Showing 30001 words to 33000 words out of 98315 words

Chapter 11 - ZAWARCI

06 Oct 2024

8016

na bada shedar halinki ikar wanda na sani amma ina nan naji shehu yace aike alashe money ne baki auren talaka sai mai kuɗi sannan kuma duk kinbi kin gama barbaɗewa saman titi, shekara ukku kina zawarci kada ya kuskura ya yayo ma kanshi jaraba,

Amma kiyi haƙuri ba faɗa maki wannan dan ranki ya ɓace ba kiyi haƙuri idan kinsan kina da wani hali wanda bai dace ba ki gyara, kamar yanda kike haƙuri akan rayuwa ki ɗaure kuma ki dage da addu"a, dan duk tsanani yaa tare da sauƙi,

Ajiyar zuciya raihana tayi sannan tace shi a gabanshi nayi iskancin ne?"" shamsu yace wallahi banda ni kima tambayi duk wanda kike so, zai faɗa maki dan cewa yayi wai kwalba kika samu idan kika kama mutum ki fara aske mashi arxiki wahala take sa ya gudu da kanshi , kina jiran mai kuɗi yaxo ki aureshi,

Raihana tace to shida Allah, kuma idan lokacin aurena yaxo wallahi bai isa ya hana ba, idan kuma ina rabon hutawa haka shima bai isa ya tare man samuna ba,

taci gaba da cewa tunda yayi aure ya aihu shima wata rana anyi ma nashi, daga nan bata sake cewa komai ba, har shamsu ya bada alewar ta fito daga cikin shagon ta nufo gida,

Tana tafiya tana tunanin wanan sharri, tsaki tayi lokacin data wuto majalissar da ake janta suka fara , ko ka gane mana *zawara* uwar san banza ke wuta kanenki ɓarawo, suka fara sheƙewa da dariya, suka ci gaba da cewa nifa ban taɓa ganin zawarar gdan talauci ba wai ita can mai kuɗi take jira don Allah kalleta, sai su sheƙe da dariya hhhhhh *zawara* haka sukayi ta mata iskancin , ita kuma raihana hawayene kawai yake bin idonta rugawa tayi da gudun tsiya, tayi cikin gda, gwaggo tana bakin murhu tsugunne taji raihana ta shigo da guda,

da sauri ta miƙe tana tambayar lafiya?"" raihana da gudu ta faɗa cikkn jikin gwaggo ta rushe da wani irin kuka mai taɓa zuciya, gwaggo ta fara salati tana cewa wai miye don Allah,

raihana tace wai gwaggo har takai idan anzo tambayar halina a anguwar nan ace man waini "yar iska ce, wai bana aure sai mai kuɗi, ni wallahi miji ko daga kauye yazo wallahi aurenshi zanyi, ni banma san mai kuɗi talaka nake so muyi zaman mu, in rufa ma kaina asiri, yanda take kukan tana ƙara ɗaga murya, abun yasa gwaggo taji tausayinta,

raihaina taci gaba da cewa ama barni da abinda Allah ya jarabeni amma sai ayi ta jaman sharri?"" to wallahi ni tunda nake ban taɓa iskanci ba, kuma duk wanda yaman sharri na barshi da Allah wallahi,

gwaggo taji tausayin raihana don haka taci gaba da rarrashinta tana bata haƙuri , raihana tace ba komai Allah zai saka man, tana cikin magana wani yaro ya shigo yace ance raihana taxo, ɗago jajayen idon ta tayi sannan cikin maganar kuka tace waye yake kirana?"" yaron yace ummarki ce, murmushi raihana tayi sannan tace ma gwaggo ina zuwa,

Tana faɗin haka tayi waje da gudu, tana fita a ƙofar gidan da zasu kama haya ta hango umma tsaye saboda haka da gudu ta isa wurin umma tana ta kuka, umma tace mi akayi maki kuma?"" raihana ta kwashe komai ta faɗa mata,

