Showing 141001 words to 144000 words out of 162126 words

Chapter 48 - ABADAN

sabani,donko tsakanin harahe da haqori ma ana sabawa,na biyu riqe sirri ki riqe sirrinki ke da maigidanki maryam,koni idan bai zama dole ba bana buqatar jin sirrinku ke da abadallah,ku riqe amanar juna,ku riqe sirrin juna,ku zauna da juna cikin amana''nasiha ta dinga mata irinta tsakanin da da uwa,kuka sosai ta dinga yi har sai da mamin tace
''a'ah,ai kuma zaki batawa abdallahn kwalliyar me akayi kenan kuma uhm.....maza share hawayenki,duk da haka kowacce mace ta saba yau hashi kowa na zaune agidanta''.


Da kanta ta kama hannun maryamun har harabar gidan ta sanyata cikin sabuwar range robber baqa wul wadda kyauta ce mamin ta yi mata,tukuici ne ta bata,kadan daga cikin irin abubuwan da take ji zata iya yiwa maryamu,yadda ta kama hannun mamin itama sai ta karya mata zuciya har sai da ta share qwalla,motocine kusan shida don akwai yayar mami da qanwarta,sai yayar marigayi alhj abdulkareem mai nasara da qanwarsa,tana nan tsaye mamin har motar ta daga suka fice daga gidan kana ta juya ta koma ciki,tun daga lokacin ta soma jin kewar maryamun,bangare daya ga abdallah dake shirin tafiya shima,babu shakka kewarsu zatayi ba kadan ba,don ma ga mero nan,amma kafin su saba su maye mata gurbin maryamunta ai ba nan kusa bane


Sai da suka fara zuwa gidansu suka kaita gun mama da malam mamuda mahaifinta kafin su wuce da ita gidanta.



Wani irin yadine ajikinsa orange colour mai bala'in kyau da taushi,dinkin babbar riga 'yar ciki da wando,fuskar nan tashi tayi wani irin kyau na musamman,hisham ke riqe da wata iriyar jaka da aka qawata ta da rubutu mai kyau suna tafe yana masa tsiya har suja qarasa gun mami,tana falon nata tana sallah ya tura qofar suka shiga,kujera suka samu suka zauna suka jirayeta har ta idar,sai data shafa addu'a kana ta tashi ta dawo kan daya daga cikin kujerun itama ta zauna,hisham ne ya fara magana
''mami gashi na kawo miki shi,ayi masa nasihar zaman aure''mirmushi mamin tayi tace''ka kyauta kuwa,shi yasa nake sonka hisham badai hankali ba''
harararsa abdallah yayi''jimin dan rqimin wayo,kana nufin zan iya tafiya banzo ga mami na ba?''
dariya ya masa don ya fuskamci yanayin fuskarshi har ya canza ya kuma san ba wani abu ne ya tabashi ba sai barin mamin da zaiyi.


''abdullahi''ta kira sunanshi da salon da bata taba ba,take ya dago idonsa ya kalleta,sai ya kasa civgaba da kallon nata ya duqar da kanshi,son ya hango magana zata masa bata wasa ba
''shi aure da kake gani girma ne da shi,daraja da shi qima gareshi,sunna ce guda ta wanda akayi duniua da lahita dominsa wato annabi muhammad S A W duk wanda ya wulaqantashi baya tare da annabi na tabbatar kuma bazaka so haka ba,a duk sanda ka dauki yarinya,aka rqbata da uwa da ubanta da inda ta taso tavgirma,aka rabata da danginta aka rabata da duk wani wanda ta saba da shi aka baka to ka tabbatar da xewa amana ce aka baka mai girma,kasan sarai hikuncin wanda ya tozaratar da amana ko yaci amana ko?,ka tuna ko yauahe cewa matarka ba siyanta kayi ba,ba baiwarka bace 'yace 'yantacci ya mai yanci,kada ka dinga mu'amala da ita irin mu'amalar bawa da ubangidansa,a'ah,ka mu'amalance ta wani lokaci kamar 'yarka,ka tsawatar mata ka bata shawaea ka tausasa mata kaja girmanka,ka mu'amalanceta wani lokaci kmar mahaifiyarka,ka tausasa mata,ka kyautata mata,ka girmamata,ka mu'amalanceta wani lokaci kamar qanwarak,ka qaunaceta ka kauda duk wani abu da zai cutar da ita ko ya,bata nasabarta,ka dorata kan hanya madaidaiciya,ka mu'amalanceta kamar qawarka,ka gaya mata damuwarka,kayi shawara da ita,kuyi wasa kuyi dariya,matarka duka tana da wannan mtsayin a gareka''.


