Showing 66001 words to 69000 words out of 120090 words

Chapter 23 - UNCLE NE Complete

Unknown   

11 Nov 2024

5839

numfashi ya sauke kafin yace "jeki ƙwanta" turo baki tayi tace "to baka daɗi yadda ake tsarkin ba..




Uncle ne isn't free is for sale just pay it before you read asusun biya 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616





By
NIMCYLUV
6/30/21, 7:12 PM - Buhainat: UCL NE

70-71




Hancinta yaja yace "ni ban iya ba to"duk da baccin dake cinta bai hana tayi dry ba cikin siririyar muryarta tace "Allah Uncle ka iya,ai komai kai ka iya kafi kowa" baice mata komai ba sai lips ɗinta da ya tsorawa idanu yana kallon yadda ta jiƙasu da yawo sai mutsawa suke a hankali, ɗauke kansa yay yace "A taƙaice TSARKI kashi biyu ne,Hadasi da Kabasi amma zan buɗa maki bayanin yadda zaifi, hope zaiki fahimta?" Kanta dake saman ƙirjinsa ta ɗaga alamar "eh" shafa sumar kanta yay shima yace "good" kana yay shuru yana tunanin irin duguwar maganar da zaiyi a wannan daren, ajjiyar zcya ya sauke kafin ya ɗura da faɗin.


Ma’anar Tsarki
Ma’anar Tsarki A Larabci.
Tsafta Da Tsarkaka Daga Kazanta

Ma’anar Tsarki A shari’a
Kawar da kari da gusar da Najasa

Kashe � Kashen Tsarki

1- Tsarki Na Voye
Shi ne tsarkake zuciya daga shirka da sabo, da duk wani abin da yake bata zuciya, babu yadda tsarki zai tabbata matukar akwai shirka a cikin zuciya, kamar yadda Allah ya ce, “Yaku wadanda suka yi imani ku sani cewa Mushirikai najasa ne, kada su kusanci masallaci mai alfarma daga wannan shekarar, idan kuna jin tsoron talauci to da sannu Allah zai azurta ku daga falalarsa in ya so. Haqiqa Allah Masani ne Mai hikima.� (At-Tauba : 28).

Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya ce, “Mumini ba ya zama najasa�. [ Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi]

2- Tsarki Na Zahiri
Shi ne tsarkake jiki daga abubuwan da suke warware alwala da najasa, ya kasu gida biyu :

1- Tsarkin Kari
Kari shi ne : Abin da yake hana mutum yin ibadar da aka sharxanta tsarki a cikinta, kamar sallah, dawafi da waninsu. Kari ya kasu kashi biyu :


Kari yana hana yin sallah.
- Qaramin Kari

Shi ne wanda yake wajabta yin alwala, kamar fitsari da kashi da sauran abubuwan da suke warware alwala. Tsarki daga kari yana samuwa ne ta hanyar alwala.

Allah ya ce, “Yaku waxanda kuka yi imani idan kun tashi za ku yi sallah, to ku wanke fuskokinku da hannayenku zuwa gwiwar hannu, ku shafi kawunanku ku wanke kafafunku zuwa idon sawu� (Al-ma’ida :6).


Alwala tsarki ce daga qaramin kari
- Babban Kari

Shi ne wanda yake wajabta wanka, kamar janaba, haila, da wanin haka, ana tsarkaka daga gare shi ta hanyar wanka.

Allah ya ce, “Idan kuna da janaba to ku yi tsarki� (Al-ma’ida : 6).


Tsrkin jiki
2- Tsarkaka Daga Najasa
Gusar da najasa wajibi ne, saboda faxin Allah Maxaukakin Sarki “Ka tsarkake tufafinka� (Al-Muddassir 4).

Da faxin Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) “Mafi yawancin azabar qabari daga rashin yin tsarki ne idan an yi fitsari�. [ Ibn Majah ne ya rawaito shi]

Da faxinsa ( صلى الله عليه وسلم ) “Idan xayanku ya zo masallaci to ya duba takalmansa, idan ya ga qazanta ko najasa to ya goge, sannan ya yi sallah da su�. [ Abu Dawud ne ya rawaito shi]


Tsarkin jiki

Tsarkin wurin sallah

Tsarkin tufafi
Kashe-Kashen Ruwa

Na farko : Ruwa Mai Tsarki
Shi ne ruwan da najasa ba ta canza kamaninsa, ko xanxanonsa ko qanshinsa ba, kamar:

