Showing 39001 words to 42000 words out of 98315 words

Chapter 14 - ZAWARCI

06 Oct 2024

8026

haka na fara siyar da abinci ina dafawa ana zuwa gida ana siya, kuma Allah yasa ma neman albarka, fara sana"ana mijina yaji daɗin haka dan yanxun shima ya samu natsuwa da kwanciyar hankali ganin abinci da abunsha baifi ƙarfinmu ba,

Muna cikin haka wata rana wata ƙawata taxo na faɗa mata halin da nake , ta tausaya man sosai sannan nace mata gaskiya na gaji zan kashe aurena ace ina aure amma nice nake cida kaina?"" tace man mufa mata wallahi bamu da adalci wani lokaci dan Allah ya ɗora ma mijina lalura rashi sai ince bazan zauna dashi ba?"" tace man inyi haƙuri tunda ina sana"a ina samun ɗan rufin asiri na, inyi haƙuri wata rana sai labari, haka dai tayi ta man nasiha, tare da nuna man inyi zamana ko a gida nake shima zaman gidan sai nayi haƙuri ita dama rayuwa haka take juyawa take wata rana aji daɗi wata rana kuma aji babu daɗi, to dole duk musulmi sai yaga nau"in jaraba idan dai har ya yadda musulmin ne,

haka dai na yadda na ɗauki shawararta da zata tafi ta ƙara jaddadaman ko a gida ne wata rana zan nemi wani abu in rasa, amma idan nayi haƙuri anan Allah yana gani aure nake kuma bautarshi ce , zai buɗa man ta wata hanyar, nayi mata godiya,

Munyi haƙa da sati ɗaya da ita, wata ƙawata taxo na ƙara faɗa mata kamar yanda na faɗa ma ƙawar farko, sai tace man zauna ki kashe kanki da ƙuriyarki da yarintarki da kanki da komai ki zauna kamar baiwa?"" ai rainin hankaline ma , wallahi maryam na baki shawara ki kashe auren nan yanda kike haɗɗaɗiyar nan sai kin samu wanda yafi shi, amma da shekarun idan kiƙa biye wahala sai ta mayar dake tsohuwa, haka tayi ta bani shawarar banza kuma nahau kanta na zauna, bayan ta tafi mai gida yana dawowa na tada mashi balbalin bala"i ya sakeni,

ajiyar zuciya tayi sannan tace kunsan abinda ƙawar tawa tayi ne?"" gaba ɗaya sukace ah ah maryam tace ni na raina mijina naga gajiyawar shi ashe ita sanshi take, ta kuma je ta aureshi ,,

Raihana ta zaro ido sannan tace subahanallah wannan wace irin ƙawa ce?"" maryam tace mabuƙaciya, tunda da nayi haƙuri da shawarar ƙawata ta farko da abin baikai haka ba, farida tace gaskiya, idan kana tare da mijinka dan ya rasa wani abu ai bai kamata kice zaki fita ba, hmmm inji maryam sannan tace ai ki tsaya kiji ƙarahen zance, raihana tace muna saurarenki,

maryam taci gaba da cewa bayan na dawo gida mamana tace tunda ya sakoni wallahi itama bazata riƙe mashi "ya"yan shi kowa ya riƙe nashi, inaji ina gani ina san yarana aka rabani dasu aka maidai mashi, da yake yar barikice ta tattara yaran nan ta riƙesu tana basu kulawa kamar ina nan,

raihana tace to wai zuwa tayi tace tana sanshi?"" maryam tace ni ina zan sani tunda ba"a gabana akayi ba?""" amma wata ƙawata tace itace ta sameshi tace mashi maryam bata sanka tunda har ta kasa haƙuri dan Allah ya jarabeka da talauci, to ni ina sanka kuma so na tsakani da Allah tunda ai kaga baka da ko sisi, ta dai haɗa da "yar barikinta, tace zata zauna dashi, shi kuma ya aureta,