Ta dora da cewa''na tabbata har yau kana iya tuna mu'amalata tsakanina da mahaifinka wanan kawai ya isheka madubi,ya iaheka littafin da zaka dinga karantawa ko yaushe koda ban ce maka komai ba game da zamantakewa da iyali,abdallah ka guji zalunci,Allah da kansa ya fada cewa ya haramta zalunci abinsa kansa,kuma ya haramtashi a tsakaninmu,ka kyautatawa matarka,ka sauke duk wani nauyi da Allah ya dora maka,yadda kake da haqqi a kanta haka itama take da haqqi a kanka,ban yarda ka take mata haqqinta ba abdallah,iya wannan nasan ya,isheka nasanka nasan tarbiyyar da na maka,don Allah abdallah kada ka watsamin qasa a ido,kayi zama zama na haqiqa da matarka,Allah zai tsadaku ranar gibe kan yadda kuka sauke haqqin jilunanku,wallahi wannan gaskiya ne babu ko tantama aciki''
idanunshi tuni sun hama hada ja,zuciyatsji zafi take masa,karo na farko da zai rana gidan kwana shi da maminsa,a hankaki ya miqe daga mazauninsa ya isa gabanta ya durqusa kangwiwoyinshi,kana ya cire hular kansa
''mami kisa kin albarka,kici gaba da yi mana addu'a,insha Allahu zanci gaba da zama abun alfahari a gurinki''
hannunta ta dira saman kanshi kana tace
'' *BARAKALLHU LAKA,WA BARIK ALAIKA,WAJAMA'A BAINAKUMA FILKHAIR*'',ta amshi ukar da kanta ta maida masa ita saman kansa,sai ya kasa jurewa ya dora kansa saman cinyar mamin yana ajiyar zuciya,tausayinsu ya kama jisham,babu shakka ba qaramar qauna nace tsakanin wannan da da uwar ba,sai ya,kasa zama shima ya tashi a hankali ya fice,uwa ba wasa ba.


Mamin bata masa magana ba don ta saba da irin hakan,majority tun yana yaro idan zuciyarsa na quna haka yake ya dira kansa saman cinyarta har sai ya huce,don bashi da qawa a lokacin ko aboki da ya wuce maminsa(yana da kyau iyaye ku zama kune abokai ko qawa na farko wanda suka matuqar shaquwa da 'ya'yansu kafin kowa,ta hakane zaki samu damar yiwa diyanki kalar tarbiyyar da kikeso mai kyau ba tqre da wasu sin samu damar ruguje miki ba,bawa yara damar shaquwa da aboki fiyr da iyaye da rashin jansu a jiki babbar illace,da abokin nan ko qawarnan zwta dinga shawara,ita zata dinga gayawa damuwarsa bake ba,kinga kenan zai iya dorashi kan irin tasa tarbiyyar,amma idan akwai shaquwa tsakaninku kece mutum ta farko da zai fara dinga gayawa matsalolinsa da damuwarsa kafin kowa,saidai idan kuma yayi aure Allah ya bashi mace ta gari sai ki koya masa neman shawara daga matarsa,saidai idan duka su biyun tunaninsu baikai nan ba ko mas'alar tafi qarfinsu,a kuka don Allah iyaye,tarbiyya abace mai tsada da wuya,amma a qarshenta kuma ke uwa ke zaki fi kowa mora da jin dadinta koda baki duniya kuwa).


