Showing 6001 words to 9000 words out of 98315 words

Chapter 3 - ZAWARCI

06 Oct 2024

8013

zagaye gida take tana cewa wallahi Allah ya rufa maki asiri, kinga kiyi aurenki, ki huta, kai wannan yarinya da sa"ar rayuwar kike,{{}} tanayi tana "yar dariyarta, kana ji kasan dan wulaƙanci take abun,, {{}}

{{}} *zawarci* {{}}
*R*aihana tace umma wallahi da baba baya nan dana fita nayi ma gwaggo magana, ince ta fita harkata, umma tace ki barta tayi duk abinda taga dama, abinda mutum yayi mai kyau ko kishiyar hakan kanshi yayi ma,,,,,,,


*U*mma tace tashi muyi sallar isha"i ki ida man labarin {{}}

������
*zawarci*
��������
*D*ariya *raihana* tayi sannan ta ɗauki buta, alwalla tayo ta dawo ɗaki hijibinta ta saka sannan ta haye saman abin sallah,,,,,,,,,,,

*AMEENCI WRITER'S ASSICITION* ��✍�� ke maku fatan alkairi, ni *jameela musa* nake cewa ku kasance tare dani, ��💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦

*page* 9⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

🔵🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵
🔵🔵
🔵 *ZAWARCI*


*R*aihana tana gama sallar isha"i, tana zaune a inda tayi sallar bata tashi ba, umma tace mata tunda kin gama ci gaba da bani labari, umma bata gama rufe bakinta ba, gwaggo ta yaye labulen ɗakin umma babu ko sallama tace, maza fito ga ango can mijin amarya yaxo, yana ƙofar gida yana jiran *raihana* farin cikin shi, ta ƙareshe maganar tana dariya,

*T*saki raihana tayi sannan tace bazanje ba, gwaggo tace ni kike faɗa ma haka?"" raihana tace an faɗa idan kinji haushi shima ki koreshi tunda dama kin saba ƙorama man samari,

Gwaggo tace wani in ƙori yusufa ace ina baƙin ciki?"" tana maganar tana taɓe baki, raihana tace ai dole yanxun kice haka tunda kinga shi ba aminu bane, gwaggo tace keji ɗiya yau kuma jarabar rashin auren naki a kaina zata ƙare?"""""

Rainaha tace dole ta ƙare a kanki tunda babu munafikar da ta kashe man aure sai ke, idanuwa gwaggo ta zaro sannan ta daki ƙirjinta da ƙarfi tace lallai yau naga sherrin rayuwa, raihana tace wallahi idanma har sharrin rayuwane baki ga komai ba, gwaggo tace to babu damuwa yanxun dai kije ga sabon miji yaxo, idan har kika yi auren banma kara zuwa gidan bare aja mani sharri,

Raihana tace zanje bisa cika umarni mahifina, tana faɗin haka ta miƙe tayi waje fuuuuuuuuu tunda dama hijabin da tayi salla bata cire ba, gwaggo tace shegiya mai baƙin hali ai gara dai a lallaɓa a aurar dake ga yusufa ko aikin gidan "ya"ya yasa ki ladafi, ɗiya tsaitsaye haka kamar an jika shinkafa da ruwan sanyi?"""" umma dai bata ce komai ba, haka gwaggo tayi ta wulaƙanci daga baya kuma ta nufi ɗakin ta,,,,,,,,


A ƙofar gida, raihana ta samu yusufa tsaye, yasha gayu fuskar nan ya nemi mai ya lafta mata sai ƙalli take, haƙoran nan nashi kuma dayaci goro suma sai yauƙi suke, haka raihana tabi yusufa da kallo tun daga tsakiyar kansa har ƙafafuwanshi,

Bayan ta gama kalleshi tsaf, ta dawo da duban ta daidai idon shi, suka kalli juna ido cikin ido, sannan tace sannu, ya yashe baki yace raihana raihana, tsaki raihana tayi sannan tace da Allah malam naji saƙonka, yanxun ka shirya auren *RAIHANA* ne?""""

Yusuf yace Eh darling, tsaki raihana tayi sannan tace to na baka daga yau zuwa jibi jibin nan, kaje ka haɗo man milayan biyar, idan har ka haɗo man su to lallai kaxo a ɗaura mana aure,

Idanuwa yusufa ya zaro sannan yace miliyan biyar fa kike magana?"""

