Showing 3001 words to 6000 words out of 98315 words
lafiya, raihana tace sai kin dawo a daidai lokacin da take kwanciya saman tabarmar kaba,,,,,,, umma ta fice tabar ɗakin,,,,,,
������
*zawarci*
������
*Raihana* tana kwanciya ta ɗaga kanta sama tana kallon izarar ɗakinsu, wasu hawaye masu zafi suka zubo mata, ajiyar zuciya tayi sannan ta gyara kwanciyarta saman hannun ta na dama,,,,,,,,,,,,,,, abinda ta fara tunawa,,,,
��������
*rayuwarta*
��������
*Khadija* shine ai nahin sunan *raihana* babanta malam ibrahim, da ɗan kasuwa ne, ya ɗan riƙe kuɗaɗe babu laifi, daga baya Allah ya kawo mashi karayar arxiki, matan malam ibrahim biyu, binta itace babbar matarsa wanda suke kira da gwaggo, tana da "ya"ya, basai na tsaya lissafo su ba, halima itace mahaifiyar raihana, wanda suke kiranta da umma, umma ta haihu sosai amma Allah bai bata wasu rayuwa ba sai kan khadija, wanda aka sakawa sunan maman malam ibrahim, yayarta ɗiyar gwaggo itace take kiranta da raihana, saboda haka shine dalilin da yasa kowama ya kekiranta da haka, dan yanxunma sunan ta ya ɓata saidai *raihana*
Gyara kwanciya raihana tayi sannan ta goge hawayen da suka zubo mata,,,,,
��������
*zawarci*��
��������
Ku biyo ni sannu a hankali don Allah donjin labari *zawarci*
Ina maku fatan alkairi masoyana , ku biyo ni sannu a hankali don jin wannan labari, *ameenxi writr's association* a shirye muke wajen ƙawata maku da daɗaɗa maku din farin cikin ku,
*jameela musa* ke cewa ku kasance dani lafiya,,,,,,
07060797938, a shirye nake da jin ƙorafinku ����
[15:02, 08/11/2017] +234 813 308 2423: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����
*page* 5⃣
*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��
*JAMEELA MUSA*
����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*
*gargaɗi a bisa wata ƙungiya, da bama buƙatar saka sunan ta, dan haka muna roƙonsu dasu guji juya mana littafi ta ko wace fuska, idan kunne yaji ���� jiki ya tsira* ����♀
������
*ZAWARCI*
������
*B*ayan ta gama goge hawayen da suka zubo mata a ido, ta tashi zaune ta zabga tagumi, sannan ta ɗora kanta saman guiwarta,,,,,
*zawarci*��
Malam ibrahim mahaifin *raihana* shine yayi kyautar raihana ga wani yaronshi mai suna aminu, yana da kirki sosai, ya bashi raihana ne, saboda ya matsa mashi yana santa, shi kuma ya bashi raihana saboda ya yaba da hankalin aminu,,,,,,
*to haka baba ya bawa *aminu* auren raihana, ansha shagali sosai kuma aminu yayi hidima saboda yana san raihana kuma komai zai iya yi, saboda ita idan dai abun baifi ƙarfinshi ba,,,,,,,,
��������
*zawarci*
��������
*Raihana* da sauri ta goge hawayen idon ta dan kiran sunan ta da taji gwaggo tanayi,,,,, ba tare da ta amsa kiran ba, ta tashi ta fito tsakar gida,,, kallo tabi gwaggo dashi har yanxun batayi magana ba,,,,,,,
Gwaggo tace, wallahi tun ɗaxu nake neman wanda zai kai mana niƙa ban samu ba, raihana ta ɗaure fuska sosai sannan tace idan baki samu mai kai niƙa ba sai akayi me?"""" gwaggo tace wannan ɗaure fuskar naki bazai hana ince kije kikai ba, tunda ba"a samu yaron aike ba,,, kam raihana tace, sannan tace lallai gwaggo kinzo da abinda baya yuwuwa, gwaggo tace ai dan zai yuwu nayi magana, saboda haka sai kinje, raihana tace bazanje ba,,,, sallama umma tayi ta shigo gidan, a daidai lokacin da gwaggo take cewa da kina gidan mijinki zanje in kiraki kikai niƙa ne?""""
