Showing 24001 words to 27000 words out of 103202 words

Chapter 9 - ABIN CIKIN ƘWAI

22 Jan 2025

4460

1k

*ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇*


Fatima Rabiu Sunusi
0037219728
StanbicIBTC Bank.


Shaidar biya tanan 👇
0810 433 5144


Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224

...........🥚👩‍❤️‍👨💥🌎....

*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇

Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇
+227 84 50 64 76

*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*




*miss green ce👉🏼*
[23/09, 16:17] Miss Green🍀: *🥚ABIN CIKIN ƘWAI...!🥚*

📃Littafi na 1




By🪶
*®️Ummu maher(Miss green)🍏*



_*TEAM GAWURTATTU BIYAR 5🔥*_

*Wattpad user name*
https://www.wattpad.com/user/Rabiatu333
-------------------------

*Arewa book user name*
https://arewabooks.com/u/rabiattu0444
----------------------

masu buƙatar talla 2k Ne,zamu dinga Ɗora muku a dukkanin shafukanmu a kowani social media don samun costumer cikin sauƘi.

*Sirrinmu*

yawan barin jikinmu awaje shine ya ke saka miyagu shiga jikinmu da kuma rashin addu'ah,Allah yasa mu dace baki ɗaya.
-------------------


19🟨20

. ..dukkaninsu kallon Hajiya kaka suke ta ce"to me ye kuma akr kallona kamar na faɗi ba dai dai ba?shi fa Damas ɗinnan ɗan shege ne ma bashi da uba,asalinsu arnan daji ne tun kakarsa ta wajen uwa,uban dai nasa ne ba'asan inda ya ke ba".ta faɗi hakan tana kallonsu.tabbas haka ne mahafiyarsu ta faɗi gaskiya sai dai mutuminne yana da hatsari sosai.

Wanene Alhaji Damas?

Adamu shine asalin sunansa nahaifiyarsa kuma Sadiya sunanta,asalin Damas ɗin sunansa ya haɗa dana mahaifiyarsa,ya taso da sonta sosai sai dai baiyi rayuwa da ita mai tsayi ba,aka shigo har cikin gida aka kasheta kisan wulaƙanci,sai dai ba kowane ya janyo mata wannan kisan wulaƙancin ba sai ɗanta Damas faɗa ne ya haɗashi da wasu miyagun mutane kuma ya cucesu akan harkar don haka suka ɗauki wannan mummunan matakin,don mutane ne marasa imani sosai tun daga mutuwar mahaifiyarsa shikkenan wani rashin imani yazo mai,kashe mutum awajensa ba kimai bane,kowa yasan yadda arnan daji ke da asiri,don ma a haka mahaifiyarsa ta musulunta kafin ta mutu shine ma yasa ta dawo cikin gari taje zaune gidan haya,tana ƴar sana'ar mai da ƙuli ƙuli dashi take samu take ciyar da ƴaƴanta,yaranta biyu mace dana miji,Ruƙayya da Adam Ruƙayya ita ce ƙarama sai Adam saɓanin Adam bashi da uba,ita kuma Ruƙayya taba da uba,shi Adam tun a garinsu ta haifesa ita kuma Ruƙayya sai bayan ta shigo birni ne ta yi auren ta haifeta auren ma kuma ya mutu.

Bayan mutuwar mahaifiyarsa ya taso cikin ƙuncin rayuwa shi ya ke zuwa ya samowa ƙanwarsa abinci ta kowacce irin hanya haka ya ke zuwa ya samo ya kawo mata,Ruƙayya ta kasance mai ƙyamar mahaifinta ako da yaushe,don wataranma idan ya kawo mata abincin bata ci don tasan ta hanyar daya samo.

Tun abin na Adam bai yi nisa ba har ya yi nisa,babu irin aikin da ba ya yi,shine safarar miyagun abubuwa daga ƙasar nan zuwa wata ƙasar,shine safarar mata daga waccen jaha zuwa wannan kai har ya zama har ƙasar waje,sai a ɗauki yara dag nan ace za'a fita dasu birni aiki amman kuma daga haka bazaka ƙara ganin ɗanka ba,shikkenan kunyi bye bye.