Har a ran umma bataji daɗi ba, amma dan tasa raihana taji natsuwa tace to miye?"" aidai ke kinsan baki iskanci ko?"" to duk wanda yai maki barshi da Allah, raihana tace haba umma sharri babu daɗi , umma tace mai sharrin zai isko maiyin da izin Allah,

ta kauda maganar ta hanyar cewa na biya kuɗin na wata ukku na bayar, yau zanje in kwaso kayanmu, raihana tace to, umma tace ki shiga kiga ɗakin, raihana tace umma basai na gani ba, ina sauri ne inje in shirya zulaiha tana jirana a gdansu,

umma tace to kije ki shirya ki tafi, raihana tacd umma kinga waya, nayi chargy ashe ma hada layi ta saka man, umma tace to Allah ya tsare , raihana tace amin, sannan tace ummana ki bani ₦20, inje in siyo ko koko insha,

Umma tace to sannan ta bata kuɗin, ta juya tayi gidan da suke siyo koko, ta siyo a leda sannan tayo gidan gwaggo,

tana shiga ta samu wuri ta juye kokon, babu sugar babu alewa, ta bara sha, gwaggo tace miyasa kika siyo?"" gashi nayi dake, raihana tace ai yau koko nake ra"ayi, gwaggo tace tou fa,

ita kuma raihana tayi haka ne dan zaman lafiya dan idan dai kana san zamanka da mutum yayi nisa dole saika nisanci abunshi, idan kaga mutum yana san abunshi tayashi sanshi sai ka zauna lafiya,

tana gamawa wanka taje tayi, kayan da taxo dasu dagan su umma ta saka , taci uban kyau idan ka kalli raihana sau ɗaya baka iya sauke idon ka, dan gaskiya raihana tana da kyau , kuma kyau mai ɗaukar hankali , tana da siga da diri mai ɗaukar hankalin duk wanda ya ganta, amma daka ganta kasan bata da wadata, danshi ƙoshi daban yake, kana kallonta zaka gane tana cikin damuwa,

haka ta gama shirinta tsaff ta fito, tayi ma gwaggo sai ta dawo, gwaggo tayi mata Allah ya tsare hanya,

tana fitowa ta ibi hanya sai gidansu zulaiha, haka tayi tafiya mai ɗan nisa sannan ta iso gidansu, a ƙofar gida ta samu zulaiha, suna gaisawa da wani abokin mijinta wanda shine zai kaisu inda zasu je, zulaiha da sauri ta iso wurin raihana ta rungumeta kawata kinfa haɗe, dan ba haɗuwa kikai ba haɗewa kikai wallahi, raihana tayi dariya, sannan zulaiha tace *K"B* ga ƙawata, sunan ta raihana,

kb ya kalli raihana sannan yace sannu raihana tace kaima sannu, ya tsareta da idanuwa sai kallonta yake, zulaija tace muje ciki,

suka shige ciki gida, suna shiga wata ƙanwar zulaiha ce ta fara cewa wallahi yaya zulaiha shine kika shafa man janbaki na?"" zulaiha tace janbakin banza, yarinya nida aka kawo ma lefe,

kanwar tace lefenkin banza ina ruwana dashi, zulaiha tace rashin kunya zaki man ne?"" wannan ba baƙuwa bace a wurina, tana nuna raihana tace da Allah wuce muje bar raihana bar banza,

babu kunya yarinyar nan tace gaki ƙatuwar banza, wanda kika kasa haƙuri da mijinki irin halin da kikai mashi ya koro ki kkke so muma nan kixo ki raina mana hankali tomu bamu barin takwana,

raihana tacd ikon Allah zulaiha tacd ke bar banza nan mi kika gani?"" ai nan ba"ai komai ba, muje ciki lokacin da take jan hannunta suka shiga cikin ɗaki,

Ita kuma kanwar zulaiha haka taci gaba da ɗago murya tana zungurawa uwar zulaihat zagi amma daga raihana har zulaiha babu wanda ya sake magana, suka fara buɗe kayan lefe,

akwati shidda hada wata katuwar jaka, an kashe kuɗi gaskiya akamar lefen budurwa, ga kaya masu tsadaɗ gaske, komai dai na aji ne aka sako mata tsayawa faɗin abun ɓata lokaci ne, raihana taima zulaiha fatan alkairi,

zulaiha tace nace mashi ranar da aka ɗaura aure zan tare ,yace to babu damuwa kuma ko kayan ɗaki da duk abinda zan buƙata shine yayi man, raihana tace masha Allah haka ake so ai,

bayan sun gama ganin kayan zulaiha tace suje kabir yana waje yana jiransu haka suka taso sukayo waje, suna fitowa kabir ya kwashe su suka biɗaɗa duniyar gayyar ƙawayensu,

haka suka yini suna gayya, amma ba kowa suka gayyata ba sun gayyaci ƙawayensu na kusa da kusa, sannan sukayo gidan su zulaiha , k"b yace to zulaihat bari inkao ƙwarki gda, raihana tace ah ah nidai ajiyeni anan , zanje dakai na, yace wallahi sai nakaiki,

zulaihat ta fita, shi kuma yace ma raihana ta dawo gaba, raihana ita tunda take bata taɓa shiga gaban mota ba, saboda lokacin data auri aminu baya da mota,

