Showing 123001 words to 126000 words out of 209775 words

Chapter 42 - DUNIYATA BOOK 1 By HUGUMA

Gaisuwar ban girma yayi mata kaman yadda suka saba sannan suka shiga tattaunawa kai tsaye akan ayyukan da takeso ta gama dasu

"Ka sani,ba kasafai nakeson dadewa da mutum ba.....nafison nayi na gama a wuce gurin ya sake sabon lale.....ciwon aishatu shine abinda yafi dagamin hankali najeeb......banason sanadiyyar wani ayshatu ta rasa ranta......inason sama mata lafiya tare da mata tanadin rayuwa da zata manta abinda ake kira da tsanani talauci ko wahala". Can qasan ransa yake hadiye wani abu,yana cika da mamakinta ako yaushe,tana yawan sanya ranta da kanta a risk,bawai don saboda jin dadinta ko walwalarta ba......aah......tana yin komai ne kawai don jin dadin wasu.

"Zamu kammala da izinin Allah......amma a wannan karon indai komai yayi kyau,adadin kudaden an samesu daidai ya kamata kema ki inganta rayuwarki sama da yadda kike a yanzu". Dan qaramin murmushi ne ya subuce mata,har jib yana iya jiyo sautinsa kadan

"JIB.....kune a gabana......har yanzu inajin mutanen dake tare dani ban kaisu matakin daya dace sukai ba". Zuciyarsa ce ta karye girmanta na dada qaruwa a ranshi

"Ko yanzun ma me ya rage?,kinyi mana komai,tunda muna iya tsaiwa da qafafunmu......mu ya kamata mu tallafeki kikai inda ya dace kikai din.....kusan dukkanmy burinmu ki samu nagartaccen miji......"

"Mubar wannan maganar jib yanzu" Ta katse numfashinsa. Murmushi kadan ya saki,shima kansa yasan ya taba inda batason aje. Sau tari yakanyi mata uzuri......koda shine yaga abinda ta gani,yaji kuma abinda taji ba shakka iya hukuncin da zaima rayuwarsa shine nisantar kowacce diya mace,saidai kallo daga nesa,indai ba qaddara me qarfi da zata hada tarayyarsu guri guda ba.

"Zakibi mashkur abuja bayan mun gama da mika'il" Ya furta a nutse bayan shurun daya gifta a tsakani na wasu 'yan mintuna

".....banason tafiyar nan jib"

"Itace hanya guda daya mafi sauqi da zamu kammala komai hankalinmu kwance......na sani baki taba bin kowa ko ina ba......amma a yanzun zakije,na miki alqawarin ba abinda zai faru,zan baki kariya da support harki dawo,zan bi bayanku idan ta kama......kwana daya tal zaki bani zan kammala aikinsa.....mashkur din nada tsananin wayo fiye da yadda kike tunani......amma kuma kinsan kutsa kai asusun mika'il yafi na mashkur hadari da kuma tsauraran matakai da sai an masa shiri na gasken gaske?" Shuru tayi tana son fasa maganganunsa daya bata su a cure. Kanta har ya soma dan hargitsewa,sai ta gyara zamanta kadan tana cewa

"Ka rudar dani jib......mashkur nada wayon da lallai sai an bishi qafa da qafa kafin cimma nasara......mika'il sassauqan wayo ne dashi......amma nasu account din yana tattare da tsaro sosai haka ne?"

