Showing 15001 words to 18000 words out of 162126 words
ta juya ta fice itama maryam ta juya ta koma dakinta
*mrs muhammad ce*π
πππβπ»βπ»βπ»
[9/17, 12:51 PM] 80k: πππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πΊ *ABADAN*πΊπΊ
πππππππ
πΊππΊππΊ
πΊππΊπ
πΊππΊ
πΊπ
π
πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πππππππ
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πΊππΊππΊππΊ
ππΊππΊππΊ
ππΊππΊπ
ππΊππΊ
πΊππΊ
πΊπ
πΊ
βΆ1β£2β£
Har gefin magariba tana gyaran kayanta cikin drower din,dakin tsaf yake don haka bashi buqatar wani sabon gyaran na daban,ta maida qofofin cupboard din ta rufe dai dai lokacin ta jiyo kiran sallah sama sama saboda haka ta shige toilet
har isha'i tana kan abun sallarta,sai da ta bada faralin isha'in sannan ta nannade ta,zaman shirun ya mata yawa,sai kewar gida ta soma damunta,ta jawo wayarta ta lalubu number din hindatu ta kira,ba bata lokaci ta daga
''wayyo ya maryam dita,i missed you wlh wuni guda kawai''
ta gatsine fuska tamkar tana gabanta
''hmmmm,ba wani nan,kinyi missing din nawa kika gaza kira na sai da ni na nemeki''
''ayyah anty na,kinsan dai halin student,wayan,ba credit,am sorry ya maryam''
''shikenan,ya gidan ina mama ta''
''gata kusa da ni bari in bata''
kusan minti goma suna hira har aka fara mata warning kudinta sun kusa qarewa sannan sukayi sallama
toilet ta koma ta hada ruwan dumi tayi wanka ssnnan ta sauya doguwar rigarta mai kauri ta bacci ta dora hijab,tsna maida kayan da suka fadl daga cikin sif din ta jiyo sallaman mami
kan kujerar falon ta taddata a zaune tana cire agogon hannunta
''sannu da dawowa mami''cikin fara'ar nan dai tata tace
''yauwa maryama,ya baqunta,na barki ke daya ko,gurin nawa ba yara ni daya ce,gun haj laura kuma basu sanki ba bare ki shiga,sannan na manta ban nuna miki kitchen ba,ina fata yunwa bata takura ki ba''
murmushin itama tayi
''banjin yunwa ma mami''
''a'ah,ban yarda ba,bari na shirya na fito saiki dafa mana wani abun mai sauqi''
''to mami''
miqewa tayi tana nuna mata jakar da ta shigo da ita
''taimaka ki shigo min da brief case din nan''inji mamin ta haura sama maryam din ta bita a baya tana mamakin sauqin kai irin na mamin,tamkar ita ba wata bace,tsabar sanin qima irin ta dan adam
saman ma wata duniyar ce,komai nashi fari ne tun daga parlour har bedroom din mamin sai dan ratsin baqi kafan wanda bai taka kara ya karya ba
''hmmm,wani aikin sai likitoci''maryam ta fadi a zuciyarta
a falon qasan suka sake zama bayan sun kammala cin abincin daren
''gaskiya maryama my son zai morewa girkinki,haka kija iya abinci''a kunya ce tayi mata murmushi
cikin seriouse tone tace
''maryam kamar yadda na fadi miki dazu inason Abdallah so na haqiqa saboda shi kadai Allah ya mallakamin,cikin irin abinciccikan da Abdallah keso akwai irin namu na gargajiya,sannan yanason kayan snacks,aikinki zai kasance ne ranar weekend zaki dinga breakfast lunch da dinner,amma ragowan kwanakin breakfast ne kawai sai dinner,amma idan ke kina da buqatar ci zaki iya dafawa,saidai majority idan da wuri abdallah zai fita yana tafiya ne da breakfast dinshi
sannan anan zaki dinga shirya masa saman dining dina anan yake karyawa,ina fata nima za'a dinga sammin idan an dafa din''ta qarashe cikin sigar tsokana,dariya ta baiwa maryam
''me zai hana mami,ai sai kince ya isheki ma''
''to godiya nake,amma please maryam ki riqe min amana don Allah,na yarda da muta ne da dama akan Abdallah na amma sun ha'inceni,and pls feel free ke 'yar gida ce''
taji dadin bayanin mamin sosai har zuciyarta
kadan kadan mamin ke janta da hira bayan ta nuna mata store da kitchen din nasu,tace ta duba idan da abunda take buqata ta fada zuwa gobe da safe a siyo tunda da yamna take tunanin zuwan Abdallan
girgiza kai tayi
''komai yayi mami''
''to masha Allah,sai waj.....''