Ganin haka yasa ƙanwarsa Ruƙayya guduwa garin mahaifinta tunda tasan garin,Adam ya yi baƙin cikin barin ƙanwarsa gida don yana sonta sosai,kai tsaye shima yabar unguwar don daman saboda ƙanwarsa ya zauna agidan,don ya yi da ita ta koma gidansa daya ƙera taƙi yadda dole ya ƙyaleta ya cigaba da miyagun aikinsa,aka daina jin ɗuriyarsa a unguwar don daman suma ya fara isarsu,ko da idan ya yi wani kaifin ka kaishi wajen ɗan sanda to fa washe gari za'a sakosa don ya samu masu goya masa baya cikin manyan masu kuɗi na ƙasa baki ɗaya.Ga shi da mugun asiri don ko biyosa akayi ba'a samunsa saboda ɓacewa ya ke.

Wannan shine taƙaitaccen tarihin Alhaji damas.
****

daga zuwa na gidan Anty Khadija gidan ya koma gidan amarya sak saboda tsafta ina tashi da safe babu abinda na ke farawa da na yi sallah na yi azkhar da karatun alqur'ani to ajjewa na ke in fita in gyara gidan tsaf ɗakinta kuma sai bayan ta tashi na ke gyarawa,sannan inyi girki inyi wanka sai dai matar gidan ta fito taci ta koma tana yimin sannu,ni kuwa har mamakinta na ke,wata shegiyar rigar bacci tun ranar da nazo gidan na sameta da ita kusan sati biyu har yanzu bata wanketa ba,kuma me wanke yana zuwa wai sai ta ce mai ya tagi bata da wanki,kuma ga kuɗin me wankin anbata amman tana baƙin cikin fitar da kuɗin,ko da daman yaya Aliyu yasan halinta sai da ya siyo komai na kayan da ake buƙata komai da komai har nama sai da ya saka a fridge don shegen son kuɗine da ita.

Ko da nazo gidan har nan yaya mk ya ke biyoni yazo ya tafi ya barni da tunanin waninsa yaya Bilal don nifa babu namijin da ke cikin ƙwaƙwalwarnan tawa idan ba shi ba,ko da na yi tunanin ciresa araina bai taɓa ciruwa.sam ko kaɗan bana son yaya mk har tausayi ya ke bani yadda duk ya matu akaina,bana son nuna masa bana sonsa ne saboda halinda zai shiga ina dai lallaɓasa ne dai mu rabu lafiya.

Babu yadda baiyi dani ba da in amshi wayar daya kawomin naƙi amsa saboda Baba ya ce baza a bamu waya yanzu ba,haka ya koma da abarsa sai dai tun a fuska naga bai ji daɗi ba don fuskarsa ta canja,na lallaɓashi na bashi haƙuri.muna rabuwa na dawo cikin gidan na sameta tana cin abinci,daman aikin kensn taci abinci ta ƙoshi shine aikinta babu abinda take sai bacci,sai kuwa ta juyo ta ce"wai ni Khairat in tambayeki?"da sauri na ce"ina jin ki anty khadija".

Gyara zamanta ta yi sannan ta ce"wai da gaske yaya mk sonki ya ke"?.ta jeho mun wannan tambayar alokacin da ban shirya ba na ce"eh sona ya ke".na bata amsa nima sai kuwa ta ce"kai ƴan gidan mu ma sai abarsu Bara'atu fa baki ga yadda take sonshi ba,kuma wallahi har soyayya suke amman shine ya komo wajenki?amman ya cika mayaudari".ta faɗi hakan tana kallona.
ɗan murmushi na yi sannan na ce"to ni yanzu Anty khadija meye na wa a ciki?ina shi ya ce yana sona ko?kinga ba ni na ce ina sonsa ba kinga ai ta ƙwana gidan sauƙi ko?soyayyarsu kuma da suke yi da Bara'atu su cigaba da yin soyayyarsu ko kada su cigaba wallahi ba damuna zaiyi ba".ina faɗar hakan na tashi na shige kitchen dan ɗora girki don ni ko san hirar yaya mk ɗinma bana son ayi,ni dai ba ni na ce ina sonsa ba?hasalima ni bana sonsa wallahi ni da zai auri Bara'atu wallahi daɗi xanji don sam bana son in koma gida ya cigaba da zuwa wajena a matsayin saurayi sam bana son hakan,wata dabara ce ta faɗomin na fito na samu Anty khadija har ta fara chat ita da yaya Aliyu sai shagwaɓe mai take wai ya dawo,ni dariya ma abin ya bani da kuma kunya bayan sun gama ne na ce"yauwa Anty khadija don Allah magana na ke son muyi".kallona ta yi sannan ta ce"to ina jinki ya aka yi"?.

"Anty na don Allah so na ke ki faɗawa hajiya kaka soyayyar yaya mk d kuma anty bara'atu".kallona ta yi sosai sannan ta ce"to wai ke ba kya son yaya mk ɗin ne?".
"Eh anty".