*t*saki raihana tayi sannan tace aike kina so kiyi man gorin aure, bayan nasan idan lokaci yaxo sai nayi, gwaggo tace wannan kuma matsalarki, dan wallahi idan baza kikai niƙan nan ba, yau bazanyi tuwon nan ba, saidai ubanki ya kwana da yunwa,,,,, umma tace ɗauki kije kikai ɗinƙan kinji,,,,, raihana zatayi magana umma ta dakatar da ita, ta hanyar cewa ba komai wata rana sai labari, gwaggo tace ba labari ba koma b.b.c ne ina ruwana,,,, ta juya ta wuce ɗakinta, inda gwaggo ta ajiye buhun niƙan da kuɗin raihana taje ta ɗauka sannan ta fita daga gidan,,,,,,,,,,
��������
*zawarci*
��������
Raihana sai Allah ya isa take har takai shagon niƙa,,,,, mai niƙan ya kalleta ya bushe da dariya, sannan yace baiwar Allah ke aka aiko?""" rahaina bata yi magana ba, ta haɗa hannuwanta ta rugummesu a ƙirjinta,,, mai niƙan yace ni wallahi da zaki yadda kawai in fito muyi aurenmu in rufa maki asiri tunda shi aminun ya kasa,,, ko inda yake raihana bata kalla ba, dariya yayi lokacin daya ɗaga buhunta ya juye masarar a cikin inji, yaci gaba da cewa matana ukku yarana ishirin da biyar, kallon ƙasa da sama raihana tayi mashi, wata irin dariya yayi sannan yace Allah sarki irin wannan kallo ai sai kisa mutum yayi fitsarin zaune dan daɗi, tsaki raihana tayi ta duƙar da kanta ƙasa har ya gama niƙan,,,, ta ɗuka zata ɗauka da sauri ya riƙe yace bari insa akai maki, raihana ta saki, kuɗin ta miƙa mashi yace tabarsu, yana yashe baki yace wannan toshine, murmurshin baƙin ciki raihana tayi taji kamar zuciyarta zata fashe wato da niƙa za,ayi mata toshi,,, yaronshi yace ya ɗauki niƙan yakai gidansu, yaron ya ɗauka yayi gaba, raihana tafi bayanshi, mai niƙa sai ɗago hannu yake yana cewa sai yaxo cin tuwo anjima,,,
��������
*zawarci*
��������
*raihaina* haka tabi bayan yaron tana zance zuci, lallai waƙƙahi mutumnn nan ya raita mata, hankali, addu"ar ta ɗaya kada yazo gudansu dan babanta yana iya cewa ya turo, tunda dama kullum sai yayi mata maganar tayi aure,,,,, a daidai lokacin da tayi sallama cikin gida,,,,
*zawarci*
Yaron ya ajiye niƙan ya fita, gwaggo ga niƙan nan, to aisai kiyi tankaɗe, raihana tace hada wani tankaɗe, tace E , taci gaba da cewa ai da uwarki ce idan tana aiki baki da zama sai kinga an gama, dariya ryhaina tayi sannan tace maida wuƙaƙen zan maki, a daidai lokacin data shiga ɗakinsu,,, hijabinta ta cire ta miƙawa ummanta kuɗin niƙan tace ki ajiye wannan , umma tace na miye?"" raihana tace nawa ne na baki, umma tace to, bayan ta nashi kuɗin ta fito tsakar gida ta fara kama ma gwaggo aiki,,,,,,,,,
��������
*zawarci*
��������
*W*ani yaro ne ya shigo da tsirin kayan wanki saman kanshi, sallama yayi sannan ya nufi inda raihana take zaune, kama mashi tayi ya sauke, sannan ya miƙa mata kuɗi yace ga kuɗin ruwa da sabulu, ta ƙarba ta ɗaure a haɓar zani tace idan Allah ya kaimu jibi ku dawo ku karɓa, yaron yace to, sannan ya fita daga gidan,,,,,
*zawarci*