Bayan aurensu kuma Allah ya koro mashi arziki yanxun baki ga yanda ubangiji ya buɗa mashi ba, dan wallahi wahalar gani ma yake, kinga da nayi haƙuri da ban zauna lafiya ba?""" raihana tace gaskiya ai rashin haƙuri baiyi ba a rayuwa, maryam tace bari kiji zamana a gida,

maryam taci gaba da cewa ina zaune gida ina fuskantar matsalali na rasa inda zan saka raina, idan mamana tana magana nima idan na saka baki ko na bada shawara sai ƙanina yace rufe ma mutane baki shegiya ke wa zaki bawa shawara?"" wanda ma gidanki kin kasa control bare nan gida, tun bana biye mashi har na fara biye mashi, idan yayi abu na rama sai zagi, tun yana zagina abun ya koma hada duka, haka nayi ta fuskantar matsaloli sosai,

muna cikin haka ne, Allah ya haɗanin da tantirin ɗan iskan lamba ɗaya namijin da baya da kunya ko kawaici, gashi Allah yayi masa batsa a rayuwarshi, lokacin daya fara zuwa wurina, rigigi ya tattago maganar aure, ga hidima yana kashe man kuɗi kamar hauka hakan yasa naji daɗi kuma nakd ganin na daice miji,

haka yaci gaba da zugani cikin shauƙin kauna tare da tattalinso tace ɗan iska kuma ya kware wurin iya soyayya, abinda ya fara ceman shine yanxun yaushe zamuyi aurene?"" nace mashi duk lokacin daka shirya danni a shirye nake, yace to abinda nake so dake, kinga gidan da zamu zauna yanxun nake ginawa ban ƙarasa ba, nace mashi ai babu komai a ɗaura mana aure in yaso daga baya zan tare, yace man ai shi bayasan irin wannan sai inga kamar bada gaske yake so na, danshi gaskiya mabuƙacin mace ne sosai danshi a rana gaskiya kafin gari ya waye haƙiƙa yana iya kwanciya da mace so biyar ko fiye da haka,

nace mashi wannan duk ba damuwa bane, dadai irin wannan maganganun ya fara jan ra"ayi na, niko gani nake duk kauna ce, ashe jugunan nan ɗan iskan duk yaudara ce,

muna nan tare dashi duk ya ɗauke man wasu buƙatuna babu abinda na nema na rasa, tarayyata da k"b lokaci guda na canja idan kika ganni zaki ɗauka wata matar minister ce, wannan hidima da yake man yasa na saki jiki dashi, idan yaxo fira muna dan rungume juna, yayi man kiss ɗan taɓa can ɗan shashshafa can, ganin na saki jiki dashi yasa abinda yake man ya ƙara lunkuwa,

wata rana yaxo yace man matarshi tayi mashi wulaƙanci saboda ni, kuma shi bai iya neman mata ba, kuma buƙace yake dan gaskiya idan bai samu an ɗauke mashi zai iya mutuwa , kuma shi babu wanda ya isa ya rabashi dani , yana magana yana kuka, na tausaya mashi sosai nace mashi yanxun miye abunyi?"" yace maryam ki taimaka man kada in faɗa halaka nace to ai nima halakar nake tsoro, hmmm k"b ya ƙwararre ne, dan haka yace man ki rufa man asiri in baki sadakin aurena dake, ki taimaka man don Allah, kinsan da an bayar da sadaki mace ta zama matar mutum don haka gashi, haka ya fito da kuɗi 50k wai sune sadaki ya bani na karɓa, ya ɗaukeni muka tafi,

A hotel ya kama ɗaki kukan ta ya tsanan ta cikin shashshekar kuka tace ya wulaƙantani sosai yayi man abinda tunda nake duniya mijina na sunna bai taɓa man kamar yanda yake faɗi a maganganun shi cewa shi ba raggon namiji bane ba, lallai ranar na yaba aya zaƙinta, haka k"b ya goge ne fess na gurzu lallai na yadda shi namijin ne cikkake,

Raihana tace kema kinyi hauka, ya za"ayi daga ke sai ke namiji ya baki sadaki?"" maryam tace gajiya da zawarci yasa na biye ma zuciya na faɗa halaka, danni banma san matsayina ba,

Taci gaba da cewa haka k"b ya mayar dani gadon kwanciyar wurin samun natsuwarshi , ana cikin haka ne yace man in shirya muje umara, nace mashi gidanmu baza"a bari ba, amma muyi aure kafin lokacin , k"b yace ai har yanxun ba"a ƙarasa guna mana gida ba, in ƙara haƙuri, wani irin ihu maryam tayi wanda har umma saida ta shigo ɗakin da gudu, tace k"b ya cuceni ashe cutar kanjamau ce dashi na bani na lalace ,