Ita ta riqo hannunshi suka sauko qasa,ya zama kamar ba abdallah ba,qwarin rai da qarfin zuciyar nan duka babu,har dariya ta dinga masa kan cewa ya girma fa,ya kamata ya koma abdallahn sa,nan da ten months yana iya zama daddy,abinda ya sashi dariya ya kuma bashi kunya kenan,bakin freezeer suka isa ta bude ta ciro wata qatuwar leda ta sake jansa har suka fito harabar gidan inda motocin security dinsa guda uku data abokansa guda uku ke jiransa,cikin motar da za'a kaishi ta bude masa da kanta ta sanyashi kana ta miqa masa ledar''Allah ya tsare hanya,a sauka lafiya''ta fada kana ta rufe musu qofar ta koma ciki,a varanda ta tsaya har sai da taga ficewar motocin duka.


Mus'ab abokinsu ke tuqa motar,usman na gefansa baya kuma hisham ne da abdallahn,cikin salonvtsokana hisham din yace
''idan bakason rabiwa da mamin kawai mu maidaka gida sai a yiwa maryam waya ta haqura kawai''harar ya galla masa bayn ya sauke ajiyar zuciya
''mami da maryam duka rayuwata ne hisham,ka sani,ba sai na maka dogon bayani ba''tsokanarsa suka ci gaba da yi tare da yi masa shaqiyanci kala kala irin na abokan ango har suka iso unguwar.





*mrs muhamma ce*πŸ‘‘


πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘
*_home of expert and perfect writers_*

β–Ά6⃣4⃣

*An karbo daga Abdullahi dan salaamin Allah ya yarda da shi yace:naji manzan Allah S A W yana cewa:((ya ku mutane,ku yada sallama,ku ciyar da abinci,ku sada zumunci,kuyi salla cikin dare lokacin da mutane suke bacci zaku shiga aljanna cikin aminci))*

_imamut turmuzi yace hadisi ne ingantacce_



*gaisuwa ta musamman gareku tare da dimbin godiya da jinjina*

*mom hanee*
*fatimah zahra haske asso*
*zainab idris makawa(takari)*
*maman farida(samun wuri)*
*maman rufaida (manal)*
*hafsat mai sharif(rayuwar aure na)*
*Billy galadanchi(hanjin jimina)*
*khairat*
*mrs ibrahim*
*maman aysha(gadar zare)*
*ummu zainab*
*rabi'ah haroun*
*maryam gital(ba halul kitabi bace)*


*KAI !KAI!!, INA KUKE MASOYAN ABDAN,TO KU MATSO NA GAYA MUKUπŸ‘‚πŸΎ*
πŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎ

*wannan page dinfa naku ne,duk inda kuke na sadaukar muku da shi kyauta,wanda na sani da wanda ban sansu ba,na kusa da na nesa*πŸ†πŸ†πŸ†


*NAGA SAQONKI AISHA GARKUWA πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ˜‚,NI DAKE AI DUKA DAYA NE MUSULMI DAN UWAN MUSULMI NEπŸ˜œπŸ˜‚,KICI GABA DA KARBAR SU AI DAMA NANA AISHA AI UWAR KOWA CE,UWAR MUMINAI R.A,NA GODE DA KIKA MIN KARAR KARBAR FANS DINA DA MUTUNTAWA KIKA BASU FURA DA NONO,ALLAH YAYI MANA JAGORA*πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ™πŸ½πŸ™πŸ½





