Showing 24001 words to 27000 words out of 162126 words

Chapter 9 - ABADAN

gada cikin katse hanzarin uwale
bakinta ta kama tana kallonta
''ai kinji irin wautar taki,ina ke ina dosarsa,ko kin manta cewa yanzu hadiza sun fiki kudin da,zasu biyashi ya musu aiki nan take,ai hannu zamu sauya,ina da wani boka na da ya jima yana min aiki,amma fa sai kin shirya,kudadenki zaki fito da su ajjiyayyun nan''
''amma fa uwale na tarin auren lubabatu ne,na fiddo su kuma a kashe?''
''a aha,to zauna mana kiga idan zasu maganta miki,kin manta cewa idqn aiki yaui kyau wanda zata aura din mai arziqi,ne?,shi zai mata komai da komai ba damu bace ai''
baki huwailan ta washe''kuma fa hakane,kinga ke kin fini hangen nesa,to shikenan babu damuwa,yanzu kina ganin idan na raba su biyi rabi zai yi?''
tabe baki uwale tayi
''kinga malama,idan dqi kina son aiki gangariya ko fiddo da kudi kawai,wai tsoron me kike yi ne?ke da,zaki zama surukar mai arziqi,idan kuma kina ganin abar maganar shikenan sai na barki''
da sauri ta tareta
''a'ah,ba za'ayi haka baai,yanzu kina ganin yaushe zamu tafi?''
sai da ta dan nisa sannan tace
''jibi,jibi laraba kenan,ta bawa ranar samu ba,don mu samu dacewa''
dariya huwailan ta qyalqyale da ita
''gaskiya ne fa,kai Allah ya bar min ke qawata,bari na tashi na tafi kada su fuskanci wani abu,sai Allah ya kaimu kenan''
''to shikenan,Allah ya nuna mana''
tana gama ficewa uwale ta sheqe da dariya
''wawiya kawai,sai na gama tatseki tas,kuma naci halas tunda ba aikin Allah bane,idn banda ke cikakkiyar shashasha ce waye yaqi gidan hutu da jin dadi,nima fa 'yan matan nan gareni na hadashi mana da wata daga ciki,ai ba ke ladai ce mai son dadi ba''ta ja dogon ysaki kana ta miqe tana gyara daurin zaninta hadi da cewa
''ai ni kuma na samu sana'a har gida ina kwance kudi zasu dinga shigowa
ta waiwayo hannunta dauke da plate cike da tsiren tukunya wanda ya ji kayan hadi ta miqawa abdallah wanda ke tsaye qiqam a bayanta hannayensa harde bisa qirjinsa yana ta zuba mata surutu
''ungo,ai yanzu kam ka qyaleni na fita ko''
yasa fork guda biyj cikin plate din sannan yace
''kin gama wannan mami na,sauranki ci,don kin sani tare zamu ci''
girgiza kai tayi tana goge hannunta da doster din kitchen
''haba abdallah,me yasa wani lokaci kake da rigima kamar yaron goye?,kace tsiren tukunya kake so nace maryama tayi ma kace baka so nawa kake so,yanzun kuma kace sai na zauna munci tare,kaci naka ka ajjyemin nawa,idan na dawo sai naci,ina da patient da nace yau suzo su same ni''
''yau througout ba inda nake so ki fita,duk sun maida min ke kamar wata engine,weekend din ma ba za su barmin ke ki huta ba,kuma ma ni mami bazan iya ci ba idan babu ke''
''alright,ga maryama nan ta wakilceni sai kuci tare''ta fada tana daukan mauafinta dake saqale kan qofan kitchen din
ya kalli maryama ta wutsiyar ido wadda ke fasa qwai cikin bowl zata hada potatoes bolls sannan ya harareta kadan ya dauke idonshi ya maida kan mamin
''mami kina ragemin matsayi gunki,babu wanda zai iya replacing dinki a guna''
''to tunda ba zaka kaci da maryama ba sai na turo maka zubaida,ita ai na zaka qi ba tunda masoyiyarka ce ko''ta fada tana ficewa a kitchen din
maryam wadda kanta yake sunkuye tana kada qwan bata san lokacin da dariya ta ciyota ba don tuna dramer din da suka gama shi da zubaidan dazun da safe,bata snkara ba dariyar ta subuce ta fito
hannayeshi harde bisa qirjinshi as usual,a hankali ya dora kyawawan qwayar idanunsa gefen fuskarta wanda dimple dinta ya fito radau saboda motsawar fuskarta,sai taji duka ta sha jinin jikinta duk da ba kallonshi take ba,cikin second daya tayi qoqarin mai da fuskarta yadda take
hijabinta taji an damqa hade da jawota wanda har hakan ya haddasa fadowarta jikinshi,cikin zafin nama taji ya ja hijabin ya cireshi sannan yayi wurgi da shi,cike da azama tayi gaggawar barin jikinshi,a tsorace take kallonshi tare da takure jikinta guri daya,sanye take da fitted gown na atamfa wanda yabi lafiyar jikinta,a qa'ida dinkin ya mata kadan amma son da takewa atamfar yasa ta kasa bayar da ita,dalilin da yssa kenan duk lokacin da ta sakata hijabi take sawa