Gwaggo tace raihana wannan wanki ma ai babu wani datti sosai, raihana dai bata yi mata magana ba ta ɗauki kayan mutane ta nufi ɗakinsu dashi, bayan ta ajiye ta fito suka ci gaba da aiki,
��������
*zawarci*
��������
Tunda safe gwaggo tazo kofar ɗakin su raihana ta riƙe ƙugu, tana cewa ki fito ubanki babu lafiya ki kawo kuɗin wankin nan inje in siyo mashi magani, daga ɗaki raihana tace wane irin kufi kuma?"" wanda kike tarawa a daidai lokacin da ta yaye labulen ɗakin ta siga ciki, raihana tace to gaskiya banda wasu kuɗin ni da zan bayar, gwaggo tace kina dasu, raihana tace faɗa man abinda nake siyawar, gwaggo tace wanki mana kina nan kin tara kuɗi dake da uwarki kin boye, dariya raihana tayi sannan tace baki son muna tara kuɗi gwaggo?""" tsaki tayi gwaggo sannan ta fita tabar ɗakin,
*zawarci*
Umma tace idan kina da kuɗi ki bata mana, raihana tace barta, zanje wajen baban dakai na, umma tace to, miƙewa raihana tayi ta fita daga ɗakin, ɗakin baba taje ta shiga tare da sallama, ya amsa , kusa dashi taje ta gaishe shi, ya amsa sannan tace baba miye ya sameka??"" baba yace mura nake, amma da sauƙi yanxun zan fita, raihana tace to Allah ya ƙara sawakewa, baba yace amin, raihana ta miƙe zata zata fita shima baba ya miƙe ya biyo bayanta, yana cewa mamana ki fito da miji kiyi aura kinji ko?"" to kawai tace tayi gaba, shima fita yayi daga gidan dan tafi wurin aiki......
������
*zawarci*
������
Raihana tana fitiwa ɗakinsu ta shiga ta fiddo wankin da zata yi, ta fara wankinta, *zawarci*
[21:18, 08/11/2017] +234 813 308 2423: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����
*page* 7⃣
*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��
*JAMEELA MUSA*
����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*
Wannan shafinki naku ne, *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION*
Godiya ta musamman, *ASMEENAT XEEYAN* ��
*Y*ana fita tafi bayanshi da harara tace banza sakarai,,, kwanciya tayi tare da jawo bargo ta lulluɓe, taci gaba da baccin ta,,,,,
*A*minu kuma yana zuwa ɗakinshi gado ya hau ya kwanta, ya fara tunanin wata ƙawar *raihana* da take masifar sanshi, ajiyar zuciya sannan yace Allah sarki itama haka take ji, yanda yake ji idan raihana ta wulaƙanta shi, gyara kwanciyar shi yayi sannan yace ita kuma babu ruwanta bata jin komai, a bayyane yace Allah sarki rayuwa,,,,,,
****** ƙarfe 9:30am ta farka daga bacci, saboda haka a hanzarce ta miƙe ta shiga toilet tayi wanka, bayan ta gama wanka ta fito, ta zauna a gaban madubi ta fara shirya kanta,,,,,,,,,****×
*A*minu yana ɗakinshi yaji ƙamshin turaren raihana, shima tashi yayi ya shiga wanka, bayan ya fito ya shirya cikin ƙananan kaya, sannan ya nufo ɗakin raihana, itama ta gama shiryawa, ta matse cikin riga da wando, yana shigowa ɗakin a siƙwane ya isa inda take, ta rungumota , ta baya, ya ɗora fuskarshi saman kafaɗarta, daidai saitin kunnenta yayi magana, kinyi kyau madam, cikin masifa ta ƙwace