"Exactly boss lady" Ya fada yanason jefa raha cikin zancan. Ya jefawa fuskarta murmushi kadan kuwa,sai taja dan qaramin tsaki

"A ajjiye wasa jib.....na soma gajiyawa da wadannan hadarurukan......inason muyi babban aikin da zan huta nima hakanan na kula da rayukan dake gabana da kyau"

"Haka nakeso miki nima......bari na qara miki wani bayani kadan......mika'il yana riqe da ragamar babban account din dake mallakin wani kamfanin sarrafa diamond......kamfani ne ne matuqar qarfin jari da huldodin kasuwanci da qasashe daban daban.......kusan rabin kudin wannan kamfanin asusunsa mika'il yana da access dashi.....hakanan duk wani kudi da zai shiga ko ya fita yana da access da hakan.....a bincikena na lura yana wadaqa da kudin yadda yakeso,saidai kuma yana bi ta hanyar lura da saka tsantseni ta yadda ba lallai a gane hakan ba,saboda mahaukaciyar riba da matsiyatan manya manyan kudaden da kamfanin ke samu a kowacce rana....."

"Matsiyata.....manya manya?" Ta jefawa jib tambayar. Qaramar dariya ya saki

"Sorry......maqudan kudade"

"Okay......naji kana amfani da wasu kalmomi ne.....eheeen......kaga kenan komai zaizo mana akan daidai?"

"Haka nake tunani......amma ki bani kwana uku,zan duba yadda zamu kutsa cikin asusun.....amma shima dole ku hadu a ranar Koda na awa daya zuwa mintuna talatinne......ki sassauta riqon tsaurinki kiyi kaman kin sakar masa komai....."

"Mtseewww....ya isa don Allah" Ta dakatar dashi,don zuwa yanzun abubuwan sun fara barin kanta,tana ji kawai lokaci ya tunkarota da zata maida kai sosai ga 'yan uwanta. Dukkansu girma suke qara yi,kuma suna da buqatar attention dinta sosai fiye da wanda take basu a baya.

Jib na 'yar dariya yace mata

"Shikenan......cikin kwanaki ukun zaki iya jina koda wanne lokaci,kibar wayar a bude,ki kuma fara shirin zuwa abujan.....nima zanyi nawa shirin"

*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 62

"Yayi" Ta amsa masa a taqaice tana katse kiran.

Shuru kawai tayi tana jin yadda iska ke kai kawo a farfajiyar wajen. Yadda iskar ke kadawa sai take jin kamar kwatankwacin yadda tata rayuwar ke garawa kenan,daga hagu zuwa dama,daga dai dai zuwa rashin daidai,amma a yanzun cikin ranta takejin lokaci yayi da zata tsaida komai.....ko a iya haka ta tabbatar tayi qwarin da rayuwarsu ba zata tagayyara ba.

Tunda ta tabbatar ta fita zuwa farfajiyar gidan ta rufe qur'aninta,ta kuma miqe da hanzari ta wuce zuwa cikin dakinsu.

Cikin mintuna qalilan ya cire dari darin da take na amsa wayarsa da takeyi cikin dakin. Tun tana a tsaye tana kai kawo da kuma leqe tsakanin labulayen dakin har ta koma ta zauna sosai a gefen gadon tana sauraren kalamansa dake da wani irin dadi suke kuma sake samun matsugunni me kyau a zuciyarta.

Yadda dukka kalamansa suke a tsaftace,ba wani kalma ko furuci maras kyau ya sanya take sake jinsa sosai cikin ranta,wani bangaren na zuciyarta kuma yana yabawa kamalarsa da kamewarsa.

Ba wani abu me muhimmanci da zaman zaiyi mata,don haka ta yanke duka tunanin tana miqewa daga inda take din tana nufar cikin gida don komawa dakinsu.

Tun daga nesa kadan dab da qofar da zata sadaka da ainihin tsakar gidansu ta hangi hadiyyan. Ta ganta sarai zance takeyi,wanda dama takanyi din lokaci bayan lokaci.

So samu tabi ta wata hanyar da bazata hada numfashi da ita ba,to amma kuma babu hanyar,saidai tabi zabi guda daya daya rage mata,ta koma ta zauna ta jirata har ta gama zancan tabar wajen. Wannan abunne kuma takejin ba zata iya ba,duk abinda ta niyyaci ko nufaci yi ba kasafai take bari dalilin wani ko wata ya sanyata ta juya da baya ba.

