Showing 6001 words to 9000 words out of 162126 words

Chapter 3 - ABADAN

ya fi wanda ya fiki ma''hindatu ta fada wadda maryam ta tura daki tana mata gargadin kada ta sake cewa komai,sai kuma abu ya dawo kanta bata kula kowa ba ta fice inda ta nufa cikin zuciyarta cike fal da tsanar halayensu

πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„

Saura kwana goma biki aka kawo lefe,lefe ne na gani na fada wanda ita kanta maryamu ta yaba qwarai da gaske,qarara rudewar su huwailan ta fito,sumbatu suka dinga yi don duka cikinsu babu wadda ta aurar da 'yar da ta samu lefe kwatankwacin haka,komai sai da suka masa dilla filla suka qare masa kallo



abinda ya bata mamaki ganin dukkan 'yan gida sun shiga shirye shiryen bikin gadan gadan,kada ma inna hadiza taji labari,duk da ba shiga sabgar su maryamun take ba,harda cin bashi da sauya furnitures din daki


maryam na zaune gefan mamanta tana lissafa mata sunayen mutanen da zata tura hindatu takaiwa cingam tana rubuta mata a takarda hindatun ta shigo,hannunta ledar dinkunanta ne da ta door mat da maryam ta bada ta siyo,ta zauna kan kujera tana fadin
''sannu harkin dawo?''
''eh wlh amma fa na sha wuya''ta fada tana shiga kitchen ta dauko ruwa cikin gorar faro da suke durawa susa a fridhe dinsu,sai da tq shanye sannan tace
''mama''
''na'am''
''nifa abun nan na bani mamaki''
''mefa?''ta tambayeta tan duba rubutun,da maryam keyi
''su hauwa mana da su jamila,gaba daya sai hidimar biki ake yi,kada ma jamila taji labari ita da mamanta,mutanen da aduniya babu wadanda suka tsana kamar mu?''
sai a lokacin maman ta kalleta duka harda maryam din
''to,banda abinki hindatu sai ku godewa Allah,me yiwuwa Allah ne ya ganar da su gaskiya,tunda babu wanda za'ace *ABADAN* zai dawwama a halin da yake,dole watarana akwai sauyi,qila Allah ya ganar da su ne''
''nima dai mama haka nayi tunani,kuma wallahi bakiji dadin da naji ba,Allah yasa silar gyaruwar tsakanin mu kenan''
''ameen''cewar mama,ita dai hindatu tabe baki tayi tace ''to Allah yasa,amma ba girin girin ba tayi mai''


sallamar jamila ce ta katse hirar tasu,dukkaninsu suka bita da kallo,don basu iya tuna yaushe ta shigo dakin na qarshe,koda sun tuna ma ba alkhairi ne ya kawo ta ba
''sannu mama''
''yauwa sannu''
''gurin maryamu nazo''
''to gani''injita
''cewa nayi yaishe zqki lalle,ina son na biki ne muje tare,kinsan qannan amarya dole su fito kamar amaryar''


sosqi maryamun taji dadi har ta saki tattausan murmushin ta
''ai ba damuwa,jibi ne sai mu tafi tare ai''
''to shikenan''ta juya ta fice
hindatu ta kalleta
''haba ya maryam,nidai gaskiya bazan hada tafiya tare da su ba''
''sai ki fasa zuwan ai''inji mama
''don kuwa ni zan biya mata ma kudin lallen,haba hindatu dan uwanka dan uwanka ne fa,kuma ka dinga kyautatawa dan uwanka musulmi zato,ki zama mai tsarkakkiyar zuciya kinji qanwata''dole hindatun taja bakinta ta tsuke



Tare suka je lallen maryam hindatu da jamila,ita biya kudin dukkaninsu


πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„

cike gidan yake da mutane kasancewar yaune ranar daurin aure,ga gauyar yan uwa daga bangaren mama da inna hadiza,kusan yawancin danginta na cike a gidan danqam,har ita kanta maman tayi mamakin hakan,amma sai ta share,batun sanin cewa babu yadda Allah baya iya sauya lamarinsa


maryam na maqotansu ita da qawayenta ciki harda raliya,tayi shar cikin atamfa super riga da zani plain,ba qaramin kyau tayi ba,fuskarta cike da walwala da farinciki


