Showing 45001 words to 48000 words out of 98315 words

Chapter 16 - ZAWARCI

06 Oct 2024

8027

shawara ɗaya zan baki,

Shawarar kuwa itace, kiyi haƙuri ki zauna lafiya kuma kiyi ma mijinki biyayya, danshi aure ibada ne, kuma ibada mai girma abu kaɗan kika kuskure sai ki faɗa ma wahala,

To kiyi haƙuri akan rashin sanin waye mijinki na tabbata tunda kina da haƙuri zaki iya zama dashi insha Allah ni ina kyautata maki zato,

ni nan nine nayi maki shishshigi a rayuwa ba tare da saninki ko yardarki ba, bayan labari yaxo kamar yanda naji a wurin taron ɗaurin aurenki cewa wanda zai aureki yace ya fasa wai ance ke karuwa ce, wani k"b ya kira ya faɗa mashi,

to ni kuma naje wurin ɗaurin aurenki ne, dan faruk ya taɓa bani labarinki cewa har gidanku ya taɓa zuwa amma akace mashi anyi maki aure, to wannan dalilin ne yasa inajin ance an fasa aurenki banyi ƙasa a guiwa na bada sadakin aurenki,

ni ba babanshi bane, kuma ba kowa nashi bane, kawai dai yaron yana da mutunci da mutum tawa ne, ni maƙocinsa ne, amma ya ɗaukeni kamar uba, dan haka ina baki shawara kiyi haƙuri kiyi zamanki lafiya, amma faruk yana da zuciya dan haka sai kiyi karatunsa dan sanin yanda zaki zauna dashi,

Raihana tace na gode sosai, haka dai ya ɗan ƙara mata nasiha sannan ya tashi ya tafi, itama raihana haka ta tashi ta koma ɗakinta jiki duk babu daɗi,

*WAYE FARUK AHMAD HUKUMA*

Hmmm faruk su biyar a wurin mahaifiyar sa, mata huɗu shi ɗaya namiji, babanshi tun daga mahaifiyar faruk bai sake aure ba, haka suke zamansu cikin mutunci da lumana,

kuma Ahmad hukuma wato mahaifin faruk shahararren ɗan kasuwa ne yana da kuɗi na ban mamaki, kuma ya daɗe da rasuwa, faruk ya ɗauki duk komai na mahaifinsa yana kulawa dashi ma"ana bayan rasuwarsa yaci gaba da irin harkokinsa,

amma ƙannensa suka tada ƙayar baya ya fitar masu da haƙƙinsu haka aka raba gado aka bawa kowa haƙƙinsa kamar yanda addinin musulnci ya tanada,

To faruk tun kafin mahifinsa ya rasu shi dama yake sha"awar akin soja, dan haka mahaifinsa ya tsaya ya dage kai da fata don biyama ɗansa burinsa,

to daya samu aikin soja kuma ya fito babba sosai , bayan mahifinsa ya rasune ya samu wani abokinsa mai gaskiya da amana ya ɗora shi dan ya riƙa kula masa da harkokin, amma shima yana zuwa idan ya samu lokaci, aikin soja ya karɓi faruk sosai yana ta samun ƙarin matsayi sosai,

Faruk ɗan gayune, ma"aboci san kamshi kuma faruk yana da kyau sosai, ganin kyau da Allah yayi mashi kuma ga kuɗi suna gaya mashi ƙarya ga kuma mulki yana ƙara hayaƙa mashi kai yasa faruk ya ɗauki rayuwa wulaƙanci da raina mutane,

ya kasance mabuƙaci ne faruk yana da yawan sha"awa sosai amma baya zina, wannan dalilin ne yasa shi ya ɗauki rayuwar auri saki, daya ga mace yana so zai auro ta, yana gama goge ta zai bata raset,

Lokacin daya ga raihana hankalinsa ya tashi yaji kamar zai haukace, saboda haka yayi alƙawarin saiya auro ta, amma a lokacin da yazo gidansu akace mashi tayi aure , wannan ne yasa yaji baƙin ciki har yaje ya bawa maƙocin sa labari wato wanda ya auro masa raihana,

shi kuma abokin alhaji ne, yaje ɗaurin aurene yaji wannan abu don haka yayi ƙoƙari ya auro masa ita,

kam tsaya muga raihana yanda ta zaunu gida da zawarci zata iya saita faruk kuwa?"" ku byoni muga irin kaifin basira nata,

