Showing 15001 words to 18000 words out of 69263 words
dinga buga mata dama ya riga ya shirya ma zuwan nata sosai ta maƙale shi tana faɗin "Ohhh Ahahhhh Sweet Lil washhh fuck..." Da ire-iren kalman nan take sake ɗaga masa hankali wanda ya sa shi sake zage damtse yana buga mata wutsiya. Suna tsaka da jin daɗi suka ji an banko ƙofar da ƙarfi yana ƙoƙarin sauka ta riƙe shi gam domin dab take da zubar da ruwa "Ohhh My God! Sweet Lil wayyo Ashhhhh Hahhhh Ohhhhh!" Kunna wutar ɗakin ta yi nan haske ya gauraye ko'ina runtsa ido Suhaima ta yi tare da yin kukan kura ta afka kansu "Allah ya isa min Dalili! Da me wannan muciyar ta fini? Ka kalli yadda kake ride ɗinta kana kiran sweet...! Da aure nake son ka ba da ƙazamin rayuwa irin wannan ba, wallahi se na kashe ku zan kashe ki ƙaruwa ƙazama kariya.." Ɗauke ta Fiddoh ta yi da wani gigitaccen mari tare da faɗin "Akwai 'yar iska irin ki, ki ce kariya wacce take bin namijin da be son ta , ki tambaye shi na taɓa bin shi? Ga shi nan ai kullum bina yake kamar zai mai da ni ciki saboda tsananin so ko ba haka ba ne my sweet Lil?" Gyaɗa mata kai ya yi yana jin takaici katse masa jin daɗin da Suhaima ta yi, ƙofa ya nuna mata tare da faɗin "Fita a nan!" Kwalbar da ke hannunta ta buga mishi tare da fashewa da kuka "Wallahi Lil Ina son ka! Amma gwara na kashe ka ita ma zan kashe ta, domin babu shegiyar da ta isa ta raɓi abin da nake so!" Ƙara Fiddoh ta yi da ƙarfi tare da ture Suhaima da ƙafa nan fa dambe ya barƙe cikin haka Fiddoh ta ɗauki fasasshen kwalban ita ma ta rotsa mata a goshi ihun su ne ya fargar da sauran jama'ar da gudu Zee ta ƙarasa shigowa ganin yadda jini ya ɓata gadon ne ya sa ita ma ta sa ihu tare da jin kan Suhaima tana jijjigata wacce tuni ta suma da gudu Na'ilah ta kama hannun Fiddoh tana janta akan su bar gurin sai dai kash! Suna fitowa sai ga 'yan sanda. Nan suka tasa ƙeyarsu Dalil da Suhaima direct aka yi asibiti da su da ke ciwon Suhaima bai shiga sosai kamar yadda ta fasa ƙeyar Dalil ba, ana gama wanke mata suka ta sa ƙeyart, kwana suka yi cikin fitsari da zarni ga cizon sauro zagi kan Fiddoh ta auna musu buhu-buhu domin sun hanata waya bare ta kira gida gashi sun hana kowa ganawa da ita Na'ilah sai sintiri take tana basu haƙuri, sai washegari aka ba su damar ganawa da mutane jiki na rawa Suhaima ta fara kiran Hajiya Larai, Sai dai wayar tata baya shiga ta yi tunanin kiran Daddyn su (Hon. Sa’id kasancewar haka suke kiran shi) sai aka yi rashin dace shi ma wayar ta sa ba ya shiga tana kuka haka ta kira Alh. Aminu tare da sanar da shi halin da take ciki.
