Showing 33001 words to 36000 words out of 98315 words
masu fizgar hankali, murmushi yayi da gefen bakinshi sannan yace wannan ai shine ɗan ƙaramin gari da arxikin man fetur,
A daidai lokacin da raihana ta iso, sallama tayi mashi shi kuma sauke glass ɗin motar yayi, sannan yace zagayo mana, raihana tace ah ah kadai fito mu koma ƙofar gida, k"b yace ah ah, ai bana iya zama zafi nake ji, ki shigo , raihana tace nidai ah ah, kwaikwayon maganarta yayi cikin sigar yaudara shima yace nidai shigo , yanda yayi abun ya bawa raihana dariya don haka tayi murmushi, yace haba zagayo don Allah in dan ganki ina da meeting ne, lokacin daya kai kallonshi ga agogon hannunshi,
uhum raihana tace sannan ta zagaya ta buɗe gaban mota ta shiga,ta zauna, yace rufo man mota hajiya, raihana tace ai inaga mu barshi haka, girgiza kanshi yayi sannan yayi mata wani malalacin kallon daya sa jikinta mutuwa, murmushi yayi sannan daga inda yake ya duƙo don jawo ƙofar motar ya rufe,
bayan ya rufe ya dawo da kallonshi kan raihana, yace to komu fa?"" raihana tayi shiru, kallonta yayi yana cije leɓonshi na ƙasa, wani irin kallo kallo yake ma raihana wanda yasa duk taji ta takura,
Fuskarshi tana fuskantar gabanshi yace ma raihana kallanni, ba tare daya kalli inda raihana take ba, raihana bata kalleshi ba, yace dake nake magana, juyo wa raihana tayi taga hankalinshi ba kanta yake ba, ta sake ɗauke kanta, yace miyasa baki san kallona ne?"" ban haɗuba??"" ya ƙarasa maganar da muryar dake sa mutum yaji kamar baya da lafiya,
kallonshi raihana tayi ido cikin ido, yace mata jiya ina ta tunaninki kila ma ke kinyi baccinki kinma wani manta dani, raihana tace a,a, nima ina tunaninka sosai, sannan taci gaba da cewa jiya ashe haka ka bani kuɗi masu yawa, miyasa haka?"" murmushi yayi lokacin da yake sassauta ganin idanuwanshi wanda idan nice zan kira kallon da zaki gane kurenki,
k"b yace ai babu komai, raihana tace to ina godiya, yace bama sai kin gode ba, ni bana san kina wani wahalar da kanki wurin kin gode kin gode, haba, raihana tace kaiko ayi ma mutum alkairi bazai gode ba?"" dariya k"b yayi sannan yace gode ma Allah danshi ne ya haɗamu,
raihana tace Alhamdulillahi ala kulli halin ai, yace yawwa, sunyi ɗan fira sannan yace mata zai tafi, raihana tace to, yace muje zan baki saƙo, raihana tace to, fita sukai daga cikin motar su dukansu,
bayan motar suka zagaya ya buɗe but in motar ya fiddo mata wata ƙatuwar jikka, wanda shima kanshi nishi yake ya ajiyeta a ƙasa, sannan ya rufe, zagayawa yayi bayan motar ya buɗe ya ɗauko wata ƙaramar leda ya miƙa mata, yace ga wayarki nan, raihana hannj biyu tasa ta karɓa tare da godiya, kusa da ita ya matsa sosai har tana iya juyo gumin jikinji, jikin raihana ya fara ƙarma, kallonta yayi sannan yace miye?"" tace ba komai gira ɗaya ya ɗaga tare da taɓe baki baki yace uhum, jakar ya nuna mafa yace ga kayan da zakiyi amfani dashi wurin bikin ƙawarki,
