Showing 90001 words to 93000 words out of 120090 words
gidan ne,tuni na barba ɗa maganin kai na taƙaice maka a kan idanu abar ta fara tashi.
*Nimcyluv*
7/15/21, 9:14 AM - Buhainat: _94-95_
Dariya Mubarak Yahya cibo yay kana yace "ai karawa dani babu daɗi,tun kafin shi mun kara da manyansa basu ji daɗin,bare shi ƙaramin ƙwaro,yanzu ni kuma lokacin hutawa ta ne,zan zo ba masa idanu yayta min mata hotel² kamar ɗan taure" dry suka tun tsire da ita gaba ɗayansu,kafin Lamir yace "kaga kowa ba ƙaramin jarababbe Za'ai ba,kana ganin yanayinsa kaga....,"sai kuma ya sanya dry, Mubarak cibo yace "kaga hajiri ko?bari ni na ƙarasa maka tunda tsoro kake"da sauri Lamir ya girgiza kai kamar yana gaban kamar ƙaramin yaro yace "kai haba² ni zanji tsoron wata halitta a nan gidan duniya never badai ni ba,kawai wani abu ke ban mamaki"ya faɗa yana kallon cibo domin ,cibo ya tsaya da dryarsa yace "me kenan kuma,hope ba'a a ɓangaren mu yake ba?"numfashi ya fesar, kana yace "no ko ɗaya"yace "to mene?"Lamir yace "kasan cewa bamu kaɗai ke neman Jalal da sharri ba,bayanmu aƙwai wajan mutane guda uku,nayi nayi malam yay min bayanin suwaye amma yaƙi"shiru Mubarak cibo yay can kuma yace "to mene matsalar mu dashi?"Lamir na danna wayarsa yace "matsalar duk abinda zamu jefesa dashi na sharri kafin mu aikata sun riga mu,shi ne kawai"cibo yace "to a ganinka su waye?"Lamir yace "i have no idea,amma duk abinda kake tunanin yiwa Jalal sun riga,dan yadda suke jifansa da sharri yaci ace sunga bayansa yanzu"cibo yace "haka ne,zanje wajan nawa bokan naji daga bakinsa"sallama sukai kana yay cikin gidansa,shi kuma Lamir ya nufi gidansa.tunda yasha ruwan lipton ɗin wanda ya sakawa lemon ciki yay rufda ciki, yana jin wata kalar masifa wacce bai taɓa jin irinta ba,banda sarawa babu abinda kansa ke masa,ya watsa ruwa har babu adadi mai makon feelings ɗin daya keji ya lafa sai abin ya ƙara tsamari,banda zufa babu abinda yake karyo masa,ga wata harbawa da dick dinsay ke masa ta tsaya gam ko mutsi ba tayi,da yaga abun sauki ya shiga kiran sunayen Allah,yana ta tsintiri daga bedroom ɗinsa zuwa parlour,idan yace zai yi sallah a haka tabbas zaiyi rafkanwa domin shi kaɗan yasan abin ya keji a cikin jikinsa, idanunsa sunyi jajir sun ƙanƙance,idanunsa biyu har akai kiran sallar farko,kana ya lallaɓa a hankali ya shiga bathroom, ɗan ƙaramin boxer'n daya saka ya zare yaga duk farin abu ya ɓata wandon,cillashi yay cikin warshing machine kana ya sakarwa kansa shower yana yi yana matsa mararsa a haka har Allah ya taimeksa ya samu sauƙi kaɗan kuma ta saki,alwala ya ɗaura tare da fitowa daga cikin bathroom ɗin sanye da towel,a ɗan gurguje ya shirya ya saka jallabiya ash kana ya ɗaura hirami, prayer mat ya ɗauka tare da fita daga cikin bedroom ɗin,a parlour ya tsaya ya data raka'atul firjir,ya daɗe yana azkar da addu'a akan Allah ya sassauta masa abinda ya keji akan sabun lamarin daya kunnu masa a lokacin dai baiyi tsammanin haka