Raihana taƙi tashi , ya sake mata magana amma ta kasa motsawa, zulaihat tace haba ƙawata miye haka don Allah wannan babban mutum zai zama drivern ki?"" zo kiji, ta matso kusa da raihana tayi mata raɗa, bansan abinda sukace ba amma naga raihana ta tashi ta koma gaban mota,

tana shiga zulaihat ta rufe masu ƙofa, k"b yaja suka bar ƙofar gidansu zulaiha,

Lafiya suke babu wanda yayi ma wani magana, k"b ne yace muga wayarki, raihana ta miƙa mashi, amsar wayar yayi ya ɗan jujjuyata sannan yace wanne wayar kike riƙewa?"" raihana tace Eh, tsaki yayi sannan yace haba ai abun kunya ne ina tare da mai kyau kamarki kina riƙe wanann ƙaramar wayar,

saboda haka zan kawo maki waya mai kyau idan Allah ya kaimu gobe, raihana tace ai wannan sabune, yace nidai batai man ba gaskiya, raihana tayi shiru, haka yaci gaba da maganarshi wata ta bashi amsa wata kuma tayi mashi shiru har suka iso ƙofar gidansu , bayan yayi parking ne , yace ma raihana yana zuwa, fita yayi daga cikin motar yaje ya buɗe but, ya ɗauko wani abu, sannan ya dawo ya miƙawa raihana,

Nidai bansan ko miye ba, amma wani ɗan ƙaramin kwaline, raihana ta karɓa tayi godiya,, sannan tayi mashi saida safe, saida ta shiga gidan da suka kama haya yaga inda ta shiga sannan ya tafi,

Sallama raihana tayi sannan ta shiga, uma daga ɗaki ta amsa mata sallamar, raihana ta shiga, umma tayi mata sannu da dawowa, raihana tace yawwa daidai lokacin da take cire gyalen jikinta, ta raye a saman ƙofa, zama tayi dan ganin abinda k"b ya bata, umma tana cewa miye wannan ?"" raihana tace nima ban sani ba, amma bara mu buɗe mu gani,

Bayan ta buɗe ɗan ƙaramin kwalin daga umma har raihana zaro idanuwa sukai da sauri umma ta miƙe tsaye ta dafe girjinta dan ganin abinda ta gani , itama raihana gabanta sai faɗuwa yake, umma ta fara cewa raihana yaushe kika canja hali? Yaushe kika koma rayuwar da ba taki ba?"" wane irin rayuwa kika zaɓawa kanki haka"??""" ina kikaje kika samo wannan kuma?"" waye shi da har zai ɗauki wannan ya baki?"""kuma raihana cewa take wallahi umma bansan ko miye a ciki ba haka ya bani da nasan hakan ne ai da bazan karɓa, na ɗauka biscuit ne, umma tace keda yunwa ta ƙare maki ko?"" raihana tace umma ba haka bane, umma tace rufe man baki aikin mi kikai masji da zan ɗauki wannan ya baki??"""" wato kin fara halin da ake zarginki dashi ko?"" raihana ta fashe da kuma tace haba umma ki kyautata man zato don Allah wallahin banyi duk abinda kike tunani ba, idan kuma zatonki haka ne wallahi umma ki dubani na yadda kiga idan nayi iskanci, tunda nake wallahi ban taɓa zuna ba, tsaki umma tayi sannan tace faɗa man abinda kikai mashi ya baki wannan iyayen kuɗin...........................
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦

*Page* 2⃣6⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

****
*K*ukan da take ta tsagaita dashi sannan tace umma babu abinda nayi mashi kuma shima baiyi man komai ba, kawai dai ya ɗauko kuɗin nan ya bani ne,