Rashin haƙuri yaja man nayi goma babu ɗaya, na rasa mijina, na rasa "ya"yana da nake kauna , na rasa mutumcina, na rasa lafiyata na rasa farin cikina, na rabu da iyayena, kuma bazan samu mai aurena ba har abadan duniya waye zai aureni da cutar h i v, wayyo Allahana ta ɗora hannuwanta a saman kai tana ta shiga ukku ta lalace, ka cuceni k"b Allah ya tona maka asiri,

Umma da shigo ɗaki da gudu tace lafiya?"" waye k"b kuma miye yayi maki?"", raihana da bata gane ko wane kabir ake magana ba, sai mamakin maza take a ranta tace lallai wallahi bata yadda kabir ya yaudareta yayi mata irin cutar da akayi ma maryam ba, niko nace lallai raihana ko wace irin daƙi minalliƙi allaxi ɗiɗif ce? 😂

Nidai har na gane ko waye ake magana amma ita ta kasa fahimta, umma tace farida wai waye ?"" farida tace ai na ganshi da raihana ne, ta ban labarinshi kuma ranar bikin zulaihat shine ya dawo da ita gida, to ina bawa maryam labarin raihana dama, shine ranar nan taxo gida na tace man ina raihana?"" nace mata tana nan ta samu miji zatai aure tace man tayi mata farin ciki,

To ita maryam dama munyi da ita zata kawo man hoton k"b dana faɗa ma mai gidana, yace ta kawo hotonshi a kamo shi dan a hukunta shi, ina ganin hoton ne na gane k"b in raihana ne, salati umma tayi sannan tace innalillahi wa"inna ilahir raji"un, raihana ko zufa kawai take keto mata, lallai k"b ya cika cikakken mayaudari,

maryam ko kuka take sosai farida tace to kinji nace bazanyi ƙasa a guwa ba zanzo in faɗa maki don haka sai ki rufa ma kanki asiri, umma dai har yanxun ta kasa magana, farida dai sai jama raihana kunne ta ƙara sannan tace ma maryam suje, suka tashi suka tafi, saboda tashin hankali raihana ko rakiya batayi ma farida ba,

da daddare da k"b yaxo raihana cewa tayi aje ace bata nan, kuma ta kashe wayarta diff , sai gode ma Allah take kiss ɗin da yayi mata ba"a cikin baki bane da itama tana nan da h i v, O ita 😄,

****
*B*ayan sati ɗaya ne, raihana tasa neman Alhaji ya aiko suyi aure, shiko yace to zaizo amma yanda raihana ta wulaƙanshi shima zai raima, yazo anyi magana kuma an tsaida ranar aure sati mai zuwa za"ayi aurensu,

Tou ku sance tare dani wai shima dan tsoho aji zaija,danma ya samu za"ayi dashi zai raina ma mutane hankali , ya za"a ƙare da k"b?"" wane irin ramuwa ne alhaji zaiyi?"" duk ku biyoni a cikin ci gaban

*ZAWARCI HAƘURI A GIDAN AURE* tare dani jameela musa , nake cewa ku biyo ni danjin yanda zata kaya, shin raihana da alhaji zasuyi aure?"" ko yadai abin yake?"" to duk dai sai munje zamu ji,

ngd💋
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦

*Page* 3⃣1⃣

*AMEENCI WRITER'S ASSOCITION* 📚✍🏻

*MEELAT MUSA* 🌹

****
*Ummu Farhan ina tayaki murnar fara sabon littafinki mai suna *jameela yanda aka fara Allah yasa a kammala lafiya, ubangiji ya ƙara basira da zaƙin hannu ameen*

****

*M*aganar auren raihana ta karaɗe cikin anguwarsu wasu nayi mata murna sosai dan ta zaunu a gida, masoyanta suna mata fatan alkairi da addu"ar zaman lafiya,

Lokacin da labarin auren raihana yaje kunne k"b ya shiga cikin tashin hankali da takaici wato yarinyar nan shi zata raina ma hankali dan kutumar ubanta a gidan uban uwarta taga ana aure da sadakin wani?""