maganr tata ta katse sakamakon shigowar kira wayarta qirar iphone 7
murmusho maryam taga tayi har haskrn haqorin makkar ta ya bayyana
''dan halak,yaqi ambato''mami ta fada a bayyane tana shirin daga wayar
''salamu alaikum my son yanxu nake zancenka''
''mami na ke da waοΌ''
''sabuwan mai dafa abinci nayi maka abdallah''
sai da ya danyi jim
''anya mami ba za'a haqura haka baοΌ''
''kada ka damu son,insha Allahu wannan karon ba za'a samu matsala ba kaji,saboda hankali na ya kwanta da ita fiye da wadancan''
''tunda kin aminta mami shikenan''maryam dake tsaye sai ta danji ba dadi,duk da bata jin abinda yake fadi amma ta fuskanta kamar bai marhabin ne da zuwanta gidan
''insha Allahu ba damuwa,yanzun ma muna tare,muna tsara tarbarka gobe''
ya narkar da murya tamkar qaramun yaro
''ayyah mami na,abinda nakw ta fargabar gaya miki kenan tun dazun,aikin ne mami bai kammalu ba sai nan da kwana uku,kinga ya zama dole na qara kwana hudu kenan,bazai yiwu na taho na barsu ba gudun samun matsala,but....i promise mami na nan da kwana hudu a gida zan kwana kiji mamina,kuma pls kada ki saka damuwa cikin ranki''
ta danji a ranta kam don tana matuqar son Abdallah,amma sai ta share
''shikenan my son,Allah ya kaimu ya kuma kare min kai,ya bada sa'a,ka ci gaba da addu'a don Allah banda wasa''
''insha Allah mami na,i love you''
sai da tayi murmushi sannan tace
''i love you too my son''
daskarewa maryam ta kusa yi a tsaye,tana sake jinjina soyayyar dake tsakanin mami da dan nata
''kinji ma maryam,abdallah ya hutashsheki,sai nan da kwana hudu zai dawo''tace da maryam wadda ke duba,cikin wani dan qaramin oven dake gabanta wanda a badini duniyar tuna ni ta tafi,ta dan washe fuska
''ayyah,Allah ya nuba mana''
''ameen ameen,mujeko sai kiyi kwanciyarki abinki''
tare suka fito falon sai suka tadda ta a zaune saman kujera,budurwar dazu ce
''sannu mami''tace tana dan murmushi hade da kallon maryam da hakanan tun ganin farko taji ta tsone mata ido,ko don kyawun da take hangowa baro baro ne kwance a halittar maryam din ohoοΌ
''yauwa sannu zubaida''
''na shigo ai dazu baki nan sai waccar na gani''
mami ta juya tadan kalli maryam
''sunanta maryam....ya akayi zubaidaοΌ''
tadan murmusa
''zuwa nayi na amshi key na part din ya abdallah zansa a gyara,naji kamar gobe zai dawo koοΌ''
'' damuwa jeki abunki zubaida zan gyara miahin da kaina,tunda kinga waccan karon yayi fada''
''to zan gyara da kaina mami''
''kada ki damu zubaida,jeki abunki''raahin,kin dadi qarara ya bayyana a,fuskarta,amma sai ta juya zata fice
''am....zubaida''mami tayi kiranta
ta juyo a sanyaye,kana ta amsa
''ku tafi tare da maryam ta gaida nene,ma'aikaciyar da na daukarwa abdallah ce''
dif zubaida tayi a ciki ciki tace ''to''ta juya tqci gaba da tafiyarta
momy ta kalli maryam''kije ku gaisheta,abokiyar zama na ce tin kafin rasuwan abban abdallah''
to din itama tace kana tabi bayan zubaida da tuni ta fice daga falon nasu har ta isa filin dake cikin bangaren nasu
Tana biye da ita har suka shiga bangaren nasu,ginishi iri, na mamin ne babu maraba sai bambancin furnitures,mutum biyu ne zaune a falon kallo suke na wani american film a M B C ACTION wanda volume dinsa ya gauraye falon,zubaidaida batayi sallama ba sai maryam wadda siririyar muryarta bata wadatar da su sun jita ba,zubaida ta zauna kusa da matar wadda ta kusa ahekara hamsin da biyar tana fitar da numfashi daga bakinta
matar na juya ta dubeta
''um hmmm,ai nasani iska ce ke wahalar da mai kayan kara,ni nasan ba baki za'ayi ba,amma tunda ke kika g....''