Na'ilah na ƙoƙarin biyan kuɗi Fiddoh ta dakatar da ita domin ta ce wlh se dai Suhaima ce za ta biya domin ita ce silar zuwanta nan gurin ƙarshe kamar za su kashe kansu saboda hayaniya duk yadda Suhaima taso taka Fiddoh abin ya wuce tunaninta domin Firdausi irin fitinannun matan nan ne masu naciyar faɗa, ba ta jin haƙuri sai dai idan ta gaji tun kanta ta ƙyale zuwan su Alh. Aminu gurin ne ya sa ta yin shuru tare da ƙure shi da ido, Bestie wancan mutumin ya haɗu fa, wlh farat ɗaya zuciyata ta amshe shi, Black beauty ga sanyin nutsuwa takun sa gwanin burgewa sugar daddy idan ya same ni 'yar sweet 17, zan shagwaɓa shi da yawa.." Cike da baƙin cikin jin kalamanta Suhaima ta ce "Ahir ɗin ki, Karuwa! Gwanjo wacce maza suka gama shiga da fita a jikinta, Dad ɗina ya fi ƙarfin kariya ballagaza irin ki.." Wani irin murmushi Fiddoh ta yi tare da faɗin "Zan nuna miki halin Karuwa ke bari ma kiji wallahi se na auri Uban naki kuma dole ki kira ni Mom! Domin ya yi min irin mijin da nake so kuma dole na yi kishi da uwarki"
Wani irin mugun kallo Alh. Aminu yake bin Suhaima da shi kuɗi ya je biya ran shi a ɓace domin bayanin da 'yan sandan suka mishi game da abin da ta aikata. Juyowa yai tare da kife ta da mari ya riƙe kunnen ta yana magana cikin ɓacin rai dama kwana biyun nan ran shi a ɓace yake musamman ma da Hajiya Umma tai mishi iyaka da abar ƙaunarsa.
"Wato ke har kin yi ƙwarin da za ki yi faɗa akan ɗa namiji kina fashe-fashen kai ko Suhaima? Ban hanaki yawon dare ba? Kodayake ba laifin ki ba ne tun da kin samu ɗaurin gindi amma ba komai zan yi maganin abin"
"Hi! Yaa Laj! Ka biya kuɗin duka har nawa domin ɗiyarka ce ta sa aka kulle ni, and pls ka riƙe faɗar har ku ƙarasa gida in ya kama ma a yi mata shegen duka, domin bata jin magana" Kallon Firdausi yai tare da jan tsaki ya figi hannun Suhaima suka nufi gidan Hajiyar shi.
Ɗauke kai Maman Nafisa ta yi daga kallon Firdausi "Yanzu Mamanmu ko sannu ba za ki ce mini ba?" A fusace ta ɗago tana nuna ta da 'yar yatsa. "Na aike ki? Wallahi Firdausi fita idona na rufe in ba haka ba zan yi mugun saɓa miki" Watsar da hannu Fiddoh ta yi irin l don't care ɗin nan sannan ta juya tana jin jawabin da Zaliha take mata game da auren da Baban su yai wa Nuriyya "Jar uban can! Na rantse da Allah se ya sake wannan auren ko kuma na yi mishi kutumar.."
"Zo ki fice min a ɗaki!" Maman su ta faɗa tare da miƙewa tana neman abun da zata buge ta da shi domin ta lura har yanzu bata dawo cikin hayyacinta ba. "Mamanmu Rass fa nake! Ban shawu ba wallahi maganar gaskiya wannan Guy ɗin ba ya kyautawa ta ya zai aurar da 'yar'uwata ba tare da ya nemi shawara ba, na rantse sena ɓata mishi rai..."
"Innalillahi wainna ilaihir rajiun! Baban ne Guy? Firdausi lallai kin riƙa Ubangiji ya shirya ki" Maman Nafisa ta faɗa kana ta nufi gurin kayan turaren ta. Kallon Nuriyya da ke zaune shuru tai kana ta ce "Karki wani damu tsaf zan sa shi ya warware wannan abin" Ta faɗa tana me kwanciya kusa da ita. "Ke! Humm! Ɗazun nan naga wani haɗaɗɗen sugar daddy yasin ya haɗu sosai, shirya muje shopping na siya miki riga ko kala biyu da hijjabi dan ba saka gyale kike ba" Da sauri Zaliha ta ce "Ayya! Ni kuma fa Aunty Fiddoh" Hararanta tai tana faɗin "Kema shirya sai muje"
Wannan Littafin na kuɗi ne domin kasancewa cikin group y ₦500. A tura ta wannan account ɗin. 2389596965 Aisha jubreel Zenithbank Sai a tura shedar biya ga wannan Number 09079740079
#Amnoor
#Sadstory
#Destiny
#Hotlove
#Romance
[5/9, 11:43 PM] FARHATULƘALB💔🤗: *♡AMNOOR...!*
_A romantic story_
®
FARIN JINI WRITER'S ASSOCIATION📚
★F. W. A★
H-P Place Group.