Tunda ta doso gurin ta fuskanci hankalinsa ya dauku a kanta. Ba baqon abu bane a wajenta saurin gane motsi ko manufar d'a namiji a kanta daga kallo daya tak. Dauke hankalinta da idanunta tayi daga wajen kamar bata san da zamansu ba tana wucewa ciki.

"Wannan 'yar gidanku ce itama kenan?" Ya maida hankalinsa ga hadiyya yana tambayarta wadda tuntuni idanunta suna a kanshi,cikin wani irin banzan kallo da bacin ran yadda yake kallon sabreen din

"Eh 'yar nan dince.....sai akayi yaya kuma?" Ta bashi amsa a matuqar fusace har sabreen dake gab da wucewa tana ita jiyota.

Kanta ta girgiza kawai tana sakin siririn murmushin nan nata maras sauti me dauke da tarin ma'anoni masu yawa. Itakam daga hadiyya har dukkan wani gajan baqo da zayazo wajenta bata tunanin akwai wanda ya isheta kallo a cikinsu.

"Ina kuma hudan?" Sabreen ta tambaya tana kallon sararin da tabar hudan a zaune kafin fitarta

"Ta shiga daki" Haneefa ta bata amsa. Labulen daya sakaya qofar shiga dakin tabi da kallo

"Daki kuma?,me takeyi a ciki?"

"Ban sani ba wallahi.....naga dai ta shige" Nadra da aka miqawa tambayar ta amsawa sabreen cikin rashin taqamaimen amsa

"Tun yaushe ta shiga din?" Ta sake tambayar nadra wannan karon qasa qasa.

"Baki jima da fita ba" Ta bata amsa itama da yanayin yadda tayi mata tambayar. Bata son saka ko darsa wani abu a ransu,don haka tadan sake rantabrana kallon nadra

"Rufe littafin data bari a bude din" Batayi gaggawar shiga dakin ba don kada ta barwa zuciyar yaran wani hasashe,saita koma ta bude fridge ta dauko ruwa,ta qarasa gaban first aid box dinsu dake ajiye cikin falon t dauki paracetamol ta taka zuwa dakin.

Daidai sanda ta shaqi wani sassanyan numfashi daya cika fal da farinciki da kuma shauqin soyyayya,daidai lokacin ta daga labulen dakin tana takowa zuwa ciki.

Mutuwar kwance tayi sanda idanunta suka ga shigowarta,sai ta kasa ci gaba da maganar da taso ci gaba da yi. Tana iya jinsa yana cewa

"Hellooo.....my love.....hello" Amma ta kasa kowanne motsi. Duk sautin maganarsa qwaya daya ji takeyi kamar zata saki fitsari,don tana ganin yadda sabreen din ke matsowa tsaf zata iya jin sautinsa.

"Me kikeyi a kwance bayan sallar magariba?.....kuma na barku ne kuna karatu?" Ta mata tambayar tana kafeta da idanu,gami da zama saman drawer dake tsakanin gadajen nasu. Shuru yayi daga inda yake zaune yana bin sakannin da suka kwashe da ita akan waya suna qara gudu,yana kuma sauraren sautin muryar sabreen dake ratsowa ta cikin wayar zuwa kunnuwansa tare da sake tuna masa abubuwa masu yawa da suka shude tsakaninshi da ita.

Numfashi taja ta sauke,lokaci daya yadda zata sauya daga ainihin yanayinta yazo mata,saita bata fuska

"Banajin dadi ne". Inda hankalinta cikin jikinta yake a lokacin ba shakka babu abinda zai hanata jiyo sautin fitar murmushinsa.

Ko iya hakan yana gwada masa samuwar matakin nasara daga gareshi. Ta yadda ya bibiyi diddigin rayuwarsu.....a yadda bincike ya fito masa.....basa iya boye mata komai.....komai girman laifinsu ko gaskiyarsu.....komai tsanani ko maslaharsu.....ba wani abu da suke iya lullube mata shi,yau gashi ya fara taka matakin nasara......ta koya qarya saboda shi.

