Showing 87001 words to 90000 words out of 103202 words

Chapter 30 - ABIN CIKIN ƘWAI

22 Jan 2025

4470

ranar daya rage saura Ƙwana biyu gidanmu ya cika Ɓam kamar auren budurwa,son hatta ankon biki,sai da shahid ya turomin kuƊi wai abawa kowa,wai su haka suke yi naƘi amsa sai gashi ya lallaƁa yaje wajen hajiya kaka,itama da farko taƘi amsa amman da taga ransa ya Ɓaci sai ta amsa,ai kuwa kowa sai daya samu ankon biki,ranar Ne kuma amminsa tazo gidanmu mata mai mutunci da sanin darajar mutane,ta Ɗakko wata mata wai za ta yimin gyaran jiki na larabawa.

daga ganin matar ma balarabiya ce wataƘil Ɗakkota aka yi,,harda Ƙanwarta tazo ita ammin,duk suna da mutunci sosai naƘi fitowa wai ina jin kunyarsu ta ce"a'ah khairat mufa bama jin wannan kunyar gwarama tun yanzu ki saba don shahid ba shida kunya wallahi".murmushi kawai na yi ai kuwa aranar aka fara yimin gyaran jikin,wowo hmm wai ko tsagar gida ma hanani fita matar ta yi sai dai ina Ɗaki ina shan a/c,Mutanen gidanmu suka dinga zuwa ganin ammin shahid,shima tun daga ranar ammin ta hanashi xuwa saboda gudun saƁawa Allah don taga yadda Ƙirar khairat Ɗin take,ba kowani namiji ne xai iya kallonta ya kyale ba,duk da ta yarda da Ɗanta mutum ne me kana kansa sosai,da tsantsae tsoron Allah,,shiyasa a kullum take godewa Allah da kyautar da ya yi mata na samun Ɗa kamar shahid,daman kuma ba yawan yara akeso ba albarkarsu ake nema.


kullum muna maƘale awaya ni da shahid ana zuba soyayya na lura su larabawa mayun soyayya ne,kamar laila majnun.


Baba na ya saka aka kirawo masa Bilal ya ce"Bilal kasan me yasa nasa ka aka kirawomin kai?".girgiza kawai ya yi,idanuwansa sunyi ciki duk ya rame abin tausayi ya ce"ina son ka yarda da Ƙaddara me kyau ko mara kyau,ka cire komai aranka kamar ma ba'ayi ba,kai Ɗinnan dai yayan khairat ne kuma uban ƳaƳanta har huƊu,to kaga aƘwau akaƘa me Ƙarfi a tsakaninku,don haka yanzu ma na kiraka ne don ka zamo waliyyin khairat,don ance babban wa uba koda ace yanzu mu faƊi mu mutu kai ne babansu su duka".


sosai wata zufa ta shiga tsattsafo masa,ya goge ta cikin dauriya da Ƙarfin hali ya ce"ba bu komai baba na gode da bani shawara da ka yi."baba yaji daƊi sosai suka cigaba da hirarsu amman can cikin zuciyarsa yana jin wani abu yana yi masa yawo sosai,ranar dai Bilal kusan Ƙwanan zaune ya yi,saboda tsananin tashin hankali,gobe khairat Ɗinsa xa ta Ɗaura aure?da wani ba shi ba?za ta tafi gidan wani?yanzu shikkenan sun rabu har abadan?tuni ya dinga kuka kamar ba shi ba,tabbas yanzu yaga illar rashin yin bincike kafin Ɗaukar mataki,kuma yanzu yaga illar yin saki har uku,da Ɗaya ya yi mata ko biyu da yanzu suna nan zamansu gwanin sha'awa.