''nene ga mai aiki nan mami tace na kawo miki ki ganta''ta katse babar tata don ta lura basu lura cewa ba ita daya ta shigo ba
lokaci daya suka zuba mata ido nenen da daya budurwar dake zaune kusa da ita har maryam din taji faduwar gaba
nenen ta maida kallonta ga zubaida
''mai aiki,kodai baki ji bane sosai''
cikin yamutsa fuska da alamun qosawa tace
''wadda zata dinga wa ya Abdallah girki da ta canza''
nenen ta dawo da kallonta gun maryam,ta dan tara qarfin gwiwarta tace
''ina yini''second kusan biyar kafin tace
''lafiya,Allah ya taimaka''
''ameen,sai da safenku''maryamun ta fada tana juyawa ta fice a bangare nasu,sai da ta fita sannan ta samu nutsuwa,don ta tabbata rakiyar idanu suka yi mata
*mrs muhammad ce*π
πππβπ»βπ»βπ»
[9/17, 12:51 PM] 80k: πππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πΊ *ABADAN*πΊπΊ
πππππππ
πΊππΊππΊ
πΊππΊπ
πΊππΊ
πΊπ
π
πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πππππππ
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πΊππΊππΊππΊ
ππΊππΊππΊ
ππΊππΊπ
ππΊππΊ
πΊππΊ
πΊπ
πΊ
βΆ1β£3β£
cikin kwanaki ukun da tayi da mami ba qaramin dadin zama da ita taji ba,maca ce mai sauqin kai da iya mu'amala,haba haba da jama'a kowa nata ne,duk lokacin da suka zauna bata da labarin bawa maryam da ya wuce labarin abdallah
halayenshi
me yakeso mene baya so
quruciyarsa da shirmensa
tun maryam na daukar abun qarami har ta maida shi babba,lallai qauna ce mai girma tsakaninsu wanda Allah ne kawai yasan iyakarta
takanyi kuka aduk lokacin da mamin ta gama bata labarin mu'amalarta da Abdallah,tana dadewa kafin tayi bacci
me yasa ita bata ganin irin wannan qaunar musamman daga gurin abbantaοΌ
me tayi masaοΌ
wanne irin laifi tayi masa da yasa take samun rashin kulawa da raahin damuwa da ita daga abbantaοΌ
saidai tana godiya ga Allah saboda uwa ta gari da ya bata mai jajircewa kan lamuranta
duk lokacin da zata fito zata tadda sashen nasu tas,ma'aikatan har sunzo sun gama aikinsu sun tafi,saboda mami gwanar tashi ce da wuei ta saba,sai aka hada biyu don itama maryam din haka saboda yanayin aikinta da tayi a abaya
ita daya take wuni bangaren nasu musamman idan mami ta fita,takanyi mamakin yadda gidan yake shiru kamar babu kowa a gidan,don ita dai tun ranar farko bata qara ganin wani ba,daga ita sai mami idan ta dawo,ta saba gidansu cike yake da jama'a,hayaniya kuwa sai dare ya tsala kake daina jinta,wannan yasa ta kuma maida hankalinta kan wayarta,research kan nai'ikan girke girke ya sake zama abokin ta wanda hakan yake sake bata damar qwarewa da samun experience duk kwanan duniya
π²ππ²ππ²π
ta fito kenan dauke da kayanta kala biyu sukayi kacibus da mamin hannunta riqe da maqullai
pakistan ne ajikinta riga da wando sai mayafinsa da ta yane kanta,yana daya daga jikin abinda ke boye shekarun mamin
tadan rusuna
''barka da warhaka mami,na zaci kin fita da muka gaisa dazu''
fuskarta a sake kamar kullum tace
''ban fita ba maryam,na tsaya gyaran dakunan Abdallah ne,kada ya dawo ya iaheni da mitar na bayar an gyara masa daki''
murmishi itama tayi
''ina fatan diya ta baki mance gobe ne aikinki zai fara ba''
gyada kai tayi
''ina sane mami''
''yayi kyau,kayan meye a hannunki''
ta kalli kayan sanna ta kalli mamin
''waje,zan dan fita ne na wanke su,bana son in tara kayan datti''
dariya tayi
''to wa yace miki bamu da mai wanki maryamοΌ,ajjiyesu,zan baki num din mai mana wanki ki kirashi yazo ya karba,zan fito da nawa duka ya hada''
''to mami''
