Showing 111001 words to 114000 words out of 162126 words
luv ur smile,maryam ke ta musamman ce u make me feel safe nd secure,ban damu da duk wani abu da na rasa ba idan ka cire mami na matuqar ina tare da ke,i know u luv me 4 who am,pls maryam tell me kina sona...kina son abdallah''
idanunta ta lumshe kana ta bude tattausan labbanta
''abdallah''
''yes ina jinki''
''abdallah ina.....''
''umh comeon baby ina jinki''
''abdallah''
''na'ammmm''
sai taji amsawar ta qarahe tamkar ido biyu ne ba cikin mafarki ba,a hankali ta fara bude idanunta don tantance a inda take,yana zaune sosai kan kekenshi idanunsa akanta kamar wanda ya samu hoto,a firgice ta miqe ta zauna dirshan kan gadon innna wuron tana mutstsuka idanu
''me nayi miki da kika zo kina mafarki da ni?,kin daga mana hankali muna ta nemanki tun la'asar gaahi har magariba ta gota ana shirin yin isha'i ashe ke mafarkina na ma kika zo kina yi?''ya fada fuskaraa dauke da murmushi wanda sai ka kuka sosai zaka gane shi kwance kan fuskarshi
haushin kanta ya kamata,kunya da taoro suka dirar mata,kada dai ace kamata yayi tana ambatar sunansa,kai amma kam da ya gama da ita,duk da ba haske bane tarwai cikin dakin sai data harareshi
''waya damu da kai da zaiyi mafarkinka? kai kadaine mai sunan?''
hannayenshi ya ware na alamun ba ruwana
''bani na kar zomon ba,ratayar ma ba'a bani ba,kuma ni din ma na dade da sanin ba'a damu da ni ba,tsabar haushina ne yasa kike ambatar suna na cikin mafarki cikin yanayi ma shauqi ko?''ya tambaueta tana tsatstsareta da kallon nan nashi,bata san me zata ce masa ba duk da barazanar kare kanta da takeyi ba,sai kawai ya juya kekenshi zai fita yana dariya qasa qasa
''ko yanzu kasuwa ta tashi dan koli yaci riba,na bada darasi abdallah ba rago bane,ki fadi abinda ke damunki idan ya kama taimako sai a taimaka miki''ya fice daga dakin,ba qaramin quluwa tayi ba,ya akayo ya sake ma ya kamata tana mafarkinsa,ta ciji yatsa tayi dana sanin ma yin barcin nan gaba daya,dole haka ta sauko daga gadon tazo ta wucesu suna zaune abinsu hisham tsoho alhaji inna wuro da abdallah,garwashi ne da wasu magunguna gaban tsoho alhajin wanda da alamu duka hade haden abdallah ne,taje ta dauro alwala tana jinshi yana basu labari
''gadonki taje ta naushe miki inna,taji laushin katifa tana ta mafarki barkatai,inaga alhaji sai ka bata magani ma don ina zaton akwai wani aljani abdullahi mai irin suna na da ya kamata''dariya ya basu yayin da ita kuma ta sake quluwa
ta daura alwalarta ta wuce dakin inna wuron ta tada sallarta
Cikin kwanakin gaba daya tayi qaura dakin inna wuro nan take kwana saboda hisham na gidan tare suke kwana da abdallan,iyakarta da tsakar gida ta fito ta taya inna wuro aikace aikace ta koma daki abunta,sam ta hana haduwar da abdallah duk cikin qoqarin tana hana kanta jin duk wani feelings dake barazanar kamata,kusan tayi a banza tunda ko shi bai ganta ba ita tana ganin giftawarsa ko ta jiyo muryarsa shi da su tsoho alhaji wanda ya duqufa ka'in da na'in wajen magungunan abdallah wanda alhmdlh cikin jikinsa yan jin wani irin sakewa da sukuni
Ko daya inna wuro bata ce mata uffan ba kan zaman daki data aura,sai ta tuqe kana zakaji tace
''ummm,Allah ya kyauta,kowa dai ya debo da zafi bakinsa''ta fuskanci sarai da ita take
cikon kwana na ukun tana kwance kan qaramin gadon inna wuron misalin uku na yammaci da littafin riyadul jannah a hannunta tana dubawa,yaye labulen inna wuron tayi tana fadin
''ki tashi kije ki gyara dakinsu hashimu,shida malam sun fita bayan gari debo ganye,amma fa idan zaki iya(da yake haka innan ke kiransa)''
