Showing 87001 words to 90000 words out of 120090 words
ciwon ya fara cin ƙarfinta,ga wani amai dake taso mata haɗe da ciwon kai zazzaɓi duk lokaci guda,duk abinda take a kan idanunsa yana zaune yana shan tea hankali ƙwance time to time yana lumshe idanunsa,amma idanunsa ko mutsawa basayi a kanta, lokaci ɗaya kuma ya fahimci abinda ke damunta,ganin bata da niyyar miƙewa ga kukan dake cin ƙarfinta,yasa ya sakko daga saman stool tare da ajjiye cup ɗin wajan sink,kai tsaye wajanta ya nufa yana tafe a hankali sbd bai son taka wani abu ko taka hannunta sbd ba sosai yake ganin komai na kitchen ɗin ba,a haka harya ƙarasa zuwa inda take,fesar da numfashi yay tare da sunkuyawa yasa duk hannayensa biyun ya ɗagota sosai ta tsorata zata saki ihu yay saurin saka hannu ya toshe mata baki, tura ta ya dingayi har zuwa jikin bango kafin ya haɗata da jikin bangon ya ɗan ranƙwafo dai-dai fuskarta yana leƙawa, bakinta kawai yake iya gani suma dalilin jan da sukai ga kuma hawaye da yawon da suka jiƙasa,ita dai Jalilerh sai leƙa fuskarsa take amma ta kasa ganin ko waye sbd duhu ga kuma wani a zaɓaɓɓen ciwo dake cinta hakan yasa ta ƙara sakin wani kukan tana zabewa zata faɗi yay saurin haɗata da jikinsa a tare suka sauke ajjiyar zcya mai ƙarfi,da sauri Nihila wacce take bakin kitchen ɗin ta juya idanunta cike da hawaye,shiru gaba ɗaya sukai sai Jalilerh dake sauke ajjiyar zcy,a hankali kuma ya dinga bubbuga bayanta yana shafa ƙwantaccen gashin kanta,a hankali kuma ta dingani ciwon na sauka sai wani gumi daya dinga sakko mata, idanunsa ya sauke a red lips ɗinsa kafin a hankali kuma ya ƙarasa kusanta bakinsa da nata ya ɗan lumshe idanunsa cikin ɗaukewar numfashi ya sauke lips ɗinsa saman nata kafin ya bata wani special hurt kiss a gefen lips ɗinta,kana ya juya da sauri yabar kitchen ɗin,yana fita ya samu Aryan a parlour ko kallansa bai ba ya ƙarasa shigewa part ɗinta, Aryan kuma kitchen ɗin ya shiga yana shiga yaji bugi abu da sauri kuma yasa hannu ya kunna hasken kitchen ɗin,tsaye ya ganta kanta a ƙasa, ƙarasawa yay inda take tsayen tare da leƙa fuskarta ganin hawaye ƙwance saman fuskarta yasa shi faɗin "Hubby...!!"saurin ɗago kai tayi yayinda zcyarta ta buga da ƙarfi,zallar tsoro ya bai yana a Zcyarta tunaninta shine badai Aryan shine ya rungome ta ba?to idan ba shi bane waye? Tabbas shine tunda gashi taji muryarsa kuma shi ta gani tsaye,to mene yake cikin kitchen ɗin?ganin tai shiru tana kallonsa yasa yace "what wrong?" Nan ma shiru tai masa hannu ya miƙa zai riƙe ta tayi sauri matsawa baya tana girgiza kanta,kallon fararan kayan baccin dake jikinta yay sai kuma ya ɗauke kai tace "You are Staired" da sauri ta kalli jikin ta sai kuma tai waje da gudu bayanta yabi da kallo yana sauke ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya. washegari kamar yadda aka buƙata Jalal ya shirya cikin wata jumper mai shegen ƙyau maroon color ya saka babbar rigar,sai Black hula da black covert shoe,hannunsa ya ɗaura agogon gucci ga farin bluetooth daya saka,da sauri ya ƙarasa fesa parfume ɗin hannunsa,kana ya ɗauki wayoyinsa ya riƙe,fita yay yana fita ya zamu Mameey ita ɗaya a main parlour kowa ya tafi wajan aiki dake Monday ce, Nihila kuma na makaranta Jalilerh na ɗaki tana bacci sbd bata jin daɗi, Abbou yana wajan masu karɓar gaisuwar da suka zo masa,kallon Mameey yay yace "Mameey I'm going,a gyaran part ɗina before I'm coming back" murmushin jin daɗi tayi ganin yay fesa kamar ango sai zabga ƙamshi yake,ga wata cikar zati haiba kwarjini daya ƙara fitowa saman fuskarsa,tace "in sha Allah, Allah ya tsare ya kiyaye" da Ameen ya amsa kana yay waje,yana fita securities suka rufa masa baya,wata lafiyayyiyar mota aka buɗe masa back seat ya zauna kana driver ya shiga,su kuma su shiga taso motar guda biyu,suka saka motar Jalal a tsakiya a hankali motocin suka fara barin gidan,da yammacin ranar Mubarak Yahya cibo ne zaune a gaban boka Saƙib yana sauraran abinda yake faɗa,boka Saƙib yaci gaba da faɗin "kayi kuskure domin abinda mukace ka aikata bashi kai ba,dole ne ka samu matsala akan zaɓen ka,dole ne kujerar tai rawa,kaci Sa'a kazo da wuri banda haka da bazan iya komai akai ba"da sauri Mubarak Yahya cibo yace "Ni dai burina kawai bai huce na Jalal a ƙasa ba, farin ciki na shi ne dukkan abinda ya sawa hannu a harkar mulkinsa ace ya lalace abun bai albarka ba,ai tasa masa ɓarnar kuɗi,idan har zai yiwu ma kawai a sa ya zama Mazinaci..
