Showing 18001 words to 21000 words out of 98315 words
haka yayi ta iskancin shi har matarshi ta gama wanka ta fito, ya dafa kafaɗarta suka wuce ɗaki,,,
Haka layi yaci gaba da ja, har yaxo kan raihana ta shiga tayi abinda zatayi ta fito ta nufo ɗakin su,
Tana shiga ɗaki ta samu umma zaune ta zabga tagumi tace umma , umma ɗago kai tayi ta kalleta ba tare da tayi magana ba, raihana tace gaskiya wannan zaman baya yuwuwa ki tashi umma mu nemi mafita?"""
Dariya umma tayi sannan tace raihana har kin gaji?""" kuka raihana ta fara tace umma naga ta kaina na rantse da Allah ko kashin da nayi a leda nayi na jefe masai kamar wata inyamura,
Dan wallahi wannan masan bana iya hawanshi umma ji nayi idan na hau kamar zan faɗa, don girman Allah kawai mudai mu koma gidanku,
Umma tace kinga rufa ma kanki asiri zaman gidanmu baya yuwuwa wurinki, dan nima ina da yayye wanda basu aure kuma ɗaki ɗaya ne gara muyi haƙuri kizo mu nemi mafita wato sana"a don mu samu abinda zamu riƙa biyan haya,
Zama raihana tayi , sannan umma tace naga tunda gidan nan yana da yawa shawara ɗaya muyi ƙoƙari mu riƙa tashi tunda sassafe muyi abinda zamuyi kafin su tashi, raihana tace to, yinin ranar dai haka suka yini suna tattaunawa dan ganin samun mafita a rayuwarsu,
****
kwanan su raihana ukku da komawa gidan haya suka fara sana"a dan biyan kuɗin haya da kuma samun abinda zasu ci ,
Da safe umma tanayi koko da kosai haka ake shigowa cikin gida ana siye, da rana kuma tayi shinkafa wake da mai da yaji, raihana take fita dashi anan ƙofar gida tayi talla, babu laifi gaskiya ana siye sosai dan duk abinda ka gyara na sana"a to insha Allah zai samu shiga,
Raihana zaune a wurin siyar da abincin ta, tayi jugum tana tunanin rayuwa, taji ana ta magana ta ɗago kanta, dan ganin maiyi mata magana, raihana tace sannu murmushi tayi sannan tace da gani dai baki ganeni ba raihana?"" murmushi raihana tayi sannan tace ai naga kamar nasan fuskar amma ta shige man,
yaron da take riƙe dashi a hannun ta ne yake cewa mama don Allah ki saiman abincin nan, raihana maida kallonta tayi wurin yaron da yake maganar, ita kuma tace to zan siya maka jira, raihana ta kalleta tace don Allah ɗan bani haske mana,
Tace mata zulaiha ce, raihana tace wace zulaiha?""" tace baki gane ni ba?"" nice fa zulaiha sani, idanuwa idanuwa raihana ta zaro tace zulaiha kece haka?"" innalilillahi wa"inna ilaihir raji"un, da sauri ta miƙe ta zuba ma yaron abinci ta bashi ita kuma zulaiha ta sauko na goyen ta ajiyeshi suka fara cin abinci,
zulaiha ta kalli raihana tace gaskiya ƙawata ki gode ma Allah ke kina cikin rufin asirin rayuwa, raihana tace to Alhamdulillah, amma a ran raihana cewa tayi hmm yarinya baki san yadda nake raɓe ba da baki wannan maganar ba , ni zama ma babu miji ya isheni, zama ba aure shine damuwata duk macen data san ciwon kanta tana can ta rungume ɗan mijinta suna rufa ma kansu asiri, amma ni hauka da ƙuricciya yasa na maida kaina *zawara* danma ban ni wata rayuwar aure bata shiga tsakanina da aminu ba, bare in ƙara tantance daɗin aure da rashin sa,
Maganar zulaiha ta katse mata tunani , zulaiha tace raihana baki cewa ya kika ganni nan?"" raihana tace aini kinsan babu ruwana da rayuwar kowa tawa nake yi kuma inda zan samu mafita nake nema,
zulaiha ta fara kuka tace baki cewa ina mijina?"" raihana tace nasan yana nan lafiya qalau, zulaiha tace ai kina gani na kinsan banda aure, tunda ke kanki gashi kin kasa ganeni"""" raihana tace dan ban ganeki ba sai kawai akace baki da aure?"" kika san ko kyau kika ƙara ?"" dariya zulaiha tayi sannan tace lallai kinma raina man hankali, raihana tace to Allah ya baki haƙuri,
Zulaiha tace raihana ina cikin matsala ina cikin damuwa ina cikin tsananin rayuwa ina cikin bala"i ina cikin masifa, subahanalla raihana tace duk miya kawo kike jawo ma kanki wannan mugun al,kaba"i a rayuwarki, ko wane lokaci bawa ya riƙa dan gana alkairi da rayuwarshi duk yanda kika ga kina cikin aƙuba ta rayuwa wallahi wani yafiki,