Anan nake jan hankalin maza akan mu kula mu daina yanke hukunci cikin fushi,an sani kuma an yarda ita rayuwar aure tana zuwa da Ƙalubale daban daban kuma sai anyi haƘuri sannan ake samun abinda ake so,don haka mu kasance masu haƘuri ako ina kuma aduk halin da muka tsinci kanmu.


to nima anawa Ɓangaren hakan ta kasance amman tsaƁanin tunaninmu ba Ɗaya bane da Bilal ni da Shahid ci ke muke da zumuƊi da son kasancewa da juna,na tuna gobe iyanzu ina rungume jikin mijina abin alfaharina,ina matuƘar son shahid son da bai ko na yaya Bilal ba,don sai yanzu na gane ashe lokacin ban san ma wani so ba,sai yanzu nasan so don shahid ya shayar dani madarar soyayya.


******


Washe gari na chaƁa adona cikin wata doguwar riga wadda shahid ya kawomin me shegen kyau,kalar skye blue ta tasha kwalliya har ya gaji,kowa sai bina da kallo ya ke kamar wata acikin zarah,gidanmu ya cika Ɓam,Ƴan huƊu ma sunsha Ƙwalliya sosai da skye blue Ɗin shadda aka dinga yi mana hotuna dasu,don tun sassafe ya aiko da wani me hoto wanda ya Ƙware yasan kuma aikinsa,kuma baƘar fata ne amman ya iya hoto sosai yasan kuma aikinsa,don duk wanda aka yiwa hoton sai ya yi murna saboda hotunan suna fita tarwal sosai.

iyaye na guda 12 duk anyi mana hotuna dasu gwanin sha'awa ga Ƴan huƊu agaba suma sunyi kyau.


Ɗaki na ya cika da Ƙawaye sosai,Mukaji shigowar angwaye bayan an Ɗaura aure,da sauri nadiya ta ce"khairat tashi ki leƘa kiga angonki sai jin kunya ya ke".

Ai banji kunyar ba kuwa na tashi ta saman bene ina hangosa,don daman baba na ya bamu mukulli muka haye saman,babu hayaniya babu komai...... .✍🏿

07068606171



*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇*


1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_

2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_

3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_

4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_

5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨
_Miss Hajo_


Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300

*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇

0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.

Domin tura shaidar biya👇

0810 433 5144

Masu tura katin MTN👇

0814 179 9224

Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇

0817 952 3215

Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f

*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨


_*Miss green ce*_🤙🏿
[23/09, 16:30] Miss Green🍀: *🏮ABIN CIKIN ƘWAI🏮*


littafi na 3


*by✍🏿*
Ummu maher(miss green)🍀


Wattpad user name
Rabiatu333

Arewabooks
rabiattu0444


*Sirrinki👂🏻🌈*

*Ciwon basir*

abubuwa da yawa suna kawo basir kamar haka👇🏻👇🏻

*Yawan cin maiƙo*
*yawan cin yaji*
*shan lemon ƙwalba*
(abu me gas)
*shan zaƙi*
(chocolate)

abubuwan da ya kamata mai ciwon basir yaci👇🏻👇🏻

*Lemon ɓawo*
(fruit)
*abinci mai ganya*
(latas,cabbage d srnsu).


basir yana lalata mace sosai don haka ki kiyaye cin abinda zai kawo miki basir.
---------------------------

89. . . . . . 90



. . . . . . .ina ganin ya taho inda muke da sauri na matso inda Shahid ya ke,ina murmushi sosai abin ya bawa Bilal haushi ya daki gaban motarsa da hannunsa saboda tsabar takaici ya shiga motar ya wucesu fuuu,aka buɗe masa gate ɗin ya shige,yana jin wani irin bugawar zuciya kamar zata fito waje.

Ko kallon ƙurarsa banyi ba Shahid ya ce"Hayatee dafatan kina lafiya"?.murmushi na yi na ce"lafiya klau dafatan kaima haka"?.na lura yaji daɗi sosai da yadda na karɓesa ya kira amminsa awaya muka gaisa.bai cemin in shiga cikin motarsa ba nima banyi ƙoƙarin shiga motar tasa ba don daman shiga motar saurayi bata cikin aƙida ta,kuma a musulunce ba dai dai bane yin hakan rashin tarbiyya ne.