Free page 21-22
A nutse ta matsa gefe inda babu hayaniya tare da manna wayar da kunnenta tana sake faɗin "Ki jira ni yanzun za mu dawo sai muyi maganar." Juyowan da za ta yi ne ta ga mutum tsaye yana ƙare mata kallo tunanin inda ta san shi take, zuwa can dai ganin taƙi yin magana ne ya sa shi faɗin Ashe dai ke ce, yau dai ba zan yi ƙuncin baki ba, ki faɗa min sunanki tare da na gidanku domin na ɗau tsawon watanni ina neman ki" Ɗagowa ta yi tare da watsa mishi narkakkun shanyayyun idanunta wanda yake ɗauke da zara-zaran gashi, cikin ƙwayar idon nata har wani maiƙo da sheƙi me fisgan hankali yake, shi bai taɓa lura da tsananin kyan nata ba sai yau da sauri ya ɗauke idonshi daga kallonta yana sakin ƙayataccen murmushin da ya ƙarawa kamilalliyar doguwar fuskarsa kyau da haiba. Waigowa yai yana sauraron zazzaƙan daddaɗan muryan da ke ratsa masarrafan da ke kai masa saƙo kai tsaye zuwa ga kunnensa.
"Sunana kuma? Me za ka yi da shi? Me sanin gidanmu zai amfane ka da shi?" Ta ƙarasa maganar muryanta na rawa saboda tsoro tare da kallon Zaliha da ke ƙoƙarin ƙarasowa wurin su. "Ki nutsu! Ba wani abu zan miki na cutarwa ba, da alkairi na zo auren ki zan yi..." Wani irin duka ƙirjinta yai wadda ya sa har tana ƙoƙarin yin ƙwarewa sai dai shaƙuwa ne ya riƙe ta, da sauri Zaliha ta ƙaraso tare da riƙe ta suka bar wurin bin su kawai yai da ido yana mamakin yadda take a tsora ce, juyawa yai tare da shiga motar shi ya nufi gidan Hon. Sa’id domin yana son ganawa da Amrah.
A rikice suka ƙarasa gida domin yanayin da take ciki abun ya ta'azzara zaunar da ita Mamansu ta yi tana yi mata fifita tare da shafa mata kanta hankali a tashe domin yanayin yadda ciwon yake zuwa ma Nuriyya ba ƙaramin kiɗimasu yake yi ba. Kallon tuhuma ta yi musu rai a ɓace take faɗin "Me kuka mata? Shi ya sa wallahi ban so fitar nan naku ba, babu yadda zan yi ne kawai dan abu kaɗan yake birkitata.." Fiddoh ta ce "Ki yi haƙuri Mamanmu!"
Zaliha da ke zaune da hannu bibbiyu tai tagumi ta ce "Mamanmu to akai Aunty Nuriyya asibiti mana sai aji me ke jawo mata wannan yanayin ko Fiddoh?" Ta ƙarasa maganar tare da kallon Fiddoh "Bari dai Amrah ta dawo don yanzu ta fita wai Daddy na kiran ta" Suna zaune shuru har Babansu ya shigo yana baza ƙamshi zama yai gefen ta gaban goshin sa Fiddoh yana washe baki domin dama zero yake ya san zai samu wani abu wurinta "Fidausi ya aka yi naga duk kunyi kalan 'yan zaman makoki sai ka ce wadda aka ce na mutu"
Wani banzar kallo tai masa tana faɗin "Da a ce kai ne ka mutu yaushe za mu yi wannan zaman? Ai wallahi DJ zan ɗauko na yi ta tiƙar rawa ina dariya dan an rage mugun iri ne, Uban da be san ci 'ya'yansa ba balle akai ga karatu, tun da Mamarmu ta yi mana ƙoƙarin muka kammala sakandiri fa muke zaune, tun buɗewar idanuna ita ce ɗawainiyarmu ta yi ayyuka ƙarfi, wahala, ga azaban baƙaƙen magana daga bakin mutane, ga zafin rana, duk don saboda mu. Ta shiwar yayarmu ta ɗaura niyar taimaka maka sai dai kash! Wasu 'yan iska suka datse mana farinciki ba su duba rayuwa da yanayin da muke ciki ba, suka take min 'yar'uwa wallahi ko ba jima ko ba daɗe akwai ranar ƙin dillancin duk ranar da na yi arangama da wa'yannan 'ya'yan Allah wadai ɗin hmm! Allah kaɗai ya san tanadin azaba da raɗaɗin da na yi musu.."