da la'asar mak wankin yace mata ya iso yana waiting parlour wato falon su na farko,ta jado kayan duka ta sameshi tsaye,yana amsa ya juya zai fice,kafin yakai ga fitar zubaida da zahariyya 'yar uwarta suka shigo,dukkaninsu dogayen riguna ne ajikinsu masu santsi,babu mayafin da suka yafa yana saqale ne agwiwar hannunsu sunyi fashion da shi,kwatan kwacin irin shigar da 'yan matan yanzu keyi espicially gurin dinner din biki(wadda a nasu ganin suke kiranta da iya ado ko wayewa,wanda sam ko kusa,tsabar rashin sanin ciwon kai ne,Allah ya yiki mai tsada amma kin maida kanki mai arha,jikin da sai mutim ya biya sadaki zai gani kin raba shi kyauta kowa yagani,tinda hatta dinkunan da akwyi na fityed gown babu shatin abinda bai bayyana ba,ki sani bakya burge mai ilimi sai jahili,duk wanda yace kina burgeshi da irin wannan shigar to qarya yake,jikinki ne yake burgeshi,aqalla nasan bazai bar qanwarsa tayi irin wanna shigar ba bare 'yarsa,kin fito sak hadisin da annabi ya siffanta irinsu wadanda yace ba zasu shiga aljanna ba baza su kuma ji qamshinta yace kaasiyatin Aariyatin masu tufafi ne amma tsirara suke,maa'ilaatin mumilaat,karkatattu ne masu kuma karkatar da hankalin maza,sadaqa rasulul kareem)
kuma da yaci moriyar ganga zai yada qoranta,tuni zahariyya wadda me qaras qaras da chewing gum ta bangajeshi,sannan ta kuma juyo cikin gatsali da qasqanci
''dalla can malami,saboda ysabar rainin wayo da rashin mutunci kana gani zaka bangaje mutaneοΌ''
''Allah ya baki haquri''yace da ita yana sake kauce mata
''wallahi next time idan ka sake ka sake kwatankwacin haka na ranste sai na maka qasqanci,kuma ka tsaya ka jada a namu wankin,aikin banza kawai,mtseew''taja wani matsiyacin tsaki ta wuce,zubaida ma nata tsakin ta ja tabi bayan 'yar uwarta ba tare da ko sun dubi maryam ba
suna tsaye sai ga zubaida ta dawo dauke da kayan ta watsa masa
''kuma kada su wuce gobe na gaya maka''tajuya tayi shigewarta ciki
maryam ce ta tayashi tsince kayan tana bashi haquri,don duk gaba daya jikinta yayi sanyi,bata son taga ana wulaqanci wa dan adam
murmushi yayi
''ai babu komai hajiya,idan da sabo ai mun riga mun saba,banda darajar hajiya mami ma da tuni cin abincinmu ya qare agidannann tun bayan rasuwar alhaji''
ita dai bata fasa bashi haqurin ba har ya fice,a tausaye ta bishi da ido,wato a fayuwa idan dai kai talaka ne to baka to da kai da banza duka daya neοΌ,mutane daidaiku ne suka san waye dan adam wanne matsayi yake da shi cikin halittun ubangiji
''aikin banza''
taji am fada cikin dan daga murya
da sauri ta waiwayo,zubaida ce tsaye,cikin valcony din benansu wanda aka yishi ta cikin waiting parlour din,dauke kanta tayi don tasan sarai da ita take,itakam idan wannan ne itama ba naqonta bane,idan da sabo ai ya zame mata ruwan shata tun tasowarta cikin sararin duniya bata huta da makamancin wadannan dabi'un ba cikin mutanen da take rayuwa da su
ππ²ππ²π
Washegari tun bakwai mami ta fita tace zata ta nada excuse wa patients dinta don gobe da jibi bazata samu fita ba saboda dawowar dan lelenta wanda ya koma england cheekup bayan dawowarsa ta farko ya sake komawa tun bayan poising din da yasha,mutum ne mai qulafucin aikinsa saboda haka ya jefi tsuntsu biyu da dutse guda,bincike suke kan wani dan nijria tun kafin ya kwanta jinyarsa ta poising din da yaci wanda ake zargi da safarar muggan qwayoyi,a dan binciken da ya fara ne ya gano ya gudu england saboda haka yana gama ganin likita ya kutsa binciken mai laifin,cikin taimakon Allah
gogewa jajircewa da qulaficin iya aiki ya gano shi,abunda ya tsaidashi ya sashi qara kwana uku shine kamo ragowan abokan sana'ar tasa guda uku wanda dukkaninsu ya samu nasarar daqumosu ya aunosu nijeria gaba daya dan su girbi abunda suka shuka