To ƙarya kike baki biyani duk hidimar da nayi maki ba kin kama kinbi ko ina in ƙanƙame sai kace mai nakuda?"" to zanzo gareki idan kin yadda kin amince dani in barki kiyi aurenki amma idan kika raina man hankali kida aure saidai kiga mata suna gidan aurensu suna jin daɗi su aihu kuma su samu lada, keko saidai ki zama karuwa karuwar k"b, yanda yake maganar ne kamar raihana tana gabanshi,

Tsaki yayi sannan ya zauna saman kujera 1seater ya ɗaura ƙafa ɗaya saman ɗaya, leɓonshi na sama dana ƙasa ya haɗa sannan ya cije su, kanshi ya sosai sannan ya miƙe tsaye da sauri kamar wanda aka yanka da wuƙa, wani irin ihu yayi sannan yace ƙarya kike ƙarya kike "yar gidan talakawa ƙaryarki ɗiyar matsiyaciya, hannunshi ya fara ɗagawa yana nunawa kamar raihana tana gabanshi yana nuna ta yace ,

Zanzo gareki kuma zan faɗa maki buƙata na, idan kin yadda shikenan idan baki amince ba, ko zan rasa rayuwata wallahi aure yafi ƙarfin shegiya banza ƙarya ya ƙarasa maganar da cikin ihu da zafin rai, hawaye suka kwararo daga idon shi, matarshi jin haukan yayi yawa yasa ta rugo da gudu ta shigo ɗakin,

Dan k"b ranshi ya ɓaci sai farfasa kayan ɗakin yake komai na ɗakin yabk ya ɓarar dashi yana ihu kuka yake sosai ƙarya kike , ƙarya kike yana maganar jikinshi yana ƙarma, baki isa ba, tunda nake a rayuwata ban taɓa nema na rasa ba, ban taɓa zubi ba face saina kwashe, don haka sai na kacaccala maki rayuwa sai nayi facafaca dake saina ci ubanki ya ƙarasa maganar cikin ihu,

Matarsa dake gefe tsaye tabishi da kallo wurin ta ya nufa da gudu tana ganin haka ta fice a tsiyace, shima da gudu ya fita, yana cewa da na kamaki yo dasai naci uwarki "yar iska ina cikin masifa kina kallona,

Yana fita wurin motarshi ya nufa, ya ɗauki motarshi yayo gidan su raihana, cikin ƙunar zuciya,

*R*aihana kuma tana zauren gidansu anwani shinfiɗa tabarma ana zance idan da darling Alhaji, firace ake yi cikin shauƙin kauna dan shima ɗan tsohon nan bada ga baya ba, sai wani murmuxa ido yake da bala"i sai ya kashe ma raihana ido, ita ko wani abun idan yayi dariya yake bata ma, shi kuma idan tayi dariya gani yake kamar ta yaba,

firar su suke cikin jin daɗi da kwanciyar hankali, Alhaji yace to raihana nidai gaskiya bana san ayi wani party, dariya raihana tayi sannan tace mai girma Alhaji ai sarki sun wuce nan, yayi dariya Ehen ehen ehenn irin dai dariyar manyan mutane, sannan yace abinda nake so dake ni gaskiya bazan wani je haɗa maki lefe ba, amma ga kuɗi nan nazo maki dashi dubu ɗari biyar zan baki sai kije ki siya duk abinda kike buƙata, maganar kayan ɗaki da komai da komai duk nine zan maki, kuma bazan haɗaki kida ɗaya da tsufin guzumayen nan ba dan hayaniyar yara bata bari mu sheƙe ayarmu ko ya kika ce?"" dariya raihana ta sake kallon alhaji, shima wata irin dariya yayi ta rainin hankali dan shima alhajin bada ga baya ba,

miƙewa tsaye yayi sannan ya gyara babbar rigarshi, ya saka hannunshi ta ciki ya zaro kuɗi kamar yanda ya faɗa haka ya bawa raihana kuɗi sannan yayi mata banƙwana, har zai fita ƙofar zauren su yayi wani muah a tafin hannunshi ya tillo wa raihana, dariya tayi ta shige cikin gida gudu, tana mamakin wannan jarababben tsoho,

