Showing 9001 words to 12000 words out of 69263 words

Chapter 4 - Amnoor Complete book Romantic Hausa Novels by Aysha JB

Aisha JB   

22 Aug 2025

297

kai tayi tana faɗin "Ban san su ba" Lawyer yace "Ki ƙara zurfafa tunani dai.." Kallon ta ya yi ganin tayi shuru taƙi tanka masa "Yarinya kinyi nazari domin a ƙwato miki ƴancin ki.."
"Yallaɓai tun da tace bata san su ba a ƙyale maganar zai fi" Zai yi magana Maman su ta sake faɗin "Dan Allah karka ce komai a hakan ma mun gode!" Dagewa yai a kan lallai Nuriyya ta faɗi wani abun ƙarshe jikinta ne ya fara rawa nan ta shiga jijjiga lamarin ya tsananta sosai domin likitotin sunyi faɗa sosai da cewan bai dace daga farkawan ta a tsitsiye ta da tambayoyi ba.


Rai a ɓace Fiddoh ta nufi ofishin ƴan sanda domin jin dalilin da yasa aka rufe file ɗin Nuriyya sai dai bata samu damar shiga ba, Domin yadda ta dinga zaginsu tana tsine musu abinda ya haddasa ƙaramin rigima tsakaninsu kenan tayi kuka tare da jin baƙin cikin abinda aka aikata musu. Wato a duniyar nan talaka ba komai bane idan abu ya haɗaka da ƴaƴan masu kuɗi in baka da mai tsaya maka sunan ka sorry abinda ya faru da Nuriyya kenan duk yadda Fiddoh ta so a dawo da case ɗin abin bai yuwu ba. Haka ta dawo asibitin nan ta kuma tarar da sabon tashin hankali domin jini ne yake zuba mata sosai tana jin azaba sosai idan ta zo fitsari gashi dai tana jin fitsarin amma bata iyawa sai dai kaɗan ya fito dalilin da yasa ta firgicewa tare da ficewa cikin hayyacinta kenan. Gashi ana buƙatar ƙarin magungunan dan ga kuɗin aikin da wasu alluran da ake buƙata. Bata da yadda zata yi domin tana son ƴar'uwarta tana son ganin ta dawo kamar yadda mutane suke duk da a kullum cikin faɗa da rigima suke akan irin rayuwar da Firdausin take yi hakan bai hanasu soyayya da shaƙuwa irin na ƴan'uwan juna ba.


Basu da wani mataimaki sai Allah dan Baban su ma maganan banza yake faɗa domin ƙwandalan shi yaƙi bayarwa. Babu irin taimakon da bata nima ba sai dai kowa yace idan ta amince ayi ban gishiri in baka manɗa dake basu da ƴan'uwa a gari dan Babansu da Maman su mutanen Sudan ne cirani ya kawo su Nigeria. Sai da Likitan ya more ta na kwana uku kafin ya yarda ya duba Nuriyya inda aka mata aiki.
***
"Wallahi Alhaji iya bincike nayi amma ban samo inda yarinyar take ba" Kallon mutumin Hon. Sa'id yai tare da faɗin "Ko sunanta baka sani ba?" Gyaɗa mishi kai ya yi "Ok zaka iya tafiya mun gode" Kallon Aminu yai yana faɗin "Muje ko?" Cike da takaicin kalamansa Alhaji Aminu yace "Muje ina bayan ban ganta ba?" Gyara tsayuwa Hon. Sa'id yai yana faɗin "Mun kai sati muna jele a nan amma babu labarin ta ina ga babu amfanin tsayuwar ta mu tun da ko mun tsaya ɗin ba zuwa zatayi ba waya sani ma ko aure tayi..." Wani irin kallo Alhaji Aminu yai masa tare da runtsa idanunsa yana jin kalmar auren nan na dukan zuciyar shi. Da yasan haka zai kasance da tun farko ya faɗa mata abinda ke ran shi. Bai san ya kamu da mugun ƙaunarta ba sai yanzun da ya nime ta ya rasa tayi ɓatar damo babu ita babu labarin ta, Abun takaici ma ko sunanta bai sani ba, Dole suka dawo gida amma gabaɗaya ba shi da nutsuwar zuciyar haka kawai sai yana ji a ran shi kaman ba lafiya ba.