ni mutum ne ma"abocin san ado da kwalli idan ina san mace ina so inga tafi kowa, in baki misali?"" raihana ta ɗaga kanta alamar E, yace kinsan fulawa wanda ake ado da ita a gida?"" raihana tace E yace idan ba"a bata ruwa ya takeyi?"" raihana tace bushewa take ta lalace, yace yawwa idan akayi mata ban ruwa ya takeyi?"" raihana tace kyau takeyi kuma ta burge kowa, yace aha, to haka nake so ki zama, duƙowa yayi kusa da ita daidai saitin bakinta ya sumbace ta, { kiss } wanda haka yasa raihana taji ƙafafuwanta basu iya ɗaukarta, shi kuma yaci gaba da cewa zan mayar dake abun ado na dan mke ɗin ta dabance, ya kula da halin da raihana take ciki dariya yayi sannan yace maza jeki gida, shi kuma yayi gaba yaje ya shige motarshi yaja yayi gaba, yabar raihana tsaye a wurin ,
yana shiga mota ya fara dariya yace kam daga sumba yarinya ta ɗauke wutar nepa?"" dariya ya sakeyi sannan yace lallai yarinya kina da aiki baki san k"b ba, dariya ya sakeyi sannan ya daki sitiyarin motarshi yace hmm ba laifinki bane an daɗe ba"a gamu ba, leɓonshi na ƙasa ya cije, sannan ya ƙara volume in waƙar da yake ji yana binta cikin nishaɗi,
ita kuma raihana tana ganin ya tafi yara ta kira suka ɗaukar mata kayan sukayi cikin gda,
umma taga raihana da kaya ɗingim ɗingim tace wannan kuma fa""?"" raihana tace shine ya kawo man wai inyi amfani dasu wurin bikin zulaihat umma tace ikon Allah kawo nan mu gani, jakar suka buɗe suka shiga duba kayan umma tace lallai anan dukiya tayi kuka, raihana ta nuna mata wayar, umma tace wai wai wai, wannan waya raihana da gani ta haɗu, itama kuɗi da yawa aka siya, raihana tace nidai ban sani ba, umma tace to idan dai ya sake dawowa kice mashi ya turo kada yaxo yayi ta maki asara amma dubu gomar da zai baya sadaki kiga ya kasa , bawai rashin su ba, ah ah, zai iya kashe maki miliyan dan ya samu abinda ransa yake so, amma bai iya bada dubj biyar a ɗaura maki aure dashi,
Kinga dai ke zawara ce, duk wanda yaxo wurin ki sau ɗaya so biyu to ki fara mashi maganar aure idan da gaske yake zai turo idan da yaudara yaxo bazaki ƙara ganinshi ba, raihana tace to insha Allah zan mashi magana,
umma tace to dadai yafi, wayar raihana ta fara ruri ta duba dan ganin mai kiranta, baƙuwar number ce, ɗauka tayi sannan ta kara a kunnenta, hello raihana farida ce, raihana tace in sani ƙawata kun dawo kenan?"" farida tace Allah ya yadda, raihana tace yaushe kuka dawo?"" tace jiya, raihana tace masha Allah, Allah yasa ibadar da kukai karɓaɓɓiya tace amin sai mun haɗu bikin farida raihana tace Allah yasa rayuwarmu takai, farida tace amin sannan raihana tayi mata godiyar abunda fa bata, farida tace bata san wannan abun don Allah, haka dai suka ɗanyi fira daga baya sukai ma juna saida safe,
umma tace sun dawo kenan?"" raihana tace Eh umma tace Allah ya cidamu baki ɗayanmu raihana tabi da amin,
sabuwar wayar da k"b ya kawo mata taji ta fara kururuwa, da sauri raihana ta ɗauko ta, dan da chargynta inji shi kuna ya saka mata sabon layi, ɗauka raihana tayi sallama bayan ya amsa, tayi mashi fatan yaje gida lafiya?"" yace lafiya, raihana ta sake mashi godiya yace no wahala, sannan ya sheda mata sai jibi idan Allah ya wurin bikin zulaihat , tace Allah a bamu aro rayuwa, haka dai sukayi ɗan fira daga baya sukai ma juna saida safe ,,,,,,,,
kwanciya tayi dan huta ma ranta, daga kwance suna ɗan fira da umma su duk biyun har bacci ya ɗauke su,
******
*Y*au juma"a, kuma yaune juma"ar da ya kama bikin zulaihat, dan haka raihana tana iya bakin ƙoƙarin wajen ganin ita ta fito dan tana so idan taje a wurin bsta da tsara, shiri take sosai, dan haka nima bari inje in samu chargy dan bama bari a bamu labari ba,