ɗan murmushi ta yi sannan ta ce"yo ke wa ki ke so"?.anxo wajen kallonta na yi babu ko kunyar ta na ce"na ce yaya Bilal."

da sauri ta tashi sannan ta ce"ah yarinya gyara zancanki wannan guy ɗin yafi ƙarfinki wallahi kina ganin mutum har mutum kamar shi ya yi kansa mutum mai izza ji-ji da kai uwa uba ƙyau da komai kin san ba fa zai yadda ya soki ba?don nasan duk nasan irin tsanar da ya yi miki sannan ki ce wai shi ki ke so?ni dai shawarar da zan baki ki yi haƙuri ku cigaba da lallaɓawa da yaya mk ɗin ina ganin hakan zai fiye miki".tun kafin ta gama naji wasu hawaye masu mugun zafi suna zubomin,yanxu idan na fuskance ta tana nufin yaya Bilal bazai iya aure na ba,saboda ni mummuna ce kuma baƙa?sosai maganganunta sukayi min ciwo sosai na tashi na tafi ɗakina na faɗa kan gado na fasa wani irin kuka mai cin rai,ciwo sosai na ke ji acikin zuciyata aduk sanda aka danganta ni da yaya Bilal bazai iya rayuwa dani ba yafi ƙarfina,tabbas nasan da hakan ya fi ƙarfina ne sa ba kusa ba,amman kuma ni a duba yadda na ke sonshi mana ayi min adalci.

ta baya na naji an dafa ni na juyo a hankali naga anty khadija ce ta ce"yi haƙuri ABIN CIKIN ƘWAI ta hajiya kaka,ki yi haƙuri kinji ban zata ranki zai ɓaci ba,insha Allah bazan sake ba kinji,ni da ki ke ganina zan tsaya miki har sai na ga kin auri yaya Bilal ɗinki".

Sosai na ji wani farin ciki ya baibaye ni na tashi zaune na rungumeta,ta buga baya na a hankali ta ce"yi shiru daina kuka kinji ta yaya Bilal".ɓoye fuskata na yi a bayanta wai ni kunya.

Tun daga ranar idan yaya mk yazo sai anty khadija ta ce mishi ai ina gidan koyon ɗinki da ta sakani,tun yana daurewa har dai rannan ya ce azuciyarsa zakusan baku da wayo idan kunsan wata baku san wata ba. rannan da ya tashi zuwa sai ya ɗakko Rashida da kuma aminiyata Maryam,wacce duk duniyw ba ni da aminiyar da ta wuce sai Rashida daman mu uku muke rayuwarmu ita maryam anan ƙasan unguwarmu take iyayanta masu matsakaicin ƙarfine ko islamiyayya da mukeyi tare babanmu ke biya mata har skull ɗinda ta yi babanmu ne ya ɗauki nauyinta,ganin dai irin zaman amanar mukeyi da ita tun muna ƙananu ita ta ce bata ra'ayin yin skull ta boarding mu kuma muka zaɓi boading ɗin to tun daga nan ne fa muka ɗan raba jaha saboda sai mun dawo hutu ne muke haɗuwa.
Ina kitchen ina girki kawai sai Naji anyi ihu an rungumeni ta baya,ina juyowa naga Maryam da gudu nima na ɗafeta muna juyi a kitchen ɗin sai kuwa ta ce mu da Rashida ne tana waje a hanya ne taji ciwo,to kinsan Rashida da kafiya yanzu haka da bin bango ta shigo ta hana ko in ɗan taimaka mata"...ai bata ƙarasa faɗar maganar ta ba da gudu na fito don ganin Rashidar to sai dai me Yaya mk na gani yana face ɗi na ya kalleni sosai ya yi dariya sannan ya ce"ah Hajiya me ɗinki ƙaraso mana"?.ya faɗi hakan yana ƴar dariya.

Wata best ce ajikina wacce ta ɗameni sosai sai zanin dana ɗaura da kuma irin hular na ta zaren lilo wadda yare suka fiye amfani da ita musamman a awajen bacci.
Na rasa yadda zanyi gashi na riga dana fito ya gama kallona tsaf,sunkuyar da kaina na yi kamar wata munafuka kawai sai naji maryam ta zuramin hijabin da ta zo dashi da gudu ta koma farlon.