_End of book 2 Allhamdulillah ³, Allah yasa muga farkon book 3 lafiya,GAREKU masu karanta min littafi ƙyauta dan Allah ku daina,wannan gumi nane idan dole book ɗina kuke son karantawa ga MOON nan shi free book ne wanda nake typing ɗinsa yanzu, littafin UNCLE NE na kuɗi ne akan 300 vip kuma 600 asusun biya 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616 NIMCYLUV😍_
7/14/21, 4:40 PM - Buhainat: _UCL NE_
Book 3
_92-93_
_this is page 1 of book 3 and this is page 92-93 of UNCLE NE, ma sha Allah littafi ya ɗauko hanyar ƙare wa,ina sane da masu karanta min book ƙyauta bayan kun san na kuɗi ne,duk wannan bai daman ba,irin wanda suka siya suke fidda min amma ka ku damu,duk mai niyyar biyana 300 babu yawa 600 for vip account details 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 081192371616, Duk mace mai aji neman na kanta take kuma halal ɗinta, rashin daraja ne karɓar abin sata😂👌🏼_
Dariya boka Saƙib yayi har wani hayaƙi na fita ta cikin bakinsa,sai da yayi mai isar sa sannan ya tsoke bakinsa kamar bashi ne ya gama dryar ba, ƙasa ya buga ya fara zane a ƙasanta kana ya ɗago kai yace "an gama,amma bisa sharaɗi guda" da sauri Mubarak Yahya cibo yace "mene sharaɗin gaya min?" boka Saƙib yace "dole ne ka saka masa wannan maganin a inda yake zama,ko kuma kasa masa cikin takalmin sawarsa" Mubarak Yahya cibo ya kalli bokan kafin ya yace "Allah gafarta babu wata hanyar da za'a iya wannan aikin dole sai ni?" Boka Saƙib yace "ita kaɗai ce hanyar da buƙatar ka zata biya,da ace aƙwai wata hanyar da tuni na faɗa baka,kuma tunda ka amsa dole kayi,rashin aikata hakan babbar matsala ne kuma komai na iya faruwa dakai" Mubarak cibo yace "menene matsalar kuma?" Boka Saƙib ya ɗago jajayen idanunsa ya shiga kallon Mubarak cibo kamar wanda yake duba wani abu a jikinsa,chan kuma ya ɗauke idanunsa yace "bazan iya gaya maka matsalar ba,amma dai ya zama dole ka aikata wannan abun cikin kwanakin nan"jinjina kai kawai Mubarak cibo yay kafin yace "shkknan I'll do my best wajan ganin nayi aikin dai-dai"boka Saƙib yace "yawwa ɓatacce wanda ya yarda aikin boka yaƙi faɗar Allah"shi dai jinsa kawai yake domin idan da sabo ya saba da wannan surutan nasa, kuɗi masu yawan gaske ya ajjiye wa boka Saƙib kana ya fice daga cikin ɗan ƙaramin ɗakin bayan ya amshi maganin,nan ya tarar da mutane da yawa ɓatattu irinsa wanda suke jiran fitowar sa,kai tsaye gidansa ya nufa yana zuwa ya tarar da Hajja Ayushert zaune tayi ta gumi kallo guda zakai mata kasan cewa tana cikin damuwa,tana ganinsa ta miƙe tsaye fuskarta babu walwala tace "haba Alhaji wai mai kakeson zama ne?mai yasa mulki ya keson kaika lahira ne? Nina kasa fahimtar abinda kasa a gabanka,baka tunanin komai sai mulki,kamar dashi aka kawo ka duniya?gsky ka nemawa kanka mafita,nifa mulkin nan ya ishe ni kana ganin dalilin haka muka rasa ƴar mu ƙwaya ɗaya tak da muke da ita" tunda ta fara magana yake kallonta harta kawo ƙarshe,hannu ya ɗaga mata yace "yaushe kika zama uwata ban sani ba Ayushert?ko kuma ke kike Aure na bani nake naki ba?to wlh ki kiyaye ne, And mulkin nan ai bake nace kiyi ba,nine nake so kuma ni nake buƙata,ruwanki ki maramin baya ruwanki ne kiƙi i don't care,kuma ki fita