jikinta,, ta juyo ta nuna shi da yatsan ta,, sannan tace wallahi daga yau sai yau, idan ka kuskura ka sake tiƙeni , ban yafe maka ba, dariya aminu yayi sannan ya sake matsawa kusa da ita, ya ƙara tallafo ƙugunta, ya ɗora hannuwanshi a saman ƙirjinta, raihana tace Allah ya isa ka taɓa, dariya ya sake yi sannan yasa hannunshi cikin rigarta, da sauri ta ciro hannu sannan ta ɗunƙule hannunta da niyyar kai mashi nushi yayi sauri yaja da baya,,,,,,,,,,
*H*aba madam ya kamata ki kawo man ɗan abinda zanyi break mana,,, raihana tace kaji wani sakarci kuma, madam sai kace wata inyamura`?"" Aminu yacd wallahi ba inyamura kike ba,,,, raihana taci gaba da cewa wallahi har inbar gidan nan bana girki kaji na faɗa maka, dan daga yau ka fara lissafi sati ukku zanyi gidanka, aminu yace Allah ya sawake, ni bana sakin mace duk abinda tayi man, raihana tace baka haɗu da irin raihana ba, dan wani abun idan nayi maka kai da kanka zaka rubuta saki ka bani, kuma idan kazo bani saika duƙa,,, aminu yace to Allah kada ya nuna mana ranar,,,, taɓe baki tayi sannan tace ka kawo man abinda zanyi kalaci, yace bara in dafa maki, ko inda yake bata kalla ba, shi kuma bai sake magana ba ya fita yabar ɗakin"""""""
*A* kicin haka ya zuge yaci gaba da aikin haɗa masu abinda zasuyi kalaci,,, ya daɗe sannan ya gama ya fito, da abinda yayi a farlo yaje ya ajiye,, ya koma kicin ya gyara inda ya ɓata,,, bayan ya gama ya dawo farlo ya zace ranki ya daɗe fito an gama, raihana ta taho cikin isa da ƙasaita, tazo ta zauna, yawo flaks tayi ta fara haɗa kalaci, sannan ta jawo flet na dankali da doya, ta ajiye a gabanta ta fara ci, aminu yabi ta da kallo, saida ta gama shi har lokacin babu abinda yaci ko yasha,,,
***miƙewa tayi zata nufi ɗaki da sauri ya miƙe ya riƙota,,,, farlo ya dawo da ita ya zauna saman kujera, ita kuma ya zaunar da ita saman cinyarshi, raihana kiji tsoron Allah, kada ki manta sadaki na bayar na auroki dan ina sanki, kuma na ɗauki hutu a wurin aiki na dan kawai in more da amaryata, a daidai lokacin da yake kai bakinshi cikin nata, raihana ta fara tureshi , amma a banza, haka taci gaba da halbe halbenta, tana tunkuɗeshi amma ko motsi baiyi ba, haka yaci gaba da bi duk inda jijiyar jikinta take yaci gaba da aika mata saƙonni, a kasalance raihana ta samu ta janye bakinta daga nashi, cikin wani yanyi tayi magana tace ban yafe maka ba, a hankali ya sake mata hannu , ya kwantar da bayanshi jikin kujera, ita kuma tana zaune a ƙasa,,, daga baya kuma ta miƙe ta nufi ɗakinta,,,, tana zuwa gado ta hau tayi ruf da ciki, zuciyarta tana mata saƙe saƙe,,,,,,
Shi kuma har lokacin yana zaune kamar yanda raihana tabarshi,,,,,,,,,,
Kiran sallar la"asar ne yasa umma cewa tashi muyi sallah mu dawo, *raihana* tace to, raihana ce ta fara fita daga ɗakin, umma har yanxun tana zaune inda take, raihana tana fita, umma tace to ai ga *zawarci* Allah ya ɗora maki raihana da ƙananan shekaru saidai addu"ar Allah ya kawo miji na gari,,,miƙewa tsaye tayi itama ta fito, a daidai lokacin da raihana zata shiga ɗaki,,, ta shige umma ta fito,,,,,,