tuni oily eyes dinta suka qara sheqi kan wanda suke da shi a da sakamakon taruwar qwalla cikin idanunta,zuciyarta bugu take wanda a take jin ya wuce qa'ida,tama kasa hada ido da shi kamar yadda ta kasa motsawa,saboda idan tace zata motsa din tofa ko ina na jikinta zai motsa din ne
hucinsa taji a gabanta,a hankali ta dago da kanta don kallin abinda ke gabanta,tafin hannunshi ne mai dauke da zara zaran yatsu bude,tsakiyarshi kuma kunama ce qatuwa,saura kadan nunfashinta ya dauke,da sauri ta ja baya sannan ta daga kai ta kalli fuskarshi
gumi ne sosai yake hadawa yayin da idanunshi suka soma sauya kala bisa dukkan alamu ta hahharbeshi bama sau daya ba,a gigice ta koma gabanshin taci burki ganin yana tsaye qiqam yana kallon abunda ke hannun nashi tamkar ba wani abu bane mai cutarwa,hannunta ta saka ta tankwabe hannun nashi kunamar tayi tsalle ta sauka gefanshi,takalminshi ya sanya ya taketa
batasan ta kama hannunshi ba tana lalubar inda dafin yake ba sai da taji ya fisge hannun yana fadin
''mtswee,sakemin hannu dafi na shigar mutum sai ua masa illa kin tsaya shashanci''
hannunshi ya saka ya riqe inda yake tsammani iya nan dafin ya tsaya
zaune yake a falon tunda ya fito a kitchen din,da alsmu xafin harbin na damunshi sosai,duk da 'yan dabarun da yayi,duk sai ta shiga damuwa tana jin itace sila,ta rasa da me zata taimaka masa,duk sanda ta matso gun da yake sai ta kasa tabuka komai saboda kwarjinin da yake mata,qarshe sai tq koma kitchen din ta dauki wayarta ta kira mami ta sanar mata
sosai mamin ta rude tace ta gaya mishi ya taho asibiti yanzun lallai
kwance ta sameshi saman doguwar kujera
a darare ta matsa kusa da shi kadan cikin sassanyar muryarta
''mami tace ka sameta a asibitinta''
sam bai ji isowarta gun ba sai saukar siririyar muryarta
jin shiru ya sata sake maimaitawa
kusan minti uku kafin yace
''leave me alone pls,bani son naci tunda ni ba kurma bane,sannan bani son gulma,har kin kirata saboda tsaban gulma,bace min a gun''
bata damu ba tunda ta isar da saqon mamin dai,kitchen din ta koma ta fara soya patatoes bolls din duk da rabin hankalinta na ga abdallah wanda bata ji motsin tafiyarshi ba,dalili kenan da yasa taa kammala suyar ta sauke man ta leqo falon,yana kwance abinshi yadda ta barshi,sai 'yar nutsuwar da ta samu tayi qaura,waishi wane irin mutum ne da ciwo ke cin jikinshi amma bai damu ba
cikin dan qwarin gwiwar da ta tattara ta sake nufarshi da nufin tunassr da shi koda qila ya manta,saidai kafin ta qarasa wayarshi dake ruwan cikinshi ta dauki sassanyar ringing alamun shigowar kira
da alamun kasala ya dauki wayar ya duba mai kiran nasa ya amsa bayan ya maidata handsfree ya dorata saman cikin nasa
''abdallah yaya me na jika shiru?,ko maryama bata sanar maka saqona ba?''
cikin murya mai kama da ta mai bacci yace
''ta gayamin mami,kawai....''
''ya isa bana buqatar uziri,na baka minti talatin in ganka a office dina ok?''
''yes mami''ya fada daga bisani wayar ta katse
cikin sanda ta juya don komawa da baya tunda bai ganta ba
''dakata a nan''ya fada cikin kaurara murya,cak ta tsaya din yayin da shi kuma ya miqe a hankali
''sai ki fito amma zan sake maimata miki ni bani son shishshigi''daga haya ya juya yayi waje
motoci hudu ne baqaqe masu azabar kyau a jere,tun kafin ta qaraso taga abdallah tsaye jikin daya,xubaida ce ke fuskantarta bisa alamu magana suke,isowarta ne ya sanyata jin maganar qarshe da abdallah ke fadi
''nacinki kullum sawa yake ina dada tsanarki,bana son shishshigi bana son naci kuma bana son takura,ki tambayi nene tun asali ke ba type dina bace,bazan taba auran macen da bata yimin ba,ba ko wacce irin mace nake so ba,for now ya kamata ki gane hakan''