jirgin da zai sauka qarfe shida na maraice ne zai sauka da su don haka tun misalin sha biyu na rana maryam ta shiga kitchen,tun jiya ta gama redy din duka abunda zata biqata ciki kuwa harda qullin waina da sinasir,miyar agushi ta soma hadawa wadda ta wadat ta da busashen kifi hade tantaqwashi sannan ta hada lemuka kala uku
bayan sallar la'asar ta hau suya wainar da sinasir,ta kammala tana shirin wanke kwanukan da ta bata ta jiyo shigowar mami,kan ta fito ta taddata cikin kitchen din,da fara'ar dai tace
''gaskiya an tayarmin da yunwata,qamshin kawai yasa naqagu inji dandanon ya yake,tunfa daga waje maryam nake jiyo qamshin nan,kai yau kice Abdallah da santi kenan''
murmushi tayi
''ko na zubo miki mamiοΌ''
sai da takalli agohon dake daure atsintsiyar hannunta sannan
''a'ah,jirginsu Abdallah ya kusa sauka,sauri zanyi na shirya kafin a daukoshi,idan naci abincina kuma ai masha qorafin don me banyi jiranshi ba''
sallamar zubaida ta ratsa dodon kunnensu,mami ce ta amsa mata tana fadin qaraso kitchen din
*mrs muhammad ce*π
πππβπ»βπ»βπ»
[9/17, 12:51 PM] 80k: πππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πΊ *ABADAN*πΊπΊ
πππππππ
πΊππΊππΊ
πΊππΊπ
πΊππΊ
πΊπ
π
πΊπΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πππππππ
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πΊππΊππΊππΊ
ππΊππΊππΊ
ππΊππΊπ
ππΊππΊ
πΊππΊ
πΊπ
πΊ
βΆ1β£4β£
Sallamar zubaida ce ta katse hirar tasu,mami ce ta amsa mata tace ta qaraso suna kitchen
taci ado ta cake cikin code lace dan ubansu wanda kana ganinshi kasan ba qananun kudi aka kashe wajen siyanshi ba
orange ne don haka ya haska baqar fatarta,tayi kyau sosai
''mami zamu je airphort taro ya Abdallah'' ta fada tana dan sunkui da kai
''Allah ya tsare sai kun dawo''
''ameen''
har ta juya mami tace
''am...zubaida,cikin ayarin su zai iso,ina ganin zaifi idn kika jira isowar a gida ko''kada kai tayi
''mota ta daban da tasu ai mami''
itama kan ta kada ''shikenan sai kun dawo''
sai da ta fice mami ta dawo da kallonta kan maryam
''zan haurq sama maryamu,idan kin kammala kema kije ki huta,sannunki,lallai kin aikatu''
''to mami,sai kin fito''ta fada cikin
murmushi
sai da ta sake biyawa ta dining din ta tabbatar komai yayi neat kana ta wuce dakinta
wanka tayi ta sauya kayanta zuwa atamfa dinkin riga da skert,gashinta kawai ta kama ta daureshi da qaramin ribbom saboda bata fiya sa babban ribbom ba kasancewar gashinta akwai tsaho da cika,gefan gadonta ta koma ta zauna bayan ta dauko man da zata sjaf ta soma sjafawar a kasalance tamkar mai tausayin kada ta jima fatar tata ciwo,haka kawai take jin wata kasala na saukar mata,ji take kamar ta lwanta abinta tayi bacci
bata kammala shafa man ba ta jiyo jiniya da hayaniyar motoci cikin harabar gidan,a hankali ta miqe ta isa bakin window din dakin ta dan yaye labulen,bata hango komai yadda ya kamata sai dan abunda ba'a rasa baba kasancewar window din ba dirwct harabar gidan yake kallo ba ya dan fi karlata wani sashen,na doguwar valcony dinsu,bugu da qaro jama'ar da auka shigo gidan cikin motocinsu wadanda dukansu yan rakiya ne
tawagar mutanen suka biyo ta cikin valcony din tanan ta hango zubaida wadda fuskarta ke a dinke tsaf da alamu cikin bacin rai take
yana tsakiyarsu,saidai dukansu ya fisu tsaho,tafiya yake cikin hanzari wanda alamu ke nuna cewa cikin kuzari da qoshin lafiya yake,fari ne sol wanda yasa ya zarta duka jama'ar dake tare da shi hasken fata,ko ba'a gaya mata ba ta fuskanci shine *abdallan mami*yawan jama'ar dake baibaye da shi ya sanya bata iya ganin fuskarshi saboda juya kanshi da yayi daya bangaren yana magana da wani saurayi da sauran jama'ar dake gefan nashi,abu uku zuwa hudu zata iya fadi a kanshi suit ne a jikinsa baqa wul mai sheqi wadda ko da bakasan kudin sutura ba kallo daya zaka mata ka tabbatar