Showing 51001 words to 54000 words out of 162126 words

Chapter 18 - ABADAN

ikwaninallazina sabaquna bil eman wala taj'al fi qulubina gillal lil lazina amanu rabbana innaka ra'ufur rahim_*πŸ™πŸ½





Sau biyi tana zuwa dubawa taga ko ya kammala sai tazo ta tarar bai gama ba,sai a zuwa na ukun ya sameshi ya ture kwanonin gefe alamun ya kammala kenan,bata ce da shi komai ba ta soma hada plates din guri guda tq zuba cikin kwandon
''ji mana''taji yace da ita,a hankali ta dago kai suka jada ido,ya kafeta da zaratan idanunshi sai ta kau da kanta gefe
''idan kin koma kuma ki sake hada ni da mami na kice ni naci abincin,ko da yake ko kin fada din dama ai aikina aka dauko ki yi ba wai ki dafawa wani qato ba,a qa'ida ma idan kika kuma gigin yiwa wani girki ba da izini na ba ma a albashinki''


ya ture kujerar da yake kai baya ya miqe ya kewayeta ya wuce,ta biahi da kallo tsanarsa da tsanar halyenhi na takura matsi da girman kai na addabar zuciyarta,sai da ta tabbatar ya ahige bangarenshi sannan ta shiga nasu bangaren

πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²

da yake azumi ne qarfe tara ta shirya taje gida,ita da hindatu suka tattauna abinda za'a shirya don 'yan kawo kudi da zasu zo jibi da safe,ruwan roba ta siya carton biyar na lemo ma haka,sai maltina itama carton uku,kujerun da aka fidda dakin mama su aka maida sitroom dinsu wanda rashin wadata yasa yake fanko babu komai a ciki,babu abinda kujerun sukayi tunda ba'a dade da yi musu kwaskwarima ba ta qarin katifa da canza yadin kujerar kuma ba yara gareta ba balke su lala ce da wuri,ko dama can ita mamsn mai tsumi tattaku da tanadi ce,ta siyi leda da labulaye duka aka sanya,sai sitroom din yayi kyau daidai talaka,tuni dama kayan gadon maman aka shiryashi bedroom din baban sun zama nashi


muqullin ta danqa hannun hindatu don tana jin su kula na rawar kan yau a ciki zasuyi zance don duka babu wanda yasan me za'ayi da dakin aka gyara shi haka,wannan rufewa fa da tayi sai taso zama dan zani sukayi dafifi a tsakar gidan suna basu amince ba ai gida dai na ubansu ne babu wanda ya isa ya musu shamakivda wani bangare na gidan,shigowar baban ya tambayi ba'asi wannan karon hindatu ce tayi uwa tayi makarbiya ta masa bayani


to shi din ma wannan karon bai basu goyon baya ba yadda suka saba samu,hakab ba qaramin qullacinsu maryam ya sake sa musu ba,da azahar sukayi sallama don tana so ta leqa raliya,mama ta dakatar da ita tana fiddo da dararen borikan fenti uku daga uwar dakanta
''me wannan a ciki mama?''ta fada tana budewa
botikin farko alkaki ne a ciki
na biyu dubulan
na uku nakiya ce


ta dago ta dubi maman
''duka na meye wannan?''
''saboda 'yan kawo kudin nsn nasa akayi,kinga za'a kuma fita kunya ko''qauna da tausayin mamanta ya sake shigarta,Allah sarki mama,farincikin dake zuciyarta Allah kadai ne ya sani,a haka ma tana alkunya tana danne farincikin nata sabida kara irin ta dan fari


''Allah ya saka da alkhairi mama sunyi,Allah ta qara arziqi,amma mama banason ki dinga tatse kudin hannunki haka,yanzu wannan kayan ai sunci kudi da yawa''
''ai aikina ne maryamu,idan da da akwai cikakkiyar wadata ma baki cancanci ki kiyi komai ba''

πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚

qarfe biyu da rqbi suna falon raliyan su biyu sai fadil dake kwance kujerar geansu yana baccinshi hankali kwance,cikin farinciki raliyan take tamkar ma itace maryam din
''wani hanin ga Allah baiwa ne maryam,yau gashi Allah ya musanya miki da jabir,sun sanya bawan Allah a tsaka mai wuya har yau yana cikin damuwa,shekaran jiya yazo gidan nan yake tambayar abban fadil ke,yana son ya nemeki amma wai kunyarki yake ji,shegiyar yarinya marasa tsoron Allah itavda uwarta,duk jabir ya fita hayyacinshi kmar bashi ba,roqon Allah ne masa ya dawo cikin tuna ninshi cikin lokaci qanqani haka''


ajiyar zuciya ta saki
''duk wanda ya debo da zafi ai bakinsa raliya,nikam wanna ya riga ya wuce tamkar wani mafarki na daukeshi''
ta zura hannunta cikin jaka ta soma laluben wayarta dake ringing hade vibration ta cirota,kiran abdur rahim ne tasan shi dinne tun kafin ta ciro saboda special tune da ta sa masa
''ranki ya dade duka yau ban jiki ba ko cigiya ta baki yi anya kuwa''ya fada cikin salin zolaya bayan sun gama gaisawa
murmushi ta saki
''yau na tashi ne cikin sabgogi amin afuwa''
''ayyah,da kinyi magana ai da nazo na tayaki,ina fata basu wahalmin da ke ba''
''alhmdlh tunda tuni na kammala yanzun nake shirin in koma gida''
sai ya danyi duf kana yace
''me yasa baki tambayeni ba da zaki fita,saiki dinga fita kanki tsaye maryam ana ganemin ke''
murmushi ta saki
''mantuwa nayi ashe fa yanzun ina da miji,baza'a sake ba''



''matsalar ban iya fushi dake maryam,yanzun dai sgikenan kimin kwatancen gidan da kike zanzo yanzun nan na maidake gida,naga hadari na haduwa kada ruwa ya dakarmin ke ya barni da zazzabi''
ba qaramin nishadi maganar ta saka ta ba ,take ta masa kwatancen inda take din sukayi sallama ta ajjiye wayar
suka hada ido da raliya tare suka saki murmushi
''gaskiya na fuskanci ba qaramin ji dake abdul din nan yake yi ba,Allah ka nuna mana wannan rana''
dariya tayi gami da dukan gefan cinyar raliyan tace
''har ya kama qafar nasir abban fadil''suka sake sa wata dariyar raliyan na fadin haba wane mutum


minti goma wayar ta sake kadawa,abdur rahim tayi tsammani shi dinne kuwa
''kiyi min afuwa maryam zuwa na bazai samu ba wani aiki ne na gaggawa yanzu aka turamu dole kuma na kasance aciki idan ba haka ba akwai matsala,amma kiyi sauri don Allah ki koma gida hadari ne sosai a garin kada ruwa ya tabaki''
macace mai sauqin kai da fahimta don haka tace masa
''babu damuwa Allah ya bada sa'a''
ya saki ajiyar zuciya
''na gode da kika fahimceni sai munyi waya''


ta dubi raliya bayan ta miqe tana hada jakarta,ta tavbata hadarin ne don tuni garin ya lumshe har ta soma jin quginsa
''wucewa zanyi raliya an samu matsala abdul bazai samu zuwa ba aikin gaggawa nebya taso muau yanzu a office''
''a'ah,yanzu da uban hadarin nan zaki tafi?ki jira abban fadil ya dawo sai ya kaiki''kama baki tayi bayan ta gama rolling mayafinta
''girkin kuma na barwa wa?,so kike kenan yau abdallah ya samu nayi ko,cikin watan nan ya tairi wani abu ko kunu ne idan bani nayiba sai ya gane,yanzun sai yace a salary dina''
ta dage girarta sama
''haka ne fa,muje in taka miki,amma jirani in shiga in fito''cewar raliyan tana shigewa bedroom dinta na qasa


kwalbar turare ta fito da shi hade da baqar leda qarama ta miqa mata
''turaren da kike ce min kina son irinsa nasa abbn fadil ya aiyo manaamma kiriqe da kyau saboda yana leeking,sai bra din nan qualitative one da mukayi maganarta jiua da muka fita na siyo mana''
''kai qawata,bani da bakin magana,Allah ya raya mana fadil ya bar mana zumuncinmu,ya tsone idon maqiya''
''ameen raliyan ta fada tana bin bayanta,haduwar jadarin ya sake rudata har ta kasa saka kayan cikin jaka,a bakin get suka rabu ta soma sauri gashi ita ba gwanar saurin bace


har ta kai bakin titin su raliyan bata ga abun hawa na haya ba,kusan dama haka yanayin unguwar tasu yake ko jama'a baka fiya gani ba,bare yanzu yanayi na azumi kowa yayi likimo cikin gida,hankalinta bai daga ba sai data tsaya atitin,taga motoci dake karakaina ma baifi ka irga au ba,adaidaita uku ne suka wuce biyu daga cikinsu duk cike take da mata dayarkuma maza ne cike har gaba kusa da mai tuqin,a hankali iska ta soma kadawa mai qura alamun dake nuna hadarin ya gama nuna a sama sauka kawai yake da buqatar yi,addu'a kawai takeyi cikin zuciyarta a haka ruwan saman ya soma sauka