Sosai muka yi hira harda dariya zuciyata ta nutsu dashi sosai.kuma ya cemin sunyi magana da Babanmu zai aiko gidanmu a saka rana nan da wata biyu masu zuwa,na yi murmushi na ce"kai gaskiya wata biyu ya yi kaɗan".murmushi ya yi shima sannam ya ce"awaje na baiyi kaɗan ba Hayatee ni da zai yiwu ma yanzu a ɗaura mana aure kawai,da nafi kowa more aure".

Dariya maganarsa ta bani na ce"haba sai kace wata ƴar tsana"?.haka dai muka cigaba da hirarmu gwanin sha'awa.kamar haɗin baki sai ga Yaya Mukhtar shima yazo wuce wa,ko kallonsa banyi ba,tunda idan na gaishesa baya amsawa.shahid da saurinsa ya matso ya miƙa masa hannu don suyi musabaha.amman sai yaya mukhtar ya kauce ya yi shigewarsa gida alamar yana mugun jin haushinshi.

Aƙwai abinda shahid ya yi daya ƙara sakawa naji ina matuƙar mugun sonshi,saboda yadda ya nuna ko ajikinsa bai damu ba,ya dawo muka cigaba da hirarmu ta masoya.



******

Hajiya kaka na shafa addu'ah Bilal ya shigo ransa amugun ɓace,Hajiya kaka ta ce"a'ah wai kai lafiyarka kuwa Bilalu?ka ke ta wani cika kana batsewa ko dai kai da wanine?".kamar yana jira sai kuwa ya fara magana cikin mugum fushi ya ce"wai kaka waye ya bawa wannan yarinyar damar tsayawa da wani awaje ne?gashi nan ta ɗakko mama wani kamar ƙwara,wai da sunan zance?to wallahi ni bazan yarda da wannan shashancin ba."

Ya faɗi hakan cikin matsanancin fushi,da sauri kaka ta kallesa kallon baka isa ba sannan ta ce"kai kaga Bilalu binan hanyar ɓangarenku,baza kazo ka ce zaka yimin ihu a kunne ba,ko ubanka Audu bai isa yazo yana yimin ihu akai ba,balle kai karan kaɗa miya.to wai ce maka aka yi khairat baza ta yi aure ba ko me?ko kuwa so ka ke ta koma maka?ku cigaba da xaman dadiro?".da sauri Bilal ya kalleta ya ce"Hajiya kaka zaman dadiro kuma?saboda me zaki ce zaman dadiro zamuyi alhali ita matata ce".


Ya faɗi hakan cikin zare idanu,jamar hauka sabon kamu,sai kuwa haiya kaka ta ce"inye ikon Allah sai kallo,Allah inajin Bilalu ka zare wallahi,ina karatun addininka ya tafi?ko kuwa lokacin da ka yi sakin mahaukaci ne kai?to bari kaji tun kafin in zagi uwarka Ruƙayya ka fitarmin daga sashe na kafin in yi maka ihu."sosai abin ya bawa Bilal mamaki ya ce"ok haka ki ka ce ko?ni ne mahaukacin ko?shikkenan babu komai indai khairat ce taje kome za tayi ta yi na daina ko kallonta".

Ya faɗi hakan yana fita daga ɓangaren Hajiya kaka,Da sauri ta ce"yauwa tafi nono fari ai jeka ka yiwa uwarka Rakiya wannan haukar don ni nafi ƙarfin haukar ka,haukar banza haukar wofi kawai,ka saki matarka saki har uku irin na jahilai sannan yanzu ni kazo ka ce zaka ƙare akaina?a'ah ba zai yiwu ba,banci nanin ba nanin baza ta cini ba."ta faɗi hakan tana kunna ƴar radionta.