zulai wani maƙoƙo yazo ya to kare mata zuciya tace wayyo Allahna na bani na lalace ni zulaihatu, bakin san baƙin cikin da nake ciki ba, da baki ce wani yafini ba, raihana tace ki rufa mana asiri don Allah a bakin titi muke kada ki tara mana mutane,
Duk wansa kika gani a duniya kowa yana da matsala, saidai ta wani tafi ta wani amma idan kowa yace zai fito yayi kuka haƙiƙa kukan mutane da yasa duniya ta rikice,
zulaiha tace ke rufa ma kanki asiri duk faɗin duniyar nan nafi kowa shiga cikin masifa, zulaiha ta ƙarashe maganar tana kuka, baki raihana ta saki tana kallonta, ita abun ma dariya yaso ya bata, amma ta kanne, zulaiha tace saboda haka abokin kuka shi ake faɗa ma mutuwa, yau ina nan sai abincinki ya ƙare muje gidanku ina san magana dake, murmushi raihana tayi sannan tace to,
suna nan zaune har abincin raihana ya ƙare sannan suka tattara suka tafi gida,
suna shiga ɗakinsu raihana wata yamutsatstsiyar tabarma ta shinfida masu suka zauna,
Umma ce ta shigo ɗakin bayan sun gaisa da zulaiha tace zata shiga maƙota tayi masu barkar aihuwa, raihana da zulaiha sukai mata fatan dawowa lafiya,
sannan ta fita daga ɗakin, zulaiha ta sake matsowa kusa da raihana tace a inajin alhakine yake bibiyata, bari un baki labarin gidan aurena, raihana ta matso kusa da ita sannan tace ina saurarenki,
Zulaiha ta fara magana, a *Abuja*
Ku kasance tare dani danjin wani hali zulaiha take ciki wanda yasa take ganin duk duniya tafi kowa shiga cikin damuwa,
a madadin *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻 masoyana nake maku fatan alkairi sau kunji ni........................💋
💦💦💦💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
*Page* 1⃣9⃣
*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻
*MEELAT MUSA* 🌹
*Wannan page sadaukarwa ne gareku Ameenci association, tare dake ƙawata ASMEENAT XEEYAN saboda kinsan kia raina bana mantawa dake ko wane lokaci ƙawata*
*Halima Yahya Allah ya baki lafiya ubangiji yasa kaffara ne, Allah ya tokari kafaɗa, muna maki addu'ar samun sauƙi ko wane lokaci, Allah ya baki lafiya ameen*
*****
*A* Abuja gidana ƙayataccen gida ne, babu abinda na nema a gidan mijina na rasa, mijina kullum baya da buri wanda ya wuce yaga ya kyautata man baida burin daya wuce yaga ina cikin farin ciki,
Mutumne mai rufen asiri kuma yana da ƙoƙari wurin ganin ya fidda haƙƙin iyalinsa,
Kinsan wani lokaci mu mata muna da namu halin da zarar munga mun wadatu iskanci sai abinda yayi gaba amma bance kowa ba, nidai zulaiha haka tawa rayuwar ta kasance shi yasa wasu mazan ke cewa idan daɗi yayi na mace yawa take abinda taga dama,
Zuwana abuja duk lokacin da mijina ya dawo daga aiki zai ɗaukeni ya ɗan zagaya dani inga gari saboda nace mashi ina san abuja tana burgeni, wannan dalili yasa yake fita dani dan nima inga yanda duniyar abuja take,
Zama muke mai daɗi dashi , wata rana nace mashi zan ɗan riƙa shiga maƙota dan idan ya tafi kafin ya dawo inayin kewa sosai kasancewar shi mutumne mai haƙuri da kuma ƙoƙarin ganin ya fita haƙƙin iyalinshi yasa ya amince da buƙatata,
Gidan wata hajiya sakina wanda naga duk yawancin matan anguwar a gidanta suke zuwa saboda haka nima ina fita gidanta na fara shiga, lokacin da naje na tadda gidan cike da mata kamar ana koya masu darasi , saboda haka nima sallama nayi na shiga, bayan gaisuwa na gabatar da kaina a wurin hajiya,
Ta nuna man jin daɗinta, ni kuma na ɗan zauna na wani lokaci, saida na tashi zan tafi hajiya ta tashi ta shiga ɗakinta ta ɗauko man wani maganin mata tace man ga wannan, nace to godiya nake tayi man bayanin duk yanda zanyi amfani dashi ta kuma ƙara da cewa idan har na riƙe wannan na wuce ƙarfin wulaƙanci a wurin miji na, haka nayi godiya sannan na dawo gida............