tsamo tsamo tayi don ya fara jiqata ta soma hade jikinta guri daya,motoci uku ne qirar land cruisser baqaqe wul hatta da glass dinsu suka tsaya a gabanta,gabanta yayi mummunan faduwa,tuni ta somacwaige waigen neman inda zata fake idan gudun ceton rai ya kama


glasan motar farko nagaba mazaunin mai tuqi suka sauka qasa,hassan ta gani daya daga cikin direbobin abdallah,sai a likacin taji ta samu nutsuwa,murmush yayi nata itama ta maida masa
''madam yi sauri ki shigo kina ta jiqewa''
taji dadi sosai kuwa,da saurinta ta qaraso ta bude mazaunin gaba ta shiga tana fadin
''na gode qwarai,amma ba tare kuke da og.....''
''me muka tsaya yine hassan?''
muryar data fito daga sit din baya ta katsse mata sauran magan
''nun dauko madam ne''ya fadi yana qoqarin tayar da motar
''waya baka izini ko tsabar iya sayawa mutum raini ne?''
''sorry sir,naga gida zamu ne,kuma itama gidan zata.....''
''ni na gaya maka haka?''ya tambaya murya a kaurare


''am sorry sir naga madam nada kirk.......''
abdallah ya katseshi ta hanyar fadin
''mtswee,shutup malam sauka ka barmin mota ka koma motarsu auwal''
da saur maryam ta kuma riqe jakarta wadda garin saurin ledar hannun ta har ta subuce ta fadi qasan motar bata sani ba
''kayi haquri,ni ya kamata na fita ba hassan b.....''
''hey,bana son iyayi shi nace ya fita din bake ba''


tuni hassan ya bude motar ya fice ganin hakan ya sanya itama ude na bangarenta tana qoqarin fita
''idan kija sake kika fita sai na karya sillar qafar taki inga ta rashin kunya''
tilas tana ji tana gani ta koma ta zauna
''rufemin mota malama don idan ruwa ya jiqata sai kin busar da ita tas a yanzu yanzu''taja qofar garam ta rufe cikin haushi,tana iya gano ragowar motocin suka zagayesu suka wuce


mujallar da yake research kanta tun dazun ya sake janyowa ya bude yaci gabavda karuntunshi hankalinshi kwance tamkar yana cikin dakinshi ne,sanyin a c din motar ya soma takurata gashi tayi mata kusa da yawa,tuni kanta ya fara sarawa ta qudunduna gu guda tarw da jingina jikin makarin motar ta lumshe idanunta tana ci gaba da jin yadda ciwon kan ke dada yin gaba


'yar qaramar qara taji tamkar ta waya ''siiit''a hankali sai dumi ya maye gurbin sanyin ac din,bata tantama maidashi akayi banaren dake bada dumi,duk da taji dadin hakan amma babu abinda ya rage mata daga ciwon kanta


mintina kusan arba'in basu tafi ba kamar yadda ruwan bai tsagaita ba,ta bude idanunta a hankali ta miqe ta zauna daidai,a karo na biyu ta kuma sanya hannunta kan mabudin qofar don ta qudiri aniyar ficewarta zatayi kome zaiyi mata saidai yayi,saidai taqi buduwa da alamu an saka lock,ya ajjiye mujallar hanun nashi ya jawo baqin space ya mannawa idanunshi sannan ya bude 'yar qaramar kyakkyawar baqar lemar dake kusa dasji ya fito ya dawo mazaunin driver


amadadin ysyi hanyar gida sai taga sun csnza titi,batason kulashi amma ya zama mata dole
''ina cewa gida zammu ko''
banza yayi da ita,ta qufula amma bata fasa sake fadin
''girki fa na can na jira na gashi yanzu hudu harda rabi''
''karki cika ni da hayaniya,baki da zance sai na girki kamar dinshi aka halicceki,ai bake daya kika iya girku cikin gian ba ko''
ya fada udanunshi na bisa kwalta,bata sake tofawa ba ta maida kanta gefe daya


cikin wata unguwar taga sun shiga wadda take kama da tasu mamun wajen kyau da tsari,qofar wani katafaren gida taga ya tsaya,ita kanta sai da ta bi gidan da kallo,duk kyau na gidansu mamin wanna ya dokeshi,bude motar yayi yay ficewarsa ba tare da da yace mata komai ba