Da ƙer muka rabu da Shahid,don na lura Shahid ɗan soyayya ne na ajin ƙarshe.ya bani wata kyakkyawar waya me mugun kyau da tsada na amsa na yi masa godiya.


Ina shigowa gida na yiwa mama bayanin komai sosai ta yi murna da jin hakan,Baba yana dawowa ya saka aka kirani kaina a ƙasa ya ce"khairat na yi bincike akan yaron nan balaraben nan,kuma na gano yaron arziƙi ne har mahaifinsa wanda Allah ya yiwa rasuwa,kuma gobe zasu zo a saka ranar aure da komai".murmushi kawai na yi kaina yana a ƙasa na tashi na tafi da sauri saboda kunyar baba dana ke ji.


Haryanzu su twins basu dawo ɓangarenmu ba,nima ban damu ba don da kansu yaran ke zuwa waje na su cika nima da surutu don haka na ke kaɗa kansu su tafi baki ɗaya ma,wannan abin ba ƙaramin tsayawa Bilal arai ya yi ba,ya shirya kayansa ya koma wajen aiki ransa duk babu daɗi don gani ya ke kome ya yiwa khairat bai cancanci ta tsanesa har haka ba.

Ƴan huɗu kuka sosai suke da tafiyar mahaifinsu,suka saka Kakarsu agaba Hajiya Ruƙayya wai su sai sun dawo banu yadda ta iya haka nan ta dawomin dasu,ai kuwa wataran har paracetamol na ke sha saboda fitinarsu,wataran idan na fita zance bina suke Shahid kuwa ya biye musu suyi ta yi masa shirme,har sai na gaji na korasu gida sannan suke haƙura.ai kuwa shahid yana yi musu hidima sosai,kuɗi kuwa kullum cikin turomin su ya ke,inyi ta fushi saboda kuɗin sunyi yawa,idan na yi magana shima haushin ya ke ji sosai don haka sai na daina yin maganar.


Rashida fa ta dage wai tana fushi dani akan abubuwan da na ke yiwa yayanta,ni har mamaki suke bani daga ita har yayan nata da duk wani meson na koma gidanshi,don gani na ke kamar ilimin addini bai ishesu ba,don duk wanda ya yi ilimi bazai ce na koma gidan Bilal ba.


*********

sosai mutanen gidanmu suka tisa gulmata agaba,wai zan auri ɗan yankan kai,don irin kuɗin da aka kawo na aure na ya girgixa kunnuwansu sosai,ya bada sadaki miliyan biyar,ai kuwa duk hankalinsu ya tashi don gani suke kamar shahid bai da hankali,don idan da yana da hankalu bazaiyi haka ba.


Hmm maganar gulma kuwa yanzu ta ƙaru alokacin da aka fara.shigowa da lefe na cikin gidanmu,aƙwatina suka ƙi ƙarewa sau shigowa dasu ake,ƴan uwa da sukazo ƙarɓar lefe sai da suka gaji da ƙirgawa,Aƙwati dozin huɗu haka aka kawo min,Hajiya kaka sai buɗa take tana yada magana a fakaice tana ce wa"ho ho ina gwanin wani ga naka,lallai yau ake harkar arziƙi agidan nan,Ba lefi aƙwati shida ba alokacin ma wai tana budurwa kenan?aka kawo mata wannan lefan kamar ƴar tsana,yanzu kuwa gashi Allah ya fidda ta,ni atarihi ma ban taɓa ganin yarinyar da aka kawowa lefe har haka ba".

Tuni aka dinga ɗaukar hotunansu ana turawa ta facebook,lefe na ya girgiza ƴan mata da dama sosai,suka shiga burin ina ma ace suma su samu wannan kaya haka.