ta fuskanci kamar da zafin ta innar ta fada,bata ce mata komai ba ta ajjiye littafin gefan gadon bayan ta saka alama,hijabinta ta,ciro ta ware ta saka kana ta fice innan ta bita da kallo tana tabe baki
''Allah dai ya sawwaqewa matan maraya wallahi''ta jita amma bata tanka ba
tsaye tayi a bakin qofar dakin zuciyarta na wani irin bugawa,kamar ta juya ta koma haka ta dinga ji,fargabar shiga takeji,jin motsin futowar inna wuro daga daki ya sanyata yin saurin daga labulen ta fada dakin tare da sallama idanunta a qasa
kan kujerar dakin wannan karon ta tadda shi zaune,yayi kyau cikin baqar rigar jallabiyya data haska fatarshi,a haka sai kayi tsammanin lafiyanshi qalau saboda kyan da yayi,ganinshin da batayi ba kwana biyu sai taga kamar an canza shi ne,wayarshi ce a hannunshi yana danne danne,da alama wani muhimmin abu yakeyi,amsa mata yayi kallon farko kadai yayi mata yaci gaba da abunda yake kamar bai santa ba
tana kallon kan katifar da kaya ke baje a aki da sauran tarkace tace
''zan danyi gayaran daki ne''
''oh,na bayar baki gidan ne har nasa a gayara din ma''
wani abu ya dan taba ranta sai tayi shiru wanda hakan yasanya ya dago kai ya saci kallonta
qasa qasa taji yace
''if u luv some one be sure to hold them close,if u don't some one else will''
''me kace?''ta fada cikin son nuna mishi bata ji abinda ya fada din ba
''no,ba dake nake ba,bismillah''ya fada yana ci gaba da abinda yake yi
katifar ta soma kintsawa,tana aikin amma jikinta na gaya mata kallonta yake,batayi qarya ba don gaba daya ya bar hankalinshi daga kan wayar ya maida kanta,duk wani motsi nata na kan idonshi,cikin zuciyarsa hakanan yaji tana burgeshi,bai taba zaton zai samu macen da zaiso ta wofantar da soyayyarshi ba,bil haqqi da gaskiya take son nuna masa iyakarsa
Wannan karon duk yadda yaso kauda idonshi kada ta kamashi yana kallonta abun ya faskara sai da suka hada ido,kamar kuma an manne idon ya kasa daukewa,ta juya ga zatonta zai daina kallonta amma sai taga yaci gaba,bata rai tayi
''gabana faduwa yake idan aka fiya samun na mujiya''murmushi ya sake yana janyo laptop dake gefansa
''ayyah am sorry''ya fada yana kunna system,bayan ta saitu ya shiga gun hotuna ya bude daya daga cikin hotunan ciki
Gefanshi taje zata dauke abun sallar dake shimfide a gun idanunta ya kai kan system din,hoton mero ne ya cika screen wanda da alama shi abdallah yake kalla
batasan ta fincike laptop din a hannunshi ba saida ya dago ya zuba mata idanunshi
''me kuma nayi?,ai na daina kallon naki ko?''ya fada a shagwabe kamar qaramin yaro
bata kula shi ba saida tayo shutting down fuska a hade cikin zuciyarta a tsinke tace
''saika tsagaita na gama gyara na tukun,baxaiyiwu ina gyaran kaya ana min janye janyen wani shirgin ba''ta fada tana canzawa computer mazauni nesa da shi
idan banda jarumtae daya aro ya tabbatar babu abinda zai hanashi fashewa da dariya
sai ya wayance da dora hannunsa guda daya kan tattausan sumarshi
''oh Allah na,mami na kin barni gashi ana nan ana gara miki ni''
shi da yayi maganar da ita kanta sai maganar ta soki zuciyarsu,tabbas ba kadan ba sukayi rashi da kewar uwa ta gari irin mamin
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Sosai ta qaranta baccinta don tayi imanin babu masifar da addu'a bata da maganinta,tana samun nutsuwa qwarai da gaske saidai gaba daya hankalinta ya karkata ga abdallah da maryam
yammacin ranar lahadi tana gida bayan ta kira baba uwaani,su biyu ne cikin parlour din,a yanzun kam da baya ga 'yan uwanta baaba uwani ce ta biyu wadda take shawara da ita
''amma hajiya tunanin da nayi,ba zamu zauna bamusan inda suke ba,mai zai hana mu nemi gidansu maryam ko suna da labarin inda suke?''