zaman kusan awa guda da rabi tayi kafin ta sake ganin fitowarsa,a dan bakin qofar ya tsaya kafin ya qaraso tana iya hango jikin wanda suke magana tare,da alama macece don ga gefan mayafi nan,ba qaramar qufula tayi,ba cikin zuciyarta
''zance yazo kenan ya barni a mota ko yaya?''ranta sai ta kuma ji ya baci,ya bude motar ya shigo
''zance da ranar Allah cikin watan azimi,wanne wane irin tsari ne''ta ja tsaki,saidai cikin subutar baki tsakin ya fito


juyowa yayi kalleta
''wa kike ma tsaki?''sai ta juyo tana kallonshi itama
''idan kika sakemin tsaki sai kin fita min a mota tunda bada kudinki aka siya ba''sai idanunta suka wal
''daina kallona''ya fada bayan ya dauke kanshi da sauri daga cikin idanunta
''kada ki cuceni''ya fadi can qasa yana lumshe idanu tarw da yiwa motar key,bata kawo komai cikin ran ta ba ta dauke idonta cike da jin haushinsa

πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²πŸŽ„πŸŒ²

Ashirin ga azumi mami ta bata kayan sallarta,a dinke suke dinki ne na gayu wadanda suka mata cif a jiki,atamfofi uku lace daya material daya,sai codelace shima daya,duka atamfofin dogayeb riguna aka mata don mamin ta fuskanci tana sonsu,jaka biyu takalmi biyu sai mayafi biyu hijabi daya,sannan tace ashirin da biyar ga azumi zasu fita sai ta zabi fashion da zatayi amfani da su,bata fasa yiwa mami gidiya ba duk da ta gaya mata diyarta ta yiwa no need tace sai ta gode mata,godiya kuwa ai tamkat wajibi ne tayi mata don ko daga gurin mahaifinta bata taba samun makamancin irin wannan gatan ba


abida kam akwati guda medium abdallan ya hada mata bayan takurawar da mami tayi masa kan ya hada matan,don shi totally baiyi niyyar mata komai ba


cikin irin kyautar da mamin ke yawan yi mata ta fidda atamfa biyu ta baiwa tela ya dinkawa mamanta,ta siya mata mayafi takalmi da jaka,albashinta na watan ciki ta cira ta baiwa hibdatu tayi siyayyar salkarta babanra ma shadda ta siya masa kala biyu ta hada mishi da kudin dinki da takalmi da hula daidai,kai kada ksso kaga baqinciki,ina wuta a saka maman da iyalsnta,godiya kam gun baban ba'a magana
''sai yanzu nasan na haifa,yanzu ne na fara cin albarkar haihuwa''baban ya fada lokacin da yake gwada hular da ta kawo masan


''oho dai,wlh malsm ka guji ranar da zaka karbi shegen jika cikin gidan nan,ka gama cin dadin dai wuyar na tafe,shi yasa gata nan har yau babu mashinshini yo kowa yasan aikin tsiyar da take aikatawa''
inji baba hadizar don daga ita har huwailsn babu wanda yasan da zancan kawo kudinta,ranar kamar Allah ya kadasu duk suka fice unguwa suda qananun 'ya'yansu,huwaila tayi gurin boksn boginta ita da uwale hadiza ma ta bazama ga nata bokan,sunacan yawon asara har yan kawowar suka tafi,'yammatan da zawarawan kuma na nade a gado suna bacci don wadan nan sukan kai sha biyu da rabi zuwa daya basu tashi ba


huwaila kuwa cewa tayi''mu namu ai shegensu mukayi muka shigo dasu gidan ko,ko ince tsinannu ne''shidai babu wadda ya kula cikinsu ya kwashe kayanshi ya shige dakinsa

πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚πŸƒπŸ‚

Qarfe goma suka dawo daga siyan kayan kwalliya da suka fita harda mami da abida,tayi sallama da mamin ta shige dakinta don da wuri take son yin bacci ta tashi akan lokaci sallar dare saboda yau an kai azimi ashirin da shida zuwa anjima daren ashirin da bakwai zai shi daren da akesa ran dacewa acikinsa


zuwa sha daya na dare takammala komai ta haye gado bayan ta gama addu'o'in kwanciya ta karanta saqon abdur rahim fuskarta fal da murmushi,kusan cikin watn gaba daya wayarsu bata fi aqirga ba sai tex akai akai,yace shikam bazai iya jurar jin muryarta ba,tana shirin kashe wayar kira ya shigo,ta zubawa lambobin ido tana kallonsu,tana tunanin inda ta taba saninsu