������
*zawarci*
������
*R*aihana, ki fito fa babu ruwa a gidan nan, gwaggo ce take magana, raihana da take zaune saman abin sallah , tace *innalillahi wa"inna ilaihir raji"un* a daidai lokacin da gwagho ta sake cewa in banda iskanci ina magana sai kiyiman shiru , to ai sai ki fito ki faɗa man idan ni kike so inje in samo ruwan nan, miƙewa tsaye raihana tayi ta fito tsakar gida, ta fara tattara kayan mutane data wanke, gwaggo tace a nan zaki samo man ruwan, wani bokiti ta ajiye a gaban raihana, amma har yanxun raihana batayi magana ba, ta gama ƙwashe kayan ta nufi ɗakin su,
*zawarci*
*B*ayanta gwaggo tabi tana cewa uwarki kika kyale, shegiya mai baƙin halin tsiya, saboda wannan baƙin halin yasa namiji ya sakoki gaki nan kin rasa mashin shini, ita dai raihana batayi magana ba, saboda haka tana ajiye kayan ta ɗauki hijabinta tayi waje,,,,,,,
������
*zawarci*
������
*A* kofar gida ta tsaya har ta samu mai ruwa, tace ya kawo mata jarka ɗaya, yace to, ya ɗauko ruwan tayi gaba yabi bayanta,, har cikin gida, inda gwaggo ta ajiye bakitin ta nuna mashi a ciki ya fara zuba ruwan, gwaggo tana ɗaki taji ƙarar zuba ruwa saboda haka tayo waje, salati ta fara tana tafa hannunwanta yanxun saboda tsabar bakin ciki kije ki samo ruwan shine ke mai arziki zakije ki karawo mai ruwa?""" wannan ai baƙin ciki ne, naira ishirin ɗin idan kika bani ai na siyi omo, raihana ba tayi magana ba, mai ruwa yana gama zuba ta bashi kuɗin shi , ya fita daga gidan ita kuma ta nufi ɗakin su, gwaggo tace kai yarinyar nan Allah yayi maki baƙin ciki , raihana Allah ya tsine maki albarka tunda kika hanani kuɗin nan, raihana da sauri ta fito daga ɗaki sannan tace , baƙin bakin ki ya faɗa kanki dake da "ya"yanki da jikokinki , sannan ta koma cikin ɗaki, gwaggo tayi ta zage zage ita ɗaya a saƙar gida,
*zawarci*
Saboda dama tun dawowar raihana gwaggo bata da yaron aike sai ita, tun tana cewa bata zuwa, ta haɗata da baba yace tayi haƙuri taje saboda a zauna lafiya,,,
***gwaggo sai Allah ya isa take tana ƙarawa tana tsine ma raihana saboda bata bata naira ishirin ba, daga umma har raihana babu wanda ya sake ma gwaggo magana har ta gaji da kanta tayi shiru,,,,,,
[21:19, 08/11/2017] +234 813 308 2423: ����������
��������
������
����
*ZAWARCI*
����������
��������
������
����
*page* 8⃣
*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ��✍��
*JAMEELA MUSA*
����������
��������
������
����
�� *ZAWARCI*
*H*aka gwaggo tayi jarabarta harta ƙoshi dan kanta,,,,,,
*Y*aro ne, tsaye a tsakar gida , sai ƙara nanatawa yake ance ana sallama da *raihana* gwaggo ce ta fito daga cikin ɗaki tana cewa uwar baƙin hali kinaji ana kiranki baza kixo ki fita ba,, to kada Allah yasa ki fito ni bara inje, idan ya shirya zance kawai ya turo, tana faɗin haka tayi waje,,,,
������
*zawarci*