Rashida tazo ta wuce ta kusa dani tana ƴar dariyar mugunta,yadda kasan in shaƙesu haka na ke ji tsabar baƙin ciki,jikina duk a mace na ƙarasa ina kallon ƙasa,na gaishe sa ya amsa sannan ya ce"sannu gimbiya mai koyon ɗinki?Khairat ban taɓa tunanin haka daga gareki ba?banyi tsammanin haka ba?nasan ke mutum ce mai gaskiya hasalima baki iya ƙarya ba?to me yasa ki ke min ƙarya ni?tabbas ko da baki faɗa ba nasan komai Khairat,bakya sona Khairat idan na fahimta kamar dole na yi miki amman ki yi haƙuri don Allah idan na takura miki,zuciyata ce bata yi min adalci akanki son da na ke miki shine ya ɓoye mode ɗin fuskarki gareni,ina son ki fito sosai straight foward ki faɗamin matsayi na agunki don Allah".

kasa ce wa komai na yi sai da yaga ƙwalla ta taru a idanuwa na alamar zanyi masa kuka sannan ya ce"sorry yi haƙuri kinji ban ɗauka wannan maganar za ta ɓata miki rai ba,amman don Allah ki yi haƙuri ki daure ki faɗamin abinda ke ranki saboda kada mu ɓatawa juna lokaci tsakanina da ke".

Cikin siririyar murya ta na ce"yaya Mk ka yi haƙuri amman wallahi bawai bana sonka bane kunyar anty khadija na ke ji shiyasa na ke ce mata ta ce na je koyon ɗinki".ɗan murmushi ya yi sannan ya cs "khairat kenan uwar kunya to shikkenan yanzu dai ayi haƙuri adinga kulani kinga duk yadda na rame saboda tunaninki ko aiki fa bana iya yi a office?sai dai inyi ta rubutu shirme".dariya ya ɗan bani rayuwa kenan shi yana sona baki ɗaya da zuciyarsa ni kuma ina son wanin sa haka.nan dai muka cigaba da hirarmu ya ɗauko wani ƙaton gift a nannaɗe na miƙomin yana murmushi don shi ma'abocin murmushi ne.

Juya abin na yi a hankali sannan na ce"na gode yaya mk Allah ya ƙara arziƙi".ɗan murmushi ya yi yana kallona sannan ya ce"ba komai matata kada kiji komai gobe Baba zai dawo daga tafiya inason in shigar da maganar aurenmu ayi komai a gama".

Ai ban san sanda na zaro idanuwa na ba cikin tsoro,kallona ya yi sosai sannan ya ce"lafiya ki ka tsorata haka?ko kuma tsoron auren ki ke"?.mayar da wani malulun da ya tokare ni na yi sannan na ce"ba komai".daga haka ban ƙara cewa komai ba har muka rabu na koma cikin gidan.har na shiga bai daina kallona ba ya shafa gashin kansa sannan ya ce"khairat ina sonki da yawa Allah ya bani ke na more mata".
Ina komawa ciki suka fara yimin dariya ba babu ma wacce tafi ban haushi irin Maryam na kai mata duka na ce"banza uwar ƙarya kawai".dariya ta yi sosai sannan ta ce"don Allah khairat ki bawa yaya mk dama mana ya fito musha biki?ki manta da wani yaya Bilal".ɗaka mata wani duka mai zafi na yi sannan na ce"aniyarki ta biki insha Allah yaya Bilal zan aura".tare suka haɗa baki wajen ce wa"to Amin tunda kin dage sai shi".

Rashida ta ce"banza shine da zaki taho ko sallama babu bayan kin tafi na ce wa baba zanzo kema kina nan gidan shine ya ce wai bazan zo ba zamu cika musu gida,to ashe ma zan yi wa yaya mk aiki mai ƙyau".duka na kai mata ta kauce muka cigaba da hirarmu anan muke ta zancen auren Su Sauran wata ɗaya yanzu muka cigaba da hirar bikin anty khadija ma tazo ta cigaba da bamu shawarar ankon da zamu fito dashi don haryanzu ruwan ido mun kasa fitarwa.

Yaya Aliyu ya dawo daga tafiyar da ya yi ranar ina kitchen ya dawo anty khadija tana bacci da gudu na je na rungume yaya nawa,ya ce "kai wai ke haryanzu baki girma ba?ko da ya ke kaka ta ɓata ki wallahi".cikin shagwaɓa na amshi kayan nasa shi kuma yana tsokanata,yaya Aliyu sam bai da hayaniya don dukkanmu mamanmu mu ka yo yaya Salim ne dai mafaɗaci shi kuma abbanmu ya yo.