cike da gamsuwa mami ke gyada kai
''qwarai da gaske baaba,wannan shawara ce mai kyau,amma cikin ni da ke babu wanda yasan gidansu maryamu tunda a lokacin bikinta bamu samu damar zuwa ba tunda ya hade da na abdallah''
''eh hakane hajiya,amma ai da hajiya ruqayya aka kai lefan maryam dinko,ina zaton ki tambayeta zata iya tuna gidan''
''af,qwarai kuwa,bari nayi kiranta''
Cikin sa'a kuwa ta samu ruqayyan qanwarta ta tabbatar mata zata gane gidan,a nan suka shirya tafiyar nayan sallar la'asar don zata tsaya ta sallami mai gidanta zaiyi tafiya da azahar
Su uku ne cikin motar hajiya bintun ruqayya sai baaba uwani,jifa jifa suke tattaunawa kan batun har suka isa unguwarsu maryam din,sukayi parking qofar gidansu kana suka dunguma zuwa cikin gidan
Gidan yana nan yadda yake daga soro zuwa tsakar gidan suka fara sallama,inna hadiza dake kan tabarma a tsakar gidan ta amsa musu don babu kowa a tsakar gidan idan ka debe ita da huwaila dake kitchen tana fama da tuwon dare
kallo daya tayi musu ta fahimci daga irin gidan da ta fito,don haka jiki na rawa ta miqe tana fadin
''lale marabanku,sannunku da zuwa''mami batasan wace ba amma ruqayya tuni ta tunata saboda diban albarkar data yi danar kawo lefe,sake karkade musu tabarmar da take kai tayi tana fadin
''bismillanku ko zauna,ko daga ciki zamu shiga?''
ruqayya ce ta karbe cikin tabe baki tana girgiza kai
''mama muka zo nema,maman maryam''turus tayi kamar bata ji abinda suke fada din ba,don ita har yau babu abinda ta tsana irin taga wani abu na ci gaba ya samu maman,har yau bata dauki izina ba,rayuwar maman kullum sake inganta take,don hindatu kadai tafi dukkan nin yayan da ita ta haifa wadanda duk suka dawo gabanta,daya ce gidan aure saboda rashin kyakkyawan training na zaman auren,hindatun bata bar maman nasu ta nemi wani abu ta rasa ba,ta sake inganta rayuwarta fiye da da,ta sani rashin adda maryam dinta ne a akusa da ta tabbatar maman ma sai ta fi haka,duk da a yanzun ma ko hasidin iza hasada sai ya daga mata qafa
Shirun taci gaba da yi har sai da huwaila ta fito daga kitchen dinsu wanda zuwa yanzu hindatun ta gyara musu shi duk da maman ta bata girki ciki,tayi me saboda babanta da kuma huwailan wadda a yanzu ta saduda,tun ranar da aka gyara kitchen din inna hadiza tabar girki a cikinsa saidai tayi daga waje
''sannunku da zuwa''inji huwaila dake wanke hannunta bakin famfo
''yauwa,don Allah maman maryam tana nan?''
''eh tana cikin daki ina tsammanin sallah take,ga dakin nata nan ku shiga''ta fada tana musu nuni da shi suka amsa kana suka shige
''an dai ji kunya wlh,an zama 'yar kora da haka za'a qare''
''ba komai,don ma zama 'yar korar amina ai tafi minke,don qaruwar da nayi da ita banyita da ke ba''ta sa kai ta shige dakinta don tasan halinta idan ta tsaya sai su raba abun fada yanzu ba kunya take ji ba
kan abun sallar kuwa suka taddata tana raka'ar qarshe,falon nata qal da shi yanata qamshin turare,koda can ma mai tsafta ce bare yanzu da babu kowa a dakin nata sai ita kadai,suna tsaye har ta sallame,duk da batasan kosu waye ba da fara'arta ta karbesu
''ya zaku tsaya ku zauna mana''ta fada tana miqewa tare da ninke abin sallarta
sai data ajjiye musu ruwa da lemo kana ra dawo ta zauna mami nata kallon ta,take ta tuna mata da maryam dinta babu tantama ita tayo,kyau tsafta da kirki
Sun taba lemon kana suka gaisa,mami ta dubeta
''nasan baki sanni ba hajiya''murmushi tayi
''gaskiya kam,ban gane fuskar ba''
''nice mahaifiyar abdallah surukinki''