1- Ruwa Tsantsa
Shi ne ruwan da yake akan siffar shi da aka halicce shi da ita, kamar ruwan sama, ko qanqara, ko rava, ko kuma wanda yake gudu ne a bayan qasa, kamar ruwan teku, da qoramu da na sama, da rijiya. Allah Maxaukakin Sarki ya ce, “Mun saukar da ruwa mai tsarki daga sama� (AlFurqan : 48)

Allah Maxaukakin Sarki ya ce, “Yana saukar muku da ruwa daga sama don ya tsarkake ku da shi� (Al-anfal : 11)

Hakanan Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) yana addu’a yana cewa: “Ya Allah ka wanke ni daga zunubaina da rava da ruwa da qanqara[ Qanqara: Ita ce qanqarar da take zuba ya yin saurkar ruwan sama.]�. [ Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi]

Manzon Allah ya ce dangane da ruwan teku “Shi ruwa ne mai tsarki, kuma mushensa halal ne�. [ Ahmad da Abu Dawud ne suka rawaito shi].

Numfashi ya sauke,bayan ya gama dugun bayani akan tsarki,a hankali kuma ya leƙa fuskarta, murmushi ya saki sbd fararan idanunta daya hango suna juyawa alamar dai tana fahimtar zancen sa,gyara kwanciyarsa yay a saman kujerar kafin ya lumshe idanunsa yana sauraran bugun zcyarsa dake fita da sauri da sauri,cikin ƙasa da murya kuma yace "sai kuma bayani akan WANKA en matan Uncle" ɓoye fuskarta tayi a jikinsa tana sakin wani sound "uhm...uhm"cije lips ɗinsa kawai yay kana yace "shima wanka kashi-kashi ne a musulunce,WANKA ya kasu kashi BIYAR sune WANKAN HAIHUWA,WANKAN JANABA,WANKAN JUMA'A,WANKAN SHIGA MAKKAH,WANKAN MUTUWA"
shuru yay yana nazartar ta ya faɗa mata ko kuma ya rabu da ita,domin baya so ya faɗi abinda zata zo tana masa surutu akai,sai dai kuma maganar addini babu kunya ko ɓoye wani abu,domin shekarunta sunkai tasan komai, pouting lips ɗinsa yayi kafin yace.

Ma’anar kalmar "wanka" a larabci
Game abu da ruwa,
Wanka a Shari’ance
Shi ne gama jiki gabaxayansa da ruwa, a kan wata siffa kevantacciya, da niyyar bautawa Allah Mai tsarki
Abubuwan Da Suke Wajabta Wanka
1- Fitar Maniyyi
Maniyyi wani ruwa ne fari mai kauri, wanda yake fita tare da jin daxi, yana tunkuxar juna yayin fitowa, mutuwar jiki tana biyo bayan fitarsa, yana wari irin warin bara-gurbin qwai.
Allah Madaukakin Sarki ya ce, “Idan kun kasance kuna da janaba to ku yi wanka� (Alma’ida : 6)
da faɗin Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ga Aliyyu : “Idan ka fitar da ruwa to ka yi wanka� [Abu Dawud ne ya rawaito shi].
Fitar da ruwa ana nufin fitar maniyyi...,"da sauri Jalilerh ta É—aga ta kallesa,bai kalleta ba ya haÉ—e rai hakan yasa dole ta maida kanta taci gaba da sauran sa.
Yace "misali shine

1- Idan mutum ya yi mafarki amma bai fitar da maniyyi ba, to babu wanka a kanshi, idan kuwa maniyyin ya fito bayan ya farka daga barcin to wajibi ne ya yi wanka.

2- Idan ya ga maniyyi, amma bai iya tuna yaushe ya yi mafarki ba, to wanka ya wajaba a kanshi saboda fitar maniyyin. Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya ce, “Ana tava ruwa ne saboda fitar ruwa� [ Muslim ne ya rawaito shi] Ma'ana ana yin wanka ne don fitar maniyyi.

3- Idan ya ji alamar zuwan maniyyi daga gabansa, amma bai fito ba, to babu wanka a kanshi.

4- Idan maniyyi ya fito saboda wani dalili ko rashin lafiya ba tare da sha'awa ba, to babu wanka a kanshi.

5- Idan mutum yana janaba ya yi wanka, sai kuma maniyyi ya fito bayan ya gama wankan, to ba sai ya sake wankan ba, saboda yawanci yakan fito ne ba tare da sha'awa ba, amma abin da ya fi ya yi alwala.

6- Idan mai barci ya farka, ya ji danshi a jikinsa, amma bai san dalilin zuwanta ba, to xayan abu uku ne :

A) Ya tabbatar da wannan danshin maniyyi ne, to wanka ya tabbata a gareshi, ya tuna ya yi mafarki ko bai tuna ba.