😍😍😍😍😍

Gida ne gini na alfarma,gini irin na gata,gini ne mai cike da tsari kyau da fasaha a cikinsa,kana shiga gifan kawai zaka tabbatarwa kanka cewa gida ne da ni'ima da kwanciyar hankali tayi kaka gida acikinsa,sanyi da iskarsa ma daban take albarkacin tsirrai daya wadatu da su,duk inda zai kasance ansa tiles cikin harabar gidan baki daya an maye gurbinsa ne da grass carfet mai ban sha'awa,duk cikin abokan nasa babu wanda ya iya tsuke bakinsa ba tare da ya yaba ba,a haka suka ajjiye motocinsu suka dunguma zuwa,cikin gidan


parlour na farko anan suka ci burki,ya dubesu baki daya babu ko kunya yace da su
''daga parlour na farko fa banjin zan iya barin wani ya shiga parlour na biyu bare na uku,saboda haka anan zamuyi sallama da ku''
mus'ab yace
''dan iska,zakayi abinda yafi haka ma,kamar a kanka aka saukar da wahayin kishi,mun gama maka amfani ai tunda mun rakoka''
dage gira hade da kafadusahi yayi
''eh da gaskiyata fa,haka kawai na kwasheku har bedroom din matata,ina da kishi gaskiya''
''muma bamu ce zamu shiga ba malam,tunda munyi na Allah ai shikenan''inji usman yana ajjiye ledar hannunshi,yana dariya qasa qaa ya dafa kafadarsa''yauwa mutumina,dadi na da kai sauqin kai''


Tsokana dai irin ta abokan ango haka sula yo masa yana ramawa,barkwanci sosai suka dinga yo kama suka juya suka fito ya rakasu,har sunyo gaba hisham ya dawo
''yauwa,inason ganinka fa''
''zaka batan lokaci kenan,na bar gimbiya fa batasan na shgo ba ma fa''murmushi hisham din yyi mai hade da dariya
''me kake ci na baka na zuba,kunnenka na tsaya na ja don naga yadda kamka ke rawar nan,wlh kayi a hankali kada ka cutar musu da diya,na sanka sarao idan kana som abu baka daukar lamarinsa da wasa''
kunnen abdallah ya turo masa yana fadim
''to daddy,ga kunnen,fadi da kyau,ko daki zan baka ne ma kusa da namu kayi sa idon da kyau''tare suka sheqe da dariya kana suka tafa
''Allah ai kaine da iua shege,kai wa yasan me zakayi ranar da aziza ta zama taka''har wani sosa kai hisham yayi kana yace
''wlh fa,na barku lafiya to''ya fada ya juya yabi sahun yan uwansa dake zaune cikin mota suna kiransa aballah ya bishi da kallo,yana son hisham mutum ne mai amana wanda samun kamarsa sai an tona,ba duka mutum bane a wannan zamanin zakamasa alkhairi ya saka maka da alkhairi,mafi yawancinsu da sharri suke saka maka sai yan kadan



Sai da ya tabbatar sun fice sannan ya isa ya rufe gate din gidan don bai kawo mai gadi ba tukun,bai koma ciki ba sai da ya tabbatar ya rufe ko ina


A hankali yake takawa yana nufar cikin gidan,iskar damina na kadashi,wani irin ni'ima ce yau lullube da sararin subhana,iska ake mai dadi da shiga jiki,gefe guda wani tawagar farinciki ne ke shawagi cikin zuciyarsa,jinsa yake cikin wata duniya ta musamman,yau gashi ga maryamunsa,cikar muradinsa cikar burinsa,sashensa ya bude ya ciro kayan bacci farare tas da towel dan qarami kana ya rufe ya dawo sashenta ta cikin parlour din gidan na biyu,a hankali ya,keta har falo na uku wanda daga shi sai wani dogon corridor wanda kana shiga zaka tadda dakunan bacci uku,sai matattakalar bene wadda saman shima ke dauke da dakunan bacci parlour toilets da kitchen,a hankali ya,haura saman kansa tsaye ya tura qofar daya daga cikin dakunan da ya gani a bude wanda hakan ya tabbatar masa a ciki maryam din take