Dakatar da ita yai ta hanyar miƙa mata hannu bayan ya miƙe yana kallon jakarta, "Bani wani abu zan wuce ne"
Cike da shaƙiyanci ta ce "Mu je sai na ba ka.."
"Kinga bana son iya shege bani kawai na yi wucewa ta"
Ya faɗa tare da haɗe fuska. Tsaki Mamansu ta ja tare da miƙawa Nuriyya ruwa tana faɗin "Sallame shi dan Allah ya tafi tun da shi Allah ya yi shi mara lura bare ya fuskanci ya muke ciki.." Dubu ukun da take miƙa masa ya karɓa tare da tattara babbar rigarsa yai gaba.
"Ta yi aure fa kika ce Amratu? Wa ta aura? kuma a ina gidansu yarinyar yake? Ya sunan ta?" Kallon sa ta yi ganin yadda ya birkice tare da jero mata tambayoyi. Alama mahaifinta yai mata a kan ta tafi miƙewa ta yi ita ma tana kallon yadda Daddyn Hisham ya birkice duk sai ta ji tausayin sa, domin ta lura ƙwarai yana son Noor ɗinta, musamman ma da Abbanta ya ba ta labarin yadda suka haɗu, ta san da shi ya aureta za ta sha gata da soyayya sai dai momy larai fa za ta iya kashe musu 'yar mutane domin baƙin kishi ne da ita, sai kuma ga shi Allah ya yi mata gyaɗar dogo.
"Wai me ya sa kake katse ni a duk lokacin da nake gaf da cimma muradina ne kam?" Ya faɗa cikin yanayin damuwa tare da kallon Aminin nasa. "Gani nai kana ƙoƙarin ƙetare dokar Allah, ita fa yarinyar matar wanin ka ce, way not kai ma ka nutsu ka bi zaɓin mahaifiyarka, wata biyar fa ana abu ɗaya, ka bar 'yar mutane da nauyin aure na farko ba sauke mata haƙƙinta ka yi ba, ta ya za a takura yarinya bayan kuma tana da miji.." A harzuƙe ya kai mishi naushi, kaucewa Baban Amrah yai yana dariyar shaƙiyanci tare da faɗin "Haba mutumina cool down ka je ku daidaita da wannan amariyar anjima fa ba a haɗu ba, Larai ta nutsu tana harkan kasuwnacinta kai kuma ta barka da rumgumar filo tare da juyi cikin dare.." Miƙewa yai yana faɗin "Idan ka gama iskancin naka ni zan wuce gidan Umma" Dariya yai sannan shi ma ya miƙe yana faɗin "Ai tare za mu, domin ta ce mu je na san duk ba zai wuce maganar wannan auren ba"
Gaba yai yana jan tsaki domin har cikin ran shi ya tsani wannan maganar, matar ma baya buƙatar ganin ta.
Yana zaune tare da sauraron kukan da Suhaima take rero masa tana ba shi haƙuri a kan ya mayar da ita wurin momynta dan Umma aikin girki take saka ta ita kuma ba so take ba, ɗauke kanshi yai daga gare ta domin ba ya jin zai mayar da ita "Dan Allah Abba ka sa baki wallahi ba zan ƙara neman rigima ba" Murmushi Abban Amrah yai tare da kallon Aminin nasa. "Tun da ta yi nadama a ƙyale min ɗiya ta koma wurin gyatumarta.." Wani mugun kallon da Alh Aminu ya auna mata ne ya sa ta barin wurin cikin gaggawa tare da fashewa da kuka. Ga shi ko ta kira wayar momynta ba ya shiga kuma an hanata fita tana son zuwa duba jikin Lil amma Umma ta yi mata iyaka da ƙofar falo balle akai ga bakin get.