guda suka dinga ji tana tashi sosai tamkar a cikin gidan akeyi kasancewar maqota ne gida jikin gidan,raliya ta saki tata gudar tana fadin
''shikenan alhmdlh an daura,tazama tazama,yau diyana ta shigo sahu,Allah yasa wata tara iwar haka mu hadu suna''dariya duka aka saki wasu na cewa amin wadda shigowar hindatu cikin gunkin kuka ya katse musu ita
maryam ce ta soma miqewa tanajin qirjinta na bugawa tun kafin taji me ya samu hindatun zuciyarta ke mata saqe saqen munanan abubuwa


zubewa tayi gaban maryam tana fadin
''ya maryam don Allah me kika yiwa ya jabir?,me kika yi masa da zai miki wannan sakayyar?,me kika yi masa da har ya guje miki ya maida aurenshi kan *JAMILA*?''
dum taji kunnuwanta sunyi,qwaqwalwarta lokaci guda ta gaza yin aikinta,sai ta daina gane komai,meke shirin faruwa d ita?tambayar da taji qwaqwalwarta na mata kenan,kafin bijirowar amsar sai taji tamkar an zare dukkan wata garkuwa da ta sata ta iya tsaiwa da qafafunta,yaraf taji ta zube,daganan komai ya dauke mata dif kamar an dauke wutar nepa adaki mai tsananin duhu........




*mrs muhammad ce*πŸ‘‘



πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ»βœπŸ»βœπŸ»βœπŸ»
[9/17, 12:50 PM] 80k: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸŒΊπŸ’–
🌺





β–Ά6⃣




''ya maryam,me kika masa da har ya guje miki ya maida aurensa kan jamila?''
maganar da keta amsa kuwwa cikin kunnenta kenan bayan ta farka,sai hawaye ya fara turereniyar fitowa daga runtsatsun idanunta da ta kasa budesu suna bi ta gefan fuskarta su sauka har cikin kunnenta,wani irin yanayi take ji daban cikin zuciya da gangar jikinta
me ta aikatawa jabir da zafi haka wanda har ta cancanci wannan hukuncin?
a iya saninta ba zata iya tuna abu guda ba mara dadi da ya taba hadasu a tarihin rayuwar soyayyarsu ba


hindatu ce ta fara ankara da farkawar tata ta sanadiyyar hawayen fuskar tata dake bi ta gefen kuncinta,da sauri ta taso
''sannu ya maryam,me yake miki ciwo yanzu''
kai kawai ta gyada mata alamar babu komai
mirya can qasa tace
''dagoni hindatu''
a hankali ta taonaka mata ta tashin ta jingina da filo sannan tace bari na kira ''mama''


maman ce ta takurata kan ta tashi hindatu ta rakata asibiti,bata biqatar fita koda falon nasu ne don bata san da wanne iso zata kalli jama'a,hakanan suma batsan da wanne ido zasu dubeta ba,ta tabbatar maganar ta gama zaga unguwar ma gaba daya ba gidan ba,amma ba zata iya misa mata ba don ita don ma so take tadan gusa daga gidan saboda haka ta zura hijabinta hindatun tace bari ta nemo dan adaidaita sahu sai tayi mata magana


bayan fitar hindatun shiru dakin yayi,baka jiyo komai sai hargowa da hayaniyar jama'arsu huwaila da inna hadiza cike da farinciki,mintuna biyar sai ga hindatun ta dawo ita ta riqe maryamun suka fito yayin da 'yan uwan maman nata dake zaune jugum a rumfar tasu suke mata sannu da jaje,don tuni wasu ma soma hada kayansu don komawa inda suka fito


Sun samu ganin likita cikin qanqanin lokaci don private clinic suka je,likitan yace zai riqe ta zuwa magariba ta huta sosai tasha magungunanta,bata musa din ba suka bata gado hindatu na tare da ita


basu bar asibitin ba sai magariba,suna hanya ne hindatu tace''anty raliya ta kira ki har sau biyu kina bacci,tace zaga sake kira,ya nasir ne yayi kiranta tunda kuma ta fita bata dawo ba''
kai ta iya gyada mata kawai don bata jin zata iya bude bakinta
suna shigowa layin gabanta ya dinga dukan uku uku,ji take tamkar ta,canza wani gidan ba nasu ba,ji take kamar ta yanka a guje ta bace a nemeta a rasa,motocine a jere har zuwa qofar gidan nasu,sauka sukayi suka biya shi sannan suka dutfafi gidan wanda har qofar gida jama'a ne