Raihana tace Eh ba raihana kake so ba?""" yace Eh tace to madamar kana san aure na, sai ka kawo kuɗin nan idan kuwa ba haka ba, kada ka kuskura in sake ganin ƙafar ka a ƙofar gidan nan,

Ajiyar zuciya yayi zaiyi magana raihana ta ɗaga mashi hannu sannan tace ba wata magana tsakanin ni da kuma kai idan har ka kawo kuɗin to idan har baka kawo ba, bazan sake saurarenka ba, tana kaiwa nan tayi cikin gida..................

Yusufa yabi raihana da kallo har ta shige cikin gida, tana shiga ya ƙare ma gidan su raihana kallo yace lallai wannan yarinyar tama raina ma mutane hankali in banda iskanci ko ubanta bai taɓa ganin miliyan ɗaya ba amma shine har take cewa wani ya kawo mata miliyan biyar, tsaki yayi sannan yace zanga uban naki in faɗa mashi tunda shi mutumin kirki ne, haka yayi ta surutanshi shi ɗaya daga baya kuma ya tafi yabar ƙofar gidan.................

Raihana tana dawowa gida, ɗakin ummarta tayi sallama ta shiga, umma dake kwance har bacci ya fara fizgarta, tace har in dawo?""" raihana tace Eh, umma tace baima wani daɗe ba, raihana tace Eh, umma tace to ya kukayi dashi, murmushi raihana tayi sannan tace umma gaskiya nace mashi kawai ya turo, ta ƙarasa maganar tana taɓe baki, umma tace to Allah yasa hakan shine alkairi, murmushi raihana tayi sannan tace alkairin ma ne, umma tace to bara inje in sanar da babanku, raihana tace tou, tashi umma tayi ta fita daga ɗakin, tana fita raihana ta kece da dariya, sannan tace duk dani ake magana, idan har bazan koma gidan Aminu ba, haƙiƙa dai in su namiji mai tsafta in aura amma na auri yusufa haka ai ko dariyar ƙawaye ta hanani sakat, gyara ƙafafunta tayi sannan ta kwanta, da hannunta ta lalabu ta jawo wani tsohon zani ta lulluɓe, bata daɗe da kwanciya ba bacci yayi gaba da ita...............


Umma bayan taje ɗakin baba ta faɗa mashi cewa raihana tace ma yusufa ya turo, baba yace to Alhamdulillah lamari yayi daɗi Allah ya tabbatar da alkairi, umma tace ameen, itama umma ɗakinta ta tashi ta nufo ta kwanta,



💦💦💦
*Zawarci*
💦💦💦

*T*unda safe raihana tana gama sallah gwaggo ta fito wai lallai yau gidan nan fa babu ruwa, saboda haka raihana ta fito ta tafi wurin mono ta samo masu ruwa, raihana dake kwance, saboda ta gama sallah ta kwanta ta huta gabanta ya faɗi,

Gwaggo ta iso ƙofar ɗakin tace ki fito ki samo mana ruwa nace gidan babu ruwa, raihana daga kwance tace bazanje ba, *innalillahi wa"inna ilaihir raji"un,* raihana saboda rashin mutunci ni kike zagi?"" kuma uwarki tana ji kina zagi na, har cewa take ki ƙara man, daga raihana har umma idanuwa suka zaro suna kallon gwaggo, taci gaba cewa saboda kawai nace ki ɗibo ruwa sai kawai kiyi ta zunguwara iyaye na zagi,

Wayyo Allah da mutunci na gidan nan tunda ɗiyar nan ta dawo take ɗura ma iyayena zagi, lallai yau basai gobe ba, zamana gidan nan ya ƙare, baba dake ɗaki ya fito yana tambayar ba"asi?"""

Kuka gwaggo take sosai tace raihana ce tun shekaran jira da tayi magana sai ta zageta kuma uwar tana ji saidai tayi dariya,

Baba yace ina raihanar take?"" umma ta fito daga ɗaki tace wallahi ba haka akayi ba, yace rufe man baki, umma tayi shiru baba ya kalli inda raihana take tsaye yace daga yau shine magana na ƙarshe nasha faɗa maki idan baki kiyaye ba, haƙiƙa zaki bar man gida kinji na faɗa maki, raihana tace tou baba insha Allah amma wallahi ban zage ta ba, baba yace koma dai miye keta shafa bani ba, maza kije ki ɗauka ki ibo mata ruwan, da kina gidanki zataje can ta kirawo ki?""" raihana tace tou, ɗaki ta koma ta ɗauko hijabinta, kofar ɗakinsu ta ɗauki bokitin ƙarfe, ta ɗauka tayi waje...............................