**
Ci gaban labari,

***

Da safe raihana haka ta tashi tayi sallah , bayan ta gama sallah ne, tabi ɗakin ta da kallo, hawaye ya gangaro daga idonta, tace ikon Allah masu kuɗi sunajin daɗinsu

wannan ƙaton gado duk na mutum ɗaya ne, tace O ko toilet ma ai yafi girman gidansu, gashi an ƙawata shi da kayan "yan gayu, dan sakata wanka ma sai an shiga kwami za"yi, ta sake cewa ikon Allah , ita umma yanxun tana can baiwar Allah niko ina nan cikin daula, haka lamarin Allah yake, haka dai raihana tabk gidan tana zagayawa daidai inda take iya zuwa, ta gaji ta dawo parlou, ta zauna, kallon ƙatuwar tv da take maƙale a jikin bango tayi taga daga bango har bango raihana tace taf muko a gidanmu ko ta girke bamu dashi,

Haka ta miƙe tayo cikin ɗaki ga yunwa tana ji ga bata san kowa ba, kuma bata da number kowa kuma bata san a ina zata samu abinci ba, haka ta haƙura ta dawo ta kwanta,

Bacci raihana take sosai, bata ma san rana tayi haka ba, tana cikin baccinta taji an kai mata wani irin halbi, da sauri raihana ta miƙe dan ganin wane ɗan rashin kunya ne, kafin ta gama miƙewa tsaye taji tana cewa ke ɗiyar matsiyata "yar gidan talakawa har kin samu wuri da zakizo ki sake jiki kina bacci?""

To ai dan uwarki munji labari a gidan naku kamar yanxun idan ba wankau kike ba, to kina can kasuwa wurin siyar da abinci, nan har kinzo kin samu wurin hutu?""

To ki sani yaya faruk yafi ki iskanci kuma ni nasan bazai yadda yazo ya zauna dake ba, sakaran banza ƙazama dake, aimu babu abinda zamuce da wancan baƙin munafikin sai Allah ya isa, dan nayi imani da ɗansa ne na cikinsa bazai yadda yaje ya auro mashi ƙaruwa kamarki ba, to ki saurara da kyau ki jira zuwan yaya idan ya iso gari yau wallahi kashin ki ya bushe,

dan mata ma masu asali da kuɗi yaci uwarsu ya korasu bareke kayan banza, jiki?"" tana nuna raihana da hannu, banza mizai so a jikinki?"" idanuwan ko gashin, kina wani zare ido kamar kinyi karo da kura, duk abinda kike taƙama dashi wallahi yaya faruk ya fiki,

mi kike dashi kyau?"" to yafi ki?" baki da gayu dan bazan ma haɗaki dashi ba, danshi kaff ƙasar nan kafin a samu ɗan gaye irin yayana sai ansha wuya,

Jaka dake, idan zuciya gareki shi idan ya shaƙe sai yaji mutum baya lunfashi yake saki, ƙara kaiwa raihana harbi tayi sannan tace idan yaxo anjimar kinyi mashi bayani danni wata ɗaya na baki a gidan nan,

ɗaya daga cikinsu tace dakata "yar uwa, ƙafarta ta ɗora saman gadon raihana sannan tace kinsan duk abinda zakai da jaki sai yaci ƙara abinda nake dake shine mu anan gidan ba"a wankau sannan kuma ba"a kawo maza dan dake da kwaratan naki duk yaya zaiyi kaca kaca da kanku da bindiga dan shi ana mashi iskanci aikin shi kawai shine sheƙewa, a daidai lokacin da take nuna kan raihana kamar dai an saita ta da bindiga, tace a wannan jakar kwalwar bindiga zata shiga tayi ma ƙoƙon kanki kaca kaca,

hawaye sai zubowa yake daga idon raihana, haka dai suka ƙaraci wulaƙancin su sannan suka jefo mata kuɗi suna cewa maza ɗauki ƙarya nadai san tunda ake a duniya ba"a taɓa ganin irinsu ba, driver zaizo anjima a ɗauke ki a wanko wannan jakin kan, a wanke ƙafafuwanki a yanke maki farci, dandai kin zama matar yaya da nace akaiki ayi maki wanka tsarki, amma ki tabbatar idan kin dawo kiyi wanka mai kyau,

wani ƙaton akwati aka ajiye ma raihana ga kayan da zatayi amfani dashi da turaruka da duk abinda zata buƙata, sannan tace Allah dai yasa kin iya fesa turare?"" dan kinsan shima iya shafawa ne,

haka dai suka ƙarw wulaƙancin su sannan suka tafi, suna fita raihana tayi ajiyar zuciya sannan ta kifa kanta a katifa tayi ta kuka,

