin Maman Mubasshir ta kuwa san sunan wa ta kama tace matarsa? Shin ta gane KO wanene a gabanta? Idan ta gane yaushe aka aura masa ita? Yaya zai yi da Abdul amininsa? Yaya zaiyi da ita kanta Rahmar?????????????????????????????????muje zuwa 😲
🇳🇪Belles écrivaines du Niger
*'YAR 👧🏻*
*MAHAUKACIYA👹*
*_Na SAJIDA_*
56
adu'ar samun sasaucin kunci da tashin hankali
*ALLAHUMA, LA SAHLA ILLAMA JA'ALTAHU SAHLAN, WA'ANTA TAJ'ANUL HAZNA, IZA SHI'ITA SAHLA*
Hajiya Hawau ya tsurawa ido yaga itama shi take kalo, ya juyo ya kali mahaifiyarsa a fuskarta ya karanci sam ba wasa a cikin bayanin ta,
Wani lalatacen murmushi ya saka yana dan juya kai cikin muryar tausayi ya ce" Eyah maman Mubasshir ba fa ni nake nufi ba, ina nufin *ABDUL* yayan Sahla ne ke son Rahma fa, "
Hajiya Fadimatu ta ce" look son, Rahma matarka ce, taya zakana hada ta da wani kuma? "
Cikin wani yanayi ya juyo ya kale su ya ce" *ku yiwa Allah ku dena hada maganar nan cos ni kunuwana suna jiyo mini wani abin daban, Wanda kuma yake impossible, Rahma dake kofa tsaye tana zance da wani saurayin, gardi, Rahamar da aminina abokina yake matukar so, sai kuma kunuwana su rinka jiyo mini cewar matata ce? Ni ?* "
Hajiya Fadimatu ta mike cikin kakausar murya ta ce" *akoy wasa tsakanin uwa d'a da , sannan akoy zancen gaskiya, Ni Mahaifiyarka ni na samu alwalinka a matsayina na mahaifiyarka da kuma Hajiya Wace ta zamto sheda kuma ta bada amanarta muka yanke wanan hukuncin, ranar juma'a ya daura aurenka da shaidu a gidansa na nan, idan kana musu kayi Kiran sa, idan kuma baka yarda da hukuncina ba to ka watsa min kasa a ido* " ta karasa cikin yanayin bacin rai, dan a ganinta Mubasshir yama raina ta ne yana so yana basarwa
Mubasshir jikinsa yayi sanyi jin furucin mahaifiyarsa da yanayin bacin rai a tatare da ita duk dan shi, da Sauri ya karasa ya tsugunna kasa gabansa na faduwa ya kama kafafuwanta ya ce" Maman Mubasshir kiyi hakuri please, ba ina nufin ban yarda da maganarki bane, KO ban yarda da zabinki ba, no abin ne ya zo min a bazata, Dan Allah kiyi hakuri"
Hajiya Fadimatu ta sauke ajiyar zuciya ta kali Hajiya Hawau dake murmushin jin dadi, a nitse ta kamo shi ta dago shi suka koma bakin gadon , cikin nutsuwa ta ce" Dan Fadimatu, zaka yi min biyaya ka rike min yata tsakaninka da Allah?? "
A ransa ya ce tamkar yanda zan rike raina da mahinmanci , a fili kuwa yayi murmushi ya ce" Maman Mubasshir koda aljana ce kika aura min dole nayi biyaya ba zancen musu " ( ehem ) ya ce GABA da fadin " damuwata biyu ce Maman Mubasshir, Abokina da kuma ita yar taki"
Hajiya Hawau ta dafa kafadarsa ta ce" abokinka ba yanda ya iya domin matar mutun kabarinsa, sanan inada kwakwaran dalili na yin hakan, dan haka kayi fatan alkhairi kawai, "
Hajiya Fadimatu ta dora da " to aman mai yasa kace da y'a ta?"
Mubasshir ya dan kawar da kai yayi kokarin kauda kishinsa sanan ya ce" kinga hanzu ma fa da igiyar aurena tana zance Maman Mubasshir , kuma kina kalo kika barta "
Hajiya Fadimatu da murmushi ta ce " Gidan ku , ta je tayi zancen"
Hajiya Hawau ta ce" aa Hajiya baza'ayi haka ba , an soke zancen"
Mubasshir ya sauke ajiyar zuciya a nitse ya Mike ya nufi bayi ya kuna ruwa ya wanke fuskarsa ya dago kansa yana kalon miror, wani murmushi ya subuce masa a saman lebensa a hankali ya furta " *Matata ce* , ya lumshe ido yana kalon kasa , sanan ya kashe pampo ya fito a ransa yana fadin "wly idan bata shigo ba zan je na dawo da ita dan kuwa ba zai yiwu ba "
Yana fitowa ya tarar basa dakin, ya sauke ajiyar zuciya sai a lokacin ya samu ya nufi window ya bude yana ta hangawa, ajiyar zuciya ya sauke ganin basa nan, ya juyo a nitse ya tada Salah saman salaya dan ya kara godewa ubangijin sa da wanan kyautar da yayi masa ba tare da wayon sa KO tashin hankalin sa ba,
Tana shigowa ta tarar da su Hajiya Hawau zaune , direct jikin Hajiya Hawaun ta je ta lafe tana dora kanta a saman cinyarta
Hajiya Fadimatu ta ce" Yar Fadimatu bakon ya tafi?"