B) Ya tabbatar wannan danshin ba maniyyi ba ne, to wanka bai wajaba a kanshi ba, hukuncinsa hukuncin fitsari ne, sai ya wanke)

C) Ya yi shakka, maniyyi ne ko ba shi ba ne? To a nan wajibi ne a kanshi ya yi kirdado, idan ya tuna abin da zai nuna masa cewa wannan danshin maniyyi ne, to ya bar shi a kan maniyyi ne. in kuma ya tuna abin da zai nuna masa cewa maziyyi ne, to maziyyin ne, in kuma ya kasa tuna komai, to sai ya yi wanka don fita daga savani da ruxu.

7- Idan ya ga maniyyi, amma bai tuna yaushe ya yi mafarkinsa ba, to wanka ya wajaba a kanshi, ya kuma sake dukkan sallar da ya yi bayan tashinsa daga barcinsa na qarshe.

2- Saduwa (Jima’i)
Shi ne haɗuwar gaban namiji da na mace, wato shigar kan gaban namiji zaya sanya cikin farjin mace, ko da kuwa bai zubar da maniyyi ba, saboda faɗin Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم )“Idan kaciyar (namiji) ta shige kaciyar (Mace) to wanka ya wajaba� [Tirmizi ne ya rawaito shi].

3- Musuluntar Kafiri
Saboda “Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya umarci Qaisu ɗan Asim ya yi wanka lokacin da ya musulunta� [Abu Dawud ne ya rawaito shi]

4- É—ukewar Jinin Haila Da Na Biqi
Saboda hadisin Aisha cewa Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya cewa Faɗimatu ‘yar Abi Hubaish “Idan al’adarki ta zo, ki bar sallah, idan ya wuce ki yi wanka ki yi sallah� [Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi].

Hukuncin jinin biqi kamar hukuncin jinin haila ne da ijma’in malamai.

5- Mutuwa
Saboda faɗin Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) a hadisin wanke ‘yarsa Zainab lokacin da ta rasu ya ce,“Ku wanketa sau uku, ko sau biyar, ko fiye da haka, in kun ga akwai buqatar hakan� [ Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi].

Yadda Ake Yin Wanka
Abin da yake wajibi a wajen wanka shi ne gama jiki gaba É—ayansa da ruwa, tare da yin niyya, koma yaya ya yi shi.

Sai dai abin da aka fi so ya yi koyi da siffar wankan Annabi ( صلى الله عليه وسلم ), kamar yadda uwar muminai Maimunatu ta siffanta shi, ta ce, “Manzon Allah ( صلى الله عليه وسلم ) ya sanya ruwa don yin wankan janaba, sai ya karkato abin ruwan da hannun damansa a kan hagunsa ya wanke hannayensa sau biyu ko sau uku, sannan ya wanke gabansa, sai ya doki qasa ko bango da hannunsa sau biyu ko sau uku, sannan sai ya yi kurkurar baki ya shaqa ruwa, ya wanke fuskarsa da sangalin hannunsa, sannan ya kwara ruwa a kansa, sai ya wanke jikinsa, sannan ya matsa gefe guda ya wanke qafafunsa. Nana Maimunatu ta ce, “Sai na kawo masa wani qyalle (hankici) amma bai karɓa ba, sai ya riqa share ruwan da hannunsa� [Bukhari ne ya rawaito shi].

- Yadda ake wankan a taqaice shi ne :

1- Zai wanke tafukan hannayensa sau biyu ko sau uku.

2- Zai wanke gabansa

3- zai doki qasa ko bango da hannu sau biyu ko sau uku.

4- Sai ya yi alwala irin ta sallah, ba tare da shafar kai da kunne ba.

5- Zai kwara ruwa a kansa

6- Zai wanke jikinsa gaba xaya.

7- Zai koma gefe ya wanke qafafunsa.

