Showing 117001 words to 120000 words out of 162126 words

Chapter 40 - ABADAN

qara lafiya''
''ameen ameen inna''
ta dubi maryam dake zaune
''ita kuma wannan fa,meron ta barwa girkin kuma?''


Ya juya ya dubi maryam da ta dan hade rai don tasan yanzun innar zata sako wani abu kuma daban,ita kam gani take sam bata sonta yanzun tafi son abdallah da mero kawai
dariya ta tasowa abdallah,bai iya hadiyeta ba sai da ya dan dara
''inna targade tayi,Allah ma ya soni ya rufan asiri saura kadan tayi iyo cikin rijiya''
cikin tsoro innar ta zaro ido
''rjiya?,garin yaya ni 'yasu mairamu?''sai ta sake yin fuskar shanu ita ala dole sai ta nuna haushi take ji,sai abdallah ne ya bata amsa
''ina tsammani santsin lakar can ne,ba shiri inna na qarasawarkewa naje na tarota''
''to Allah ya rufa asiri''ta fada tana dan masa magana da ido,shi ma ya maida nata amsa ta hanyar langabe kansa da daga hannunshi alamun ban haquri



mairo ko dake bakin wuta cikin zuciyarta take cewa
''shi kuma baya tashi warkewa sai ranar da wani abun zai sameta,haka ma fa bakinsa yayi''
(hmmm,abdallah na maryam)

πŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒ

Washegari da hisham suka wayi gari cikin garin ni'ima cikin kuma gidan inna wuro,dukkansu tare suka zauna karin safe,kowanne ka dubi fuskarsa zuwa zuciyarsa cike take da farinciki mara misali,hira suke a tsakaninsu har suka kammala,maryam ta kwashe kayan ta gyara gurin


tsoho alhaji yace
''to alhmdlh abdullahi,kaga dai yadda ubangiji ya karbi addu'armu cikin lokaci qanqani''
kanshi a qasa yace
''hakane,malam naga darasi cikin rayuwa sosai,naga abunda da can bansan da shi na sai da Allah ya jarrabaceni da lalura,rayuwa abar tsoro ce haka duniya ma abar tsoro ce,darasi ne babba na koya cikin lalurar da Allah ya jarabceni da ita''


''gaskiya ne,dama wani abun baka saninsa ko gane shi sai ka shiga wata jarabtar,Allah ka bamu ikon cinye jarrabawarsa''
dukkaninsu suka amsa da ameen
tsoho alhaji ya dubeshi
''yanzu sai shirye shiryen tafiya gida kenan''
murmushi ya saki kana yace
''banjin barin garin nan da wurwuri haka,garinku ya yimin malam sosai,yaci sunanshi ni'ima,bazan taba mance wa da garin nan cikin tarihin rayuwata har abada,baya ga haka neman aure nake malam cikin garin naku''


dum kunnenta taji gaba daya yayi tamkar ba zata iya ci gaba da sauraren komai ba,sai ta rasa gane a wanne bigire take a zaune?,duk wata laka ta jikinta ta daina aiki,so take ta tashi ta bar dakin amma haka ya gagara
''a cikin karkaran nan tamu kuwa?''tsoho alhaji ua fada cikin mamaki,cike da tabbatarwa ya gyada kansa
''eh malam''




*mrs muhammad ce*πŸ‘‘


πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½
[5:05pm, 10/4/2017] HugumaπŸ‘‘: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘
*_home of expert and perfect writers_*

β–Ά5⃣5⃣



*Daga abdullahi dan mas'ud Allah ya yarda da shi yace:Manzan Allah S A W yace ''duk wanda yayi nuni(fara aikatawa) akan wani aiki na alkhairi yana da kwatankwacin ladan wanda ya ya kwaikwayeshi(ba tare da an tauyewa kowa cikinsu daga ladansa ba''(haka yake ga wanda ya qirqiri wani aiki na sharri kuma wani koyi da shi shima yana da zunubi kan duk mutum daya daya aikata irin aikin kwatankwacin zunubin wanda ya aikata aikin)*