duhun da garin yayi yasa babu wanda ya shaidasu har suka shige gidan wanda tun daga soron suke jiyo tashin muryoyi cike da hargowa,babu wadda tace da 'yar uwarta komai har suka shigo ainihin tsakar gidan,ga mamakinsu qofar dakinsu ne cike yake da jama'a wanda ya tabbatar musu da koma mene ya shafesu


da qyar suka kutsa cikin rumfar tasu,mamansu ce zaune bisa kujera fuskarta dauke da tashin hankali,sai anty kubra qanwar mamansu,inna hadiza da baba huwaila sai jamila dake gefansu tana zuba ruwan bala'i har daurin zaninta na kwancewa anty kubra na maida mata da raddi
baba huwaila ke riqo,jamilan ta fincike kana ta zabga mata harara
''kinga malama ki qyaleni kawai,wallahi babu inda zani sai da lefena koda motocin daukar amaryar zasu shekare,a qa'ida ai lefe nawa ne kuma sai in zuba ido a take min haqqina,wallahi babu wanda ya isa ko duk duniya gatanshi ne yau sai kun fiddo lefen nan''
''qwarai kuwa haqqinki ne ai''babarta hadiza ta fadi cike da nuna goyan baya,wani abu ne ya tsirga wa huwaila,wato tsiyar ma har da ita a ciki yau


'yan mata biyun dake tsaye bakin qofa cikin 'yan daukar amarya suka hada ido,cikin tashin hankali dayar ta cewa 'yar uwarta,muryarta can qasa''mun shiga uku malika,wacce iriyar mace ya jabir ya kwaso mana''babu mai amsar duk cikinsu,saboda haka jiki a sanyaye suka zame,suka fice daga gidan


hindatu dake jiran qiris ta saki jakar hannunta tana huci ta qaraso gaban jamila
''rufe mana baki matsiyaciyar banza matsihaciyar wofi 'yan taka hayen arziqi,lefen banza lefan wofi,mj jabir ma yanzu bai ishemu kallo ba balle abinda ya fito daga hannunsa,idan kinsa ranki a inuwa ma zamu fito muku da gayuar tsiuarku ba sai kinzo kina haushi kina ragewa kanki daraja ba idon dangin miji ba''
sai ta,hau ihu
''e hooo,munji dai duka haushin rashi ne ,kaya dai sai kun bada su''
''ai dama zamu bada din amma ba saboda wannan hayagagar taki ba,zamu baku ne saboda mu a gun mu ba yanke talauci jabir ya bamu ba,kune nake tsammanin zai iya zama yanke talauci a gunku''
hannu inna hadiza ta saka zata zabga mata mari,tuni ta tare ta kana ta sake taku uku zuwa gabanta tana huci da nuna ta da yatsa
''kada ki kuskura wallahi,don idan a baya kin saba tabani ina qyaleki ta yanzu babu wannan maganar,idan kuma kika yi gigin aiwatar da hakan wallahi ko kadan bazaji kunyarkk ba daga hannu zanyo nima in nuna miki salon nawa iya marin,tsohuwar banza wadda shekarunt basu dade ta da k.....''


tsawa mamarta ta daka mata''kada ki kuskura kici gaba,zo ki wuce ki debo musu kayansu kawai idan na isa da ke''yarfar da hannun inna hadizan tayi a fusace ta shiga dakin maman inda anan kayan ke ajjiye ta soma fiddo da su tana watsosu falon
''kada fa ta barnata muku kaya kuyi mata gana''
''ina ruwanki,da muka zo da ke wanne taimako kika iya yi,tunda dai sun fiddosu ai shikenan''inji jamilar
takaici yasa huwaila jiyawa ta bar dakin


a warwatse haka hindatu ta dinga jefomusi su tas tun mama na mata magana har ta gaji da qyaleta,bayan kuma ta gama tace wallahi ian basuyi gaggawar kwashesu daga rumfar tasu ba zasu ga qasqanci,duk iya ikancinsu sun sqn halin hindatu sqrai bata iya fushi ba,don haka cikin rawar jiki suka dinga kwashewa ciki harda uwar amarya inna hadiza


sai da suka gama sannan taji kuka yazo mata cikin dakin nasu da ta shiga da niyyar rage qincin zuciyarta,sai ta tadda maryam nayin nata,kasa lallashinta tayi hala suka hada kai suka dinga risgar kukan da qyar anty kubra ta sha kansu


haka suka kwashi amaryarsu suka kaita gidan da aka shirya shi da sunan maryam din,wanda hatta kayan gado fiye da rabi kudinta ne ta baiwa baban nata ya hada da na gurinsa aka siyesu,abu daya ne inna hadizan tasa aka jado aka dawo musu da shi kayan kitchen,duk da haka sun cire manya manyan warmers masu tsada da maryam din ta siya cikin albashinta


πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„

kwana biyu gidan yayi da ragowar baqin su inna hadiza da basu ida tafiya ba,kwanakin biyun nan daidai suke da shekara goma na tsanani gurin maryam,kallo daya zaka mata ka dauke kai,hatta da mamarta wannan karon ta kasa daurewa zuciyarta sai da ta taya diyar tata kokawa

πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„πŸŽ„

ciwon kwana na hudu bayan sallar la'asar raliya ta iso gidan,maryam na kan dadduma bata kai ga tashi ba tunda tayi sallar la'asar,suna hada ido ta soma share qwalla,itama raliyan sai ta kasa daurewa duk da alqawarin da tayi ma nasir din bazata zo su hada kai suyita kuka ba


kusa da ita ta zauna suka soma aikin kuka wanda mama dake dakinta bata ji shigowarta ba sai rishin kukansu,leqowa tayi don ganin waye''ashshsha,haba raliya,abu da ya riga ya wuce kuma,don Allah ya isa haka,tashi ku shiga daki''ta fada tana karbar fadil daga gunta ta fice ta bar musu rumfar


da taimakon ambato Allah da take ta samu zuciyarta ta rage zugin da take
''raliya me n yiwa jabir haka da zafi?,wace iriuar qiyayya ce wannan ya gwada min,idan yasan tun farko baya sona me yasa bai gayamin ba tunda ba tilas aka mishi ba?''
girgiza kai kawai raliyan take
''maryam,ke kanki idan kika ga jabir sai kin tausaya masa,kallo daya zaki masa ki tabbata ba'a cikin hayyacinsa yake ba,kinsan me ya fafu ne?,lafiya suka zo gurin daurin auren amma kafin a kai ga gama taruwa ana zaune kawai su nasir suka ga jabir ya sume,mintina kadan ya dawo hayyacinsa,kinsan abinda bakinsa ya fara fada?,jamila nidai jamila nake so wallahi,zan iya rasa rayuwata idan ban mallaketa ba wallahi,abbanshi uazo yabi ba'ason maganar sai yace shi wallahi baisan wata maryam b ai tab cewa yana son wata mai suna marym ba,abbanshi ya dauka iskanci ne ya hau maa fada yace bazai maidashi mutumin banza ba,


abu kamar wasa sai ga jabir ya sake sumewa jin an hanashi jamila,da babanku yaga haka sai yace wa abban nashi ya barshi ai dake da jamilan duka daya ne''ajiyar zuciya maryam din ta ski mai tafe da hawaye,idon raliyan ciki natan tace
''maryama don Allah ki dinga saka abir a addu'o'inki,don ya hadu da jarabta,jiya nasir ya debeni muka je gidan,kinga yadda ake zaman?,yadda kika san bawa da uban gidansa,jabir ya zama abun tasayi,da jamila ta yi magan sai kiga ya zabura,tana saman kujera kwatankwacin bawa da uban gidansa''


a maimakon haushi takaici da tsanar jabir sai tausayinsa ya maye gurbi,take taji fiye da rabin quncin zuciyarta ya tafi,bata jin komai a ayanzu sai tsantsar tausayinsa,lallai ya fada cikin jarrabawa mai girma,sun dade tare da raliyan suna tattuna lamarin har daf da magariba sannan tayi musu sallama ta tafi


Bayan sallar isha'i baban su ya shigo falon nasu,bayanin da yayi musu kusan tishi ne kan wanda raliyar ta musu,ya rife da cewa''dln haka ke maryam sai kiyi haquri ki fidda wani mijin,tunda ke da jamilan duka daya ne 'yar uwarki ce''lamarin baban nasu na daure musu kai saidai ko daya maman tasu bata bari suyi maganar da ita kan yadda yake nuna wariyar launin fata qarara su da sairan yaran gidan,daga haka ya kade rigarshi ya fice yace idan ta samu wani mijin ta sanar masa






*Mrs muhammad ce*πŸ‘‘



πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ»βœπŸ»βœπŸ»
[9/17, 12:50 PM] 80k: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸŒΊπŸ’–
🌺