Umma tace to ai so nake inji abinda kikai mashi ne, tunda nidai banga kin fita da wani abun siyarwa ba, raihana tace wallahi umma ki yadda dani babu wani abunda mukai dashi, zulaihat tace man yace yana so na, shine daya kawoni gida ya bani kuma yace zaima canja man waya ,

Ajiyar zuciya umma tayi sannan tace to kidaiyi hankali dan idan anga mace na zawarci kowa kallon sakara marar kamun kai yake mata, kinga dai kin taɓa aure hukuncin zina ga wanda ya taɓa aure kisa ne, idan kuma kikaje kika ɓoye kikayi Allah ubangiji yana kallonki zai linka maki nauhin wahala wanda yafi wannan,

Raihana tace insha Allah umma bama zanyi ba wallahi, umma taci gaba da cewa kuma ga cututtuka sunyi yawa a duniya, kinga idan kikayi sakaci aka cuceki kinfa tashi aiki zaki rasa mai aurenki ne kiyi ta kanki kuma ki nema ma rayuwarkk mafita,

Raihana tace insha Allah, zama umma tayi sannan ta jawo kwallin kuɗin ciki ta fiddo ta fara irgawa, hankalin umma dai ya ƙara tashi ganin kuɗi zunzurutu har dubu ɗari biyar, umma tace raihana kinga yawan kuɗin tunda nake a duniya wallahi ban taɓa ganin ko dubu hamsin ba a hannuna, lallai idan dai da gaske yake kawai kice mashi ya turo,

Raihana tace insha Allah , haka dai umma taci gaba dayi ma raihana nasiha tare da nuna mata illar da zina take haifarwa da kuma masifar da mutum zai fuska idan yana aikata ta, haka dai sukaci gaba da fira jefi jefi , har bacci yayi gaba da raihana, umma taji tana ta magana ita ɗaya babu amsa, tace au ashe kinyi bacci ina ta surutu kamar radio, itama kwanciya tayi, tana tunani iri iri a ranta har baccin itama ya tafi da ita........................,

****
Da safe bayan raihana ta tashi tayi dan abunda zatayi, sannan tace ma umma bari inje gidan gwaggo in kwaso kayana, umma tace mata to, raihana tace umma ko ki bani cikin kuɗin nan inkai ma gwaggo ko 2k ne,?"" umma tace to bari in baki, inda ta ajiye kuɗin taje ta ɗauko, ta bata, raihana ta karɓa sannan ta fita daga gidan,

A gidan gwaggo raihana tayi sallama gwaggo tana shara tace ɗiyar nan ina kika kwana?"" ba tare data amsa sallamar ba, raihana tace ai mun dawo nan unguwar a gidan daka tsalle muka kama haya, gwaggo tace to ai najiki shiru ne, raihana tace kuma banyi dabara ba nace idan kinji shiru na wuce gda, gwaggo tace gaskiya,

Raihana gaishe da gwaggo tayi bayan sun gama gaisawa ne, raihana ta bata kuɗin tace umma tace a baki, gwaggo tace na miye?"" raihana tace wai kawo mata akayi shine tace bara ta kasafeki, gwaggo ta ansa sai godiya take, raihana ta shiga ta tattaro kayanta sannan tayi ma gwaggo sai anjima ta fita daga gidan,

tana fitowa taga badiyya wato uwar ɗakinta da sukai faɗa wanda mijinta yakai raihana asibiti lokacin da tayi rashin lafiya, raihana na ganinta ta cika fuska ta ɗauke kanta, dan ta tsani badiyya tun lokacin da taxo har gidansu tayi mata wulaƙanci,

Dariya badiyya sannan tace daga baya kenan anyi sadaka da karuwa, aikin banza mijina dai yafi ƙarfinki haka za"a balbaɗe ba"a gidan ango ba"agidan amarya, keda mijina kuwa sai gani sai hange,