*An karbo daga abu ayyubal ansari Allah ya yarda da shi yace:naji Manzan Allah S A W yana cewa''duk wanda ya raba tsakanin uwa da danta,Allah sai ya raba tsakaninsa da masoyansa ranar qiyama'',a wata ruwayar ta abi musa yazo da lafazin ''Allah ya la'anci wanda ya raba tsakanin uba da dansa,da dan uwa da dan uwansa''*






tuni ta miqe sabida kunnuwanta ba zasu juri jin abinda zai fada ba,saidai kafin ta kai ga ficewar har tsoho alhaji ya sake tambayarsa
''wacce yarinya ce abdullahi ka gani din,yar wajen wace?''
''ba wata bace ba malam,ta gida ce,mar........''
cike da gaggawa ra qarasa ficewa daga dakin don tuni zuciyarta ta riga ta bata sunan wadda zai kira din,dakin inna wuro ta wuce ta haye can quryar gadonta gami da cusa kanta tsakanin filalluka
''me abdallah yake so na masa ne da zai fahimceni,wacce hanya zan biyo masa da zai fahimce ni?ta yaya abdallah zai nemi auren wata?watan ma mero?eh tasan bazai wuce ita din ba don duka take takensa ya gama nuna mata haka''tambayar data ringa nanatawa kanta kenan


tana nan kwancen kimanin minti talatin da wani abu ta jiyo maganarsu,muryar inna wuro ta fara jin
''Allah ya tabbatar da alkhairi a tsakaninku,ni dama tuwo na maina ne,da kai da itan duka daya ne a guna''
wani irin abu taji ya tsirga mata da bata taba jin makamamcinsa ba,babu shakka kishi bala'i ne,bata sake gasgata kanta cewa tana kishin abdallah mai tsananin zafi ba kamar ranar,take ta yankewa kanta daga yau bata sake kwana a garin tunda ta gama iya abunda zata yi din,cikin qanqanin lokaci zazzabi mai zafi ya rufeta


Duk yadda inna wuro ta so fa fito ta qiya,gani take duka basu sonta,har,hisham wani irin haushinsa take ji,ko kowa zai goyawa abdallah baya ai bai kamata shima yabi yarima yasha kida ba,kwanciyarta tayi kan gadon tana jin yadda jikinta ke fudda hucin zazzabi ta kuma qi yarda ta gayawa kowa,sallar magariba da isha ne kawai ya tasheta daga gadon shima din sai taga innan ta fita a dakin

πŸ‚πŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚

Daga alwalar sallar asuba ta hada da wankanta baki daya ta dawo dakin inna ta canzq kayan tunda ta debo kayanta ganin hisham yazo tasan dole tare da abdallah suke kwana bazaiyiwu kuma tayi ta ziryar dauko kaya ba shi yasa ta debo duk abinda take da buqata


abin sallah ta saka tayi raka'atanil fajr wadda falalarta Manzan Allah S A W yace tafi duniya da abinda yake cikinta alkhairi,bata ko jira tayi azkar ba ta koma gadon ta sake nadewa,tanajin inna wuron na tada ta tayi banza da ita duk da idanunta biyu,ta baza kunnuwanta ne a tsakar gida ko zataji fitarsu abdallah ta shiga dakin ta dauki abinda ya mata saura


Tun tana azkar tare da tsumayin fitowarsu har wani dan qaramin bacci ya sacera sabida rashin isashshen bacci da bata samu ba jiya


Da addu'a ta tashi,ta zabura ta zauna kan gadon ganin rana ra gama fitowa sosai,ta,duba agogon dakin qarfe sha daya har da rabi na safe,takaici ya lullubeta,duka lissafinta iwar haka ta tsufa a kano,ta soma yaye bargon jikinta cike da takaici
sallama aka yo cikin tsakar gidan,kunnenta ta kasa sosai don tantance da gaske ne ko irin mafarkan da ta saba yi ne,kamar kuwa ansan tantamar da take yi aka sake rangada wata sallamar


Habawa ai duk tsawon gadon inna wuro mai rumfa batasan lokacin data dirgo daga kai ba kana ta kwasa a guje,bata dire a ko ina ba sai tsakar gidan,saura kadan suci karo da MAMI wadda ke tsaye tana son sake yin wata sallamar ga zatonta masu gidan basu jita ba


Zubewa tayi gaba daya a gaban mamin ta saki wani kuka mai cin rai,bata taba tunanin ganin mamin na a irin wannan lokaci ba dama zuciya kuma a kusa,ita ma mamin kasa daurewa tayi ta durqusawa ta dago maryam din hawaye na fita daga idanunta,rugume maryaman gaba daya tayi a jikinta cikin wani irin yanayi,daidai lokacin da inna wuro ke fitowa daga bayi dauke da buta a hannunta tana mai amsa sallamar don tana cikin bayin yake jiyo ta ya zaci maryam na bacci ne,dan tsayawa tayi tana kallonsu,take jikinta ya bata mahaifiyar abdullah ce saboda diban kama kadan da sukeyi


