Showing 105001 words to 108000 words out of 162126 words
dinga tsinto halin da taga abdallah,abunda ya faru da ita ranar da zata soma rayuwar mai kama da mafarki,a hankali tunaninta ya dawo zuwa yau,maganganun nene sunqi daina yi mata amsa kuwwa a kunne,a dazun sam hankalinta bai nasu muhimmanci ba sabanin yazun data dage kai da fata sai ta tuna dukkan wani abu da nenen ta fada,ficewar da adnan yayi da sauri daga gidan
''taurin ran abdallah ne duka ya jawo mana halin da muke ciki,idan da ya mutu salin alin da mun huta''
maganar nenen ta qarshe kenan sanda take surkuda mata allurar bacci
taurin ran abdallahοΌ
ya mutuοΌabdallah kenan abdallah naοΌ
tambayoyin sun mata tsauri da yawa,saidai data hada dukkan abubuwan dake wulgawa cikin idanunta sai taso sansano qamshin wani abu wanda ya sata ta qarasa shugewa rudani na haqiqa,ita kadai ke fadin duk inda abdallah yake sai ta nemoshi
ba zata iya rayuwa,cikin duniya ba cikin salama ba tare da tasan ina abdallah yake ba,wanne hali yake cikiοΌ,a kullum addu'arta shine Allah yasa ta riga abdallahn mutuwa,zata masa addu'ar samun juriya da qarfin gwiwa kan rashinta,sabanin ita da bata da wanda zai mata wannan addu'ar,ta yaya zata jure rasa abdallah da mahaifinsa ta iya ci gaba da ingantacciyar rayuwa cikin dunuya
A hanzarce ta kima sashenta ta wuce bedroom dinta kai tsaye,kayan jikinta ta sauya ta dauki muqullin motarta,haqiqa dukkanin wani zatonta game da yadda rayuwarsu ta cukurkude lokaci guda ra dorashi ga nene,duk da ta sani wani bawa,bai isa ya dora maka wani abu ba face da izinin ubangiji amma akwai silar komai,nene ita ce sila haka zuciyarta ke gaya mata
ta bude motarta ta shige tana qoqarin tashinta usaini ya qaraso
''hajiya zaki fita gasu ibrahim kuma na zuwa''ta dubeshi kana tace
''idan sum qaraso kowa ya koma bakin aikinsa na maidashi,gobe idan Allah ya kaimu zamu tattauna da ku duka''ta samu damar fada sakamakon ambaton Allah da take yi cikin zuciyarta wanda hakan ya taimaka qwarai da gaske wajen zaunar da nutsuwarta cikin jikinta
Allah yana fada cikin alqur'aninsa mai girma
(KU SAURARA,TABBAS DA AMBATON ALLAH KADAI ZUKATA KE NUTSUWA)
Babu inda yafi dacewa ta dosa irin gidan kawunta wanda yake a yanzu tamkar mahaifi a gareta,mutum ne mai nutsuwa qwarai da fahimta babu bata lokaci ta fice a gidan kanta tsaye ta nufi can
ππππππ
Ranar wunin gaba daya akanta ta qare tana zaune qofar gidan ta tasa uban ruwan dake ambaliya agabanta,tun tana zuba ido taga ta inda jirgin agajin su nene zai dira har ta sare baki daya,ta sake laluba wayarta da niyyar kunnata ko zata iya kira saidai sama ko qasa ta nemi wayar ta rasa,wasa wasa ta miqe ta hau zazzage zazzage saidai ko qyallin kalarta bata hango na,abu kamar wasa sai da ta zazzage dukkan akwatunanta amma babu ita babu alamarta,dariya taji ana qyqyata mata ta dago kanta da sauri,malam na hayi ta gano yana keta ruwan yana takashi da qafafunsa tamkar wanda yake kan tsandauri ba ruwa ba,ya qaraso gabanta ya ya daga hannunshi sai ga wayar
''duk abinda kike aiwatarwa yau na sani,kina tsammanin kubuta daha hannu na neοΌ,to kinzo gidan da idan aka shiga saidai a fidda gawarka,ina jinku habiba ta baki labarin abunda ya faru da ita koοΌ,wato wanna bai zamamiki izina ba ke yar masu taurin kai,bari na baki shawara qwaya daya a taqaice,ki fidda sa dan komawarki gida muna tare mutu ka raba,koda yan uwanki ma sunzo basu isa su gane hanya ba haka zasu qaraci walagiginsu su koma,mune maganin makwadaitan mata irinku masu butulcewa hanyar Allah,kunqi Allah muma munqi shi kinga kenan mu muka fi dacewa da ku,kin riga da kin zama matar malam na hayi na zama mijinki''