Matarshi ta lura da yanayin nasa sai dai bata wani damu ba. Ta mayar da hankalinta ga kasuwancin tare da ƙoƙari tura Hisham Ƙasar waje domin tun da wannan lamarin ya faru shi ma a firgice yake shi yasa take son tura shi can yaje ya ƙarasa karatun sa babu ɓata lokaci kuwa ta gama mishi duk wasu abubuwan da ya kamata na tafiya waje inda yai sallama da abokansa tare da Hajiya Umma suka nufi airport sai da suka ga tashin jirginsu sannan suka dawo gida.


Lamarin Alhaji Aminu kuwa abun ya babu daɗi domin har ƴar jinya sai da yai na kwana biyu Amininsa ne yake sanar da Umma abinda ya haddasa masa wannan damuwar taji matuƙar mamakin jin dalilin rashin lafiyar nasa "Allah mai iko Aminu yanzun da girman ka soyayya tayi maka irin wannan kamun? Ɓatan basira ɗaya da ku kayi na rashin sanin sunanta da inda take da an san wannan bayanan da komai yazo da sauƙi amma duk da haka ka yawaita Addu'a idan rabon ka ce In Sha Allah zaka same ta, In kuma ba rabon ka bace Ubangiji ya musanya maka da mafi alheri.." Da sauri ya tari Numfashin ta gurin faɗin "In Sha Allah rabo nace" Murmushi kawai tayi domin lamarin na shi har mamaki ya bata wai Aminu yake kwance a kan SO? Duk wannan wainar da ake toyawa matar shi bata sani ba, domin har ya gama kwanciyarshi a asibiti bata leƙo shi ba. Suhaima ce kawai ke kaiwa da komowa a asibiti.


Kwana biyu kenan da a ka sallamosu daga asibiti sai dai abin sakawa a bakin Salati na niman fin ƙarfin su ga Nuriyya ma jikin sai a hankali dan bata iya wani ƙwaƙƙwaran motsi tana daga kwance ɗan aikin da Maman su take ma yanzun babu domin Hajiya Larai koran ta tayi a kan kwana biyu bata zo ba, Duk da ta faɗa mata dalilin rashin zuwan nata haka matar nan ta baɗawa idanunta toka ta kore ta.
Ɗan tallar da Zaliha take Nuriyya ta hana ta domin tsoron abinda ya faru da ita ya faru kan ƴar'uwarta take ji. Ga Baban Su ba taimaka musu yake ba abinda Maman su ta ɗan nimo ta dafa musu ma ƙoƙarin cinyewa yake duk da takaici halinshi jikin Nuriyya yake daɗe taɓarɓarewa gashi kullum bashi da magana wadda ya wuce ta miƙe taje ta nimo mijin aure ko kuma ya yi sadaka da ita lamarin babu daɗi domin tana cikin ƙuncin rayuwa dole aikatau Maman su ta koma a yanzun dai Fiddoh ce ke ƙoƙarin samo musu abinda zasu ji duk da kullum sai sunyi daru da Nuriyya take karɓan abincin "Idan baki ci ba taya zaki sha magani? Ni kaina ba son rayuwar nan nake ba babu yadda na iya ne kawai Dan Allah Nuriyya ki daure ko dan ki sha magani saboda ki samu lafiyan jikin ki bana jin daɗin ganin ki kwance"


Da ire-iren waɗannan kalaman take samu taci abincin haka rayuwa taci gaba da tafiya da daɗi ba daɗi haka suka dinga haƙuri dake Allah ya basu jajirtacciyar uwa sai abubuwan suka fara musu sauƙi aiki ba irin wanda ba tayi dan samun abinda zasu ci sai dai kuma kwatsam watarana suka tsinci kansu cikin halin rashi na ƙaramar ƙanwarsu Nafisa lamarin da yayi sanadiyar rugujewar ɗan farincikin da suka samu nan komai ya sake kwaɓewa.
Sannu a hankali rayuwa ta fara juya musu baya domin wani irin rashin lafiya da Fiddoh ta kwanta ganin abu goma da ashirin ya haɗu ma Maman su ne yasa Nuriyya dauriya ta fara ƙarfafama kanta gwiwa domin wacce take ɗan taimakon nasu gata kwance.