Sosai na shiga gyaran jiki na ciki da waje,mama da kanta ta hau gyara ni sosai na yi kyau kamar ba ni ba,Mama ta ɗaukomin me gyaran jiki har gida ai kuwa kafin kace me na yi wani irin mugun kyau kamar ka ɗauke ni,sau ɗaukar ido na ke,na karɓi hutu a skull saboda gyaran da na ke,abin mamaki kawai sai ga Xuhra ta zo wai taji labarin biki na,na yi mamaki sosai harda dariya ta,wato daman tana gaba da nine saboda kada in auri mijinta?babu yadda zanyi don daman ni ban riƙe ta ba,muka cigaba da al'amuranmu tare har yanzu bata haihu ba Allah bai kawo ba.

Shahid ya maƙale murya kamar yaro ya ce"gaskiya Hayatee na gaji ki fito ko kaɗanne in ganki mana?tunda aka fara sha'anin biki bana ganinki,sai ɓoyemin kanki ki ke?".shgwaɓa ya dinga yimin kamar yaro,babu yadda zanyi dole na saka wata arabian gown,me kyau sosai kalar yellow,na yafa velt ɗin akaina na fito,gashi na yasha gyara sosai.

Tun daga nesa ya sakani agaba da kallo kamar zai cinye ni,kunya duk ta ishe ni Iman ta biyo ni da gudu wai zata bini,maimakon tazo inda na ke sai naga ta canja ƙwana tana ce wa"Baba oyoyo". Da sauri na ɗaga kai na ina kallon wanda take kira da baban Bilal na hango yana sanye cikin kayan sojinsa ya haɗe rai kamar bai taɓa wata dariya ba.. ... .✍🏿

07068606171



*GAWURTATTU BIYAR, TAFIYAR TA MUSAMMAMN CE. 👯‍♀️👎👇👇*


1, *MU GANI A ƘASA...*🔥
_Ummu Affan_

2, *ABIN CIKIN ƘWAI..*🥚
_Ummu Maher_

3, *GUNTUN GORO..*💥
_Mom Islam_

4, *GISHIRIN ZAMAN DUNIYA*🌎
_Mrs Bukhari_

5, *AUREN WATA TARA*👩‍❤️‍👨
_Miss Hajo_


Guda biyar 1k
Guda huɗu N700
Guda uku N600
Guda biyu N500
Guda ɗaya N300

*DOMIN TURA KUƊIN KAI TSAYE*👇

0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank.

Domin tura shaidar biya👇

0810 433 5144

Masu tura katin MTN👇

0814 179 9224

Ƴan Ƙasar Niger zasu tura nasu anan.👇

0817 952 3215

Guda biyar 1000f
Guda huɗu 700f
Guda uku 600f
Guda biyu 500f
Guda ɗaya 300f

*TEAM GAWURTATTU BIYAR TAKUN FARKO TAFIYA TA MUSAMMAN.* 🔥🥚💥🌎👩‍❤️‍👨


_*Miss green ce*_🤙🏿


[23/09, 16:30] Miss Green🍀: 91. . . . . . .92



. . . . . . .nunawa na yi kamar bansan abinda suke ba,na yi wuce wata gaba zuwa wajsn masoyi na,fuskata Ɗauke da murmushi,wani irin kallo me cike da soyayya ya ke yimin yadda yaga na komar kamar Ƴar shekara goma yarinta na ta Ƙara fitowa sosai,ga wani irin mugun Ƙamshin dana ke fitarwa me gigita namiji,ai kuwa shahid ya gigice Ɗin sosai amman duk da haka hankalinsa na kan Bilal wanda ya Ɗaga iman sama yana yi mata wasa.

Ya ce"hayatee wannan shine baban lovely children Ɗina"?.sosai gabana ya faƊi ahankali na ce"eh shine na manta ban faƊa maka ba,yaya ya ke gare ni".sai naga fuskarsa ta haƊe nan da nan,na lura shahid shima namijin kishi ne sosai,daman kuma ance larabawa sunfi kowa kishi.