Bayan ya kammala ya sauke wata wahalalliyar ajjiyar zcya tare da jan numfashi yace "kinji wanan" shuru yaji sai kuma yaji saukar numfashinta mai zafi a saman ƙirjinsa, leƙawa yay yaga tuni bacci ya ɗauke ta,waro idanunsa yay da mamaki yana addu'ar Allah yasa dai duk taji me yace bai wahalar banza ba, miƙewa yay da ita a jikinsa tare da ficewa daga ɗakin,kai tsaye parlour ya nufa,a zaune ya samu Mama tana cin soyayyan nama da kuma lemo,kallo guda yay mata,ita kam baki ta saki tare da rafka salati tace "me zan gani yau?wai ɓatan nono a ƙirjin budurwa,zabgegiyar budurwa ka ɗauka kamar yarinyar goye,maza maza sauketa na gani"haɗe rai yay kafin yace mata "hannunki ne?" Cikin ƙufula tace "to sallamamme yimin rashin kunya,da matarka ka ɗauka ma da sauƙi" waro idanunsa yayi waje kafin yace "ok bari na ajjiye ta na ɗauke ki" zama tayi saman kujera tare da fasa kuka tace "wlh ba hali na ka ɗauka ba sai dai na dangin ubanka,amma tirrrr da mummunan hali irin wannan yanzu ni zaka ɗauka Jalalu?" Mummy dake saman upstairs ta danne dryar dake cinta kafin tace "Bobo maza jeka ƙwantar da ita kazo ka shige ka bamu waje" baice komai ba ya haura upstairs ɗin,yana zuwa ya nufi part ɗin su,babu wani haske ɗakin sai wani light blue bed ɗin ta ya nufa ya ƙwantar da ita,kana ya zare nata hijab tare da gyara mata kwanciyar, jikinsa yazo zamewa tayi sauri riƙesa tare da turo baki gaba,kai kawai ya girgiza ya ɗauki ƙaramin pillow ya saka mata da sauri ta rungome pillow,sosai yay mamaki yadda tasan daɗin jiki gashi shi duk lokacin da suka ɓata babu abinda yaji a kanta,tsaki yaja kana ya tofa mata addu'a ya rufeta da duvet,wajan Nihila ya ƙarasa tana jin zuwansa tayi saurin rufe idanunta,ba tare da wani tunani ba,itama yay mata addu'a kana ya bata light kiss a saman goshinta ya gyara mata kwanciya, remote ya ɗauka ya ƙaro masu gudun a.c kafin yaja Ƙofar ya rufe,da idanu ta bisa harya fice daga ɗakin kafin ta juya ta kalli Jalilerh wacce take bacci cikin nutsuwa ta rungume pillow,rufe idanunta tayi a haka bacci itama ya ɗauke ta ta.