*Wannan littafin kuɗi ne domin kasance cikin group zaki/zaka tura ₦500 ta wannan account 2389596965 Aisha jubreel Zenithbank sai a turawa wannan Number shedar biya 09079740079 Please Idan ba siyan littafi za kiyi ba karki ɓatawa kan ki lokaci gurin min magana*
[5/9, 11:42 PM] FARHATULƘALB💔🤗: *_♡AMNOOR...!_*
_A Romantic Story_


®
FARIN JINI WRITER'S ASSOCIATION📚
★F. W. A★


Free page 17_18


*H-P Place Group*


"Ki yi haƙuri Nuriyya ta ko wanne yanayi Ubangiji ya kan jarabci bawa domin ya gwada ƙarfin imaninsa ta ki ƙaddarar kenan babu ta yadda za ki kauce masa Allah ya ƙara miki lafiya da sannu za ki ga sakayya akan duk wanda ya aikata miki wannan aika-aikar, me ya sa ba ki kira number dana ba ki ba? Yanzu da ban biyo Na'ilah duba ƙawarta ba shi kenan ba zan san abin da ke faruwa da ke ba? Har yanzun kin kasa sakin jikinki da ni bayan da zuciya ɗaya nake ƙaunar ki, Allah ne shaida"
Sunkuyar da kai Nuriyya ta yi tana jinjina irin ƙaunar da Amrah take mata "Na gode sosai Amrah!" Hannunta ta riƙe tana faɗin "In Sha Allah zan tsaya miki a dawo da case ɗin.." Cire hannunta ta yi daga nata tana faɗin "In har da gaske ƙaunar da kike min daga zuciyarki ce dan Allah kar ki ɗaga wannan maganar koma waye na yafe!" Ta ƙarasa maganar tare da ɗauke hawayen da ke zubo mata "Shi kenan ba zan tada maganar ba tun da ba ki so zamu wuce ki riƙe wannan zamu dinga magana" Kallon waya tare da tulin kuɗin ta yi da sauri Maman su ta ce "Amratu! Wannan kayan arziki haka? Ubangiji ya yi albarka mun gode ƙwarai!" Murmushi Na'ilah ta yi sanan ita ma ta miƙawa Fiddoh kuɗi tare da ajiye mata jakar da ta zo musu da shi wanda yake ɗauke da kayan abinci "Beb! Ki yi ƙoƙari ki miƙe Please ana ta cigiyarki kowa ya yi missing ɗin ki duk casu idan babu ke ba daɗi wallahi gashi kwana biyu ba wani update tun bayan na Alh. Aminu bamu sake fitar da komai ba, after zan dawo tare da Dr ya duba mana ke" Gyaɗa mata kai Fiddoh ta yi tare da faɗin "Thank you Bestie!"
Bayan tafiyarsu Maman su ta kalli kuɗi haɗe da kayan tana jinjina lamarin a zuciyarta ashe har yanzu akwai mutane irin Alh. Aminu a duniyarnan? Zaliha ce ta katse mata tunani ta hanyar faɗin "Wayyo Allah daɗi kashe ni! Allah yai musu albarka yanzun Mamanmu tun da kin iya turare Allah a ware wasu kuɗin ki faɗa min abubuwan da za a sayo sai ki fara yi kawai kuma a duba mana wani ɗaki daban kinga da ma nan ya yi kaɗan wlh tsawon shekaru muna zaune a ɗaki ɗaya yanzu ka a ware mana namu." Maman Nafisa ta ce "Kin yi gaskiya, amma ina tsoron kar Babanku ya zo ya ɗauke kuɗaɗen dan wallahi muddin ya shigo na san sai ya ga wannan kuɗin.."
"Aikuwa bai isa ya je inda kuɗin nan suke ba, wallahi muddin ya taɓa zan yi mishi rashin M.." Fiddoh ta faɗa tana gyara kwanciyarta.
Da yamma kuwa sai ga Na'ilah ta dawo tare da likita nan ya shiga duba jikinta sannan ya bata magungunan haɗe da allurai bata ƙyale likitan ya ta fi ba sai da ta sa shi ya duba jikin Nuriyya.
Kwana biyu tsakani Fiddoh ta miƙe ta fito ras da ita nan ta tsaya ta ƙarewa matan gidan kowacce sai da ta zageta sannan ta fita ta nufi gurin Emanuel da ma a takure take daga nan ne fa lamarin ya canza salo nan suka faɗa duniyar masha'arsu Fiddoh kamar mayya haka ta kanannaɗeshi suna abu ɗaya sai da ta fanshe kwanakin da basu tare sannan ta ƙyale shi tana kwance saman jikinshi tana murza nipples ɗinsa cikin yanayin da ke nuna har yanzu bata samu gamsuwar da take buƙata ba, hannunta ya riƙe yana magana cin Hausar da be gama ƙwarewa. "Mene kuma Fiddoh? Na yi sosai ki bari na huta haka.." Wani irin numfashi ya ja sakamakon kamo bananarshi da ta yi tana matse saman "Hmmm!" Ya sauke wani gwauron numfashi yana jin yadda take tsotsar abin sai da ta sa suka koma tana ride ɗin shi kamar ba za ta ƙyale shi ba. Sai da ya ga abin nata na neman fin ƙarfin shi kafin ya ƙwace daga jikinta yana mayar da numfashi duk da shi ya fara buɗe mata ido amma ya lura jarabarta ya fi ƙarfin sa. Kallon sa ta yi tana yamutsa fuska sannan ta shirya ta fita.
Bayan ta karɓi dubu biyar gurinshi domin yanzu rashin mutunci take ji.