Yar Mahaukaciya ta dan sine kanta irin jin kunyar nan bata ce komai ba ,
Hajiya Hawau ta shafa kanta cikin nutsuwa ta ce" Yar Gidana muna son yin magana da ke" ,
Yar Mahaukaciya ta dago gabanta na faduwa , badan komai ba sai dan tsoron kar ace ta koma gidan su Abdul, don kuwa KO da anyiwa Sahla aure mahaifiyarta na nan shi ma Abdul din yanzu tsoronsa take .............
Hajiya Fadimatu ta gyara zama ta ce""""""""",,,,,,,,,,,,,"""""""""""
[truncated by WhatsApp]
🇳🇪Belles écrivaines du Niger
*'YAR 👧🏻*
*MAHAUKACIYA👹*
*_Na SAJIDA_*
57
Hajiya Fadimatu ta gyara zama tayi gyaran murya ta ce" Yar Fadimatu shin na isa na sakaki abu kiyi , KO na hana ki ki guji yinsa?"
Yar Magaukaciya ta yi gaggawar daga kanta jikinta na rawa dan haka kawai ta tsinci faduwar gaba a tatare da ita ,
Hajiya Fadimatu ta kawar da kanta domin sai yanzu wani nauyin tunkarar Rahma da zancen nan ya darsu a zuciyarta , ta kuma juyowa daidai Lokacin da Mubasshir ke saukowa ya canza kayan jikinsa sai zuba kanshi yake ya fesa tiraren Hajiya Fadimatu , ja yayi ya dakata yana kalon su , shi kansa a yanzu gabansa faduwa yake bai san dalili ba ( zaka sani )
Hajiya Hawau ta ci gaba da fadin " shin kin dauke mu a matsayin iyaye? Wa'inda suka isa da ke , wa'inda zasu iya yanke hukunci dan inganta rayuwar ki? Wa'inda zasu guji ganin kin halaka sai inda karfin su ya kare? Shin a yau idan muka zo miki da wani hukunci da muka yanke a kanki zaki yarda da shi? "
Zuwa wanan lokacin Yar Mahaukaciya ta gama jika da gumi, domin KO ba komai ta san wanan zancen mai matukar mahinmanci ne, tabas wanan zancen mai mahinmanci ne tana rokon Allah ya sa alkhairi ne, idanuwanta ta dago wa'inda suka kara girma na tashin hankalin da ta shiga ta sauke su a fuskokin su hajiya , wani irin kwarjinin su ya daki kwayar idanuwanta da Sauri ta sada kanta kasa cikin gargadar murya ta ce" Mamana, hajiyata, iyayena, kun yanke hukunci a kaina shine kuma kuke yi min shawara? Wacece ni? No a duniya banda mahaifiyata sai ku gareni , kun isa da ni , Ko mai kuka yanke a kaina ni na san alkhairi na ne dan haka bani da musu KO ja da maganar ku"
Wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyoyin su, kaunarta da Karin ganin darajarta da kunyarta suka darsu a zuciyoyin nan uku,
Hajiya Fadimatu ta sauke ajiyar zuciya da ido ta yiwa Hajiya Hawau nuni da ta fadawa Yar Mahaukaciya abinda suka yi ,
Hajiya Hawau ta kara gyara zama ta ce" *Daman ranar juma'ar can da ta shige aka daura miki aure ke da Dan Aljannah* "
Bugawar zuciyar Yar Mahaukaciya daidai da kiftawar idanuwanta, domin kwatakwata idanuwan ta kasa tsayar da su sai kikifta su take, jikinta gaba daya rawa yake, kafafuwanta dake tankwashe ta samu ta hau saman su ta yi tamkar zaman rakumi a hankali cikin rawar jiki ta dauko hanunta guda ta tokare habarta , hawaye wani na bin wani
Jikin Hajiya Fadimatu yayi sanyi, ta taso a nitse ta kamo Yar Mahaukaciya ta dora kanta a saman cinyar ta tana shafawa tana gyara mata gashin kanta da shi kansa ya jike wajen hudodin, har a lokacin jikinta rawa yake sanan bata furta komai ba,
Ta kai minti goma a haka , zuwa wanan lokacin shi kansa ji yake kafarsa ta kasa daukar sa, a hankali ya cire hular kansa ya jinginu da jikin abin hawa benen, ya dora hanunsa na dama daidai zuciyarsa yana irga bugawarta ,
Can kamar an tsikare ta ta zabura ta sauko kasa ta hada hanayenta biyu kamar ta zo neman gafara ta ce" *Mamana ki yi min rai, kar ki saka ya kore ni daga inuwarki, shi ya fada min da bakinsa cewar na fitar da miji cikin satin nan ya aurar da ni ya huta da gani na, yanzu idan ya ji cewar an aura masa ni ai har ya hadiyi zuciya ya mutu daman ba lafiya gare shi ba , dan Allah dan Annabi a kashe auren nan tun kafin ya ji ya kore ni mama Dan Allah, kinga sai Abdallahn yayi ya fito daman yanzu ya gama fadar hakan* " ta karashe zancen tana rushewa da kuka , ta mike da gudu ta nufi hanyar dakinta