"Me yake damunki haka nan da nan?" Cikin qwarewa wajen iya bankado abinda ke lullube ta tambayeta. Tambayar data sanyashi jingina bayansa da kujera yana jiran jin amsa ta biyu

"Kaina ne yake ciwo" Sai ya tsinci muryar sabreen din tana bada amsar da hudan ce ya kamata aji haka daga bakinta.

Yadda ta bada amsar ya sanya huda daukewar numfashi daga jikinta na wucin gadi,tare da sanya Naseer tattara hankalinsa akan wayar,kadan kadan fargabar kada ya zamana ta gano meke lullube tana son saukar masa.

"Ga magani tashi kisha" Ta sake cewa da huda tana miqa mata kofin ruwan dake hannunta tare da satches na maganin.

Ruwan da maganin duka tabi da kallo,ta fara motsawa kadan sannan ta miqe da sauri ta zauna tana sakin wayar. Santsin pillow din ya sanya ta zame ta kuma sulale ta sauka a gefen cinyarta saita matsa kadan tana qarasa danneta.

Ci gaba tayi da dubanta har zuwa sanda ta balla maganin tasha,sai ta miqa hannu ta karbi rayuwar ruwan da maganin itama ta balla ta sanya a bakinta tabi da ruwa

"Ba abu mafi sauqin fade irin ciwon kai.....amma ki sani,yawan kiran sunansa yana iya jawoshi koda babu shi a wajen" Ta fadi tana qarasa sauke idonta a kanta.

Tsoro da fargaba ya sake cikata,saita lumshe idonta tana son dasa gaskiyarta a zuciyarta

"Nima zamana kenan na jishi ya saukar min,na dauka nadan lokaci ne xai sauka idan na kwanta"

"Allah ya sawwaqe" Ta fada a taqaice tana takawa a hankali hadi da ficewa daga dakin.

Wata ajiyar zuciya ta sauke tana fidda idanunta waje,tana iya jin yadda bugun zuciyarta ke kai kawo wanda ta tabbata tsoro razani da kuma firgici ne ya haifar mata dasu.

*****Tsakanin asabar da kuma lahadin yana da isashe lokacin da zaiyi shirin komawa bakin ayyukansa zuwa litinin,wannan ya sanyashi maido da dukan ayyukansa da suka tsaya sakamakon tafiyar da yayi.

Shi kansa yasan satin da zasu shiga din ba satin zama bane,babu hutu sam a tattare dashi. Aikine me yawan gaske,don bayajin zai zauna ya huta har sai yakai ga gacin kammala komai ya kuma bude kamfanin da a yanzu shine cikar burinsa.

*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 63

Sassanyan yammaci ne dake bada wata irin iska me dadin shaqa da samar da nutsuwa ga zukata,hakan ya sanya zaman wajen yayi masa dadi ,wanda tun bayan sallar azahar ya zauna a nan din. Yau din zama sukayi sosai da mu'allim,wanda shi yake kula da bangaren masu buqata ta musamman da kuma neman taimako. Ya karba list na mutane masu yawa,ciki harda list din anni dana maamah wanda ya jima yana kallonshi.

Sunaye na mutane barkatai,wanda yafi kyautata zaton an shirya sunan ne kawai an kuma shigar. Ya karba takardar da zummar zai duba din,don hatta da numbers na wayoyinsu dake a jiki kallo daya yayi musu yaji sunfi masa kama da lambobin bogi.

A yanzun ya gama shigar da komai cikin laptop dinsa da kusan zaiyi wahala ka ganshi ba ita. Tana dauke da muhimman bayanansa da kuma sirrika sosai a ciki.

A yanzu da yake zaune yana karbar kira ta kai tsaye ta cikin system dinsa. Video call ne da daya daga cikin kamfanin narka gold da wankeshi daga qasar china,farouq ya tako yana isowa farfajiyar.