''assalamu alaikum warahmatullahi wabarakatu''ya shiga da sallama wanda hakan ba qaramin rage mata fargaba yayi ba,gefan kujerar dakin take zaune,kanta na duqe lullube da alkhyabbar jikinta,tsayawa yayi cak kana ya kingina da bangon dakin yana qare mata kallo duk da bai ganin fuskarta,ya kashe a qalla mintina biyar a haka zuciyarta na bugawa a hankali kanta na a qasa,ta tabbatar har yanzu yana cikin dakin saboda qamshin turaransa da ya cakude da nata ya lullube dakin,haka nan ya sake haifarwa da dakin wani irin ni'imtaccen yanayi,sannu a hankali ya dinga takowa gareta bayan ya ajjiye kayan hannunshi duka saman dan qaramin table na glass dake a gaban gadon,ya isa gabanta ya zube duka kan gwiwoyinshi,hannayenta ya kama ya sanya cikin nasa yana qarewa qunshinta kallo,tamkar yasa harshensa ya lashe haka yaji,sai da ya more kallonsa sannan ya dora kansa saman cinyanta yana leqen fuskarta,bai ga fuskar sosai ba sakamakon hular alkyabbar ta sanya ta yin duhu,a hankali ya sanya hannunshi ya janye hular take fuskarta ta bayyana saidai idon nata a rufe dai yake


Cikin wata sassanyar murya da bata zaton yana da ita ba taji yace''zan rayu dake zan mutu da ke *ABADAN* dani dake zauna''murmushi ya subuce mata don bata taba jin waqa a bakinsa ba sai a wanan karon,sai taji tafi dadi a bakinsa ma fiye da mawaqin,a hankali ta dago brown oily eyes dinta ta zuba masa,dama abinda yakeson gani kenan,shima murmushin ya sakar mata wanda saura kadan ya narka mata zuciya,ajiyar zuciya ya saki ya lumshe sexy eyes dinshi kadan sannan ya sake budesu''ya Allah ka gafartawa mami na,kayi mata albarka data sauqaqamin hanyar samunki,ta shiga lamarina'' kana ya daga girarsa
''yes....zan rayu da ke har *ABADA* maryam,haka kuma nake fatan koda mutuwa tazo min ta daukemu tare....''


Sake maida kansa yayi yi ya kwanta a cinyarta
''soyayya gaskiya ce baby,haqiqa,babu abinda ya kai so dadi,so shine abu mafi girma dake iya sarrafa zuciya kota wanene,haqiqa so ba ruwanshi da kyau nasaba ko cancanta mulki ko wata dukiya,yakan kama mutum ne kansa tsaye ba tare da qwaqwasa qofa ko neman izini ba,maryam kici gaba da zama tawa ni kadai har *abadan* don Allah''idanunta a runtse suke ya riga da ya gama kashe mata jiki baki daya a hankali ta dora hannunta saman sumarsa
''ni taka ce abdallah,takace ni,ina ji a jikina saboda kai aka halicceni,kaga kuwa har *abada* maryam ta abdallah ce,to ta yaya jiki zai iya rayuwa babu daya barin nasa?,ta yaya zuciya zata iya rayuwa da tsagi guda ba tare da daya tsagin ba?,ka zama ni na zama kai *mutu ka raba*'',qanqameta yayi kamar za'a qwace masa ita yana mata godiya tare da sheqar daddadan qamshinta dake barazanar juya akalar tunaninsa