Ina zuwa yanda hajiya taman bayani haka na aiwatar da maganin nan, aiko magani naga amfaninshi, gari na waye wa na koma gidan hajiya nayi godiya, sannan kuma nace nawa ake siyarwa?""" ta faɗa man nace to aini bani da kuɗin siye saboda da yawane kuɗin ta faɗa man, dariya hajiya tayi sannan tace ai da wannan zaki kama mijinki duk matar da kika ga tana hawa ƙatuwar mota tana jin daɗinta wannan shine mutumcinta a gidan aure,
Hajiya tace zauna ayi lecture yau dake, abinda karatun hajiya yake nunawa mace idan har mijinta yanajin daɗin kwanciya da ita haƙiƙa ta riƙa ja mashi aji, sannan kuma saima ya biya kuɗi,..
duk wacce take san zama *kasaitacciyar mace* wanda take so a dama da ita a duniyar ƙasaitaccin mata ta nan zata samu itama ta fito,
Maimakon hajiya ta koya mana abin arxiƙi sai ta koya mana abun da zai wahalar da rayuwarmu, """ niko nace ai duk abinda zai zamar maka alkairi kasanshi kuma ido ba mudu ba yasan kima"""""
Karatun hajiya kullum ya za"a samu a ƙwalƙwalo kuɗi a wurin miji, haka shine huɗubarta ,
Wannan hali na ɗaukeshi kafff a kaina kinsan duk abinda aka koya maka sai kayi zarra, wanann huɗubar ta zauna man kaff a cikin kai saboda haka , a gidana shi kanshi mijina yasan na canja, sannan ga wani yawo dana gane, sai naci gayu na sannan zan ɗauki mota in fita, in fita lokacin da nake so in dawo lokacin dana ga dama,
Wannan abu ya damu mijina lokacin daya zaunar dani yaman nasiha abinda nace mashi nan bariki ne saboda haka kuma tunda ya kawo ni saidai yayi haƙuri,
haka naci gaba da kutsawa cikin abuja kullum idona ƙara buɗewa yake iskanci sai abinda yayi gaba,
Ganin haka yasa yace man in shirya muzo gida, anan neman mu, na tattaro na biyo shi, dan yace duk abinda nasan zan buƙata in ɗauka saboda zamu daɗe bamu dawo ba, nace to, haka na tattara duk abinda nasan inaso, mukayo gida,
Bayan mun zo gida na shiga , na samu bbanmu yana nan, dan haka ya shigo suka gaisa, sannan ya zaro takadda daga gaban aljihunshi yabawa baba , sannan yace ga zulaihat nan na dawo da ita bisa dalili kaza da kaza, kada taje ta shiga cikin wata rayuwa kuma ace nine sila, baba ya bashi haƙuri yace ah ah shi kaɗai yasan yanda yake zaune dani, """ sannan ya tashi yayi tafiyar shi,
Ni kuma huɗubar hajiya na riƙe, ina da kyau da diri zan samu wanda yafi shi komai koda an sakeni, baba ya nuna rashin jin daɗin shi amma nace yayi haƙuri insha Allah saina samu wanda yafi shi komai da komai,
*****
Sati na biyu a gida duk abinda nake taƙama dashi wanda nazo dashi daga abuja ya ƙare rashin kuɗi da rashin abin wanki da wanka ya fara damuna, yayana yana kiyon kaji sai sharar ɗakin kaji da wanke masu abun shan ruwa ya dawo kaina saboda tsabar babu da talauci yana bani naira hamsin idan na wanke mashi,