Gyaran murna Hajiya Umma ta yi ta shiga musu faɗa ta inda take hawa ba ta nan take sauka ba, ganin yadda Alh. Aminu ya watsar da maganar auren an shafe watanni a gefe guda kuma gantalin da Laraba take na yawon garuruwa da sunan kasuwanci ba ƙaramin ƙona zuciyarta yake ba, domin dai ta tabbata har yanzu bata ɗauki Aminu da wani muhimmanci ba,
"Wallahi wannan zaman da za mu yi ya zama na ƙarshe ka tafi gidan su yarinyar nan ku daidaita kanku dan a satin nan zata tare ba wani magana ɓata lokaci tunda abu na tafiya shekara" Ɗagowa yai tare da gyaɗa mata kai yana faɗin "In Sha Allahu za a yi yadda kika ce" Da mamakin kalamansa ta sake kallon shi ganin yanda ya sauko babu jayayya kamar lokacin baya, "Yawwa Madalla Ubangiji yai maka albarka Aminu na" Murmushin yaƙe yai mata sannan ya fara laluben makullin motarshi tare da ficewa a falon ya barta suna tattaunawa da Abban Amrah nan ta sanar da shi inda gidan su Nuriyya yake da kuma yadda take so a yi komai ba tare da Labara ta sani ba sun tattauna sosai inda ya tsayar da maganar da cewar zai gyara part ɗin Amrah domin yarinyar ta zauna a can na ɗan lokaci. Yana fitowa ya shiga mota tare da kallon Aminin nasa ya ce "Na ji daɗin yadda ka amince mata ba tare da jayayya ba, yanzun muje gidan su yarinyar" Shuru kawai yai masa har suka ƙarasa anguwar tsayar da motar yai yana ƙarewa gidan da suke fuskanta kallo. Dama tun fitar su Umma ta kira Baban su ta sheda mishi za su zo, yana ganin tsayuwar motar ya ƙaraso kallon up and down Baban Amrah yai masa ganin yadda yake taku ɗaɗɗaya yana maza gare.
"Barka da zuwa Alh" Ya faɗa tare da miƙa masa hannu nan shima ya miƙa masa suka yi musabaha sannan ya gabatar musu da kanshi tare da musu iso zuwa ɗakin shi da ke wajen gidan. Ɗakin fess yake kasancewar shi mutum ne me tsafta ɗan ƙwalisa domin ya ƙawata ɗakin da kayan ƙyale-ƙyale na zamani cike da shaƙiyanci yake magana tare da gabatar musu da kayan motsa baki kana ya ce "Har yanzu ban gane wane ne angon ba" Kallon Alh Aminu da ke ta murmushi yaƙe Baban Amrah yai kana yai masa nuni da cewar "Ga shi nan" Sunkuyar da kai Alh Aminu yai ganin yadda Baban su yake ƙare mishi kallo yana gyaɗa kai. "Madalla bari na turo muku ita" Yana fita Baban Amrah ya ce "Amma da ganin wannan sirikin naka ɗan duniya ne" Shi dai bai ce masa komai ba. Lokacin da Babban su Nuriyya ya shigo ya yi daidai da zura ƙatuwar hijjabinta tana ƙoƙarin yin Sallar la'asar da ya wuce ta domin yau da zazzaɓi ya wuni, "Nuratu ki shirya kina da baƙi a ɗaki na, ki yi sauri domin ba jimawa za su yi ba"
"Ai ka bari ta yi Sallah ko kuwa?" Maman Nafisa ta faɗa tana hararar shi. Jiki a sanyaye ta yi Sallar tana sallamewa ya azal-zala musu wuta ta yi ta fito Fiddoh da fitowarta kenan daga banɗaki ta kalle shi tare da faɗin "Ai ta amsa za ta zo, ka je mana, ka tsaya kana surfawa mutane ruwan bala'i haka za ta je ba tare da ta shirya ba?" Fita yai yana masifa. "Dalla ke ma ki shirya kin yi tsaye se rawar jiki kike ba dole a cika mutane da surutu ba" Fashewa kawai Nuriyya tai da kuka domin ta rasa ya ma za ta yi. Ɗauke kai Maman Nafisa tai domin wannan ba maganar da za ta saka musu baki ba ne. "To ni me zan yi? Dan Allah shirya mu je tare.." Zaro mata ido Fiddoh ta yi tana faɗin "Wa? Taɓɗi! Ai