Raihana na shiga cikin gida ko hijabinta bata cire ba, wata yarinya ta shigo tace wai ance raihana taxo, raihana tace waye yake kirana?"" yarinyar tace wani mutum ne?"" raihana tace babba ne?"" to ita yarinya a wurinta babba ne don haka ita raihana tunanin ta alhaji tace jeki ce gani nan zuwa, yarinyar ta fita, ita kuma raihana ta ajiye kuɗin sannan tace ma umma tana zuwa, tashi tayi sannan ta fito ƙofar gida,

A jikin motarshi ya jingina ya harɗe hannuwanshi kanshi yana kallon ƙasa, raihana ta fitowa taga k"b gabanta ya faɗi , amma dole tunda ya ganta bata da ƙaryar da zatayi don haka ta haƙura ta matsa inda yake tsaye,

Sallama tayi bai amsa ba, itama matsawa tayi ta jingina da motar kamar yanda yayi itama haka tayi kua daga sallamar bata sake cewa komai ba,

shine ya gaji da tsayuwar sannan ya ɗago kanshi , hannunshi yakai a fuskarshi ya cire glass ɗin idonshi sannan ya saka a cikin aljihun rigarsa na gaba, iska ya cika da bakinshi sannan ya murzar sannan yace,

malama raihana, gaban raihana ne ya bada wani irin dasdasdassss, ɗago kanta tayi ba tare da tayi magana ba, shi kuma yaci gaba da cewa wato a rayuwa ita mace kullum ta raina hankalin mutane, waike nan "yar tatsitsiya dake har kin iya yaudara, raihana tace waye na yaudara?"" kamar jira yake raihana tayi magana yace, wato dan kutumar ubanki ni zaki raina ma hankali?"

yaci gaba da ɗaga murya ma"ana duk wanda basu san abinda suke ba su sani kuma suji, yaci gaba da cewa ƙarya kike dan kutumar ubanki babu macen da ta isa ta latsani saidai in latsa banza in hauta kamar mashin waike ni zaki yaudara to ƙarya kike bake bama uwarki tayi ƙarya,

Raihana ta katse shi ta hanyar cewa duk mi yayi zafi haka?"" yace dan ubanki wuta, raihana tace to sai hauka kake kana man ihu bisa kai ni banma san inda maganar ta nufa ba, k"b yace zan durin uwarki haka nan zanzo inyi ta bauta maki an faɗa maki ni bawan uwarki ne?"" in bada sadaki na, dan kin ɗaukan mahaukaci inji zakiyi aure?"" to wallahi bazan yadda ba,

Raihana tace kai bari ganin ina lallaɓa ka nan da kake gani na, nima kwalluwar "yar tasha ce, idan baka sanniba bara in bada maka, ni nafi ka iskanci kuma nafi ka rashin kunya dan kafff ahalinku babu tantiraya kamar raihana, idan na fara bala"i bana gajiya kuma bana sanyayawa danni idan na fara sai nakai kuma banda alamar zanyi sauƙi, idan maganar arxiki ta kawo kayi ta idan tashin hankali kake so ina da tashar yanxun nan in kunno maka ita,

Wani irin fari yakai ma raihana ya sake kai mata wani, wurin daya mareta ta dafe sannan tace ni ka mara?"" yace an mareki kamar yanda na mareki haka zan keta maki mutunci kicin unguwar nan ina kayana da na baki dan ubanda ya hafe ki?"""" a daidai lokacin daya matsa kusa da ita ya shaki wuyanta, raihana cikin yanayin wahaltuwa tace kayanka?"" anci an cinye ko za"aje a sako ma police headquater wuta bazan bayar ba idan kana da ubanda ya tsaya maka ka kwata,

Wata irin shaka ya sake kai mata ya riƙe wuyan ta gamm, mutane da suke jefi jefi tun basu san abinda ya faru ba, har suka ankara ganin an shaƙe raihana yasa mutane suka fara turawa,

aka fara haba malam sakarta mana kana namiji zaka biye wa mace?"" duk wanda ya taɓa k"b sai yakai wa mutum nushi, ya sake yo kan raihana, yace sai ta biyashi abinda ya bata ko yayi banten baƙin biri da uwarta,

itama kafiyayyar sai cewa take baza ta biya tunda ba roƙarshi tayi ba, k"b ganin raihana itama tantiriyar kanta ce, ya fara saukowa dan raihana ta

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login