a idona na gaya maki"yana faɗin hakan ya shige part ɗinsa da sauri,da kallo kawai ta bisa yana shigewa ta ɗauki wayarta ta shiga dailing number yayarta Hajja Saudat,tana shiga ta nemi waje ta zauna tare da faɗin "Assalamu alaiki" Saudat dake tare da babban ɗan ta Bashir tace "Wasalamu alaiki Hajja Ayushert" Hajja Ayushert tace "Yaya Saudat aƙwai matsala wlh,dan Allah kina gida ne?"hankalin Hajja Saudat a tashen tace "yasubuhanallah!, lafiya?meke faruwa dake?"cikin kuka Hajja Ayushert tace "Nidai Yaya ki gayamin idan kina gida yanzu zanzo" da sauri Hajja Saudat tace "eh ina gida sai kin ƙarasu"kashe wayar sukai a tare kafin Hajja Ayushert ta miƙe ta fara shiri.bayan sallar magrib Lamir yay sallama cikin gidan Mama ce zaune a parlour sai Jalilerh wacce take ƙwance ta lumshe idanunta tana jin muyarsa ta miƙe da sauri kamar zata kifa tai upstairs,da kallo kawai ya bita yana wani irin Murmushi yana gyara hular kanta, Mama kam tunda ta kansa ta ɗura ƙafa ɗaya kan ɗaya ta shiga girgiza wa,zama yay yace "ina yini Mama?"shiru tai masa ba tace masa komai ba,shima shiru yay mata bai ƙara magana ba,ana haka Jalal ya shigo cikin bakinsa ɗauke da sallama hannunsa riƙe da key ɗin motarsa,a hankali yake tafiya kamar bai son ɗaga ƙafarsa sbd gajiya,tun safe daya fita zuwa gidan gwamnati ana shirye-shiryen Rantsuwa dake saura ƙwana biyu kacal, idanunsa ya ɗan wara jin Muryar Lamir yana amsa masa sallamar,kallo guda Jalal yaywa Lamir ya ɗauke kansa kamar bazai magana sai kuma yace "ina yini?"Lamir na Murmushi yace "lafiya ina tayaka murna fa"kamar ancewa Jalal ya zauna haka ya samu kansa da zama a saman sofar dake kallon Lamir,saurin runtsa idanunsa yay sbd wani abu da yaji ya sari kansa a hankali yaji kansa na juyawa,cikin ransa ya dinga ambatar "La'ilaha illallah Muhammad Rasulullah" haka ya dinga Nana tawa a cikin zcyarsa,da sauri kuma ya buɗe idanunsa jin mararsa na halbawa da ƙarfi tana ƙoƙarin miƙewa tsaye,abun ya keji kamar almara tunda yake haka bai taɓa faruwa dashi ba, cinyoyinsa ya haɗe waje guda yana ɗan maza Babbar rigar sa gudun kasa su kaga yadda mararsa ta miƙe tsaye,duk abinda yake akan idanun Lamir Murmushi kawai yake yana jinjina kansa, Mama ce ta kalli Jalal tace "Muhammadu yaushe ka zama sallamamme bani da labari?idan kai zcyarka mai ƙyau ce an gaya maka ta kowa mai ƙyau ne? Ka manta abinda ya aikata gareka har kake gaishesa,na ɗauka sa tamkar ɗan dana haifa a cikin jikina ban taɓa kallonsa a wanda wani ya haifesa bani ba,kana dai kallo kana jin abinda ya aikata ga gudan jini na,ba tai masa komai ba,babu abinda ta tsare masa tana kallonsa matsayin yayanta,amma yau shine ya nemi tuzarta rayuwata ya sanya akai mata abinda ko maƙiyinka baka son ya kasance da ita,dukkan abinda ya samu Zulfa shine sila,mai makon duk abinda zai yi ya aikata a kaina sai ya nemi tarwatsa farin cikin ƴarta,mai Zulfa tai masa? Me ta tsare masa?idan gadonta yake magana ba ubanta ya mutum ya bar mata ba?ko kuma kuɗin na uban wani ne?wlh wlh tllh da wasa naga ka ƙara gaida wannan mutumin sai ranka ya ɓaci,sai kaga ɓacin rai da baka taɓa ganinsa a waje na ba,tashi kaban waje?"kasa miƙewa yay sbd yadda ya keji baƙon yanayi a jikinsa,ga