cikin zafi ta bude bakinta da niyyar yaba mishi rashin kunya,bakinta cike yake fal da maganganu masu zafi da takeson ta gaya masa,raahin mutunci ta nado mai uawa zata masa wanda tana tsammanin tunda yazo duniya ba'a taba yi masa makamancinsa ba,da saurinsa ya daga hannunshi na hagu take bakinta ya rufe qam
''daga yau ba zaki sake magana ba sai idan na baki izini ko naso,ba zaki sake min musu ba ko wani ma ba ni ba''kai kawai take gyada masa kamar bawa da ubangidansa
''wuce ki tafi dakinki,daga gobe zaki amshi girki,yau na daga miki qafa kiyi jimamin rabuwa da gida irin na amare iya na yau kawai''nan ma kai ta gyada masa ba tare da tace komai ba ta tsugunna zata kwaahe akwatunta
''shiga ciki kawai,kafin ki isa su sun riga ki isa''nan ma kai ta gyada kana ta juya sum sum sum ta shige cikin gidan,ya isa gaban kayan ya dafa su take suka bace a gun bat,wata magaukaciyar dariya ya saki yaba yiwa kansa kirari kala kala,sai kuma ya dinke fuskarsa cikin yan sakanni tamkar bai taba dariyar ba ya juya ya shige cikin gidan
ππππππ
Su biyu ne ita da inna wuron zaune qarqash bishiyar lalle take kwabawa innan wanda zata saka a qafarta saboda dawiqar tsoho alhaji gobe daga qasa mai tsarki,har mamakin tsohuwar take bata ganin tsufan kanta ko na mijinta,adonta take daidai shekarubta wanda zai burge mijinta,dazu ta saka sabulu mai qamshi ta wanke kanta tas tace maryam din zata yi mata kitso
Tun kafin ta dago ta jiyo muryoyinsu,gabanta ya soma faduwa don ko kusa ko alqma bata sha'awad ta bude ido taga yarinyar,haka suka shigo cikin gidan tana tura wheelchair din suna hira abinsu,tunda ta dago kanta suka hda ido da abdallah ta dauke kai bata sake marmain kallonsu ba,miqewa tayi tsam ta isa bakin rijiya ta wanke hannunta sai tayi shigewarta daki duk da ba wani abun zatayi cikin dakin ba,tsaye tayi tana jin uadda suke hirarsu su ukun sun ma maisheta tamkar wata bare,kada ma abdallah yaji labari wanda a a yanzun ya koyi zuwa masallaci daga nan idan yaga damq yayi zamansa qofar gidan nenen suyita hira da samarin qauyen,idan kuwa ya tashi dawowa to mawuyacibe ka ganshi ya dawo shi kadai ba tare da mero ba,duk yadda taso danne zuciyarta da hanata jin kishin abdallah abun ya faskara yafi qarfinta,daga qarshe ta yiwa kanta hukunci ta yarda tana kishin abdallah saboda amanarsa da mami ta barta amma ba wai don so ba
Ko daya bata ji shigowarsa ba sai gyaran murya da ta ji a bayanta,ta dan waiwayo da sauri wanda hakan kadai ya isa ya gaya maka tunani takeyi
''excuse me madam''ya fada yana nuna mata hanyar da zai wuce din ba tare da ya kalli fuskarta ba
sai ta janye gefe ta zauna saman kujera ya qaraso ya wuce bangon dakin inda laptop dinshi ke ajjiye,tayi qasa da yawa hannunsa bazai iya kaiwa ba,tayi zaton wannan karon zai nemi taimakonta sabida gaba daya yanzun duk abinda hannunshi zai iya da kansa yake yi,ta manta yaushe rabon da ya sata wani abu,ko kwanciya ce ko dorashi saman kujerarsa mustafa ke taimaka masa
Bata ankara ba taji yana kiran mero,cikin rawar jiki ta qaraso dakin ganin maryam sai jikinta ya mutu kuma,ta soma rabe rabe
''shigo mana,wancan computer din zaki dauka min da ita zamu tafi saboda hoto koοΌ''sai ta washe haqoranta ta rave maryam ta wuce ta dauko conputer tana qare mata kallo din ba qaramin burgeta tayi ba ta miqa masa suka fice a dakin,wani dubqulallen abu ne ya tokare mata wuta ya hanata ta hadiyi koda yawu ne,tana jiyo su suna yiwa inna wuro sallama sun tafi rafi sai kawai ta qarasa zamewa ta kwanta gaba daya kan kujerar tana hawaye sosai