������
*A* zaure gwaggo ta sameshi ya jingina da bango, ƙafarshi ta dama ya ɗorata a bango ta baya,, ya rungume hannunshi a ƙirjinshi, kanshi yana kallon ƙasa, kana ganinsa, sallama gwaggo tayi , ya masa ba tare daya kalli inda take ba, gaban gwaggo ya faɗi, da sauri ta leƙa kofar gida, dan taga ko mai sallamar yana waje, babu kowa dowowa tayi, kallon da tayi mashi yafi ƙarfin ace yaxo neman *raihana* saboda haka ta dawo, tace kaine ka aika yaro cikin gida?"" sai a lokacin ya ɗago kanshi , da sauri gwaggo ta sauke idon ta ƙasa saboda wani abu taji ya shigar mata cikin ido, zuuuuuuu, yace Eh , *raihana nake nema, gwaggo cikin rawar murya tace , lafiya dai?"" yace lafiya qalau ia san ganin ta ne, har yanxun kan gwaggo ƙasa yake, tace an ɗaura mata aura, ummm yace, ba tare da ya sake magana ba, hannunshi ya saka a aljihu ya ɗauko bandir na 1000, ya miƙa mata, gwaggo da sauri ta ƙarɓa, tana godiya shi kuma ya fita, da sauri gwaggo ta miƙe tayi cikin gida,,,,,,,,,,,
<<>> {{}}~~¤
*A* ɗaki gwaggo ta duba kuɗin sannan ta jinjina kanta, tace lallai ina da sauran aiki a gabana,, wannan mai kuɗin idan ya auri *raihana* ai ina cikin matsala, hijabinta ta jawo daga saman kyaure ta zura tayi gaba{{}}}<<>>
������
*zawarci*
������
*S*allamar baba tasa da umma da raihana suka fito tsakar gida, baba sai ƙara faɗaɗa murmushin shi yake,, tabarma umma ta shimfida tana ƙara mashi sannu da zuwa,, yawwa yake cewa lokacin daya ke zama, suma zama sukai baki ɗayansu, baba yace albshirin ku?"" da umma da raihana suka ce goro, sannan umma tace ai yau yanda naga kana murmushin nan, nasan an samu nasara, baba yace gaskiya alhamdulillah a daidai lokacin da gwaggo tayi sallama ta shigo, inda suke zaune ta nufa tare da ɗauko kujera tayani gulma ta zauna, baba yace to yaudai *raihana* Allah ya temakeki kin samu mijin aure, gaban raihana ya faɗi da sauri tasa hannunta ta dafe ƙirjinta,,, cikin zaƙuwa gwaggo tace sirikin namu daga ina yazo?""" baba yace ai ba ɓoyayye bane , *yusufa* mai niƙa ne,!'""""""" idanuwa raihana ta zaro sannan tace haba baba, ka daina wannan naganar don Allah mutum da mata ukku yara ashirin da wani abu, gwaggo tayi karaf tace rufa ma mutane baki munafikar Allah, ubanki yana magana kina magana?"" wannan ai rashin tarbiyya ne, sannan ta juya wurin baba tace a gaskiya idan kana biye ma yarinyar nan babu ranar da zata aure, tunda an samu mai santa kafin ya zare kawai kace ya turo, baba yace, ai yace zaizo su fahimci juna dai, saboda haka yaune zai fara zuwa, wata irin guɗa gwaggo tayi , sannan tace lallai yarinya kinyi goshi{{}}
*zawarci*
*U*mma batayi magana ba, ta tashi tayi ɗakinta, raihana ma ta rufa mata baya,,,, gwaggo ta zauna taci gaba zuga baba, lallai yace ma yusufa ya turo, kawai a ɗaura aure in yaso daga baya ta tare, haka dai taci gaba da maganganunta, daga baya ta tashi tayi ɗakinta, shima baba ɗakinshi ya shige,,,,,,,,,{{}}
{{}} gwaggo sai