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
*ZAWARCI*
💦💦💦💦💦
💦💦💦💦
*Page* 2⃣7⃣
*AMEENCI WRITER'S ASSOCIATION* 📚✍🏻
*MEELAT MUSA* 🌹
*Wannan page naku ne masoyan wannan labarin a duk inda kuke a faɗin duniya, ina maku fatan alkairi, kuma ina alfahiri daku, fatan alkairi a gareku baki ɗaya, Allah ya ƙara ba kowa zaman lafiya da mijinta, wanda kuma basu da aure Allah ya basu mazaje na gari ubangiji yayi mana zaɓi dan matsayin fiyayen halitta S. A. W, ameen,*
*Asmeenat xeeyan ina maraicinki a kullum kina raina , alkairi ya taddaki har sokotton shehu*
*Hafsat Isa Mamman, godiya mai tarin yawa dan kina nuna mana godiya sosai kuma mun gode, muna maki fatan alkairi tare da duk "yan babban birnin katsina ta dikko ɗakin ƙara, kunya gareku badai tsoro ba,*
***
*S*hiri mai kyau raihana tayi , komai na jikinta da ta saka mai kyau da tsada ne, ta gama shirinta casss, sannan ta fito tayi ma umma sai ta dawo, umma tayi mata fatan alkairi tare da ja mata kunne ta kula da kanta, godiya raihana tayi sannan ta fice daga gidan,
Tana fitowa ta fara ƙusowa cikin unguwa, bakin titi take ƙoƙarin zuwa dan samun abin hawa, tana tafiya hankalinta yana wani tunanin daban, haka tabi ta gefensu ta raɓa, suka fara aikin nasu, zawara uwar san banza, an ɗaurayu pha, kuma wa"aka dafe ne?"" raihana dai batayi masu magana ba taci gaba da tafiyarta, daga can wani ya ɗago murya da ƙarfi yace kinfa yi kyau babu ƙarya, banda kika sa girman kai ai dana zo na kwashe ki, gaba ɗaya wurin suka ɗauki dariya, raihana dai bata juyo ba haka ta wuce tabar sakarkari,
Wani yace kai yarinyar can fa bahba shegiyace, ya fara nuna yanda raihana take tafiya, yace kai amma fa aminu yayi asara wallahi, ai mai kyau haƙuri ake dashi idan kana ganin mai kyau ko ba komai kaji natsuwa, wani yace shegiya kaji turarenta?"" ni wallahi ma zuwa zanyi inba aminu shawara ya dawo layi,
Wani yace yo Allah na tubo idan ta koma gidan Aminu aisai na tsine mata albarka, kai dan bakaji wulaƙanci da yake mata ba, wani yace ai aminu kare ne mara bindi, da Allah ku saurara kuji, shi wulaƙanci babu daɗi gaskiya mu daina janta, amma fa ƙarshen wulaƙanci aminu ya wulaƙanta yarinyar can, wai barba kasan abinda yake cewa?"" gaba ɗayansu suka ce ah ah, yace to ku tsaya kuji abinda uwarsa tace,
Ita maman su aminu ai kunsan aminu yana santa kamar ya mutu ko?"" to uwarshi taje ta tsare aka saketa, ita kuma matar uban tana zuwa tana faɗa masu halin da ita raihanar take ciki, ashe uwar daɗi takeji, ita gwaggo har gaya masu take raihana tana wankau tana surfe kaɗin taliya sai ta yini ta kwana baaci abinci ba, duk abinda raihana tayi sai ita gwaggon taje ta faɗa masu, shine maman aminu tace a barta wai idan ta gurzu da zawarci sai aminu ya mayar da ita, idan ya mayar da ita duk abinda yayi mata wai dole zata haƙura,
Yace aini inasan inje in bata shawara amma yarinyarce bata da fuska kullum fuskarta tana nuni bata wasa da yaro, dariya suka sake sheƙewa, daga nan zancen nasu ya sake salo wasu na cewa raihana irin matan nan ne masu wahalar samu kowa dai yana kiyasta irin ni"imar da Allah yayi mata, labarin nasu nidai yafi ƙarfin ƙwalwata kuxo muje gidan biki,...............