Dukkansu suna zaune kan tabarmar suna jimanta al'amarin,har yanzu maryam ta kasa matsawa daga kusa da mamin ganin take kamar har yanzu mafarki take,don ranaku daidai ne bata mafarki da mamin cikin baccinta
kasa daurewa mamin tayi tace
''banga Abdallah ba,ina yayi ne?''
''ya fita tattaki shi da hashimu nan bayan gari bakin rafi,kinsan an kwana biyu ba'a taka qafar ba''
cikin mamaki mamin tace
''hisham dai,dama hisham na tare da ku?''kai maryam kawai ta iya gyadawa
''Allah mai iko,shi yasa na rabu da ganinshi,babu irin cigiyar da ban ma hisham din ba ashe kuna tare''


kasa zama maryam din ma tayi ta shiga dauki ta dauki hijabinta ta sulale ta fice
tun daga nesa ta hango su zaune su biyu shida hisham da alamu magana suke mai muhimmanci sosai,a hankali ta dinga takawa tana qarasawa inda suke dukka idanunta na kan kyakkyawar fuskar abdalla



''taqi ta gane hisham taqi ta fuskanta,basan ta yadda zan fasalta mata ba,bansan hanyar da zanbi ba hisham,am doing my best hisham,ka gaya min ya zanyi?''
abinda taji yana fada kenan ba tare da ta fuskanci kan me yake maganar ba,sai ta qara sauri ta isa garesu data tuna maqaaudin zuwanta gurin,ji yayi kawai an kama hanninshi kana ta fara jansa,a mamakance ya dago yana kallonta,kasa tambayarta ma yayi sai ido da ya zuba mata,ganin yadda ta dage tana janshi ya sanya shi sauqaqa mata wahalar ta hanyar tashi ya bita tamkar raqumi da akala



bata bar jan hannunshi ba har sai da suka isa ga tsakar gidan inna wuro kana ta kauce daga gabanshi,tashin farko idanunsa suka sauka kan maminshi,runtse idonsa yayi ya sake budewa don ya tabbatar shin da gaske ne ko kuwa mafarki shina yake yi kamar yadda ya saba
''mami ce''hisham dake tsaye gefansa ya fada,ita din ma ajikinta ta ji zuwan nasa a hankali ta waiwayo suka hada ido da tilon dan nata,wani irin rauni abdallah yaji ya shigeshi,kewa qauna da soyayya irin ra da ya iyayensa ta taso masa,take jikinsa ya kama rawa yaji qafafunsa ba zasu iya daukarsa ba,yau maminsa ce a gabansa?


durqushewa yayi a gun a kan gwiwoyinsa kansa na duqe a qasa,hawaye ne ya balle masa tamkar mace,jikin mamin a mace ta miqe ta isa gabansa ta kira sunanshi
''abdallah,abdallah na ka yafewa maminka'' da sauri ya miqe ya kama hannayenra hawaye na sauka kan fuskar kowannensu,rawa bakinsa yake yama kasa magana,duk abinda yayi niyyar furtawa sai ya kasa,qaunar mahaifiyar yasa ke sake tosa masa,shaquwa da soyayya dake tsakaninsu ba qarami bane,yana jin bashi da kowa idan ba mamin ba,a lokacin data guje musu ji yayi kamar ya mutu,tawakkaki da imani da Allah ne yasa ya iya danne zuciyarsa yasa mata yadda da qaddara kafin daga bisani ta gano cewa koma meye ta aikata musu ba bisa hankalinta bane


Qarshe fadawa yayi jikinta yana jin nauyin da zuciyarsa na dada raguwa,wani sauqi ma samuwa cikin zuciyarsa daga abinda ya cunkushe mafa a da


hagu da dama suke zaune sun sanya mamin a tsakiya,ko qwaqwaqwaran motsi sunqi yi,ta dubesu cike da tausaya da qauna
''abdallah ku tafi ku kwanta hakanan,Allah ya kaimu gobe ko?''murmushi duka sukayi abdallah ya girgiza kansa
''yau mami komai iya satar baccin banjin zai iya saceni,ko na kwanta din bazan iya baccin ba,itama haka don babu ranar da bazata yi maganarki ba koda cikin zuciyarta ne,saidai idan ke kinajin sai mu qyaleki ki kwanta ko''



girgizq kantq take cikin zuciyarta tana sake jinjina qaunar dake tsakaninsu,tsanar nene ta qara cika zuciyarta,tana jin mawuyacine ta iya yafe mata haqqinsu data dauka,raba qaunar data yi dake tsakaninsu na tsawon lokaci ba tare da sunji ko sun gani ba,haqiqa Allah ne ke saka soyayyar dan adam cikin zuciya