''meramu fito,ki saka min lallen nan mana,so nake na cireshi kafin mangariba ki kitse min kan nan,don malam alhaji saukar hantsi zaiyi''ta jiyo inna wuro tana fada,da zata iya da ta cewa inna wuron ba zata iya fitowa ba ta saka da kanta,tilas ta miqe ta goge fuskarta bayan ta sake saka kwalli duk don kada innar ta gane ta fito
tana kan tabarma lallen na gefanta,kallo daya ta yiwa maryamun ta maida kanta kan kwanon lallenta ba tare da tace mata komai ba,tun inna wuron na sako hira taga maryam din bata karbarta hannu biyu itama sai taja bakinta ta tsuke suka ci gaba da zaman kurame,duk yadda taso ta hana qwallar fita hakan ya faskar,haka ta dinga sulalowa tana sa gefan dankwalinta cikin dabara tana gogewa
''hmmmm,duniya kenan,Allah yana baka kana bana so,ba shikenan ba,garin kallon ruwa dama kwado kema mutum qafa,dana dam kuma dama ai butulcinsa yawa gareshi''shiru tayi gana jujjuya maganganun inna wuron cikin qwaqwalwarta masu zubi da gugar zana,sai tayi ta maza don kada ta gano kuka take ta tambayeta kanta na duqe kan qafar inna wuron da take sawa lallen
''lafiya inna,wani abu ne ya faruοΌ''
tabe baki tayi ya kau da kanta
''a'ah a'ah,babu abinda ya faru,Allah dai ya rufa asiri,amma shi aure komai lalacewarsa ai aure ne,yafi gaban ace za'ayi shakulaton bangaro da shi''
''hakane''maryam din ta fada tana ci gaba da abunda take,wani takaici ya kama inna wuron har taja qwafa duk da yadda taso daurewa
bayan ta gama sa mata sai taja gefe,gani,zaman shirun ya,isa don innar bata sake tanka mata ba sai ta jawo kwanon lallen wanda yayi ragowa ta qunsa a yatsunta na qafa da hannu
daf da kiran sallar magariba suka cire duka ita da innar,yatsun sunyi kyau kam,lallen ya kama ram da shi gwanin sha'awa
tana gama daura alwala taji sallamarsa,wanann karon ma sai da gabanta ya fadin,idanunta ya sauka kan mero dake riqe da laptop dina abdallah taba ta shafawa bakin nan kamar gonar auduga,har uanzu jan jambakin data sanya kan ta kile yana nan radam baje baje kan bakinta,ta sake saura dankwalinta sai ta shige kawai dakinsu don ta tabbata zaman hirar,nan zasuyi,hirar da ayanzu babu abinda ta tsana kamar ta
Tana shiga ta shimfida abun salla ta tayar da sallar,ko bayan ta idar zamanta tayi kan daddumar bakinta cike da addu'o'i wadanda suk riga da sun zame mata jiki,a kunnenta abdallah ya fita sallah ya dawo,inna wuro tayi kiranta ta fito taci abinci to tace mata har suka kammala bata fito din ba saboda tana jiyo muryar mero
Awa daya tsakani ta sake jiyo innar
''ki fito ki lallabe min kan nan tunda ba zaki ci abincin ba,inaga azumin yammaci zuwa dare kika fara''
abdallah ya kalli innar qasa qasa yace
''inna dama bata ci abincin rana baοΌ''
baki ta tabe
''ina fa taci ta dorawa kanta nunqufurci''
ya marairaice fuska kamar yqdda yakewa mami idqn yanason wani abu
''amma inna banda zama da yunwa fa''
''qyale shu'uma,cikinta ai da kanta zata nema idan yunwar ta rarakota''
kai ya kada yana jin ba dadi cikin zuciyarsa
''a'ah inna''
''ka qyaketa nace bawan Allah,ai ba wani ya hanata ci ba''
kwanukan ya dauka ya danna kekansa ya nufi dakin,a kwance ya taddata,amsa sallamarsa tayi tana qoqarin boye hawayen fuskarta don kada ya gani,ta miqe tana gyara hijabin jikinta zata fice a dakin
''dawo ki zauna''taji ya fada,haushinsa take ji fal cikin zuciyarta don haka ta masa shiru,taku biyu ta qara ta sake jin muryarsa mai cike da dakewa da kwarjini