Sabuwar gaisuwa suka sake yi da mamin cikin mutunta juna kana daga bisani mamin ta gabatar mata da abinda ke tafe da su,sosai mama taji dadi don ko mamin bata fada ba takowar da tayi ta fara neman yaran ya tabbatarwa mama sihirin dake jikinta Allah ya kawo lokacin karyewarshi
a nutse mama ta gaya mata inda su maryam din suke,fadar irin dadin da mamin taji bama ita kadai ba harda baaba uwani bata baki ne
''ba shakka gobe zan je na dauko yarana,alhmdlh Allah na gode maka''
a take ta daga waya ta kira baffanta ta sanar masa,cewa yayi ta jinkirta zuwa goben,don bai kamata kai tsaye a dawo da su din ba,akwai abubuwa da ya kamata mafin dawowar tasu,baya ga haka magani yake karba,ta bari nan da wasu yan kwanaki idan ya gama tsara komai zai mata maganar
Bata musa din ba saboda tasan baffab akwai hangen nesa,cikin farinciki da zumudi suka baro gidan zuciyoyinsu fal farinciki da godiya ga Allah,ba qaramin qimar mama mami ta sake gani ba data hada diyarta da danta ta kaisu ga mafaka cikin ikon Allah,sosai ta kuma ganin qimarta
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Washe gari hisham ya shirya don komawa katsina,yanason duba company din abdallah guda biyu dake can wanda abdallan yace a fidda wa ma'aikatan companies din salary dinsu tunda wata yazo qarshe
Kai tsaye ya isa dakin tsoho alhaji wanda dama abdallah na ciki suna tare bayan gama shan rubutunshi wanda ya zama shine ruwan shansa a yanzu,yana duqe gaban tsohon
''banda abunka hisham tafiyar dare ai sam bata da dadi,da ka jinkirta zuwa gobe''cewar tsoho alhaji da yaje yiwa sallama,murmushi yayi kanshi a qasa
''banso komawa ba ma malam,naso naga yadda jikin abdallah zai kaya duk da yanzun ma alhmdlh yana gayamin yana jin canji a jikinsa,tafiyar ce ta zo min haka amma insha Allahu kwana uku kawai zanyi na dawo''
''to shikenan Allah ya tsare hanya,a gaida manyan''
''ameen ameen,Allah ya qara girma''ya fada yana miqewa,ya juya ya miqawa abdallah hannu suka yi musabaha,inna wuro ta shigo da jarka biyi daya man shanu ne a ciki daya nono tace ya kaiwa gwaggonshi,godiya ya mata sosai kana suka juya dukka zasu rakashi bakin motarsa
hannunta taji an riqe da sauri ta juyo,abdallah ne,ya wani narke yana mata wani krin kallon dake sake karya duk wani makaman zuciyarta,tanajin da biyu yake mata irin wannan kallon
''baby maryam''
''abdallah mene haka''ta fada a zuciyarta
''inaji a zuciyata na kusa warkewa nan kusa,hakan na nufin mun kusa rabuwa?''
wata mummunan faduwar gaba taji,ta lumshe idonta kana race cikin muryarta nai sanyi
''sun fita fa,ka sakarmin hannu muyi sallama''
''hisham ai ba baqo bane,gwara ki zauna nayita kallonki,naga alama da gaske so kike kifi qarfina,tun jiya rabona da na ganki,jiyan ma batan kai nayi na sa kai na bandaki ashe kina ciki kina wanka''
Ba tare data shirya ba ta waiwayo tana dubanshi idanunta a waje,take kuma suka kawo qwalla,dama abinda yakeson gani kenan
''ina wanka?,ba kaya a jikina kenan''
dariyar da bai shirya ba ta subuce masa,ya dinga yi yana kallonta,sai yaga gaba daya ta kuma qaramar yarinya sosai da bazata wuce shekaru sha hudu ba
''wai ke kam shekarunki nawa,i thought ba zaki wuce twenty four ba,kamata yayi Allah a maidaki shekara goma,dubeki kamar wadda aka cewa saurayinta ne ya ganta''
ta lura ma ya maidata wata abar tsokanarshi bayan wasan kura da yake mata da zuciyarta duk lokacin da suka hadu
''Allah sai na gayawa inna wuro leqen mutane kake a bandaki...''
''a'ah,ba dai mutane ba gyara zancanki yammata,leqen mata ta nake,sai kuma mero......''