Tsaki raihana tayi sannan ta juyo tace, aikin banza karw da gudun layya, aike ba namiji kike aure ba, kuma baki cika mace ba da har mijinki zaiga mace yaji yana santa a ranshi, baki iya kula da miji ba shi yasa har yaga wata yaji ta mashi, toni idan baki sani ba ki sani idan kuma kin sani ki ƙara sani, mijinki yaman datti sosai na farko baya wanke baki bare insa ran idan na aureshi zanji daɗi idan ya sumabaceni, baya wanka shi yasa idan ya tun karo mutane suke kauda kansu dan wari yake,

kiji ki tsaftace shi sai kixo kiyi kishinshi, banza wanda baki ajiye komai ba sai shegen kishi da ƙazanta,

badiyya tace Ey naji dai kuma babu ke ba mijina har abadan duniya, raihana tace a banza anma kare wanka, na gaya naki lalurarshi, amma idan ya gyara yazo yabi layin *zawarawa* tana faɗin haka tayi gaba, badiyya ta tsaya a wurin sai zage zage take, raihana dai ba ta sake bin ta kanta ba,

*****

bayan sallahr magrib zulaiha tayo ma raihana waya cewa ga k"b nan zaizo ashe jiya bai karɓi number inta ba, raihana tace E cewa yayi ya raina wayana, dariya zulaiha tayi sannan tace k"b kenan ai shi komai nashi yasha banban, raihana tace shin nidai ina jiran zuwanshi, zulaiha tace to, sallama sukai da juna sannan raihana ta kash wayarta,,,,,

Wayar ta ajiye sannan tace bara taje tayi wanka, umma tace wanka kuma?"" raihana tace E umma baƙo zanyi, umma tace eh lallai a bada himm, dariya raihana tayi sannan ta fita ta zuba ruwa a rober ta ɗauka ta nufi bayi,

bayan ta fito daga wanka sallah isha"i tayi bayan ta gama ta shiga shirin tarar baƙonta,

shiri tayi cikin baƙar rigar da farida ta bata, tayi kyau sosai abinka da farar kala sai raihana ta fito kamar wata balarabiya, ta haɗu iyakar haɗuwa, dan idan raihana ta samu hutu gaskiya zaiyi wuya ka ganta kace tasan wani yare waishi hausa, kana ganin ta labarci zaka fara mata dan tafi kama da larabawa,

ta gama shirinta tsaffa ta koma ta zauna tana jiran zuwan rabin ranta, wato k"b,

wai waye wannan kabir ɗin?"" kabir sangartace ne ya taso ne babu kwaɓa babu kyara a wurin iyayenshi duk abinda yayi mai kyau ne, kuma k"b bayajin magana, yana da "yan canjinshi a hannunshi saboda haka baya san zama da mace sama da ɗaya, dan bature ne sosai, amma kwallon ɗan iska ne, zai iya kashe ma mace kuɗi dan kawai ya biya buƙatarshi ya wuce wurin, dan idan ya saka mace ƙahon zuƙa sai ya zuƙeta sannan zai samu kwanciyar hankali ,

k"b matarshi ɗaya itama bada niyyar aurw yaje ba, iskanci yakai shi iyayenta suka riƙe mashi wuya gam saida ya aureta, hmm k"b ya kware wajen iya yaudara, tantirin ɗan iskane na bugawa a jarida, duk yanda zan faɗa maku halinshi baza ku gane ba amma ku bari muje cikin labarin tarayyar shi da raihana muji,

wai ance raihana taxo, raihana cikin zaƙuwa tace jekace ina zuwa, ta miƙe da sauri jikinta sai karma yake,

umma ta kalleta tayi tsaki sannan tace ki daina wannan rawar kan, ki matse ajinki sosai, kuma ki daina yawan dariya dan dariya ta zubda mutimci idan tayi yawa sosai, kuma tunda ance ana kiranki sai kibi a hankali kuma ki bari yaron ya tafi idan ya daɗe saiko fita, , raihana tace to, umma taci gaba da cewa bari ganin ya ɗauki kuɗi haka da yawa ya baki idan kika saki jiki yana iya tadaki aiki ya barki da raba, raihana ta jinjina kanta alamar gamsuwa, sannan umma tace jeki,

raihana ta fito jiki a saɓule, tayo waje, inda ya ajiyeta a jiya a wurin yake ya haske ƙofar zaurensu da hasken fitalar motarshi yana cikin motar bai fito ba,

Tafiya raihana taci gaba dayi, shi kuma yana cikin mota yana hangenta, hannushi ɗaya ya riƙe sitiyarin mota ɗaya kuma ya riƙe haɓarshi, idanuwanshi ya sake warewa ya ƙura ma raihana ido,

ajiyar zuciya ya sauke sannan yace ikon Allah "yar yarinya ƙarama da ita, amma tana da haluttu

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login