tabbas ta taba sanin numbers din,har wayar ta tsinke ta kasa dagawa,second biyar tsakani wani kiran ya kuma shigowa,jiki babu qwari ta sanya hannunta ta daga ta kara akunnenta
''assalamu alaikum wa rahmatullah''itace abinda yavdaki sodon kunnenta,mummunar faduwa gabanta yayi,babu inda zata ji muryar ta kasa ganeta,amma tan tama take kiran nata ne ko batan kaine,ta sake cire wayar akunnen ta tayi ta kuma duba screen din wayar mai kiran dai na bisa layi kuma ita din aka kirar




*mrs muhammad ce*πŸ‘‘


πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½
[9/17, 12:54 PM] 80k: πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–
πŸ’–

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊπŸ’–
πŸŒΊπŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–πŸŒΊ
πŸ’–
Β© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*πŸ’‘
*_home of expert and perfect writers_*

β–Ά3⃣4⃣

*_daga abu hurairah Allah ya qara yarda da shi yace:an tambayi manzan Allah s a w wanne musulmi ne yafi falala?,sai yace:wanda musulmi suka kubuta daga sharrin harshensa da sharrin hannunshi(ma'ana bai cutar da kowa da harshensa ta hanyar magana,ko kuma da hannunshi ta hanyar ayyukansa,daure ka/ki zama daga cikin musulmin da suka fi falala,abun ba wuya πŸ‘ŒπŸ½matuqar ka jajirce kafi qarfin zuciyarka,Allah ta bamu iko ameen)_*

''wa alaikumus salam''ta fada asanyaye
shiru ya dan ratsa tsakani kadan
''da alamu baki ji dadin jina da kika yi ba ko maryamu?,hala ma kin manta da ni?''
''ko daya,ban kuma mance da kai ba''
''da fari kafin nace momai maryam,nasan bani da kalmomin da zasu gamsar da ke gurin ban haquri,amma duk da haka ina roqarki don Allah don annabi ki yafemin,ba da gangan abinda ya faru tsakaninmu ya faru ba,bada sani na bane maryam,ki yafewa jabir masoyinki''

tausayinshi ya kamata ta dan kumshe idonta kadan ta bude
''kada ka bata bakinka gurin bani haquri jabir,tuntuni gaskiya ta dade da yin halinta,anyi walqiya komai ya bayyana''
yaja dogin numfashi kana ya sauke ajiyar zuciya
''alhamdulillahi rabbil aalamin,dukkan godiya ta tabbata ga Allah,babu shakka ke din jaruma kuma nagartacciyar masoyiya ce,bana tantama zaki zama mace ta gari uwa ta gari gurin 'ya'yanta,bazanyi nauyin baki ba ba kuma zanyi qauro ba maryam inason ki bani damar fitowa neman aurenki karo na biyu,tare da cikakken fatsn babu wani da ya sha gabana''

sai da gabanta ya fadi,tayi shiru tana son daidaita bugun zuciyarta sannan daga bisani tace
''qaddara ta riga fata jabir,Allah ya qaddara run da dama ni ba matarka bace,hakaza matar mutum kabarinsa,bai wuce sati biyu da kawo kudin aure na da wani ba''
''la haula wala quwwata illah billah''ita ya dinga maimaitawa tsawon mintina biyar
''yanzu kina nufi maryam na rasa ki kenan,zaki auri wani na?,ki bani dama maryam mai rabo shi zaya samu tunda har yanzu ba'a daura aurenku ba balle kice kin haramta a waje na''

''kai mai sani ne jabir bakin gwargwado,ka sani cewa nema akan nema haramunne,baya ga haka ma daga ni har kai babu wanda aka bawa qudirar rubuta kundin qaddararsa da kansa,kuma buwayin sarkin dake rubuta msna din mai dumbin adalci ne,babu yadda za'ayi ya rubuta mana abinda zai zama zalunci ne a garemu''
''haka ne maryam,alhndlh Ala kulli hal,na gode maryam,na gode matuqa da gaske,bazan taba iya mantawa dake cikin kundin rayuwata ba,na barki lafiya''

tafi minti biyar riqe da wayar ra kasa ajjiyeta,tausayin jabir dinne kadai ke dawainiya da ita,babu shakka bazata iya manta dumbin alkhairansa gareta ba,koda ta tashi sallar dare bata mantashi cikin

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login