Gidan ya ɗauki harami duk wanda ka gani yana cikin farin ciki kowa yasha gayunshi, a gefe ɗaya kuma zulaihat amarya ce da ƙawayen ta zawarawa da masu aure da wanda Allah bai basu mazan aurw ba, sun haɗu a wurin kowa da abinda yake faɗa, irin dai nasihar nan tasu ta zawarawa ,
Wata ƙawar zulaihat ce tace to nidai abinda nake so na faɗa maki shine, kindai ji rayuwa, kuma yanxun kinsan mahimmacin aure da rashin aure kina nan sai abinda aka dafa aka baki, daki ƙoshi da kada ki ƙoshi suma ƙannenki jira suke a basu, duk abinda kike dashi a gidan aure idan kika dawo zawarci ba bajeshi zakiyi kiyi amfani dashi ba, kaiwa za"ayi a ajiye sai kin tashi wani auren, a gado ɗaya zaku cakuɗa keda ƙannenki, duk abinda zakiyi baki da sirri a gabansu suna kallonki, kuma duk abinda kikai mai kyau ko kishirya haka dake zasuyi koyi, idan suma sunyi aure mijin yayi masu abu kaɗan zasuga gara su taho gida sai suce kema da akayi maki kaza da kaza gida kika dawo, to kinga yanxun sai ki gyara, babu yaji barw kija abinda za"a sake ki, dariya akai baki ɗaya ,
Sannan wata tace kin manta magana ɗaya , baki faɗa ba, a daidai lokacin da raihana tayi sallama, gaba ɗaya suka ɗauki shewa da iskanci,
gangarowa tayi ta iso wurinsu, kowa sai yabawa yake tare da dai irin abun nan namu na mata, zulaihat ce tayi dariya sanan tace kai raihana kinyi kyau , wallahi raihana tace na gode, wata daga gefe tace kai mai kyau da kyau yake inji baƙin jaki daya ga magon doki, gaskiya raihana kin haihu, murmushi tayi batayi magana ba, wata tace miye magon doki?"" wanda tayi maganar tace farin doki ne yasha gayu baƙin jaki yana ganin shi yayi magana kinsan ko a mutane idan kaga wanda yafika idan dai ba hassada kake ba dole ka yaba, zulaiha tace aike bakijin magana, raihana zauna kiji wa"azim *zawarawa*
suka ce muna jinki miye ta manta bata faɗa ba?"" tace to kuna surutu zan faɗa maku?"" raihana tace to kuyi shiru muji don Allah, shiru wurin yayi kamar irin abinda yaran suke cewa mutuwa ta ratsa da ba"ai shiru ba data ɗauka,
Mai maganar kana ganinta kasan batajin magana, kuma itama tasha zawarci ta har ta fefe, idanuwanta sun gama bushewa da rashin kunya,
Zulaihat nidai abinda zance maki shine, kinga nan dai duk ɗaya muke, dan haka munsan sal musan tal, nidai nasan gidan nan zaman haƙuri kikai, kuma haka zaki hau saman katifa kiyi ta juye juye, sanyi dare dana asuba ya hanaki bacci, ama idan kina gidanki mijinki ya rungumeki kiji ɗumin jikinshi kema yaji naki, to abundai duk na temakekeniya ne, idan kuma kinji yunwa abinci biyu zakici gaba ɗaya suka sheƙe da dariya hehehehhhhhh ni dariyarsu ma ta hana inji wane irin abinci zataci so biyu?""