A taqaice kwanan zaune sukayi su duka ukun don sai bayan sallar asuba kowanannsu ya kwanta



Qarfe uku na rana suna tare da ita maryam abdallah da hisham,mamin ta dubi Abdallah
''gobe nakeson mu koma gida abdallha,saboda haka ku fara hada iya abinda ke da muhimmanci,saura ku barwa mutan gidan kafin komai ya qarasa daidaita ku sake waiwayarsu''
cikin shagwabar da ya jima baiyi wa mamin ba yace
''mami a daga min qafa zuwa jibi,akwai muhimmin abinda nakeson qarasawa kafin mu wuce din''
girgiza kanta tayi
''a'ah,gobe zamu tafi''cike da ladabi yace
''shikenan mami,amma sai la'asar ko''
''Allah ya kaimu la'asar din''
wani abu ya darsu cikin zuciyar maryam,duk da zuwan mamin ya mantar da ita kaso sittin cikin dari na damuwar data shiga duk da cewa abun na manne cikin zuciyarta,ta bisu da kallo lokacin da ya miqe yana cewa hisham yazo ya raka shi,wani dan banzan kishi ua lullubeta hakanan zuciyarta ke gaya mata gurin mero zashi


''sannu maryama''maganar mami ta dawo da hankalinta,murmushi maryam din tayi ta sunkuyar da kanta,kama duka hannayenta mami tayi
''na gode na gode na gode maryam,haqiqa bani da abinda zan iya biyanki da shi,halaccinki da alkhairinki mai tarin yawa ne a garemu,haske ce hakanan alkhairi ce ke a rayuwarmu ni da dana *ABADAN* ba zamu taba mantawa da ke ba maryamu,tabbas babu wadda ta cancanci abdallah sai ke maryam,'yar halak ce kw gaba da baya,kin riqe amana da alqawarin da kika yimin tun washegarin ranar da aka kawowa abdallah ke,baka taba sanin masoyinka na asali sai wani abu ya sameka maras dadi a rayuwa,maryam ina sonki kamar yadda nake son abdallah,hakanan ina sake baki amanar abdallah,ki kasance a gefansa *ABADAN* duka tsawon rayuwarsa,na tabbatar cewa matuqar kina tare da shi koda bani duniya bazai shiga mawuyacin hali ba,don Allah maryam kici gaba da riqe abdallah kamar yadda kika yi a yanzun''


Gaba daya maryam taji mami ta rikito mata wani qaton nauyi ta dora mata ne,kamar ta daureta ne da jijiyoyin jikinta,girman mamin na da yawa a idanunta,tana daukarta ne kamar mamanta data haifeta,ta rasa mai zata ce da mamin


_kuyi haquri da wannan_



*mrs muhammad ce*πŸ‘‘


πŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘
*_home of expert and perfect writers_*

β–Ά5⃣6⃣


*_Daga abdullahi dan umar Allah ya yarda da shi yace:Manzan Allah S A W yace''mutum bazai gushe ba yana tambayar muta ne(roqo) had sai yazo ranar qiyama fuskarsa babu tsoka daya ta nama(qwarangwal)'',ruwayar bukhari da muslim ce_*




*FANS NA ABDLLAH DA MARYAM,YA BANI SAQO YACE NA GAYA MUKU BA'A SHIGA TSAKANIN MIJI DA MATA FA😎😎,TSAKANIN MIJI DA MATA SAI ALLAH,WANDA YA SHIGAVTSAKANIN MIJI DA MATA QARSHE SHI ZAIJI..........πŸ™ˆ*πŸ˜ŽπŸ˜‚





Itama kama hannun mamin tayi
''insha Allahu mami muna tare,babu abinda zai raba mu da ke tare zamu rayu''
giriza kanta tayi
''ko ba dade ko ba jima dole wataran na tafi na barku maryam,baya ga haka ma duk musulmi na qwarai ana son ya dinga tunawa da mutuwa ko da yaushe,haka annabi muhammad S A W ya horemu yace mu yawaita tuna mai yanke jin dadi''


''haka ne mami amma don Allah kiyi shiru,kina tare da mu insha Allahu''
mirmushi kawai mamin ta sake yi

πŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒ


Kayan sawarsu kadai suka diba amma komai sun barwa inna wuro
''bawan Allah ku cire wannan abar taku mai karbar hasken rana ku tafi da ita''daroya ta basu abdallah yace
''a'a inna,ku barta ai kuma zata muku amfani,kudin shekara guda aka sanya mata kinga idan aka cire ai anyi asarar kudin ciki,tunda mu muna da inverter acan''bata fuskanci me yqce ba dai amma ta masa godiya
''mune da godiya inna,karamcin da kika mana bazai fadu ba''



Kudi mamin ta ajjiyewa tsoho alhajin amma qeme me yaqi karba,yace shi abdallah jika ko da ya daukeshi,ba don a biya shi ya masa aiki ba,ko a hanya ya ganshi yana da buqata irin wannan shi mai taimaka masa ne
mamin tace itama ba biyansa tayi ba Allah ne kadai zai iya biyansa amma sam tsoho alhaji yaqi karba bisa dole ta haqura,itama inna wuron qin amsa tayi,sai dabara mami tayi ta cusa mata qasan tabarmarta yadda bazata gani ba har sai sun tafi


Dukkaninsu suka rakosu har bakin mota cike da kewa,maryam kam harda qwallanta don tasan zatayi kewar qauyan ba kadan ba
''ka shiga motar hisham kai da hisham din idan yaso ma taho a tawa ni da maryam''
cikin shagwaba irin wadda ya sabawa mamin yace
''gaskiya mami qafata qafarki,a zamu raba mota ba''qememe yaqi yarda kuma ya kasa ya tsare maryam ba zata shiga kowacce mota ba


Dole hisham ya shige motarsa shi daya,maryam da abdallah na gaban motar mamin ita kuma mami na baya,gaba daya ta hade gabas da yamma na fuskarta don mami ce tace dole ita zata shiga gaban,shi kam dadi ya kamashi ya dinga satar kallonta yana son ta kalleshi ya tsokaneta,kamar kuwa tasan da hakan taqi uarda ta dubeshin


Yana shirin tashin motar mero ta leqo daga soron gidansu da alamu tana labe ne tun dazun a nan,idanh shabe shabe da hawaye,sai abdallahn ya kashe motar ya bude murfin ya fice yana fadin
''ina zuwa''
maryam na kallonshi ya qarasa inda meron take,sai ta rufe fuskarta da mayafi ta hau kuka sosai,tana iya hango yadda bakinsa ke motsi da alamu wani abun yake gaya mata,daga qarshe dariya ta saka,yasa hannunshi cikinaljihu ya fiddo da dubu biyar cikin kudin da jiua hisham ya rakashi cikin gaya ya ciro a ATM machine


Sai sata shige gidansu sunan ya juyo ya dawo cikin motar,yana shirin daura belt mami da hankalinta ke kan wayarta tace
''ita kuma waccan yarinyar fa wace?''
murmushi yq dan saki kana yace yana kunna motar
''zan miki bayani idan mukaje gida''
bata amsa masa ba ya tashi motar bayan yayi addu'a ta matafiyi ya soma tafiya


La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu kinaz zalimin ta dinga maimaitawa cikin zuciyarta sakamkon wani irin daci da take ji,yana tuqin shima yana satar kallonta,so yake ta kalleshin kuma taqi kallonsa,ya juya ya dubi seat din baya mami ta kashingide abinta tana gyangyadi,ai dole kam sam tunda tazo garin bata yi wani barcin kirki ba tana ta 'ya'yanta


Ya cire hannunshi guda daya daga kan sitiyarin ya saka cikin tafin hannunta
''baby,me ya faru?,naga kamar baki farinciki da dawowarmu gida''
zame hannun nata tayi cikin hade rai
''ka kula fa malam da kyau,tuqi kake,kada kaje ka zubar da mu''murmushi ya kuma yi yana qoqarin sake lalubar hannunta
''mutane biyu wadamda duk duniya babu wanda ke muhimmanci a gurina sama da su fa nake tuqawa,kinga ya zamarmin dole na kula iya kulawa''


bai qyaleta ba sai da ya kuma kamo hannun nata yana murzawa a hankali kuma atausashe yana lumshe ido,ta sake zamewa wannan karon tana fadin
''ada ka jimin ciwo bana bayan kai ka adana taka amaryar''
ba don ya daure ba saura kadan ya sheqe da dariya,ya sami sarai abinda ke cin zuciyarta kenan
''anzo gurin kadan kika gani yarinya,nayi alqawari kuma sai ya cika,da bakinki zaki furtawa abdallah

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login