ba,masjeed ya nufa sai da suka zauna zaman jira kasancewar da wuri suke zuwa,bayan ya sallame ya tsaya yay karatu,bai shigo cikin gida ba Sai wajan 7 na safe,yana zuwa ya shige kitchen Laure ya samu tana haɗa breakfast da sauri ta zube ta shiga gaisheta,da ƙyar ya amsa mata,bisa dole yace ta zuba masa ruwan zafi a cup ta matsa masa lemon ta sanya lipton guda biyu,yadda yace haka tai masa kana ta bashi cup ɗin wanda tasa spoon a ciki,a hankali ya dinga shan ruwan lipton ɗin,tun kafin ya gama shanye wa ya fara zufa remote ya ɗauka ya ƙaro gudun a.c,kana ya ajjiye cup ɗin, miƙewa yay saman 3seater cikin ƙaramin lokacin bacci yay gaba da shi,kasancewar kuma weekend yasa babu wanda ya fito daga cikin part ɗinsa,wajan 10 na safe Jafar yay sallama ya shigo cikin parlour'n ganin babu kowa yasa ya ƙara so ciki,sosai yay mmkin ganin Jalal ƙwance yana bacci kamar ba shine ya gaya masa yau da wuri zai fita ba sbd gobe Sunday shine ranar da za'a rantsar da shi ba, ganin ƙafarsa ta zame yasa ya nufesa domin ya gyara masa ƙafar yana zuwa wajan yaga marar Jalal ta ɗaga sosai da sauri ya ɗauke idanunsa,kana ya gyara masa kwanciya shi kuma ya nemi waje ya zauna,Laure ce ta fito ta fara shirya danning,ganin Jafar yasa tace "Barka da zuwa" Murmushi yay mata yace "yawwa yaya aiki?"tace "Allahamdulillah"yace "ma sha Allah" kallon Jafar tai sai kuma ta kalli Jalal wanda yake bacci yana fidda numfashi a hankali tace "ko za'a haɗa maka breakfast ne?" Girgiza kai yayi yace "no bari zuwa anjima,nima wajan Abbou nazo ai" miƙewa tare da faɗin "ai ina jin yanzo mutum gidan zaso fito" bai ce mata komai ba sai wayarsa daya ɗauko ya fara dannawa,yana nan a zaune Mameey ta sauko daga upstairs da sauri,tana sanye da green ɗin atamfa ɗinkin riga da zaki sunyi mata ƙyau sosai,a ɗan gurguje ta nufi kitchen tsayawa tayi sbd ganin Jafar zaune yana danna waya tace "a'a Jafar zuwan yaushe?kazo duk muna ƙwance" Murmushi yay mata tare da rusunawa yace "ina ƙwana Mameey?"tace "Allahamdulillah,ya maman taka"yace "tana lfy,tace ai gaidaki Sai gobe idan tazo"Mameey tana murmushin jin daɗi tace "to ma sha Allah, Allah ya nuna mana gobee"yace "Ameen" kallon danning sai kuma ta kallesa tace "mai makon ka sanya Laure ta haɗa maka breakfast"Murmushi kawai yay kafin yace "daman Abbou yace nazo yana son gani na"kafin Mameey tai magana Abbou ya sauko cikin wani boyal milk tare da babbar riga sai zabga ƙamshi yake,idan ka gansa ba zaka taɓa yadda shine ya ajjiye manyan masari irin su Jalal ba, fuskarsa cike da Murmushi ya ƙara so cikin parlour'n tare da neman kujera ya zauna, idanunsa a kan Jalal domin tunda yake mai taɓa ganinsa yay bacci a parlour ba,kallon Jafar yay yace "wannan kuma lafiya?"Jafar ya durƙosa yace "haka na taddashi Abbou"jinjina kai kawai Abbou yay, Jafar kuma yace "ina ƙwana Abbou?" Abbou ya shafa kan Jafar yace "Allahamdulillah,ya Abban Maman taka?"Jafar yace "tace a gaidaku" gyara zama Abbou yay yace "zauna