*GAWURTATTU BIYAR,5🤚TAFIYAR TA MUSAMANCE*



1, *MU GANI A ƘASA..🔥*
_Ummu Affan_

2, *ABIN CIKIN ƘWAI..🥚*
_Ummu Maher_

3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_

4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_

5_ *AUREN WATA TARA👩‍❤️‍👨*
_Miss Hajo_


Guda ɗaya N300
Guda biyu N500
Guda uku N600
Guda huɗu N700
Guda biyar 1k

*ZAKU TURA KUƊINKU TA WANNAN HANYAR👇*


Fatima Rabiu Sunusi
0037219728
StanbicIBTC Bank.


Shaidar biya tanan 👇
0810 433 5144


Masu tura katin MTN👇
0814 179 9224

...........🥚👩‍❤️‍👨💥🌎....

*ƳAN NIGER GA HANYOYIN BIYAN KUƊINKU👇

Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f
Kai tsaye ku tura da katin Airtel ta wannan number👇
+227 84 50 64 76

*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU TAKUN FARKO*

*Miss green ce*
[23/09, 16:17] Miss Green🍀: *🥚ABIN CIKIN ƘWAI🥚*



MALLAKAR
*ummu maher(miss green)*🍀🍏



*GAWURTATTU BIYAR🔥🔥*




23🟨24


... . .zaro idanuwa na na yi kamar maryam Ɗin tana kallona na ce"kai maryam ni fa bana son wasa wallahi"?.ina faƊar hakan na saka takalmi na na fito tsakar farfajiyar hajiya kaka A cen Ɓangaren maryam ta ce"ni wallahi khairat abin ma mamaki ya bani".

"ikon Allah to daman wai yaya Aliyu yana sonki ne ko kuwa?".jan numfashi maryam ta yi sannan ta ce"haba khairat idan da yaya Aliyu yana sona ai zaki sani ko?".

Nan dai muka cigaba da hirarmu ni da maryam awaya har take cewa gobe zata zo mu Ƙarasa maganar,na tsokana ta da ce wa"to matar babban yaya sai kinzo".dariya ta yi sosai sannan ta ce"hmm ni dai wallahi ki yi a hankali kada anty khadija ta jiyo ki".sosai na Ɓarke da dariya na Ce"kin san Allah ni dai koma manene naji daƊin haƊin nan don idan yaya ya aureki to tabbas ya samu mata,ga Ƙyau da ilimi ga tsafta".dariya ta yi sannan ta ce"hmm ke dai sai nazo khairat yanzu ma umma ce ta aike ni gidan anty hajara kin san ba tada lafiya laulayin ciki ya saka ta a gaba".



"kash!to Allah ya bata lafiya".ta ce amin muka kashe wayar a tare na dawo Ɗakin kaka na zauna na kalli anty khadija wacce i'tama ni take kallo ta ce"yauwa daman hajiya kaka so na ke muyi wata Ƴar magana dake".


gutsirar goronta ta yi wanda ya bada Ƙara ras,sannan ta ce"ke uwar iyawa ina jinki?Ba'a banza uwarki take a buzuwa ba saboda ƙazantar ta da kuma iya son asanta take da shegen iyayi,amman fa ni duk iyawarta kallonta na ke tsaf,don ni Ɗinnan duk iyawar mutum kallonsa kawai na ke."

ganin Hajiya kaka na Ɓaro zance anty khadija ta ce"haba hajiya kaka to me ye kuma na sako iyaye aciki?Ke fa sai ana magana ta arziƙi sai kuma ki hau zagin mutane".


"Au kinji tsoro kenan?a'i wallahi ni dai jika na ya shiga ukunsa da fitinanniyar Ƙazanta,daman Ɗana yana fama da ƙazanta,babu yadda banyi ba akan inga ta daina Ƙazantar nan amman babu yadda zanyi,Allah ya haƊa Ɗana da Ƙarfen Ƙafa shiyasa ma na sallama mata shi kawai,to yaya zanyi a'i dole ma in sallama tunda anfi Ƙarfina".ta faƊi hakan kamar za ta yi kuka.

sosai abin ya bawa anty khadija haushi fuuu ta fice daga Ɗakin duk ranta a Ɓace,duk wani Ɗan tattalin farin cikinka da ka ke idan kazo wajen kaka sai ta Ɓa ta maka rai musamman ma idan baƘwa shiri da i'ta don ita daman kaf gidan mutum biyu ne mutanenta Bilal da kuma khairat.
tana fita na kalli kaka cikin sanyi na ce"haba hajiya kaka?i'tama fa anty khadija naga jikar kice kuma meye na yi mata haka?".sheƘeƘe hajiya kaka ta

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login