*zawarci* babu daɗi na shiga cikin fitina da musiba dan haka wani yana zuwa neman aurena babu bincike babu komai kawai nace ya turo,
hawaye ya zubo daga idon zulaiha tace raihana naci ubana, raihana dai batayi magana saboda kawai tana kallon zulaiha bata da hankali, zulaiha tace duk wannan aƙubar dana sha a gida bayan nayi aure,
Wannan wanda na aura yana da rufin asiri wanda ci dasha baifi ƙarfina ba, shi kuma abinda ya haɗamu,
Yafi kuka da rashin tattalina dan idan na toya dan kali ko nama man zubar dashi nake, idan nayi wanka da sabulu so ɗaya bana ƙara amfank dashi saidai in buɗe saboda , iskanci dai iri iri,
A haka dai muka daddafa har na haihu ɗaya, bayan na haihu iskanci yaci uban na da, idan ya kawo man pampers sai in ɗauka in siyar ga shige shige maƙota, bana zama gida wannan abun yana mashi ciwo , ga rashin kunya da rashin gurmamawa ,
Tsakani na da "ya"yanshi sai zagi sai tsunuwa yana nuna man rashin jin daɗin hakan amma dan nasan baya so kullum sai na nayi ,
Muna cikin haka ne, wata maƙociyarmu ta kirashi tace mashi taga yana ƙokarin kyautata man amma bana godewa saboda haka yazo ta bashi ɗiyarta, ta ƙara da cewa ai duk macen da ƙoshi yai mata yawa iskancin da take baya kalluwa, shi yasa maza da dama suke tafiya su auro yar ƙauye , duk abinda zata ba miji saita rusuna sannan kuma ga biyayya amma su matan binni sai raini da girman kai suka iya,
tace ka auri ɗiyata ina da yaƙinin zata maka biyayya, kuma ni bazata fito cikin unguwa ta wulaƙanta ka ba, ko a cikin gida baza tayi maka ba, bare har ta fito a idon duniya ta maka rashin kunya,
Haka ya amince da buƙatar ta, haka aka tsayar da lokacin aure , aka ɗaura mashi aure da ita, haƙiƙa nayi tashin hankali nayi bala"i nayi masifa amma a banza, tana shigo babu sanya taci gaba da kyautata mashi
Ladabi biyayya aka barni da haukan banza, ina da ciki na biyu, na kama matarshi nayi mata shegen duka yana dawowa shima na rufe shi da masifa, haka ya gaji da bala"ina ya sakeni saki ɗaya, nace mashi saina samu wanda yafi shi yace man baya baƙin ciki, Allah ya bani inma auri shugaban ƙasa baya man hassada,
Haka na dawo gida ga mahaifiyata babu rai, matar babana baba yace mata tunda abun iskanci ne abuna inji baba miyar gidan nan kada a sake kaɗata da gishi sai naci ubana tunda dai *zawarci* na zaɓa, raihana wahala ta isheni na rasa inda zan saka rayuwata, ajiyar zuciya raihana tayi sannan tace kema banda abinki sai a sakeki kuma sai ki kwaso "ya"ya jagal jagal ki taho?
wannan rayuwar babu wanda yake san ɗan wani, shawara ɗaya da zan baki yaran nan ki mayar dasu wurin ubansu, kima ji da kanki ko Allah ya fito mana da mazaje muyi auren mu,
zulaiha tace to zan mayar dasu, raihana tace to yanxun shi ina tsohon mijinki na abuja?"" zulaiha tace yana can , kuma har yanxun baiyi aure ba, raihana tace miya sa baza ki koma wurin shi ba?"""