mana Jafar" a kunyace Jafar ya miƙe ya zauna,domin idan ya tuna Abbou ya kusa zama sirikinsa Wata kunyace take kamasa,wata rana har Jalal kunyarsa yake, Abbou ne ya tattara nutsuwar sa yace "Muhammad Jafar bani hankalinka nan"haka nan yaji gaban sa ya faɗi kansa dai a ƙasa yana sauraran abinda Abbou zai ce masa,kallon Jafar shima Abbou yake kafin yace "nasan kana da hankali,kana da ilimi both sides arabi da boko right? Kuma kasan muhimmanci ƙaddara da kuma wasiyya,alfarma zan nema a wajanka Jafar,ina neman alfarma ka janye maganar auran baby,bawai dan baka cancanci a aura maka ita ba, a'a kana da nagartar sa dukkan wani uba zai so haɗaka da ɗiyarsa,amma dole ce ta sanya nace maka haka,sbd wasiyyar mahaifiyarta ce haka,kuma kusan a akan wannan wasiyyar da kuma burinta komai ya lalace,ta riga ta faɗa tun kafin numfashinta na ƙarshe ya fita a kan tana buƙatar haɗa auran Jalal da Nihila,Nima na shiga tashin hankali da ruɗu sbd Jalal da kansa ya zaɓa maka Nihila matsayin mata,ba komai yasa yay hakan ba sai nagartarka da kuma jajir cewarka,dan Allah a matsayina na uba a wajan Jalal da kuma uba a wajan kayi hqr ka janye maganar auran baby,na maka al'ƙawarin duk yarinyar nan da kakeso zan tsaya maka wajan ganin ka sameta"tunda ya fara magana Jafar yake kallon Abbou,kasa cewa komai yay tunaninsa gaba ɗaya ya tsaya,wani shocked ya shiga wanda bai taɓa shiga irinsa ba,ya hqr da baby?ya janye maganar aurata?ko wannan dalilin ya sanya baby ta sauya masa? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un,yaya zai yi da zuciyarsa yanzu?tayaya zai cire son Nihila?wacce mace zai samu wacce zartai replaced ɗinta a zuciyarsa?runtsa idanunsa yay da ƙarfi yana jin duniyar na juya masa,gaba ɗaya ya rasa amsar da zai bawa Abbou daya tattaro wata maganar zai faɗa sai ta ƙwance masa, Mameey ce ta zauna kusa da Abbou tace "kayi hqr Jafar,munsan cewa bamu ƙyauta ba,kuma zaka dinga kallonmu a masu son kansu ko ƴar ƴarn su,dakai da Jalal duk ɗaya kuke garemu babu bambanci,amma damu dakai dashi kansa Jalal ɗin babu yadda muka iya,shi kansa ba'a son ransa ba,amma mahaifiyar yarinyar ita ta buƙaci haka da kanta,kuma bamuyi haka da cin ZARAFIn ka ba"kansa ya shiga girgiza wa kafin a hankali ya shiga faɗin "babu komai Abbou,dani da Jalal duk ɗaya ne,zan iya mallakasa masa abinda na mallaka kamar yadda nake da tabbacin zai iya mallaka min abinda yake dashi koda ban nema ba,kuma daman Ubangiji ya ƙaddara ba matata mace,matar mutum kabarinsa, Allah yasa albarka ya masu zama lafiya da zuri'a masu albarka"gaba ɗaya suka amsa da "ameen"kana Abbou ya ɗura da faɗin "Nagode sosai Jafar, Allah yay maka albarka kaima ya haɗaka da mace ta gari wacce tafi baby"kasa amsawa yay sai mikeway da yay zai fita Mameey tace "a'a ka tsaya kayi breakfast mana"girgiza kai yay yace "I'm not hungry Mameey,zanje daman unguwa ne shine na fara zuwa nan,bari naje sai goben"Mameey tace "to Allah ya tsaye kuma ya kaimu goben"da