Wata zuciyar tace raihana ki tafi, "yan uwanshi sun maki wannan wulaƙanci ina ga shi Ogan yaxo?""

wata zuciyar kuma tace ke banza rufa ma kanki asiri kinji, kin manta baƙar akubar da kika sha a zaman zawarci?"" haba raihana kada ki bani kunya mana kamar ba mace?"" kwantar da hankalinki kiyi amfani da dama ki saki jikinki sai kin mayar da faruk kamar bawanki,

wata zuciyar ta sake cewa na haneki, mutum mai zuciya ai baya zaunuwa, tsaki raihana tayi sannan tayi magana a bayyane tace ƙarya kake, raihana zata ɗora ka saman makarantar da baka taɓa shga irin ta ba,

kuma duk matan daka saka su daban raihana daban kuwa da irin yanda ta iya kula da rayuwar aure, dan raihana taci ɗamara zan zamar maka karuwa kamar yansa akace amma ta cikin gida zaka ga tsantsar rashin kunya wajen kula dakai sannan kuma zanyi haƙuri , har zuwa lokacin da zan anshi matsayi a wurin ka,

wata munafikar dariya tayi sannan ta miƙe taje tayi wanka ta shirya, ta zauna tana jiran zuwan driver,

ta daɗe da gama shiri sannan aka zo aka tafi da ita, mai tuƙa motar sojane, raihana an kashe a gidan baya,

yanda sojan yake bawa raihana girma da biyayya yasa raihana tace a ranta ai raihana taxo bata komawa wallahi,

haka suka tafi har wurin wankin kai idan akace yakai raihana, acan aka wanke mata kai aka wanke mata ƙafarta, aka gyara mata farce, aka funfa raihana ta finfo, har yanxun driver n baifa tafi ba, ana gamwa raihana ta fito, jakar hannunta ya karɓa sannan ya buɗe mata ƙofa ta shige sannan yaja suka fece daga wurin,

raihana tace lallai mai girma da girma yake, murmushi tayi sannan tayi magana a zuciyarta tace ke raihana ajiye girman kai kiyi ma rayuwarki yaƙi, kici arziki har na kusa dake su samu,

Mata mu kula da wani abu ɗaya, wai sai kiga miji da mace a waje kafin ayi aure suna kaunar junansu amma da anyi aure sai wulaƙanci da rashin mutunci a tsakaninsu, kuma wannan ba sakacin kowa bane sakacinmu ne wallahi,

Abinda kike a gidanku idan kinzo gidan aure kin daina, babu tsafta babu gyara komai a barshi tun a zaure wurin zance, kuma kina zuwa kika fara aihu ƙazanta saita ƙaru,


kula da mijinki sai kice wai kunya kike ji, ta kunya ai ta ƙare tunda ya aure ki duk abinda kike ɓiyo kada wani ya gani shi ya gani, yasanki yajiki to miye abun kunya, don Alƙah fa sai mun fitar da girman kai idan har muna san mu zauna lafiya,

Kuma wani sakaci da muke waisai kiga mace bata iya neman mijinta ita a dole mai aji ce sai idan shine ya nemeki, kuma idan ya nemeki sai ki tsaya kina girman kai waike sai kin wana shi, kuma wannan abun da muke wallahi kanmu muke jama raini miji yaji ya tsaneki,

tunda shi sex ba"ayin shi dole sai da amincewar juna, idan anyi ta ƙarfi ko rashin amincewar juna shi baiji daɗi ba, kuma ke bakiji daɗi ba, shi da yayi yana wahalce kema a wahalar kike, bayan mijinki ne, lada zaki samu , idan kin wulaƙanta mijinki mi kikayi, sai kiji mace taje ta haɗu da abokanta tana cewa aini mijina kaza kaza ,idan zai sadu dani saina ja mashi aji sai yayi biyayya kaza kaza, wallahi ba mijinki kikai mawa ba, kanki kikai mawa, kinga ga zunibi a wurin Allah sannan kin rage ma kanki ƙima da marta ba wurin mijinki,