Daidai zata hau ta ganshi nan tsaye gabanta ya yanke ya fadi ganin irin yanda yake da kyau haka gashi da alama fuskar sa tamkar ransa a bace, gabanta ya kuma yankewa ya fadi , a ranta ta furta *wutsiyar rakumi tayi kadan ta taba kasa*
Shi ma gabansa ya yanke ya fadi domin idanuwansa sai suka hango masa tsanarsa a kwayar idon Yar Mahaukaciya, nan take kalmar *I HATE YOU* da ya furta mata nan da yan awanni suka dawo masa , ya bi bayanta da kalo har ta shige dakin ta rufo
Hajiya Fadimatu ta mike da niyar bin bayan yarinyarta , Hajiya Hawau ta dakatar da ita ta ce" kar ki bita a yanzu, ki barta ta gama shawara da zuciyarta , "
Hajiya Fadimatu ta koma ta zauna jiki bâ kwari ta ce" tabas idan Yar Fadimatu ta ce bata son Dan Fadimatu zan raba auren nan , dan kuwa bazai yiwu ni da kaina na aurawa yar Amana abinda bata so,
Muryar Mubasshir suka tsinta yana fadin" *NO MAMAN MUBASSHIR BAZA'A RABA AUREN DA BA'A TARE SHI BA MA , BA KYAU* "
Hajiya Hawau da Hajiya Fadimatu suka zuba masa ido irin yanda jijiyoyin hannun sa suka mimike,
Hajiya Hawau ta kawar da kanta tana kokarin danne dariyarta dan kuwa da ka kali fuskar Mubasshir zaka karanto tsantsar tsoron kada a raba shi da abinda yake matukar so, ta kali Hajiya Fadimatu ta ce" *wanan aure mun hada shi ne da niya mai kyau, sanan shi aure raine da shi, kuma wanan karamin dalili ba zai saka mu raba auren nan ba saï da kwakwaran dalili, Rahma na cikin tsoro ne da fargabar yanda Dan Aljannah zai karbi maganar, bayan shi ban karanci tsanarsa a kalamanta ba, ki barsu su sasanta kansu ya nemi soyayar matarsa da kansa ki zira ido hakan shi zai kawo alkhairi ba wai a raba auren ba* "
Mubasshir ya gyada kai uwa shi ake fadawa ya ce " yawa Hajiya , ai shi kansa sakin ba kyau ana yinsa"
Hajiya Fadimatu ta zabga masa harara ta ce" ai Dole ka fadi haka bayan ka gama fada mata tayi ta fitar da miji kai ka gaji da ganinta KO? Kai ga dadynta, to sai kayi kokarin fahimtar da ita kaine mijin idan ba haka ba kuwa ,i'm sorry sai dai ka sakar min y'a "
Tana gama fadar haka ta Mike ta nufi kicin dan samawa Hajiya Hawau wani abin Marar nauyi ta ci...
Da ido suka bita sanan a tatare suka sauke ajiyar zuciya , Mubasshir ya kali Hajiya Hawau ya ce""""""""__,,,,,,,"""""""""""""""",,,,_______"""""""""""""
🇳🇪BELLES écrivaines Nigériennes
'YAR 👧🏻
MAHAUKACIYA👹 na
58
*Tabas soyaya ita ke sakawa a damu da mutun idan an ga shiru, idan na ce zan tsaya zano ku wly sai mu cika page din bamu gama bâ, Alhamdulilah Allah na gode da ka bani ikon rubutu tabas alkhairin rubutu shi na samu ba sharin sa ba, sisters godiya marar addadi , tsakanina da ku sai fatan alkhairi, daga taku yar Mutan Niger*
Mubasshir ya zubawa Hajiya Hawau ido , yana matukar son ya kara fada mata kar ta yarda Maman sa ta raba auren sa , aman ina ai da kunya KO ba komai kakar Sahla ce, Dole ya ji kunyar wani abin, Hakan ya sa ya Mike yana kokkarin FITA daga dakin dan bai ga ana marhabun da shi a cikin gidan ba
Cikin murmushi irin nasu na Manya ta ce" dawo ka zauna Dan aljannah,"
Mubasdhir ya juyo yana tafiya kansa a kassa ya dosanu ya zauna stil yana kalon kassa
Cikin nutsuwa ta ce" ni na jajirce da taimakon ubangiji aka daura maka aure da Marainiyar Allah,
Cikin firgicci ya dago yana kalon ta,
Hajiya Hawau ta ci gaba" kwarai kuwa , abinda ya saka ni aikata hakan dan ina tsoron aurawa wani yarinyar amanna ya cutar min da ita, tabas na san bazawarra ce aman idan kayi hakuri ta fi budurwar dadin zama ,"
Mubasshir