tace ai baya kirana, raihana tace kina da number shi?""" tace banda ita, raihana tace yanxun dai ki fara maida yaran nan wurin ubansu tunda duk maza ne sai musan mafita, zulaiha tace , to
haka sukayi ta "yar firarsu daga baya ta tashi ta goya yaronta ta kama hannun ɗayan tayi ma raihana sai anjima, a bakin zauren gidansu raihana ta rakata sannan ta dawo,
Raihana ta dawo gida tana ta nunanin wannan urin hauka na zulaiha, tsaki tayi sannan taje tayo alwalla don an kira sallar magrib,
hmmm Allah dai yasa mu dace,
💦💦💦💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
*Page* 2⃣0⃣
*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻
*MEELAT MUSA* 🌹
*****
*R*aihana tana shiga ɗaki zama tayi a gefen katifa, hawaye yaci gaba da ambaliya daga cikin idanuwanta, kuka take sosai tana addu"a Allah ubangiji ya bata mijin tayi aure wannan musifa ta isheta, shin wai da tana da ƙanne ya zatayi?"" lallai da ba ƙaramin raini zasuyi mata ba,
Kanacin gashin kanka amma ka dawo gida sai abinda aka kasa aka baka, wannan wace irin rayuwa, amma ita zulaiha Allah ya bata dama amma tayi sakaci, kuma ta tashi ta kwaso yara jagal jagal to banda hawanta inama zata wuce a so ta?"" hawayen ta goge sannan ta miƙe ta fara sallah,
Raihana tana cikin sallah ta jiyo gida ya kiɗime, wasu na salati wasu kuma suna cewa gara da akai haka, wasu kuma kamar dai suna ɗan kuka kuka, raihana ita kuma tana gama sallah ta dawo bakin ƙofar ɗakinsu ta cikin labule ta laɓe don tabbatar da abinda taji gaskiya ne?"""
Lallai kunnen gaskiya ya jiyo mata, wato an siyar da wannan gidan da suke ciki kuma ga wanda ya siyi gidan tsaye a tsakar gida yana cewa yaba duk wanda take cikin gidan nan notices daga yanxun zuwa gobe da safe duk wanda takai la"asar a gidan nan tou pha zataga abinda zai biyu baya,
Ajiyar zuciya raihana tayi sannan taja jikinta ta koma saman katifa, *innalillahi wa"inna ilaihir raji"un* kwai take iya faɗi, raihana a bayyane tayi magana tana faɗin wannan wacd irin rayuwa ce?"" amma lallai bari Umma ta dawo dole gidan gwaggo zamu koma saidai duk bala"in da za"ayi ayi dan basu da inda zasu zauna,
Taci gaba da cewa gashi nan munma fara "yar sana"ar mu muna samun abinda zamu rufawa kanmu asiri, wayyo Allahna ya Allah kaji ƙaina ka rufa man asiri dan matsayin manzan Allah S. A. W, ka taimakeni ka bani miji inyi aure wallahi nayi hankali in Allah ya yadda nayi aure ko bansan mijin wallahi zama zanyi Allah ka yaye man haka nan, ta sake farkewa da wani irin kuka, sannan tayi magana ƙasa ƙasa tace Allah ka taimaka man kada in mutu banyi aure ba,
Umma ce tayi sallama ta shigo ɗakin da sauri raihana ta goge hawayen idonta tunda ɗakin da duhu umma bata san raihana tana kuka ba,
Umma sannu da zuwa, umma tace yawwa raihana tace kin daɗe baki dawo ba, umma tace wallahi, raihana tace kinji kuma abinda aka zo mana dashi?"" umma tace miye?"" hmmm umma wai an tada kowa na gidan nan, umma tace bisa wane dalili?""" raihana tace mai gidan ya siyar wanda ya siya kuma yace kada wanda takai mashi la"asar a gida, ajiyar zuciya umma tayi sannan tace Allah yasa haka shine alkairi,
Raihana tace haba umma wand alkairi kuma don Allah a tashe mu kina cewa Allah yasa alkairi ne, Umma tace haba raihana da ilimikin da hankalinki ya kike abu irin na jahilai?"" duk abinda kika ga ubangiji yayi a rayuwa yana da sila, jin umma zata fara wa,azi ita kuma tana cikin zafi dan haka kawai tace shikenan,
yanxun ina zamu koma?"" umma tace mu bari da safe sai musan nayi, raihana tace Allah ya bamu aron rayuwar, umma tace amin, anma fara kiran sallah muje muyi sallar, raihana tace ita tana da alwalla buta umma ta ɗauka ta fito tsakar gida donyi alwallah,
****
*G*ari na waye kowa fidimar gabansa yake masu fita da kayansu dan mutanen