Idan kin hanashi idan wanda Allah bai tsare bane daga nan sai ya fara neman mata idan ke baki so wata tana can tana buƙata sai ya barki da kayanki kin huta, daga nan sai tsya sai kuma ki tashi hankali ki ɗauki makaman yaƙi wai dashi kuma zakiyi adawa, to kina nan kina sakarci wata zata kwace maki a barki da haukan banza, don haka don Allah mu gyara idan muna san ci gabanmu, da kuma samun tsira ranar gobe ƙiyama, Allah yasa mu dace amin,

raihana suna dawowa gida , da sauri ya fito ya zagoyo ya fuɗe mata mota, yana ta bata girma da girmamawa, jakarta ya riƙe mata tana gaba yana bin bayanta har cikin gida, saida ta shiga parlou shima ya shiga ya ajiye mata jakarta a saman kujera sannan ya fita,

Yana fita raihana tace ikon Allah wani aikin sai manya, wani irin juyi tayi sannan ta kalli agogon bangon parloun ta taga 6:02pm, da gudu tayo ɗaki ta shige bayi dan yin wanka, baya ta gama ta fito ta fara shirin ta, kayan da aka nuna mata ta saka sune taci gayu cikinsu, haka ta ɗauri turare ta fara fesa shi wuraren daya dace, dan akwai idan turare yafi buƙatar a shafashi, shima zamu xo wurin,

bayan ta gama shirin ta tsaf ta koma parlou sauran abincin da ta taho dashi daga wurin saloon ta ɗauka taci, bayan ta gama taje ta wanke bakin ta , sannan ta haye gado tayi kwanciyarta,

Bata daɗe da kwanciya ba, bacci yayi gaba da ita, bacci take sosai can cikin bacci taji ƙarar buɗe get ƙarar motocine kawai kake ji suna shigowa, har yanxun basu lunfasa ba, raihana gaban ta yaci gaba da faɗuwa taji kamar fitsari zai zubo mata, wani irin tashin hankali taji lokaci guda kuma zufa ta fara kwararo mata, wata zuciyarta tace haba raihana kada ki bani kunya mana bare har ki sagar ma sauran mata da guiwarsu, sai kace ba mace ba?"" kiyi amfani da irin baiwar da Allah ya baki dan ci gaban rayuwarki,

Tashin hankalin raihana ya ƙaru lokacin dataji ƙarar buɗe ƙofar farlo, wani irin kamshi taji ya fara isowa inda take, jikinta ya fara ƙarma, da sauri ta koma ta kwanta sannan ta lulluɓe kanta cikin bargo,

Kar kuce nayi maku ƙarya nace bazanyi typing ba nayi, na samu dama ne, kuma na dawo lafiya na gode sosai da saƙon fatan alkairin ku yanda yayi ta zuwa man kai tsaye Allah yabarmu tare,

Jameela musa nake cewa ku kasance tare dani,
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦

*Page* 3⃣4⃣

*AMEENCI WRITER"S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

****
*Masoya littafin YA ABUN YAKE? Ina baku haƙuri ashe bata gama ba, kunji ni da zumuɗi to ina baku haƙuri don Allah bata kammala ba, sai kunyi haƙuri dan naɗan kwana biyu ne pha,*

***

*KISSAR MAGANA*:• "yar uwa ba"a magana da miji cikin tsawa kuma ba"a magana da miji cikin kururuwa da hayani,

Mace bata ɗaga muryarta tafi ta mijinta duk inda mace take da mijinta tana yin ƙasa da harshenta, tana rage zaƙin muryarta tayi sanyi da muryarta ta rinƙa marairaicewa tana maganar cikin kwantar da murya tana lanƙwasa harshenta cikin salon iya kissar magana,

Ta marairaice muryarta tayi ƙasa da ita tayi sanyi kamar mai shirin yin kukua, sai ko rinƙa tausa murya kina yin maganar cikin tattausan lafazi ƙasa ƙasa kamar kina yi masa raɗa,

Maganar da idan kinayi zai tattara hankalinsa ya mayar gareki saboda kin tsumashi da tattausan lafazinki , kin gigitar dashi da daɗaɗɗar muryarki,

Zaki ga idan har kina maganar baya so yaji kin daina, domin yana jin muryar taki tayi masa daɗi sosai,

"yar uwa a kula a yi ƙoƙarin tausasa harshe, ba ki rinƙa ɗaga murya kina hayani ba kamar kina tare da mai gadi ko "yar aiki ba,