''mero?''
ta maimata sunan ba tare da tasan ta fada din ba
girarsa ya daga mata
''eh mero mana,itama matata ce baki sani ba?''ai a,hanzarce ta qwace hannunta ta fice a dakin,dariyarsa yasha sosai yana raina wayon maryam din da ta gaza gano abinda yake nufi
Ta gama shirin baccinta ciki doguwar riga mai sulbi mai hannun shimi maroon doguwa ce har qasa ta maida qaramin farin hajabinta jikinta ta haye gadon inna wuro tana karanto addu'o'in bacci,bayan ta kammala ta ja bargon inna wuron ta lulluba zuwa qugunta bayan ta lumshe idonta
Da sauri taji an yaye bargon,ta bude idanunta inna wuro ce tsaye a kanta riqe da torch light donta kashe qwan solar din dakin
''me nake shirin gani meramu?''
cikin rashin fahimta tace''me ya faru inna?''
tana nuna qofar dakin nata da yatsanta tace''ki baro dakin mijinki kizo kimin qabe qabe kan nawa gadon da yake ni ba miji gareni ba ko?''
fuska ta yamutsa
''kai inna,naga dai tsoho alhaji ai yana da turakarsa ko?''
''iyeeee''ta fada tana kama haba
''to tashi ki barmin daki,idan yaso in kinga dama kiyi shimfida a tsakar gida ki kwana can''
ta sake yamutsa fusjar tana kallon innar ba tare da ta ko motsa da niyyar tashin ba
''kai inna ni wallahi kamar ma kwanan nan kin tsaneni''
''eh koma me zaki fada ki fada amma saikin fitarmin a daki,dama kuma ni bana tarayya ai da mai kynnen qashi....zaki taahi ko sai na samo madoki?''ta fada tana dube duben abinda zata dauka na duka din,tasan kadan daga aikinta yadda take qaunar abdallah yanzun ta maketan ta sauko tana guna guni taja bargon
''ajjiye min bargona,kuma kuna da shi''ta fada tana kallonta,tilas ta ajjiye mata din ta fito
tana gab da shiga dakin taji maganar tsoho alhaji yana fitowa daga dakinsa,ta qarasa cikin girmamawa,wata 'yar farar roba ya miqo mata yana fadin
''da dakinnaki zani,tunda kuma gaki shikenan,wannan maganin banason ya wuce yau ba'a shafa shi ba,daga cinyoyin abdullahi zuwa yatsunsa na qafa,a tabbatar ko ina ya samu,kada ki barshi ya taba da hannunshi don a qa'idarsa wani ke shafa maka,sabida jikin shi har yanzu akwai ragowar abinda aka yi masa''
''to malam,Allah ya qara girma''ya amsa nata ya juya ya koma dakinsa ita ma ta shige
kan katifar ta hangoshi zqune jingine da pillow,laptop ce kan cinyoyinshi kallon wani film yake na tarihin sayyadina umar,vest ce a jikinsa da short nicker wanda iyakacinshi saman gwiwarsa,dauke kanta tayi da sauri,shima tunda ya amsa mata din ya maida kansa kan allon computer din,ta haura kan katifar ta dauki pillow qwaya daya,har zata sauka sai ta tuna da maganin
''tsoho alhaji yace a shafa a daren nan''ta fada tana miqa masa maganin
fuskarshi ba walwala yace
''wa kike son ya shafamin bayan na jishi yana gaya miki kada na taba?''shiru tayi cikin rashin sanin amsar da zata bashi,bata ankara ba taji ya damqi hannun nata bayan ya ajjiye computer din tasa can gefe ya janyota yana fadin
''malama zauna ki shafa min''take kuwa ra samu masauki kan cinyoyinshi,qoqarin miqewa tayi take amma ya danne rigarta,yasa idanunshi sosai cikin nata
''kika sake kika gudu....q'nnn,ni dake ne''ya fada cikin dakiya
''dagan rigarta to zan shafa maka''
bai amsa mata ba sai hannu da yasa yana qoqarin,zare hijabin jikinta,hannayenta ta hada ta cukuikuye hijabin saboda rigar jikinta mai fadin wuya ce bugu da qari kuma mai lafewa ce a jiki
kicin kicin yayi da fuska kamar bai taba dariya ba
''ki bar ganina a zaune bazan iya tashi ba,to kada ki kuskura na sa miki qarfina zaki sha wuya,daga ni sai ke a dakin,na bama kallonki zanyi ba,zan cire miki don kada ki shafa min ba daidai ba ko ki bata hijabin naki,ki shafa min kawai idan kinso ki koma soro ma ki kwana''
ta gama amanna da gaske yake ganin uadda yayi maganar ba wasa a fuskarshi,sakin hajibin tayi yasa hannunshi ya zare shi ya ajjiye mata shi gefe
''fatabarakallahu alhsanul khaaliqin'' ya ambata cikin ranshi saboda ba qaramin kyau night gown din tayi mata ba
''tafaddal''yace da ita bayan ya tattare short nickers dinsa can sama,kallo daya tq masa ta dauke kai,bata taba ganin wani namiji a haka ba tunda take,santalan