ya sanya hannunsa ya janue hannunta data tokareshi da shi ya bude bayan motar da kanshi
''naji abdallah,amma atleast dai a yanzun ka barni na raka ka asibitin bai cancanci ka tafi kai daya ba''
ko kallo bata isheshi ba don tuni ya gama maganarshi da ita
ya juya bayanshi yace da daya daga cikin security dinshi su rage biyu daga cikin motocin da biyu za'a tafi,ya rufe maganar da fadin
''ko kun manta muna bincike kan alhj haladu uba mai qusa,kuma banson yasan ina cikin garin nan,ku kiyaye''
''yes,sir''ya fada cikin girmamawa
kusan tare shi da zubaida idonsu yake kan maryama dake tsaye daura da su
''me kika tsaya kina wa mutane a gurin?''
cikin tattausan muryarta tace
''bansan wacce mota zan shiga ba ai''
''saikiyita sanqamewa anan har a tashi qiyama''ya fada yana shirin shigewa motar
''amma abdallah wannan ita kuma fa?''
wani kallon biyu babu ya mata cike da quluwa da tarin tambayoyin da nabu macen da isa ta masa su idan ba maminshi ba,tsaki ya ja mata sannan ya ja motarshi ya bame
sun gama reverse suna shirin ficewa maryama dake motar baya cikin gidan baya a takure saboda su uku ne maza biyu ita ta ukun taji an dakatar da su,abdallah ne ya fito ya qaraso har gaban motar,glass din duka motar yasa suka sauke ya qare musu kallo sannan yace da na gaban motar
''you are verry stupid lawal,oya getout ka koma baya,ke kuma ki fito ki dawo gaba saunar yarinya kin shige cikin maza kin wane qwame''
yana tsaye akayi hakan sannan ya bisu da tsaki ya kona tashi motar duka direbobin suka ja suka fice a gidan
*ABDULLAHI SPECIALIST HOSPITAL* shine abinda ke rubuce jikin wani makeken allo dake maqale a goshin ginin benan asibitin,wanda ko daga ina ka taho zaka gani saboda girman allon da rubutun da kuma tsahon benan,gini ne na alfarma tamkar ba asibiti ba,komai neat bisa tsafta tsari da kuma qwarewa,tun daga parking space ma'aikatan dake cikin harabar asibiti leburori da masu gadi suka soma tururuwar zuwa gaida abdallah,ga mamakin maryam hannu yake basu suna mudabaha cikin fara'a da sakin fuska
a haka suka ratsa cikin asibitin har zuwa sashen da office din mami na musamman yake
''wonderful,abdul dama kana nigeria?''suka ji an fada,wani matashi ne wanda ke nufosu yake fadar haka,sanye yake cikin qananun kaya wanda kallo daya zaka mishi kasan dan birni ne yasan gayu gayu ya sanshi,ba wani mugun kyau ne da shi ba amma iya adonshi ya bashi sunan kyakkyawa
da fara'a sukayi musabaha da abdallah
''idan ban manta ba shekaru biyar rabona da kai abdallah,yanzu laifin kudrat sai ya shafi mansur?''
dan qaramin murmushi ya saki kana yace cikin basarwa
''manta kawai friend ya bayan rabuwa?''sai alkhairi abdul,hala wannan ce madam din tamu?''
wani haushi ya kama abdallah don yasan ba kowa yake nufi ba sai maryam,sai ya zuba mata ido yaga yadda zata karbi maganar,babu abinda ya fuskanta tattare da ita don kanta a sunkuye yake jinta take kamar ta,zura a guje,ta takura matuqa cikin tafiyar nan
maida kallonshi yayi gun mansur
''kada ka sake fadi,cook dina ce,nazo ganin mami na ne ta shigo cikin sahun bodyguard''
murmushi mansur din yayi
''tofa wannan karon babu rabuwa abdul,bani adress dinka,zan sameka har gida,ina da magana da kai''
saboda yanayin aikinshi yasa bai bashi adress din gidan ba kai tsaye sai ya amshi phone num din mansur din yace zai nemeshi duk lokacin da zasu hadun,sukayi sallama kana suka nufi office din mami
duka a waje suka tsaya abdalla ne ya shiga ciki,fitowar mamin kenan daga toilet ta daura alwala
''ina maryam din''ta tambayeshi tana shimfida abun sallah
''suna waje''
''kana nufin har ita din''
''eh mana mami,har da ita''
''koma ka shigo min da ita''
cikin shagwaba yace
''yanzu mami a gabanta za'a min treatment din bayan da zafi kuma salon ta raina ni''
ita dai mami bata kulashi ba ta tayar da sallarta,tilas ya koma yace da lawal ya shigo da ita
*mrs muhammad ce*
[9/17, 12:52 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶1⃣9⃣