''zan saba miki idan kika sake koda taku guda''cak ta tsaya kana ta dawo da baya tayi zaune kan ledar dakinta bayan ta cusa fuskarta tsskiyar cinyoyinta,keanukan ya tura mata
''dauki ki cinye banason inga komai cikin kwanon''ba tare data kalli kwanon ba tace
''bana ci na qoshi''
''tunda bakici ki fadi me kike son ciοΌ''
''na qoshi nace''
''baki isa ba''ya fada kanshi tsaye,yanayin yadda yayi maganar ya tabbatar mata da gaske har cikin zuciyarsa bazai barta ba sai taci
''me zaki ci nace''ya kuma tambayarta cikin dakewa da ginshira
''fura mai kwakwa da shawarma''tana sane ta fadi hakan don tasan mawuyacine a nan a samu abinda ta fada din
baice komai ba ya danna keken ya fice
Awa guda ya dawo da baqar leda
''karbi kici''taji yace da ita
ta miqa hannu ta amshi ledar fuskarta a qunshe,ga mamakinta duk abinda ta lissafa din ne a ciki
babu yadda ta iya haka taja ledar ya tasata a gaba da zazzafan kallonshin nan yace a gabansa zata ci
sosai ta bata masa lokaci duk don ya gaji ya fita amma sai ta lura baiko damu ba gyara zamanshi yayi ma,tamkar ma nishadi yangarta da zaunar da shi din da tayi take sashi
duk motsin da tayi idanunshi na kanta musamman dan qaramin bakinta mai dauke da pink din lips dake motsawa yana rauna shawarmar cikin rashin son cin abincin,wani abu ya darsa cikin zuciyarshi wanda ya sashi limshe idanunsa,ji yake kamar ya kamaau ya tsotsesu tas,wani,barin na zuciyarsa ke gaya masa loka cine
*mrs muhammad ce*π
πππβπ½βπ½βπ½
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
πΊ *ABADAN*πΊ
ππππππ
πΊπΊπΊπΊπΊπΊ
ππΊππΊ
ππΊπ
πΊπ
π
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πΊππΊππΊπ
πΊππΊπ
πΊππΊ
ππΊ
π
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*π‘
*_home of expert and perfect writers_*
5β£2β£
*_Manzan Allah S A W ya hana bacci bayan sallar magariba haka nan ya karhanta zance/hira bayan sallar isha'i_*
*_daga nana Aisha R A tace na kasance ina wanke janaba daga tufafin Ma'aiki S A W sai ya fita sallar asuba da tufafin alhalin akwai ragowar danshin ruwan a jiki_*
*_a wata ruwayar ta muslim kuma yace nana aisha tace''na kasance ina kankare janaba daga tufafin Manzan Allah S A W (kamar busashen maniyyi kenan)sai ya saka ya fita salla da tufafin_*
*_wannan shafin sadakarwa ne gareki dungurun gum baki dayansa SADNAF bama ke kadai ba har da 'ya'yana AFFAN DA IKRAM Allah ya rayasu ya yiwa rayuwarsu albarka,Allah ya bar zumunci_*
Idanunsa suka sake sauka kam yatsunta da take gutsirar shawarman da ita,yanayin yadda take ci kawai ya isa ya gaya maka kan tilas take ci din,don dama asalam ba cimarta bane da biyu tace ita don take so ga zatonta basai samo ba
ba qaramin kyau suka yi masa ba,kasancewar yana gan da ita yasanya ya kamo hannunta
''yaushe kika yi wannan abunοΌ''
ya fada yana kallon qwayar idonta,sai ta soma qoqarin zame hannin nata ba tare da ta bashi amsa ba
''maryam''ya kira sunanta can qasan maqoshi kamar maijin barci,nan ma bata amsa masa ba ya kuma fuskanci bata da niyyar amsa masa din,sunkuyo da kanshi yayi ya tura yatsunta guda biyun cikin bakinshi ya soma tsotsa a tausashe har yana lumahe iso tamkar wanda ya samu wani abu mai dadi
wani irin abu ta dinga ji yana tsirga mata tun daga tafin qafarta har qwaqwalwarta,take jikinta ya mutu baki daya hakanan ta rasa kuzaron hana shi sai idanunta ma da taja ta rufe tana ajiyar zuciya qasa qasa
A hankali ta bude idanunta jin ya daina shan hannun,wata iriyar kunya ta kamata kamar qasa ta tsage ta shige,ashe ita ua zubawa idanu tana kallonta bata sani ba