kuma yadda mararsa take ƙara miƙewa tare da harbawa sai haɗe cinyoyinsa yake,lokaci ɗaya idanunsa suka kaɗa sukai jajirr kamar wanda yaci kuka ya ƙoshi, miƙewa Lamir yay tare da kallon Mama yace "Ni ba tashin hankali ya kawo ni,kuma dukkan wannan abinda kike faɗe na aikata ne?hujja ɗaya da zata nuna ni mai laifi ne baku da ita,ko aƙwai hujja a wajanku ne?" Ko kallon inda yake batai ba,kuma bata tanka sa ba, Lamir yace "ko kuma zargina kike a kan wanda ya tuna asirin mahaifiyar Jalal da kuma Alhaji Kabeeru,to bani da niyar faɗa maku,ni bana da hannu a yaɗa cewa mahaifiyar Jalal mahaukaciya ce,abinda baki sani ba bayan ni Lamir kuma bayan ex Governor Mubarak Yahya cibo aƙwai wanda yake farauta rayuwar Jalal,kuma shi yake da hannu wanda faɗin abinda ya faruwa a ranar zaɓe,idan har zaku tashe tsaye ku tashi ni daga nan garin ma zan bari,kuma ni bani jin tsoran faɗin abinda nayi dukkan abinda na aikata zan iya faɗa a gaban kowa,maƙiyyan Jalal nada yawa na ɓoye dana sarari na jikinsa da kuma wanda bana jikinsa ba ok!" Yana faɗin hakan ya fice daga cikin parlour'n ya nufi waje,da idanu Mama ta bisa tana watsa masa harara kamar ta bishi ta shaƙe haka ta keji,kallonta ta dawo sashi zuwa ga Jalal tace "ka dai ji ko?to ni babu ruwana wlh,idan zakai hankali gwamma kayi niba shasha bace haka nan,kai dai girman kawai Allah ya baka da shekaru amma baka da wayo sam wlh,sai uban tunbi da aka ajjiye gaba kamar mai tsuhun ciki,to Wlh ka nutsu ni babu ruwana wlh na sha ruwan tabara da yasin na shayar da Zulfa dashi dan haka babu abinda zai sameka,wlh lalata ta zamanin yanzu ya lalace,abu daga wannan sai wannan kamar cin ƙwan makauniya"ta faɗa tana ficewa daga cikin parlour'n ta nufi part ɗinta,shi dai Jalal abin duniya ya ishesa abinda ya keji kaɗai ya ishesa,a sanyaye ya miƙe yana baza babbar rigar sa,harya shige part ɗinsa,girgiza kai kawai Abbou yay kafin ya juya ya nufi upstairs,daman ya fito ne domin ya tabbatar Jalal ya dawo kuma yana saukowa yaga abinda yake faruwa da sauyawar Mood ɗin Jalal har abinda Lamir yake faɗa da wanda Mama yake faɗa, Jalal na shiga part ɗinsa ya shige bedroom,kayan jikinsa ya fara cirewa ya sanya cikin datti clothes,yana gamawa ya shiga cikin bathroom ya sakawar kansa ruwan sanyi,iska ya fesar ta cikin bakinsa gaba ɗaya abu ya ishesa baya jin daɗin yanayin daya tsinci kansa a yanzu,yana jin wata kalar a zaba wacce bai taɓa jin ta taba, a gurguje ya kammala wankan,yay brush ya ɗaura alwala kana ya fito daga cikin bathroom ɗin sanye da bathrobe a jikinsa, wajan dressing mirror ya ƙarasa ya ɗauki body lotion ya fara shafawa saman fresh skin ɗinsa,yana gamawa ya ɗauki comp ya taje sumar kansa wacce take ta gyalli, parfume ɗinsa ya ɗauka mai sanyin ƙamshi ya fesa,kana ya je wajan wardrobe ɗinsa ya ɗauki wata maroon color ɗin jallabiya ya ɗauka,sai wani farin boxer ƙarami daya ɗauka ya sanya sosai ya kama waist ɗinsa amma haka yasa dan yafi son ya danne masa mararsa,yana gamawa ya ɗauki wani farin hirami ya ɗura saman kansa lokacin ladan ya fara kiran sallah,yana kammalawa ya fito daga daga cikin part ɗinsa,tsaye ya samu su Imran suna jiransa, haɗa baki sukai wajan faɗin "barka da fitowa"kansa