Ameen ya amsa bai tsaya jin abinda zasu ƙara faɗa ba ya fita,tunda gabar gidan yake zagaye a motarsa yay tunani harya gaji yama rasa wacce mafita zai sabawa kansa,bai taɓa tunanin abin zai kasance ba,ya gama sakar jiki zai mallaki baby ashe Abun na haka yake ba,daman ance matar mutum kabarinsa, Jalilerh kam abun Duniya yake mata zafi idan ta tuna maganar Abbou cewa Aryan ne zai aure ta hankalinta tashi yake,gefe na zuciyarta ga wani sabon abinda ta keji game da Uncle ɗinta,yanzo haka bata taɓa yarda ta haɗu dashi,duk sanda ta ganshi gabanta ya dinga faɗuwa kenan,ta rasa nutsuwar ta,hankalin ta ya tashi,musamman shima idan ta tuna baby zai aura,takan shiga ɗaki taita kuka kamar ranta zai fita,Birnin nufar Jabir ne akan tattausan carpet sai Zulfa dake ƙwance ya ɗura kanta saman cinyarsa yana ta mata addu'a,sai ihu take tana zabura take kiran sunan Hubby,tunda suke da ita banda lokacin da bakinta ya buɗe tace sunanta Zulfa,babu abinda take iya faɗa sai ya jabbaru ya rahamanu,sai kuma yau da bakinta ya fara furta Hubby,yasan hakan na nufin bai yanar abu da dama,kuma kullum cikin addu'a yake,abu guda ke damunsa,yadda zata ɗauki teddy ta rungome tai ta kuka ko kuma tace zata fito da brest ɗin ta ta bashi,sai kuma yawan jinin da take zubarwa ga wani zazzafan zazzaɓi dake damunta kullum, lokacin da yaji labarin zaɓen su Jalal da kuma samun nasarar sa sosai yay murna, Abba Papa ya ƙwance wayarsa koda wasa yaƙi bashi bai son kuma dalilin hakan ba, ɓangaren Papa kuma uwa sundu ce ta sanya shi yin haka,ya rasa yaya zai yi idan yace zashi Ibadan ba lalle ya samu ganawa da Jalal ba, musamman yanzu daya samu babban matsayi ganinsa zai wahala,idan kuma ya tafi wa zai barwa Zulfa, Papa ya hana kowa zuwa inda take bare har yay tunanin bada riƙon ta zuwa wajan wani har yaje ya dawo,hatta Katarina Papa ya hanata zuwa wajan Zulfa,shi yake mata komai,dalilin hakan yaso Papa ya sahale masa auran Zulfa,amma yaƙi,yana jin baƙin cikin yadda yake samun kusanci da ita,amma yasan bashi da nufi tunda taimako yaya kuma baiyi da wata niyyar ba, Joshua ne zaune gaban Uwa sundu tana sauraran abin yake faɗa, "Allah ya taimaki Uwa sundu, Uwar mu maganin kukanmu,kiyi min izini naje neman wancan yaron da kaina,nasan zuwa yanzu ya girma,shekara wajan huɗu ai ba wasa bace,na gaji gashi har watan haɗa aure ya kusa kamawa"dry Uwa sundu ta ƙyaƙyace da ita,sai da tayi mai isar ta kafin tace "wannan aiki nane,na kira aljanun da suka shiga jikinta domin su azallata ta dawo garemu,amma sun ƙasa sbd wahalar da wanda take tare dashi yake bata,shiyasa nima na fara lalata masa tasa rayuwar ta hanyar amfani da mazantakarsa,amma maganarka ta sanya naji ina son tura mata da wasu baƙaƙen ALJANU wanda zasu tunzaruta su ɗaga mata hankali taji babu inda take son zuwa sai wannan birnin nawa,a kuma lokacin zamu samu damar haɗaka da ita domin ka amshi budurcinta.dukkan abinda aka sanya rana babu shakka zaizo sai dai idan ba'a