Raihana bayan ta fita, baba yace ma gwaggo kema banda masifa tunda safe sai kice yarinya saita ibi maki ruwa?""" gwaggo tace ai tuwo zan ɗora dan anjima gidan biki zani, baba yace to miyasa tun jiya ba"a samo ruwan ba?"" gwaggo tace saboda sirikina zai zo, kuma almajira ma idan ka kira basu zuwa, tsaki baba yayi sannan ya nufi ɗakin shi itama umma ɗakinta ta koma gwaggo kuma tabi baba ɗakin shi ta fara tattaro kayan shi da sukai datti........................




A madadin *AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* ni *MEELAT MUSA* nake cewa ku biyoni ..........................................
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦

*Page* 1⃣0⃣

*AMEENCHI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

🔵🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵
🔵🔵
🔵 *ZAWARCI*

*T*saye take a bakin mono ta jera layi da bokatin ta, ga ɗan sanyi sanyin asuba, Raihana ta buɗe idanuwanta duk wurin babu mace sai maza, baƙin ciki ko miye raihana ta tuna oho?"" kawai hawaye ya fara gangarowa daga cikin idanuwanta, haka taci gaba da kuka tana gogewa da gefen hijabinta,

Kuka take tana matsawa da layinta idan an janye, haka kowa yaci gaba da ibar ruwa har layi yazo kanta, haka ta matsa ta tara nata, ta koma ta fara bugawa, har bokatin ya cika, tazo ta janye ta ɗauka ta nufo gida tana mai nadamar wannan *zawarci*

Sallama raihana tayi ta shiga cikin gida, a ƙofar ɗakin gwaggo taje ta ajiye ruwan, har zata juya gwaggo tace yawwa ga kayan babanki nan sunyi datti sai ki siyo sabulu da ruwa ki wanke, raihana tace sabulu da ruwa kuma?"" to a ina zan samu kuɗin siye?"""

Ggaggo tace cikin kuɗin da kikai wanki jiya?""" murmushi raihana tayi sannna tace to Alhamdulillah Allah ya ƙara rufa mana asiri, gwaggo tace Allah ya tona maki asiri raihana muje abinda kike boyewa, raihana tace innalillahi wa"inna ilaihir raji"un Allah dai ya tona maki asiri gwaggo ni kuma nawa ubangiji ya rufe man shi,

Gwaggo tace lallai raihana iskancinki kullum gaba yake, yanxun nan ubanki yayi man tsakani dake amma shine dai baza ki fita hanyata ba?"""

Raihana tace nima idan har baza ki fita tawa ba banga abinda zai fitar dani taki ba saidai a raba gidan nan, dani da ummana daban ke kuma dake da baƙin halinki,


Wannan magana tayi ma gwaggo ciwo saboda haka ruwan da raihana ta ibo ta ɗauko bokatin ta kwarara mata su duka a jikinsu, sannan ta ɗaga bokitin taci gaba da kwaɗa ma raihana,

Raihana sai kuka take tana faɗin a taimaketa gwaggo zata kasheta, baba da bacci ya fara ɗauka da sauri ya fito tsakar gida, amma umma duk abinda ya faru tana ji , amma bata ce ta tafasa bare a shiɗe, kuma haka bata fito tsakar gidan ba,

Baba yazo ya riƙe bokitin sannan yace ma gwaggo wai wannan wane irin masifa ne?""" gwaggo cikin shashsheka ta alamar gajiya kamar wanda tayi gudu sosai, tace tun da safe ɗiyar nan take zungurawa sale mai kanwa zagi, baban gwaggo kenan, taci gaba da cewa kuma idan mutum yayi magana a bashi rashin gaskiya,,,,,

Inda raihana take tsaye tana kuka baba ya kalla wanda duk gwaggo ta farfashe mata kai, baba yace ke kuma baki zaunuwa wallahi, baba na faɗin haka raihana bata sake bi ta kanshi ba tayi ɗakin umma,

Baba yabi ta da kallo, ita kuma tana shiga ɗakin ta fashe da kuka tace umma saboda Allah ni babu mai goya man baya?"" baba kullum bayan matarshi yake bi, umma tace kema da a gidanki kike ai mijinki zaibi bayanki ne, raihana tace Allah yaman sakayya umma dai batace komai ba, ita kuma raihana zama tayi sai Allah ya isa take yi,

Daga baya umma ta fita daga ɗakin, ita kuma raihana zama tayi taci kukanta ta ƙoshi, saida ta gaji dan kanta sannan ta tashi ta cire kayan jikinta, ta kwanta wani wahalallan bacci yayyi gaba da ita,,,,,,,,,,,


*zawarci*

Ƙarfe 12:30pm raihana ta farka daga bacci, fitowa tayi tsakar gida, a ƙofar ɗakin umma taga wani tashin wanki, an kawo mata, inda gwagg take ta kalla, ita kuma gwaggo surfe take k uwarmi take surfawa oho?""""