Washegari,tun safe Jalal yabar gida sbd saura ƙwana guda Election,kusan a office ya ƙare yininsa,daga Wannan mutane suzo sai wannan suzo,haka yayta manyan baƙi wasu kuɗin compaign,wasu kuma abubuwan zaɓe suke karɓa, Jafar kuma yana can shida Prince Hassan suna ta shiga local government da ƙauyika, Abbou ma ba'a barsa a baya ba dukkan abinda yake gani zai taiamy ɗan nasa dashi shi yake, kuɗi kowa ya fitar babu adadi,haka Irfan Imran kowa da nasa ɓangaren, Mummy da Mameey suma a gida sukai taran mata aka cika sosai yadda Hajiya Atine, Aryan kam yana ɗaki abinda yana sharar bacci sabida bashi da matsala da wani zaɓe a cewarsa, Governor Mubarak Yahya cibo hankalinsu ƙwance yake shida masu mara masa baya da kuma Lamir,domin sun tabbatar a wannan karan plan ɗinsu bazai taɓa barin Dr/Muhammad Jalal Kabeer bobo ba,Lamir ya ajjiye juice ɗin dake hannunsa yace "ai wlh da zarar an saki wannan vedio kare bazai iya binsa ba,badai sakarar ɗan uwan nasa na ɗura sa bisa hanya ba,to Tabbas nan da jimawa zance ya turo min da vedio'n ta whatsapp, mu kuma zamu sakesa matsayin breaking news kaga shi kenan mun tashi hankali jama'ar IBADAN,zamu sanya masu shakku da wasi-wasi a zuƙatansu,kasan mene zai faru ƙarshe?"gaba ɗaya suka ajjiye juice ɗin hannunsu suna kallonsa kafin Hon Faisal Lawan yace"wannan kitimurmurar ai naka ne,tayaya zamu sani?"dry Lamir yyi kafin ya tsuke bakinsa yace "daga ƙarshe hukumar inec za tace the election was cancelled"gaba ɗaya suka saka dry hadda riƙe ciki, Wani mutum a cikinsu wanda ake cewa Baba Tunde yace "kai Lamir you're so selfish,kai mugune exactly abinda nake imagine kenan" ya faɗa cikin gurɓtacciyar hausarsa,Hon Faisal Lawan yace "kaga ana haka za'a ƙara tabbatar da Ur excellence a matsayin cikakken Gwamnan jihar Ibadan" gyaran murya Governor Mubarak Yahya cibo irin a dole yama riga daya zama Governor lokacin kawai yake jira,yace "idan harshashenmu ya zama gaskiya kowa ni kaɗai nasan me zan maku,albashin na kune,zan dauwama ina maku hidima,and tuggun farko da Jalal zai fuskanta rabashi da wannan ƙabilar da zanyi kuma saina tabbatar maku da magana ta gsky ce"
Jalal bai dawo gida ba sai wajan 12:30,a hankali drever yayi parking motarsa sai kuma motocin securities ɗinsa,yana parking wani security ya buɗe masa ƙofa,cikin nutsuwa yake tafiya hannunsa riƙe da babbar rigar sa daya cire a hanya,ya ɗan tura hular kansa baya,gaba ɗaya a gajiye yake bama gajiyar ke damunsa ba sai yadda yake yawon faɗuwar gaba wacce bai san menene dalilin afkuwarta ba,murya can ƙasa yay sallama, Mummy na ganinsa ta miƙe da sauri tare da amsar rigar hannunsa sai jera masa sannu take,da idanunsa kawai yake kallonta ya kasa cewa komai, ɓata fuska tai tamkar zatai kuka tace "wanne irin abune wannan wai?ace tun safe daga fita sai yanzu?ina da tabbacin ko abinci baka ci ba" ta faɗa tana ɗura hannunta a cikinsa,zaro idanu waje tayi kafin tace "what ina zuwa zauna a parlour ka jirani" Mama ta amshe zan can da faɗin "ke kuma saiki kama gabanki tunda ya dawo,algugguma ka ganta nan ta hana ranta sakat sbd baka dawo gidan ba,daga ƙarshe ma kuka ta sawa Mutane"ta ƙare maganar tana nuna Jalilerh wacce take tsaye tun shigowar sa,yana da inda Mummy ta ajjiye sa ya ɗaga gajiyayyun idanunsa ya sauke a kanta,cikin Sa'a suka haɗa ido,da sauri ta janye nata idanun kana ta haura upstairs tana goge hawayen idanunta, idanunsa yaja ya rufe ba tare da yace wani abun ba,kallonsa Mama tayi tace "to Mijin yaya ake ciki ne yanzu?" Shuru yay mata dan baya jin zai iya mata amsa,dan ko yawon dazai haɗiya a bakinsa babu,yana nan zaune Mummy ta fito daga kitchen hannunta riƙe da wani babban tray,tana zuwa ta ajjiye saman carpet kana ta kallesa tace "sauko ƙasa" bai mata musu ba ya sakko yana sakkowar ya zame rigar dake jikinsa,ya rage sai farar singlet a jikinsa,dugwayen ƙafafunsa ya miƙe har ƙarar gajiya sukai,duk abinda yake akan idanun Mummy sosai take tausayin ɗan nata musamman yau,tasan dukkan abinda daza ta basa a yanzu ba lalle yaci ba,dambun shinkafa wanda yaji zugale da gyaɗa da kuma manyan albasa,yasha kayan ƙamshi da zallar hanta ta zuba masa a plat,sai kunun gyaɗa mai zafi da zuba masa madara kana ta haɗa masa mug,sai kuma ƙwaɗon zugala data haɗa masa yasha tomato da albasa da kuma ƙwai,da haɗaɗɗan ƙuli,gaba ɗaya ta jere masa a gabansa,kamar yaro haka Jalal ya kwaɓe fuska tare da langwaɓar da kansa gefe, cikin wata muryar sangarta yace "Mummy na gaji bacci" bata kulasa ba taja ƙafarsa ta ɗura saman cinyarta ta fara matsa masa su tare daja masa yatsun ƙafarsa,zuro Mama tayi masu da idanu,domin a wannan lokacin tunanin mahaifiyar Jalal ne fal a Zcyarta,ko tana raye ko babu uhhhu,bayan Mummy ta matsa masa ƙafar ta miƙe tsaye tare da faɗin "bari na kira daughter, ƙilan taci abinci yanzu" harya buɗe baki zai magana sai kuma yay shuru sbd wayarsa da yaji tana ringing,kallon makeken screen ɗin wayar yay yana sunan Jabir na yawo akai yay,rasa waye Jabir yay har wayar ta yanke yana kallon screen ɗin,a haka wani kiran ya shigo, ɗauke kai yay tare da ɗaukan spoon ya fara cin ƙwaɗon zugalan a hankali,yana zaune Aryan ya fito da sauri daga part ɗinsu yay waje,da sauri Aryan ya buɗe wayarsa da tun ɗazo take a rufe,yanzu haka yazo buɗewa wane domin ya tura wasu photona da vedio'n,fuskarsa fal farin ciki ya buɗe wayar sai dai abin

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login