sanya masa ba,kamar yau Deen yaci zaɓe gashi yau ake shirin rantsar dashi a matsayin Governor Ibadan,harabar gidan gwamnatin cike da dubban jama'a baƙi da kuma na cikin garin,kowa ka gani yasha sabbin kaya,wasu ma kallar tutar jam'iyyar suka sanya a jikinsu,su Abbou suna can cikin bayan baƙi kowa yasha ado cikin sabbin kaya masu tsadar gske, Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo kowa yana zana saman wata lafiyayyiyar kujera,gabansa da bayansa wasu sabbin securities kuma manya wanda gwamnatin garin ta turosu,sanye yake cikin wata jumper fara tass mai manyan zane, ya ɗura wata baƙar hula a saman sumarsa,ga farin bluetooth daya maƙala cikin kunnansa,yay wani ƙyau na musamman,amma ya faɗa idanunsa sun janye sbd masifar daya tsinci kansa ciki, yanzu haka ma azumi yake,taro yay taro baka ganin komai sai securities da ƙarar jiniya,su Mameey na can ɓangaren manyan baƙi na mata ita da Nihila wacce tasha ado cikin wani Maroon ɗin lace, Jalilerh kama cewa bata jin daɗi, Jalal bai san bata zo wajan ba, a hankali Jalal ya miƙe tsaye sbd umarnin da Cheap joji ya bashi,kana ya riƙe Alkur'anin a aka mashi,cikin harshen turanci Cheap joji ya umarce Jalal ya dinga maimaita abinda zai faɗa,tsaiwarsa ya gyara tare da lumshe idanunsa yana fesar da iska ta cikin bakinsa,kafin ya ware idanunsa ya sauke saman dubban jama'ar da suke sauraransa, idanunsa ya mayar ya rufe kafin ya buɗe bakinsa cikin wani wata iriyar murya mai daɗin sauraran ji yace "Ni Dr Muhammad Jalal Kabeer bobo nayi al'ƙawarin kare haƙƙin al'ummar da kuma kula da dokiyoyinsu cikin yadda da aminci,na rantse da Alkur'ani mai girma zanyi aiki tsakani da Allah kamar yadda na ƙudiri niyyar yi, zanyi mulki cikin ja..ja.",shiru yay sabida kasa faɗar kallamar da yay,a Cheap joji yay magana ba tare da kowa yaji mai yace bai ba,kallonsa Jalal sbd still kalmar bata zauna bakinsa ba,sai da Cheap joji ya ƙara faɗin JAJIRCEWA, lumshe idanunsa kana ya buɗe su ya saita bakinsa saman speaker yace...
*Nimcyluv*
7/22/21, 8:02 AM - Buhainat: _96-97_
Zanyi mulki cikin jajircewa da kuma zaƙwaƙuranci,nayi al'ƙawari da littafin Ubangiji cewa babu wani rai da zanci ZARAFI ko kuma na tauye masa haƙƙinsa,nayi al'ƙawari kuma zancika alfarmar Annabi da Kur'ani"gaba ɗaya wajan aka sanya tafi wasu kuma sukayi kabbara, lumshe idanunsa yay yana jin wani mai girma ya hau kansa,yasan rantsuwarsa bazai taɓa sanyawa yaci abinda yay al'ƙawari ba,sai dai kawai ya roƙi Ubangiji akan ya taimake sa,ya bashi ikon cika al'ƙawarin daya ɗauka akan talakawan sa, Cheap joji ne ya amshi Kur'ani ya miƙawa wani,kana ya rataya wa Jalal wani abu a wuya daga nan aka shiga ɗaukan photonan,gidan TV kuma suka shiga ɗaukan vedio,gidan redio kuma suka shiga ɗanar recording na abinda ake,bayan nan wajan bawa Jalal key ɗin office a tafi,sabbin securities,sabbin motocin,sabbin ma'aikata,sabon gida a cikin gidan gwamnati,sosai akai shagali,kana taro ya watse su Abbou