Kanta ta dafe da yake mata wata irin sara, dafe kan tayi sannan ta duƙa ta ɗauki buta ta nufi bayi, { *toilet* } tana fitowa ta nufi inda suke sanwa ta fara bubbuɗe kwanuka, gwaggo uwar mi kike nema?"" ko inda take raihana bata kalla ba, taci gaba da buɗe buɗenta, dariya gwaggo tayi ta dakata da dakan da takeyi, ta ɗora guwar hannunta kan taɓaryar dake cikin turmi, sannan ta tallafe fuskarta da tafin hannun ta, tace yarinya babu abinci, sai kinsan matsayi na a gidan nan sannan zaki fara cin abinci, murmushi raihana tayi sannan tace aikin banza kare da gudun layya, tana kaiwa nan tayi ɗakin umma, gwaggo tace saida a mutu da yunwa""" raihana dai bata sake magana ba, ta koma ɗaki madubi ta ɗauko tana kallon yanda gwaggo taci ma fuskarta mutunci,

Allah yayi man sakayya haka rainaha kawai ta faɗa , ta koma ta kwanta, wani bacci wahalar ya ƙarayin gaba da ita,,,,,,,,,,


💦💦💦
*zawarci*
💦💦💦

*R*aihana tashi kiyi sallah mana, umma ce take tashin raihana , a gajiye raihana ta fara buɗe idanuwanta da sukai mata nauhi, hawayen wahala suka fara safa da marwa a idonta, umma tace ki tashi kiyi sallah nace, a daidai lokacin da umma take cire hijabin jikinta,

A gajiye raihana ta miƙe ta fito, buta ta duƙa ƙofae ɗakinsu ta ɗauka, gwaggo sai habaici take, tsaki raihana tayi sannan tace idan dai kare yana haushi idan bai samu aboki ba ya zama mahaukaci, gwaggo tace uwarki waccan tana nuna ɗakin su to itace mahaukaci, kuma itace karya, dariya raihana tayi sannan tace ga irin halin nan kinayi , gwaggo tace shegiya mai baƙin hali, raihana tace ai a turbar kika ɗrani tun ina yarinya,

Gwaggo tace zawarar banza, raihna tace , Allah ya kaddara man kuma kema dake da ahalinki Allah ya ɗora maku jawarci kuji abin idan daɗi ne,

Gwaggo tace ni kike cewa "ya"yan na zasui *zawarci*? Tsaki raihana tayi , bata sake magana ba ta fara alwalla,

Gwaggo sai masifa take, ala dole wai raihana tace za"a sako mata "ya"ya daga gidan aure, taci gaba d cewa ke kaɗai kika zamo haka kuma kece kaɗai zaki lalace haka , a daidai lokacin da raihana ta gama alwalla tace tare dai zamu lalace mai faɗa da ɗiyar cikin ta, ki kashe mata aure dan ki aura ma ɗiyar aminiyarki, sai Allah ya maki abinda baki zato, tana faɗin haka ta shige ɗakin su,


Gwaggo kuma taci gaba da cewa anje an kashe aure uban waye yasa tun farko baki san mijin,?"" kuma har ki mutu baza ki samu wanda yakai darajar aminu ba, yar banza lalata,

Raihana dai bata sake magana ba, gwaggo ko banda tsinuwa da la"ana babu abinda take yi,,,,,,,,


Bayan raihana ta gama sallah , uma tace mata ga abinci can badiyya ta aiko maki dashi, kuma tace zata kawo maki wanki idan Allah ya kaimu, raihana tace tou, ɗauko abinci tayi ta matsa kusa da uma tace suci, ua tace ta ƙoshi, haka raihana ta caka hannu ta fara cin abincin,

Tana cin abinci umma tace raihana, kada ki kuskura ki sake cewa gwaggo ta kashe maki aure, abincin data ibo zata kai bakinta ta fasa kaiwa, tace umma wallahi itace ta kashe man aure, umma tace haka Allah ya ƙaddara kada ki kuskura ki sake faɗin haka kinji na faɗa maki ko?"" raihana tace Eh, umma tace gama cin abinci yau ki ƙarasa man labarin nan, murmushi raihana tayi tace to,


Haka tayi ta cin abincin bayan ta gama, ta fita ta wanko hannunta ta dawo, maganin da umma ta siyo mata ta miƙa mata, bayan tasha maganin ne, tace umma zan fara murmushi raihana tayi sannan taci gaba da cewa...........................