teburin mamin yayi zamanshi yaja laptop dinta yana danne danne ya barta nan a tsaye,a haka mamin ta kammala sallarta ta shafa addu'o'inta
''sannu maryama ya akayi kunama ta sami abdallah?''mamin ta fada cikin kulawa tana linke sallayarta
''tsautsayi ne mami''taji abdallah ya amshe zancan yayin da tayi duru duru tana tsaka da neman amsar da zata bawa mamin
''Allah ya tsare gaba to,amma ya kamata ka daina zuwa gun da ta samekan,don nasan bazai wuce cikin garden ba''ta fada tana hada allurai cikin syringe


maryama tsayawa kawai tayi tana kallon yadda abdallan keta marairaita kamar qanqanin yaro,ita abun ma kunya ya dinga bata,amma shikam ta fuskanci ko ajikinshi wai an tsikari kakkausa
''wannan matarshi zata sha fama da shagwaba,mami duka ta sangartashi''tayi gulmarshi cikin zuciyarta,da sun hada ido sai ya maka mata harara hakan ya sanya ta dauke kanta ta maida kan dan wani qaramin frame me masifar kyau dake kafe kan table din mamin,hoton wani yaro ne wanda bazai haura shekaru takwas ba cikin shigar tazarce da hula da takalmi sawu ciki,ko shakka babu wanna hoton abdallah ne lokacin quruciyarshi,kyawunshi ba loka in girmanshi ne kawai ba kyawu ne na tun usuli


ya lura hoton take kallo don haka ya miqa hannu ya tuntsurar da shi,ya dan bada qara sakamakon haduwarshi da table din har sai da mami ta dago ta dubeshi sannan ta dubi frame din,ta fuskanci abunda yake nufi don haka murmushi kawai tayi can qasan ranta taci gaba da abunda take


bayan mamin ta kammala bashi duka wani taimako na kashe radadi da kuma tsaida dafin sai ta hada mishi da magani,minti goma tsakani mami tace ya taahi su wuce amma sai ya marairaice kan cewa bari ya huta,wayarshi dake gefan system din mami ta dauki kida,kamar bazai daga ba amma yana dubawa yayi hanzarin dagwa
''sir,munga alhj haladu uba mai qusa yanzu cikin asibitin nan''abinda aka fada kenan da ya sanyashi hanzarin miqewa,mami ta dubeshi
''lafiya abdallah?''
''mami ina zuwa,just twenty minute''bai tsaya sauraron komai ba ya fice daga office din,yayin da mamin ta bishi da kallo cikin ranta tana masa addu'a,ita kanta mqryam din binshi tayi da ido cikin mamakin me ya sanya masa kuzari haka lokaci guda,mutumin da anyi anyi ya tashi a tafi gida ya qiya?ya tsaya shagwaba


shudewar kusan sa'a biyu har mami ta soma nuna damuwa sai gashi ya dawo,zufa duka ta wankeshi,cikin kulawa mamin ta dubeshi
''lafiya dai abdallah?''ta sake tambayarshi karo na biyu
''mami na samu nasarar kama alhj haladu,saura alhj hamza naira''ya bata amsa yana tsiyaya ruwa mai sanyi cikin tambulan na glass



ba mami ba,hatta da maryama dake zaune can gefe ba qaramin burgeta yayi ba,tana tsammanin dazun nan taji uana zancan neman mutumin amma har ya sami nasarar cafkeshi cikin abunda bai gaza awa daya da rabi ba,fuskarta qunshe da madaukakin murmushi take fadin
''masha Allah masha Allah,lallai dana daya da daya ne,baka tsinta aqasa ba abdallah,fata na Allah ya tsaremin kai yaci gaba da yi maka jagora,ya baka ikon ci gaba da tsayawa akan gaskiua,ya rabaka da aikinka lafiya''


yana kurbar ruwan sanyin yana ratsa qwaqwalwarsa sannan sanyin dadin addu'ar mahaifiya na sake shigarshi
''ameen ummi na,kullum addu'arki ita ce sirrin nasarata a rayuwa''
cikin mintina gona suka bar asibitin harda ummin don lokacin tashinta yayi