''uhmmm,madam,zan iya ci gabaοΌ,na kamar kema kina enjoying koοΌ''ya fada yana kashe mata idonsa na hagu,bata san me zqtq ce ba don ya gama kunya tata saboda hakq kawai saita fara hawaye tare da qoqarin zame hannunta saidai ko daya ya janata ya kama hannun ya riqe tsam ya kima zuba mata mayun idanunshi har tayi mutsumutsinta ta gana tq bada kai ta hanyar haqura tayi qasa da kanta kawai
Hannun ya sake mata bayan ya gama kallonta iya son ranshi,jikinsa gaba dayq ya gama yin laushi muguwar kasala ta lullubeshi
''ta yaya zan iya wanka qarfe takwas na dare,kinga ina zaman zamana kin jawo min koοΌ''
rasa inda zata tsoma ranta tayi,sam abdallah bai da kunya kwata kwata,lamuranshi yake gaba gadi,ko ita qaramar yarinyace ai ta gane abinda yake nufi bare da hankalinta
''ka jawowa kanka dai tunda bani na kirawoka ba''ta fada can qasan maqoshinta
''erhmmm,me kike cewaοΌ''ya fadi yana matso da kunneshi,shaf ta mance yadda abdallan ke da shegen ji kamar maciji
''najiki sarai abinda kika fada,amma ba komai Allah zai saka min,nima na kusa aure in sha Allahu nan kusa na huta''wani abu ne ya takareta har batasan lokacin da dago kanta ba bayan ta dubeshi tace
''toni me ruwana,idan ka tashi ka aure matan duniya ma baki daya sannan ne zansan ka cika jarababben ma.......''sai ta kasa qarasa fada saboda nauyi da maganar tayi mata da kuma yadda ya tsatstsareta da mayun idanunshi wanda bai gajiya da kallonta da su
ta cukuikuye hijabinta gu daya ta miqe da sauri zata fice adakin,hannu daya yasa ya fincikota atausashe sai gata gabadaya ta fada saman cinyarshi
''babu inda zaki sai kin qarasa fadar abinda ke ranki''
kai ta girgiza gabanta na faduwa cike da danasanin fara furta maganar
''na gama magana ta ai''
''qarya kike,akwai saura''batasan sanda ta rantse ba
''wallahi babu''
''ummh,sanannan ne zaki san na cika jarababben mayen mata koοΌ,dama can ni mauen mata ne ai ko kin mantaοΌidan baki sani na kuma to kibi a hankali don ta kanki zan fara maitar tawa kafin na sallameki''
tamkar tace wayyo Allah haka taji,kansu sake cewa komai an dago labulen dakin,mairo ce riqe da laptop din abdallah
''yaya abdullahi wai meramun kitson da....''sai ta kasa qarasawa sakamakon ganin maryam din kwance kan cinyar abdallahn,shi kuma ya mata rumfa da faffadan qirjinsa,hakanan sai maryam din ta samu kanta da sake narkewa kan cinyar abdallahn ta saki jikinta tare da saka idanunta cikin naahi sosai abinda bata taba yi ba,hakan yasa ya kasa daga idonshi ya kalli mero din baison yayi missing kallon kyakkyawan oily brown eyes dinta ba dake matuqar jan hankalinshi,ganin ba wanda ya dago ya kalleta yasa sakin labulen bayan ta ajjiye masa laptop din ta fice a dakin
Sai da taga alamun fitarta sanna ta janye idanunta,cikin fitar hayyaci ya kama fuskan tata don baison ta daina kallonshin sabida wasu zafafan abubuwa da yake karanta daga qwayar idanunta wanda shi kansa yasan bata san da su ba,satar amsa yake samu sosai ba tare da saninta ba,tana son qaace fuskarta yace
''ko na aure duka matan duniyan ma meye naki a ciki''
cikin fushin da batasab ya fita ba tace
''wallahi kuwa,tunda ni dama yar amshin shata ce ba,na kusa sanin inda dare ya yimun,su mero na kusa ai baka da damuwa''
Dariya taso kamashi hanin tsabar miskilanci da qarfin hali irin na mutum,ga gaskiya amma ka qita qiri qiri
''gaskiya ne''ya fada yana kamo hijabinta da take qoqarin,ficewa a dakin
''alfarma daya nakeso kiyimin don Allah,ruwa zaki dan duma ma min ki kaimin bandaki,idan inna ta tambayeki kice mata zafi nakeji duk da nasan halin innan sarai ba zata tambaya ba,amma idan da takura ki barshi sai naje nayi haka''
bata bari ta kalleshi ba don gaba daya