suka dawo gida cike da farin ciki,hakama Jafar da ƴan Uku zana dawowa gida aka fara shirin dinner ɗin da Jafar ya shirya domin taya Jalal murna,sai dare za'a gabatar da dinner ɗin a babban event, shirye-shirye su Mameey suka fara, shigowar ta kenan ta samu Laure ita da Mama da kuma sauran mutane da suka zo tayasu murna,suna zaune sai cin abinci take, Mameey ta kalli Laure tace "Jalilerh ta sauko kowa?"Laure tace "wlh hajia bata sauko ba,sau biyu ina zuwa dubata sai naga ƙofar a rufe"kafin Mameey tai magana Mama tayi saurin faɗin "mu dai har yanzu bamu gama sanin zuciyar yarinyar nan ba,banda baƙin ciki yarinyar ƙirmishishi kije wannan taron nan amma ta murzawa idanunta toka, meye wannan da tayi?yaya sunansa? a'a wlh baƙin ciki kawai takewa Jalalu,yaro ɗan marayan Allah ya ɗauki rimi² domin gyara gobenki,amma ki watsa masa ƙasa a idonu,to Wlh nidai babu ruwana,idan ba baƙin ciki take gwamma musani tun yanzu ko ba haka ba?"Mameey tace "ayyya ba haka bace Mama,kinsan bata jin daɗi ne shiyasa"wani kallo taiwa Mameey sheƙeƙe kafin ta yatsuna fuskarta tace "au haba?" Mameey tace "eh wlh,sai amai take ga zazzaɓi" nama ta tura a bakinta kafin ta haɗiye da ƙyar tace "banda kema kin zama sallamammiya ina ke ina biyewa wannan Salamatu?wlh fita a idona tun tuni na rufe,yanzo dan waye ya kejin daɗi a wannan rayuwar ta yauma ta komu? to ai shikenan nan tunda kema kin zama sakarya,yarinya baƙin hali fal zuciya,ga shegu aljanu irin na gado kai ita dai abu goma da ashirin,bai laifi kuma tana da ƙyau abinta shiru² da ita gwanin sha'awa,to waya sani ko ƙyan ɗan maciji ne?"ita Mameey ba tace komai ba ganin abin na Mama ya fara zama shiririta yasa ta haura sama tana ƙunshe dryar dake cinta,da wani kallo Mama ta bita kafin ta juyo wajan wata ƙawarta tun ta yarinta tace "to ga ta nan dai Asabe,kinga tun daga haihuwar ƴan ukun nan shikenan haihuwar ya tsaya,kila juya da Za'ai sai Allah ya taimaka" tsohuwar da aka kira da Asabe ta ajjiye ƙashin da take ta faman tsotsa tace "na sai wani kallon tara saura take mana ai.." Mama ta miƙe tsaye tace "a'a wlh kedai anyi natsoraciya,me yasa baki gayan ba sai da ta tafi,nidai banji daɗi ba,meye nata da zata yi maki harara?bayan itama aurota a kai,ai anjima ƴan uwanta zaso sauka akan su zan rama maki" haka dai sukaci gaba da surutai irin nasu na rikitattun tsofaffi,kafin su sanya Laure ta kawo masu farfesun kan ragon da akai, Mameey na shiga part ɗin su Jalilerh ta tura ƙofar a hankali,a ƙwance ta sameta ta kifa kanta cikin pillow tana sauke ajjiyar zuciya,jin alamun mutun yasa tayi saurin ɓoye photon Jalal dake hannunta,kana tai lamo kamar mai bacci, ƙarasawa cikin bedroom ɗin Mameey tayi tace "daughter har yanzo jikin ne?"shiru Jalilerh tai mata tai kamar bacci take, ganin haka yasa Mameey taja mata ƙofar ta,tana fita Jalilerh ta sauke ajjiyar zuciya tare da lumshe idanunta wasu hawaye Masu zafi suka shiga fita daga cikin idanunta,a hankali kuma ta zaro