a ƙasa yay gaba ba tare kuma daya amsa su ba,a main parlour suka samu Abbou,gaba ɗaya suka nufi masjid ɗin,bayan Jalal ya kammala jansu sallah ya zauna ya fara gabatar da karatun Alqur'ani ga jama'ar da suke jiransa,bai shigo cikin gida ba sai wajan 9:5 gaba ɗaya ya samesu a saman danning harya shige part ɗinsa sai ya tsaya sbd Muryar Abbou da yaji yana faɗin "Muhammad"tsayawa yay kana ya nufi wajan kujera yaja ya zauna,tunda ya zauna taji Zcyarta na bugawa da ƙarfi ga wani mayataccen ƙamshin parfume ɗinsa daya daki hancinta, lumshe idanunta tayi tana sauke ajjiyar zcya,tsaki kaɗan Nihila tayi sbd taji saukar ajjiyar zcyarta,kansa a ƙasa yace "gani" spoon ɗin hannunsa Abbou ya ajjiye ya ɗauki tissue ya goge bakinsa tass,kafin ya ɗauki gorar ruwa mai sanyi ya sha,samansa ya gyara tare da kallon yaran nasa sosai yace "ku ko shirya ko kada ko shirya na riga na yanke hukunci da zuciyata da kuma mahaifiyarku,bayan rantsuwar Jalal da sati guda duk za'ai bikinku, ni ba wata bidi'a za kuyi min ba,daga ɗaurin aure sai walimar da za'a haɗa bayan ɗaurin aure da sati ɗaya, tsakanin Jalal da Aryan kowa ya san wazai aura daku nake ƴan uku,ko hanzarta fitar da matar aure tun wuri"shiru gaba ɗaya sukai yayinda baby da tsorawa Jalal idanu tana son taji mene zai ce,jin shirun yay yawa yasa abby cewa "ko baku ji abinda nake faɗa bane?" Irfan ne yace "Abbou daman naiwa Mameey maganar ni wacce na keso a familynta ne, mai suna Ikram kuma nan da 2daya zaku ƙarasu"kallon Mameey Abbou yay Murmushi tai masa ta ajjiye cup ɗin hannunta tace "eh tun ranar baƙwan Mummy ya sanar min,daman yau nake son faɗa maka"idanunsa ya mayar kan Imran yace "what about you?"Imran ya sunkuyar dakai yace "a'a ni bana da wata budurwa Abbou duk abinda ka yanke shikenan" Mameey ce kallesa tace "kai sakaran kawai,kace tsoran matan kake,amma duk matan da suke duniyar nan kace ka rasa budurwa?" Abbou ne yace "don't worry ka shirya gobe kaje gidan Alhaji Zubairu kaga yarinyar wajansa Fatymerh" kallonsa ya mayar kan Jalal yace "ina magana kai baka ce komai ba,ko kuma auren ne baka shirya yinsa ba?" Girgiza kai Jalal yay kafin ya fesar da numfashi idanunsa a kan Jalilerh wacce kanta yake a ƙasa tana cakalkala abincin gabanta yace "Jafar fa?" Murmushi Abbou yay yace "kada ka damu gobe za nemesa,yay hqr ya janye maganar auran baby kai zaka AURETA" da sauri Jalilerh ta ɗaga kanta ta sauke ganinta a fuskar Jalal shima kallonta yayi da sauri kuma ta miƙe ta nufi upstairs tana rufe bakinta sbd kukan daya taho mata,da kallo gaba ɗaya suka bita banda Jalal daya sunkuyar da kansa yana jin kansa na sara masa ga wata azabar da mararsa ke masa,shima miƙewa yay ya nufi kitchen yana zuwa ya buɗe babban fridge ɗin yaga lemon da yawa guda goma ya ɗauka ya shiga matsesu cikin cup sai da ya gama sannan ya ɗan zuba ruwan zafi kaɗan tare da sanya lipton guda biyu,fita yay daga kitchen ɗin ya nufi part ɗinsa, Lamir yana fita daga cikin gidan kai tsaye gidan Mubarak cibo ya nufa a guest room suka zauna,bai jiran gaisuwar da Lamir yake masa ba yace "yaya² ka gama aikin naka?"dry Lamir yay sosai kafin yace "aini abu sai dai idan banyi niyya ba,kana tunanin haka kurum zanje wannan