Tana fitowa suka yi karo da Baban su dakatawa ta yi tana ƙare mishi kallo ganin yadda ya sha shadda me ruwan goro sai maiƙo yake ga dukkan alamu sabo ne kallon takalmin ƙafarshi ta yi nan ma dai sabo ne hatta agogon hannunsa. "Allah ya sa dai ba kayan wasu aka ƙwamuso ba, dan na ji ana sanar da cewa an yi sata.." Hannunsa da ya miƙo mata ne ya sa ta katse maganar tata alamu yai mata akan ta ba shi na shi kason "Wallahi ba zan ba da ba! Domin gumi na ne, yadda kake buga jiki kake ɗauke-ɗauke haka ni ma nake sake jiki na yi abin da za a ba ni kuɗi.."
"Au haka ne abun?" Cike da baƙin cikin halinsa ta ce " Ya fi haka, lokacin da nake kwance me ka tsinana min? Mamanmu ke ɗawainiya da mu ita ce take fita tana yawo a rana domin samo mana abin da za mu ci.."
"Ba za ki ba ni ba kenan?" Tsaki ta ja sannan ta ce. "Muje na gwada idan ya mun sai na ba ka." Tana gama faɗar haka tai shigewarta ba tare da ta ba shi ko sisi ba.
Komawa yai gun Ema yana tambayar shi yau bata shawu ba ne? "Ta sha amma ba sosai ba" Gyaɗa kai ya yi tare da miƙa ma sa hannu "Mene ne kuma?" Emanuel ya tambaye shi tare da ɓata fuska. "Money! Ai na faɗa maka duk lokacin da kuka yi wata mu'amula ina da nawa kason ɗiyata ce, ni na ba ka go and hed ɗin da kake kome da ita" 2k ya zaro ya ba shi. Lokacin da ta shiga gidan direct ta nufi ba yi bayan ta ɗauki ƙaton butar da Maman Nafisa take alwala da shi kallon Zaliha da ke girki ta yi sannan ta ce "Ki kawo min ruwan zafi" Taɓe baki Zaliha ta yi sannan ta ɗibi ruwan tabi bayan ta da shi.
Washegari bayan fitar ta sai gata ita da su Na'ilah da leda niƙi-niƙi cike da kaya ta direwa Maman Nafisa tana faɗin "Kayan haɗin turaren na kawo miki tare da haɗin gwiwar 'yan group ɗin mu" Cike da mamaki Maman Nafisa ta ce "Wani group kenan?" Dariya suka yi sannan suka fita Fiddoh tana faɗin "Group ɗin 'yan sirri masu tona asirin abin da ba'a sani ba" Wani iri take jin abun, daɗi ne ba daɗi ba, rayuwar da Fiddoh take yi sam bata so babu yadda za ta yi, ka haifi ɗa ne ba ka haifi halinsa ba, mutane da yawa suna mata kallon uwar da 'yarta ta gagare ta bayan kuma ba haka ba ne, da ana buɗe zuciya da ta buɗe kowa ya ga irin baƙin cikin da ke ciki wanda ya danganci halin da Firdausi take yi, duk iya ƙoƙarin da Uwa take Allah ya gani ta yi shi amma abun sai dai a barwa Ubangiji...
"Ki yi haƙuri Mama addu'a za ki ci gaba da yi mata. Komai yana da ƙarshen sa haka watarana zai zamto tamkar ma ba a yi sa ba". Cewar Zaliha, ɗauke hawayen da ke zubo mata ta yi tare da faɗin. "Haka ne Zaliha Ubangiji ya daɗe shirya mana zuri'a." Amsawa ta yi sanna ta kwashe kayan ta je ta adana su. "Mama!" Juyowa ta yi tana kallon Zaliha. "Na'am Zaliha ina sauraron ki."