Ya ce"ayya kada ki damu don na tambaye ki ki yi haƘuri,amman wannan yayan na ki wata macece za ta ce bata sonshi?babu abinda Allah bai yi Masa ba,amman na yi mamakin rabuwarku,kuma kema khairat nasan ba zai so rabuwa da ke ba,sai dai Ƙaddara amman duk namijin daya sakeki khairat wallahi ya yi asara gaskiya".

Murmushi kawai Na yi don bani da amsar da zan bashi,don kada yabi inda muke sai ya Ɗauki Ƴarsa suka yi gaba abinsu.Ina jinsa yana tambayarta Ƴan uwanta,sai kuwa iman ta ce"dady mamanmu ta Ƙara yi mana wani dadyn ka ganchi cen ma".ta fara nuno inda Muke.Bilal bai san lokacin da wasu hawaye masu zafi suka fara zubo masa ba ya yi saurin gogewa ya wuce.

to ranar dai da Ƙer shahid ya barni na wuce gida na lura bai gajiya da kallona,idan na biye masa kuma sai muyi ta tsayuwa awajen,don haka na ce"habibee ni zan tafi gida fa mun daƊe".na faƊi hakan cikin shagwaƁa,sosai na burgesa ya ce"ah lallai baki so kije gida yanzu,ni wannan shagwaƁar taki tafi komai tafiya dani",yauwa khairat ki yi haƘuri ni dinner bata cikin tsarina sam,duk kuwa kuƊin da na ke dashi,amman mu al'adarmu a musulunce shine bayan anyi aure ana walima washe gari,to ni dai hakan yafi Ƙwantamin".


murmushi na yi sannan na ce"kada Ka damu nima duk wannan bidi'ar bata gabana albarkar auren shi na keso".sosai na burgesa amman fa muna cikin zancen naji alert Ɗin kuƊi awayata na ce"habibee naga ka turomin kuƊi me zanyi dasu haka"?.murmushi ya yi sannan ya ce"ki yi wani abin dasu,amarya ta me sirrin kyau".ya faƊi hakan yana murmushi,bai bani damar Ƙara magana ba ya yi shigewarsa cikin mota ya yi gaba.

Sosai na keson shahid,ba don kuƊinsa ko kyau ba,a'ah sai don tsare mutuncinsa,sam bai taƁa koda taƁa hannuna da sunan wasa ba,balle kuma wata maganar banza,muna mutunta kanmu mu duka,anan na ke jan hankalin Ƴan mata da zawarawa adinga riƘe mutunci da kyau,saboda ke mace duk abinda ki ka yi bai Ɓoyuwa namiji kuwa ko zai yi sau Ɗari ba'a Ganewa,kuma a musulunce ma hakan sam ba shida kyau kuma ma ba tarbiyya bace.kuma matuƘar ki ka sadaukar da mutuncinki ga wani to fa wannan mijin koda tare ku ka yi lalatar bazai taƁa ganin darajarki ba,balle kuma akaiga zancen mutuntawa,don shi aure anfison ayisa da ganin mutuncin juna.


da kai na na ware kuƊi masu yawa aka sakewa hajiya kaka sabbin kayan Ɗaki aka yi mata sabon fenti,mama na itama aka sake yi mata furnitures duk da basu daƊe ba,sannan mama ta faƊawa babana duk kuƊin da shahid ya ke bani,baiyi mamaki ba ko kaƊan don yaron yasan tarihinsa tun farko har zuwa yanzu,mahaifiyarsa da mahaifinsa suna da kuƊi sosai kuƊi kuma masu mugun yawa,shi da kansa shahid a iya nigeria ma yana da company's sunfi ashirin,ga kuma na Ƙasashen waje,uwa uba kuma likita ne me zaman kansa me kuma lasisin kowacce Ƙasa,likitan zuciya ne shi,mahaifiyarshi kuma unguwar xoma ce.kuma ba Ƙaramin kuƊi suke samu ba.

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login