Farida ce tayi sallama ta shigo, raihana da sauri ta miƙe taje tayi mata Oyoyo sannan suka zo suka zauna, farida tace mi ake tattaunawa ne?"" raihana tace nasiha ake ma zulaihat farida tace ke kinyi taki?"" raihana tace aini zawarcin kawai nake amma banyi rayuwar auren ba, farida tace to ku saurara in faɗa maku,
shiru suka sakeyi, farida tace zulaihat nidai zawarci aure nayi, kuma zaman gida ɗan lokaci nayi, amma na gane kurena, kinga na saba kwanciya da mai gida a tare muke kwana ya rungumeni amma ranar dana dawo gida bacci ya gagareni, sannan kuma idan ina kwance na tuno irin abubuwan da suke faru tsakaninmu dan gane da rayuwar aure wani lokaci bana iya bacci saidai in rungumi pillow inyi ta kuka, kuma na gode ma Allah ubangiji ya tsarenk da bana zina, da tuni idan naji buƙatuwa waje zanje a biya mani, don haka zulaihat kiyi haƙuri kiyi zaman ki, kafin ma kiji kina buƙata namiji ya nemeki, ki rufa ma kanki asiri wallahi kiyi zamanki kada ki kuskura baki riƙe mijinki ba,
kije da sabon salo kici kisha tare da mijinki kiyi wanka dashi ki kyautata mashi kiyi mashi biyayya, duk abinda ya kawo ki tattala mashi kayanshi ki kiyaye duk abinda zai ɓata mashi rai duk abinda zaisa shi farin ciki kiyi mashi, ki ɓoye sirrinku ki kuma kiyayi duk ƙawar da zata zo ta baki shawarar banza, kiyi sabta kiyi ado idan mijinki zai fita zulaihat bishi kiyi mashi rakiya tare da addu"oe masu dadi kuma duk abinda ya kawo maki kiyi gadiya kada ki kuskura ki raina ko kiga gajiyawarshi nuna mashi kullum yana ƙoƙari sannan kuma nuna mashi duk duniya ke kinfi ko wace mace sa"ar miji ,
farida ta lunfasa sannan tace ko ya kika ce raihana?"" raihana tace gaskiya wannan batun naki raihana tace nima bari ince wani abu,
Matan bahaushe gaskiya muma muna da tamu matsalar sai mu duba matan yare mu gani?"" sunfimu kula da mazansu , waimu matan malam bahaushe bamu ajiye komai ba sai girman kai da iyayi, ke kinaji da aji kada kiyi ma miji biyayya wai gani kike zibar da girma ne, to gaskiya sai mun aje girman kai idan har muna so mu gyara aljannarmu, zan shi aure ibada ne, kuma duk abinda kikai a gidan aurenki ladace ake rubuta maki, ki kalli mijinki kiyi mashi murmushi idan yaji daɗi lada ne, amma idan kikayi ma wani ƙaton banza zunubi ne,
kiyi gayu kisa turare mijinki ya gani idan yaji natsuwa lada ce, amma idan kince zawarci kiyi wanka kibi titi wani ma kallon banza baki isheshi ba, bare kisa ran samun wata lada, don haka shi gidan aure gaba ɗaya anan kike nema ma kanki wuta kuma anan kike samun aljanna, idan kiyi biyayya a gidan aurenki to lallai zaki sama ma kanki tsira duniya da lahira,
Wata tace to mun gode amma ni ina so inyi wata magana amma nake ganin kamar wuri ya ƙure, amma bari in baku satar ansa mata,
Zulaihat wannan sirrine ni zan faɗa maki amma wasu matan girman kai baya barinsu, zulaihat a gidanki ina so mijinki kafin ya nemeki a kwanciyar aure nuna mashi ke kina buƙarta shi, ki nemi mijinki ba kiyi kwance kullum sai yaxo ya nemeki wannan sirrin idan kika haɗa da tsafta da gyara da kamshi, haƙiƙa ni na gaya maki maza suna san macen da take nemansu dan namiji ji yake shima yakai namiji har kina buƙatar kwanciya dashi, ki riƙe wannan sirrin ki kisa mijinki farin ciki kema sai Allah yasa kiyi farin ciki duniya da lahira {matan aure bance zawarawa ko wanda basu da aure}
To lamarin nasu babba ne, haka dai sukayi ta iskanci da magagganunsu, daga baya akaci aka sha, sannan aka ɗauki amarya zulaihat sai gidan mijinta,
Farida da mijinta ya siyama wata irin ƙatuwar mota, itama ta kwashi masu daga cikin masu kai amarya, ita kuma raihana a motar k"b suka tafi,
ankai amarya a gidan mijinta, sun ƙara mata nasiha, da shawarwari, daga baya kua kowa ya kama gabanshi,
Raihana k"b ya ɗaukota suka nufi gida, a ƙofar gidansu yayi parking, raihana tayi mashi godiya zata fita, ya riƙo hannunta, juyowa tayi ta kalleshi sannan tace lafiya?""" yace ku haka ake biki baku bamu abinci a wurin bikinku, raihana tace ai bansan bakaci ba, yace to bani yana maganar ne cikin sigar iskanci ,raihana tace to bara inje in kawo maka a gida?"" yace ah ah saidai muje mu samu abinci, raihana tace nidai a , a, k"b yace to miye?"" nine fa?" ki yadda dani nine zan aure ki ko kin daina sona ne?"""
raihana tace ina sanka yace to muje, a daidai lokacin daya tada mota, raihana tace dare fa yayi , yanxun 8:45pm kana gani k"b