Sashensa ya wuce mami ta haura sama itama don kintsawa yayin da maryam kuma ta koma kitchen don kammala masu abincin dare tunda tuni an fara ahirye shiryen kiran salla,fashin sallar da take ne ya bata damar ci gaba da ayyukanta
shigarta kenan ta kunna gas tana shirin aza tukunya samanshi taga kamar anyi wuf an fice daga kitchen din,da sauri tabi hanyar fitan itama tana dube dube,bata ci nasarar ganin kowa ba sai adnan yayan zubaida dake shigowa cikin waiting room,wanda sairan qiris suyi karo da shi tayi saurin ja baya atsorace


kallo yake qare mata hade da wani shu'umin murmushi wanda hakan ya sanyata ta tsargu,ta tsani namini mai kallo don a aqidarta takan fassara mutum ne kawai da dan iska
''yi a hankali mana baby kada ki jiwa wannan kyakkyawan jikin ciwo ko''babu abunda tace da shi sai juyawa da tayi cikin sassarfa ta koma kitchen shi kuma ya mata rakiyar idanu,sai da ta bace ya wani lashe labba kana ya shige bangaransu


nene tayi saurin damqo wuyan rigarshi don ta fuskanci baima gansu ba a inda suke labe ita da zahariyya suna gano farfajiyar waiting parlour wucesu zaiyi,a razane ya juyo
''banza solobiyo kawai,harka wani tsorata,amma ka iya tsayawa kana qarewa jikin yarinya kallo''
kansa ya shafa yana fadin''to ai nene ba laifi bane''
''kaga ni ba wannan ba,kaga alamun yarinyar nan ta fuskanci an shiga kitchen dinsu ne?''
''eh to,ni dai na ganta a gurguje da alamu wani ta biyo''
''hanyar ina kaga tayi?''
''hanyar valcony''
ajiyar zuciya nene ta saki
''Allah na gode maka bata ga ko waye ba,kuma da alamu bata fuskanci komai ba''


''ya?nene?''adnan ya tambaya yana dagawa uwar gira
''mun aiwatar da aikin mu,saidai mu jira sakamako kuma,indai kuwa sakamako yazo da kyau,to mafarkin kowannen mu ya gama cika,don wannan karon indai aikin mu yaje inda ake buqata to babu makawa burinnu sai ya cika''
tsallen murna yayi
''that's why nake sonki nene,amma....''
ya katse maganar jin takun saukowa daga saman bene,zubaida ce,itama dubansu tayi kamar yadda suka dubeta,ganin yanayin fuskartq bai sauya ba ya tabbatar musu bata ji komai ba,gurin t.v ta nufa ta kunna sanna ta kamo tashar da take da buqatar kalla ba tare da tace da su komai ba,haushinsu duka take ji don dazun sun dqn haura sama kan yadda take son abdallah yana yarfata



_kuyi haquri da wannan sakamakon na wuni gurin mama na da bata jin dadi sosai,muna buqatar addu'o'inku,na gode_




*mrs muhammad ce*👑






📚 📚📚✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:52 PM] 80k: *ABADAN*20
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
Gab da isha'i ta kammala tuwon semovita miyar busashshiyar kubewa,kan dining ta jera konai yayi net sannan ta barwa baba uwani gyaran kitchen kamar ko yaushe ta shige bedroom dinta,wanka tayi ta shirya cikin atamfa doguwar riga ta haye gadonta don ba salla zata yi ba
research ta shiga yi kamar yadda al'adarta take lokaci bayan lokaci idan ta samu kanta free kamar yanzun
takwas da rabi da mintina hudu kiran mami ya shigo wayarta,a ladabce ta daga
''maryamu an kammala abinci ne?''
''eh mami na kammala''
''ok,taimaka don Allah ki shirya abincin cikin folding basket ki kawo nan sashen abdallah anan zamuci,nazo bashi magani kuma ya ruqeni''
''to,amma mami

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login