"Da ma na ce yaushe za ki fara yin turaren? Dan na faɗawa Malaman islamiyyan mu zan kawo musu su saya kuma ma na ce da ƙawaye na su faɗa a gida.." Shuru ta yi ganin Maman Nafisa tana murmushi "Tun ba a fara ba har kin soma tallar?"
"Ai da zafi-zafi akan bugi ƙarfe in ji masu salon zance" Miƙewa Maman Nafisa ta yi tana faɗin. "Ai da ma sai masu salon zance dan Hausar ma jinsa muka yi, zan yi ƙoƙari na fara amma fa gaskiya bana son maganar tallar nan domin na riga na yanke shawarar na fita da shi..." Cikin shagwaɓa ta katse mata maganar "Haba Mamanmu! Bafa tallar ba ne, iya makaranta ne fa dan Allah kin ji Allah daga makaranta shi kenan" Da ƙyar dai ta lallaɓa Maman su ta yarda akan in ta yi zata bata ta je da shi. Duk wannan budurin da ake Nuriyya tana daga kwance tana sauraron su ba tare da ta ce komai ba.
Domin har yanzun jikin nata ya kan motsa mata, cikin kayan da Na'ilah ta kawo musu suka yi dafa dukan taliya suka ci su uku domin Fiddoh bata dawo ba, suna cikin cin abincin Baban su ya shigo shi ma suka zuba mishi sai da ya gama ci sannan ya tambaye ta inda ta samu kayan turare shuru ta yi masa ba tare da ta yi bayani ba. Nuriyya ya dakawa tsawa yana tambayar ta. A firgicewa ta yi nan jikinta ya fara rawa kamar wacce aka jonawa lantarki, tsaki yai tare da barin ɗakin da sauri Maman su ta yi kanta ita da Zaliha suna taɓa ta hankali a tashe Maman su ta kwantar da ita tare da riƙe mata hannuwa dan har idanunta sun firfito tamkar wacce rai yake shirin barin gaggan jikinta domin har wani shiɗewa take tana jan numfashi, da ƙyar dai jikin ya daina rawa. A lura irin na Maman Nafisa Nuriyya ta kamu da cutar ɗimuwa wadda muddin aka yi mata magana me ƙarfi nan da nan take ficewa daga hayyacinta musamman ma idan namiji ne yai mata ihu abin na fin haka tsanani.


Alh. Aminu ne zaune gaban Hajiya Umma yana jin kalaman da take jero masa tare da miƙa masa hotuna murmushi kawai yai mata kana ya ce "Umma duk wannan hotunan basu yi mini kyau ba.."
"Daure dai ka duba dukkanin su kyawawa ne" Gyara zaman sa ya yi yana faɗin "Ita ma tana da nata sihirtacciyar kyau ɗin, doguwa ce me dirarriyar jiki, tana da nutsuwa yanayinta ba mace ba ce me son hayaniya, zagayyen dogon fuskanta yana ɗauke da hanci zar idanuwanta irin shanyayyun nan ne wadda da zaran ta kalle ka za ka ji wani yanayi, a gefen kuncinta na dama tana ɗauke da dimful bakinta ɗan daidai tana da tsayi sai ita ba fara ba ce yanayinta mace ce me sanyi domin ko tafiyarta a sanyaye take yin sa.." Dakatar da shi Hajiyarsa ta yi tana jinjina irin wannan soyayyar da

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login