Kujera yaja ya zauna,sannan ya fidda wayarsa yana duba saqonnin WhatsApp da tun daxun ya sauka da zummar zai koma din. Hira sosai suka shiga yi da fannah,don kusan duka saboda ita din ya hau. Jifa jifa yana mata gajeran voice note don kada ya janye hankalin fu'ad da baqonshi.

A nutse ya kammala amsa kiran,yayi disconnecting sannan ya maida dubansa ga farouq. Idanu yadan zuba masa,yana mamakin yadda yakejin dadin soyayya gaba daya,wai shin mene a cikinta har haka da take iya maida mutum wawa ne?.

"Ya dai?" Yaji muryar farouq din yana katse masa tunaninsa

"Am just wondering...."

"For what?" Farouq ya katse masa magana yana maida masa tambaya murmushi dan kadan yana fita a fuskarsa

"Yadda mutum me hankali yake komawa kaman soko.......wannan abar farouq It doesn't make sense wallahi" Ya fadi iya gaskiyarshi,gaskiyar da har saman fuskarsa zaka hangeta kwance quru quru.

Dariya ce sosai ta qwacewa farouq har yana duqawa,abinda ya sanya fu'ad tsaiwa ya zuba masa ido yana kallonsa.

"To abun kuma ya fara cin qarfina,to be sincere ka fara bani tsoro sama dana baya.......nafi tunanin kuma yanxun bawai aljana bace ta aureka ba,tunda koda aljana ce saida soyayya ai ko?"

"Kai ka sani qaton banza" Fu'ad din ya fada yana jifansa da wata harara data sake sanyawa farouq ya fashe da dariya,don irin wannan hararar kawai yake iyayi masa idan ya quleshi ya kaishi bango.

Qoqarin daidaita nutsuwarsa yayi don kada ya jawowa kansa jagwal ko yaqi bashi hadin kai akan batun da yazo masa dashi,ya sani sarai kadanne daga aikinsa ya murje idanunsa,musamman yanzun da har ya shiga gonarsa ya kuma tsokaneshi.

"Mu ajjiye wannan batun.....ina nan dai inayi maka addu'a.......na saka a duba mana ticket zuwa abuja Saturday in sha Allah......already ma nayi payment zai mana printing ne kawai"

"Bazanje ba" Ya bashi amsa kai tsaye yana qoqarin shutting down system dinsa idanunsa saman screen din.

Fuska farouq din ya narke yana koma masa kalar tausayi

"Sai na tafi ni kadai.....amma kuma idan ta tambayeka,zan bata labarin ka saba Alqawarin da mukayi da kai ne" Yakai qarshe yana zuba ma side na fuskarshi idanu.

Shuru yayi kawai bai sake cewa komai ba,wanda alamu ke nunawa farouq zaiyi wahala yace bazaije din ba. Sau tari shuru a wajensa alamu ne na accepting abubuwa,idan baya so kai tsaye zaice baiso kuma bazaiyi ba kaman yadda yanzu ya fada mishi da farki,yana sane kuma ya sanyo zancan cika alqawarin......don ya sani shi din mutum ne da ba abinda ya tsana irin qarya sam sam,idan kanaso kaga tunzurarsa ko fadansa to kayi masa qarya.

"Ya ake ciki maganar ginin?" Farouq ya sanyo masa maganar da yasan yanzun itace a gabansa sama da ko wacce. Sai kuwa ya qarasa kashe system din ya rufeta yana dora fararen idanunsa akan farouq din.

"Ending month dinnan nake sanya ran gini zai kammala,sai preparation kawai na budewa wanda shima banaso ya wuce watanni biyu.....duka engines da sauran kaya next week zasu iso in sha Allah" . Kai farouq yake jinjinawa,yana matuqar yabawa da hazaqa da qoqari irin na fu'ad din.

Tun farko yasan idan don ta shine bazai iya ba......don haka ma ya saki

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login