β–Ά7⃣


*WACE CE MARYAMA?*




Maryama diya ce ga *amina* da kuma malam *mahmud*,za a iya cewa itace diya ta farko da suka fara haifa shi da ita,asalin su fulanin kano ne cikin wani qauye da ake kira da gaya dukkansu shi da amina mazauna garin ne,yanayin nema ya dawo dasu cikin garin kano



amina maca ce mai matuqar haquri da kawaici tsantsar kyau nafulanin usuli,hakan yasa take da farinjinin samari da dama wanda hakan ya kusa haifar da rigima cikin qauyen nasu,dalili kenan da yasa babanta yayi saurin aurar da ita ga mahmuda dan maqocinsa wanda duka cikin samarin nata dama tafi karkata gashi,kasancewarsa shine kadai mai ilimin primary a cikinsu,amina maca ce maison karatu matuqa da gaske saidi a lokacin lokaci ne da ake qamatar karatin boko hakanne yasa bata samu wannan damar ba shi yasa tayi kwadayin auren mahmud din


kusan shekara uku da auren nasu kafin Allah ya azurtasu da samun qaruwa,da namiji ta haifa saidai baizo da rai ba,sosai mamuda yayi takaici kasancewarsa mai son 'ya'ya musamman maza,babu yadda ya iya haka ya haqura


bayan wannan haihuwar saida amina ta sake wata guda biyu duka maza kuma babu rai sai akan maryamu Allah ya tsaida mata,saidai wannan karon mahmuda baiyi wata murnar azo a gani ba kasancewar ba abunda yake so ba ya samu wato namiji,itakam amina hakan yayi mata dadi don a ganinta duka daya ne fatan dai Allah ya kawo mai albarka


bayan yaye maryam ta sake wata haihuwar macen itama babu rai a haka sai da ta haifi hudu dukkan ajajjere tsiran watanni ne ta kuma samun wani cikin duka dai basu zauna ba,lokacin ne mamuda yace ahikam aure zai qara,bata wani tada hankalinta ba tace ''Allah ya sanya alkhairi''
huwaila ya dauko wadda tunda tazo gidan ta fuskanci ba wani girmamawa yake wa amina ba,don haka ta tayashi takata,kusan tuni ya sakar mata duk wata ragamar kulawa da ta rataya tasu a kansa


Ba'a taba yiwa Allah dole,hakan ce ta faru ga mamuda domin huwailan ma da ya qwallafa rai a kanta haihuwarta ta fari da mace ta fara,a haka ahaka saida ta tara yara shida duka mata,ganin ita din ma babu biyan buqata sai ya tafi ya auro hadiza ya kuma zubar da lamarin huwaila kamar yada ya yowa aminatu


to ita din ma hadizan bata sake zani ba,matan ne dai sai da ta haifo bakwai sai daga qarahe ne Allah ya kawo namijin wato *ISHAQ* da suke kira isyaku,sunan mahaifin mamudan ne,to fa,babu zama wai an saci dan barawo,nan fa hadiza aka shiga daga kai an haifi namiji,rashin mutunci babu kalar da bata shukawa cikin gidan,hakkane yasa huwaila boye kishinta ta shige jam'iyyar hadizan suke gallazawa aminatu baiwar Allah wadda a lokacin ta sake samun qaeuwar diya mace shekarunta takwas kenan


Rayuwa tayi da rayuwa,yau da gobe kayan Allah,babu da talauci ta ishi jama'a hakan ce ta sauka gidan malam mamuda,ya taraau ya sanar da su cewa saidai fa kowacce tayi haquri da abunda zat gani don gaskiya bai da abun ci da su,ranar da ya samu ya bayar a dafa,ranar da babu kowa ya ci da kanshi,to dama ko can baya ba abinda yake masu,abinci ne zai baki kudin awo ranar cefanenki sai makaranta mai sauqin kudi ya sanya yaran ita din ma don ya dan san dadin ilimin kadan,to sai kuma salla salla ya dinkawa kowa kala daidai dama maryamu bata cikin duka wani budget nasa,idan akayi magana sai yace ai ita babbace ta dauki girma daga haka babu dadi babu ragi


huwaila da hadiza sukayi tsallen albarka suka ce sukam ba zasu iya ba,dukkan yaran nasu suka fidda su daga makaranta suka hau yin

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login