*MEELAT MUSA* ke cewa ku kasance tare dani!!!
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
💦💦💦
💦💦

*Page* 1⃣1⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

🔵🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵🔵
🔵🔵🔵
🔵🔵
🔵 *ZAWARCI*

*H*ar yanxun yana zaune inda raihana ta barshi a farlo , ya ɗan zame saman kujera ya kwanta, lallai wannan wane irin fitina ne?"" yana da mata amma shida babu uwarsu ɗaya ubansu ɗaya, tsaki yayi ya miƙe ya nufi ɗakin shi,

Yana zuwa babu ɓata lokaci wanka yayi ya shirya ya fito fess abunshi , ɗakin raihana ya dawo, bayan ya shiga ya sameta kwance saman gado, shima saman gadon ya hau, da sauri ta matsa da baya, hannunshi yasa ya jawo ƙafarta zuuuu ya matso da ita kusa dashi,

Saman ruwan cikinta ya hau, ya matsar da fuskarshi kusa da tata, daidai bakinta ya ɗora nashi, idanuwanshi suna kallon nata, sannan yace wallahi kiji tsoron Allah idan har kika kuskura a wannan halin kika mutu zaki haɗu da fushin Allah nine mijinki so da kauna yasa na aureki ki baki sona raihana ya kamata wani abun ki riƙa ragewa saboda rayuwa,

Wai miyasa ma baki sona?""" shiru raihana tayi saboda bata da dalili, riƙo haɓarta yayi da hannu, ya haɗa bakinshi da nata, da sauri ta fizge bakinta ta jawo wani kallabi ta goge bakinta , dariya yayi yace kyamata kike?""" raihana tace bana kyamarka nidai kawai bakai man ba,

Yace miyasa ban maki ba?""" a daidai lokacin da ya sauka daga saman jikin ta, raihana tace nifa ban taɓa ganinka ba, duka sau nawa na ganka aka ɗaura mana aure dakai?""" Aminu yace to miye aibuna?"" raihana?"" ya ƙarashe maganar yana kwantar da kanshi yayi yanayin tausayi,

Yace kiji tsoron Allah , ubangiji yana fushi da matar da take ma mijinta irin abinda kike man, ki daina abinda kike tun kafin ki haɗu da fushin Allah,

So nawa aka aurar da mace ga namijin da bata taɓa gani ba?"" kuma suna zamansu hankalinsu kwance, kiyi haƙuri ki soni kinji raihan?""" wallahi zan jiyar dake farin ciki?"" ya ƙareshe maganar hawaye yana bin fuskarshi,

Ajiyar zuciya raihana tayi sannan tace to kayi haƙuri duk abinda nayi maka insha Allah bazan sake ba, yace yawwa ko kefa?""" haka yayi ta mata nasiha, raihana tanajin nasiha tana bin jikin ta, amma fa har yanxun baiwai dan tana san Aminu ba, kawai saboda yana faɗi nata nau"in azabobin da Allah zaiyi ma wanda bata biyayyar aure yasa jikin ta yayi sanyi,,,,,,,

*** *** *** ***

*B*ayan haka da sati biyu, wata rana gwaggo ta kawo ma raihana ziyara da ita da aminiyarta *Ladi* raihana tayi farin ciki da zuwansu sosai sabida haka taje ta kawo madu ɗan abun ci da sha, bayan sunci sunsha, gawaggo tace raihana niko na ganki duk kinyi baƙiƙirin kin rame,

Murmushi raihana tayi sannan tace babu wani abu da nayi gwaggo, kawai dai dan kin daina gani na kike ganin haka, ta ƙarasa maganar tana taɓe baki, gwaggo tace to ya zaman naku yake?""" raihana tace *alhamdulillah* gwaggo tace amma gaskiya yaron nan yana cutar dake, raihana tace babu wani cutuwa muna zaune lafiya,

Gwaggo tace ai kece kike zaune lafiya dashi shi kwata kwata baya kaunarki, cewa yake daya samu yayi maki ciki zai sakeki ya auro wata, tunda dama baki sanshi, raihana ta ɗago ta kalli gwaggo cikin zaro idanuwa, raihana tace a,a, gwaggo Aminu bazai man haka

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login