A hankali ya dinga rage mata kayan jikinta tana zaune don ba musua tsakaninsu,a yadda taga mayen sonta cikin idanun abdallah zatayi matuqar qonashi a wanann lokaci idan tayi masa musu,da undeies kadai ya barta kana ya shige bandaki yayi nashi wankan ya fito bayan ya hada mata ruwan,kafin ta fito har ya zura kayan baccinsa ya saka 'yar hularnan tashi ka fiya naci fara ya nutsu saman abun salla,gefe taga nata kayan bacci,sai da ta qare musu kallo tanayi tana satar kallon abdallah dake salla,babu yadda zatayi haka ta juya ta sanyosu,gaba daya bata da maraba da babu dadinta daya akwai babban hijabi dogo a gun shita zura ta koma gefan gadon ta zauna,yayi sallama kana ya mata izini ta taso suyi sallah,raka'a biyu suka gabatar,addu'a mai tsaho suka yi ta neman alkhairai da samun zaman lafiya da haduwar kai a tsakaninsu sannan ya waiwayo ya kama kanta ya karanto addu'ar da annabin rahama ya koyar da mu
'' *Allahumma inni as'aluka khairaha wa khaira ma jabaltaha alaihi,wa a uzu bika min sharriha wa sharri ma jabaltaha alaihi*'',da salatin annabi ya rufe musu suka shafe tare


idanunsa cikin nata wanda a yanzu fargabarta ke dada yawa,girarsa ya daga yana murmushi
''wai duka tsoron nan na meye ne?''cikin nuna dakiya ta noqe kafada
''wanne tsoro?''
''gashinan ina ganinshi cikin idanunki?,kada kice a'a maryam,ina iya karanta abinda ke zuciyarki kai tsaye ta cikin idanunki,ko kin mance zuciyarmu guda ce?''
murmushi tayi cikin son nuna dakiya da jarumta amma sai ta sake ce masa
''ni tsoron me zanji''
tafa hannunshi yayi sau uku yace
''good girl,naji dadin samunki jaruma,kinsan kuwa irinki,nake so saboda irinkin ne kawai zasu iya jurata,ko da yake....nafa gasgata zancanki,kefa kince yadda kike kallon mace yar uwarki haka kike kallon *abdallah* kinga kenan ya kamata yau mu gane hakan ne ko ba hakan ba,uhmmm....are u ready?''
ta tuna sanda ta gaya mishi hakan cikin jirgi,take sai idanu suka raina fata,qwalla ta tarar mata,tana tsoron kada ya mata mugunta fa,cikin shagwababbiyar murya irinta me sonyin kuka tace
''kaima ba ka tsokane ni bane a lokacin?''dariya ya mata
''wasa nake miki matsoraciya,kwantar da hankalinki,babu abinda abdallah zai miki kinji,bacci zamuyi dukkan mu a gajiye muke,koke baki gaji ba ayi miki?''wata iriyar kunya ta dirar mata sai ta cure guru guda ta cusa kanta tsakanin cinyoyinta tana dariya qasa qasa,waishi abdallah wanne irin dan kai tsaye ne?''na gaji,na fika ma gajiya''kai yake gyadawa yana sake gano yarinta quruciya da rashin wayonta
''to kin gani,so ki saki jikinki kinji,ni yayanki ne ko?''da sauri ta gyada kai kuma taji nutsuwa ta saukar mata,umartarta yayi ta samo musu plate da cups a kitchen


da hijabin jikinta ta miqe har ta soma tafiya ya kirata ta dawo,hannu ya miqa mata kana yace
''ciro min hijabina dama aro na baki ai''
sai ta dan zare ido
''amma fa jikina...''
ya katseta ta hanyar dora yatsanshi kan lips dinshi yace
''shshshsh,i know....haka nakeson ganinki,kin mance ba musu?,idan kika qi kuma to yau....''bata ma barshi ya qarasa ba ta zareshi ta miqa masa ya amsa idonsa akanta a haka ta fice zuwa kitchen din ya mata rakiyar idanu


wayon da ya mata yasa ta dan saki jikinta kadan taci naman da dan drinks,sai da ya tabbatar ta kwanta yaja mata bargo har zuwa kafadunta kana ya sunkuya ya sumbaci goshinta
''kiyi bacci baby,kina tare da ni''a hankali ta gyada kanta kana ta lumshe idanunta,shi ya tattara kayan da sukayi amfani da shi duka ya fidda zuwa kitchen


A qalla mintina

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login