Dan kinsan hakan bai dace ba, saboda girma da matsayi da Allah ya bawa miji a kan matarsa,

Don manzan Allah cewa yayi, ```da za a yi wa wani sujjada bayan Allah da mace zata ce zatayi wa mijinta""```

Wuri ɗaya ne akace kada kibi mijinki , idan ya kauce hanya,

Allah yasa mu dace```

*ZAWARCI HAKURI RIBAR AURE*

*****
*T*ana cikin bargo sai mazurai take kamar munafika, shi kuma ya shigo cikin ɗakin baki ɗaya,

Wayarshi ta fara ƙara, bayan ya duba mai ƙiran ne ya ɗauka, hello, yana faɗin haka ya fita daga cikin ɗakin , yana fita tayi ajiyar zuciya, sannan ta goge zufar data ƙwararo mata,

Shi kuma yana fita a parlour ya zauna saman kujera 1seater ya ɗaura ƙafa ɗaya saman ɗaya, bayan ya gama wayarne, ya miƙe ya nufi hanyar ɗakin shi,

Ya daɗe a cikin ɗakin sannan ya fito, ya fita waje, bayan wani lokaci ya dawo dashi da mutumin da yayi jagorancin auren raihana, a parlour suka zauna dukansu, kowa ya kame saman kujera,

Shiru ya ratsa na wani lokaci sannan alhaji wato wanda ya auro ma faruk raihana, yace ina ƙara baka haƙuri a bisa shishshigin da nayi maka, na auro maka yarinya ba tare da izininka ba, dan naji kacr man kaje wurinta,

ni kuma jin ance an fasa aurenta na auro maka ita, amma don Allah kayi haƙuri na roƙeka, ajiyar zuciya faruk yayi sannan ya jingina bayanshi da jikin kujerar ya ɗauki ƙafa ɗaya saman ɗaya ya sake harɗe su,

Robar ruwan dake gefensa ya ɗauko ya zuba a kofi yasha, bayan yasha ne ya ajiye kofin ne, yace Alhaji tunda nake baka taɓa man abinda banji daɗinshi ba, kuma nasan babu abinda nake boye maka,

Amma gaskiya wannan karon an samu matsala, a daidai lokacin da raihana taji wannan maganar da sauri ta sauko daga saman gado dan taji abinda faruk zai faɗa akanta,

Yaci gaba da cewa nidai kasan ban zina kuma bana tare da mazinata, tsakani da Allah nikam bazan iya zama da karuwa ba,!!!!""" gaban raihana ya faɗi "yan cikin ta suka yamutsa, faruk yaci gaba da cewa,

"yan uwana sun kirani sun faɗa man komai , nasan nine nace maka naje wurin ta, haƙiƙa naje kuma ban samu haɗuwa da ita ba, danni a lokacin an gaya man tana da natsuwa da kamun kai, bayan nan ne ta sake hali, to gaskiya nidai kayi haƙuri bazan iya zaman da ita ba, danni ina kyamar mazinaci tun kafin in ganta naji na tsani rayuwarta ban santa,

Alhaji cikin rawar murya yace kayi ma Allab faruk ka rufa man asiri kada ka rabu da yarinyar nan kayi man alƙawari, faruk yace gaskiya bazaka samu wannan ba, Alhaji yace dan girman Allah kada kama haka ka taimakeni dan darajar manzan rahma, S. A. W,

Faruk yace naji amma ka sani wata ɗaya na bata a gidan nan, da tayi su zan korata ta koma daga inda ta fito, Alhaji yace wata ɗaya yayi sauri ka taimakeni don Allah, faruk yace baka san matsalar dana samu da mamana ba kan wancan yarinyar,

alhaji yace kayi haƙuri kabarta ko zuwa 2month ne data cika hakan ni da kaina zanzo in tafi da ita kafin kaxo,

Faruk yace ka yadda?"" yace na yadda, faruk ya sake cewa kayi alƙari?"" alhaji yace nayi alƙawari!!!! Faruk yace babu damuwa, Alhaji yayi godiya sannan ya tashi ya tafi,

Raihana tanaji Alhaji ya fita, da sauri ta ruga ta haye saman gado, tana jinjina wata biyu zatai a gidan nan, hawaye ya zubo mata daga idon ta, ta goge tace lallai haka maza zasu riƙa man wasan kura da rayuwa?""

tace lallai sakayya

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login