Showing 126001 words to 129000 words out of 132995 words

Chapter 43 - TUBALI Book 1 Complete Document by GARKUWA

22 Aug 2025

157

shigowa cikin kitchine din.


“A’a Jannart ki bar aikin nan ba damuwa, jekiyi kwanciyarki kinga ana sanyi, kuma yau dinma bawani aiki mai wahala zanyi ba, abinci mai sauki zan dafa.”
Mamyn ta fada mata haka cikin kulawa.


Hakanne kuma yasa Jannart din ta d’an langwabar da kai, murya asanyaye tace.


“Dan Allah Mamy ki bari na tayaki, banajin bacci shiyasa.”


Murmushi Mamyn tayi, Ganin kuma Jannart din ta dage ne yasa ta, matsawa gefe tare da cewa.


“To ga Irish patatoes nan ki fere, ni bari na k’arasa had’a wannan farfesun, Idan kika gama saiki soya mana chips ko.”


Kai Jannart din ta jinjina, alaman to, Cikin nutsuwa kuma ta d’auki abun fere dankalin ta somayi.


Cikin abunda bai wuce mintuna kad’an ba kuwa ta kammala, da kanta ta kunna gas, tare da soma soya chips din, suna dan hira da Mamy harta gama.


Wanda zuwa lokacin tuni Mamy ta gama had’a ferfesun, harta fara soya kidney sauce din da za’aci chips din dashi.


Ganin hakane kuma yasa Jannart, had’a musu had’adden sandwich, sai kuma green apple juice wanda acikin mintuna 15 kwata kwata ta kammala had’a shi.


Sosai Mamy taji wani irin farinciki ya cika mata zuciya, musamman saboda yanda taga Jannart din na taimaka mata da ayyuka batare da ganda ba, aikin da zatayi acikin 2hour sai gashi, da taimakon Jannart sunyi shi, acikin awa daya da yan mintuna.


Bayan sun kammala had’a breakfast dinne kuma, Jannart da kanta ta kwashe abincin ta jeresu akan dining table, Yayinda Mamy kuwa ta kwashi food flask din da aka sawa Abba abincin aciki Ta kai masa zuwa sashinsa, sai kuma nasu Baba Maud’o, wanda sai gari yayi haske za’a Kai musu.


Duk wani abu da suka b’ata kuwa saida Jannart din ta wanke, bayan ta gama kimtsa komai ne kuma Mamy ta kalleta, murya atausashe tace.


“Allah Ya miki albarka Jannart, yanzu kije kiyi wanka saiki zo muyi breakfast ko.”


“To Mamy.”
Jannart din ta amsa, kana anutse ta juya ta nufi part dinta.


Koda ta shiga cikin bedroom dinta, kayan dake jikinta ta cire, wani sabon towel ta daura, kaitsaye kuma ta shige Bathroom tayi wanka da ruwa mai ɗan karen ɗumi sabida yanayin ciwonta yafi tashi a irin lokutan sanyin haka.


Koda ta fito feshe jikinta tayi da turare mai sanyin kamshi, bayan ta murzawa jikinta mai ne kuma, ta shafawa fuskarta powder, sai kuma wani brown lipstick da ta gogashi sama sama akan labb’anta, dama kuma ba al’adarta bane yawan kwalliya.


Wani dogon riga mai kaman Kimono ta zaro, tare da sakawa ajikinta, d’as rigan ya mata ajiki, kasancewarsa Maroon color kuma shiya kara bayyana kyau da hasken fatarta.


Dogon gashinta ta tubke atsakiyar kanta, tare kuma da d’aukan mayafin rigar ta yafa akanta, wanda ya sauko harzuwa kan kirjinta.


Alokacin da ta kalli madubi kuwa, murmushi tayi saboda ita kanta tasan tayi kyau.


Agogo ta kalla, wanda yake nuna mata karfe Takwas harda wasu mintuna.


Wasu lallausan takalma flat ta saka ak’afafunta, cikin yanayinta na nutsuwa kuma ta bud’e kofar dakin ta fice wayarta na rik’e a hannunta.


Kaitsaye Falon Mamyn ta fito, fitowar nata kuwa yayi dai-dai da fitowar su Ramadan da Riyyam.


Riyyam ne ya kalleta tare da k’arasowa, inda take Cikin sakin fuska yace.


“Barka da safiya my kyakkyawar Aunty na, gaskiya Hamma Rayyern yayi dace, Yah Allah Nima kabani kyakkyawa mata.”


Lallausan murmushi ta sakar masa, tare da yin k’asa da kanta, cikin dakekkiyar murya tace.


“Barka da safiya Tiktoker Riyyam.”


Dariya Riyyam din yayi, Yayinda Ramadan da sai yanzu yake k’arasowa, shima fadada fara’ar dake kan fuskarsa yayi, cikin kulawa yace.


“Barka da safiya Aunty Jannart fatan kin tashi lafiya.”


D’agowa tayi fuskarta dauke da murmushi ta kalli Ramadan din, kamar yanda yayi mata magana a mutunce kuwa haka itama ta mayar masa.


Dai-dai lokacin kuwa Mamy ta fito daga sashin Abba.


Riyyam kuwa Wayarsa ya zaro, tare da Kallon Jannart din, cikin kulawa yace.


“Hamma Ramadan Aunty Jannart kuzo na d’aga mana selfie, Mamy kema ki shigo.”


Murmushi duk sukayi, Mamy kuwa Kanta ta girgiza, fuskarta dauke da dariya tace.


“A’a nikam kudai kuyi selfien ku.”


Tsayuwa sukayi inda suka saka, Jannart din atsakiyarsu, Riyyam din kuwa shiya d’aga musu wayar yayi musu selfie, har kala uku.


Bayan sun gama ne kuma Mamy tace.


“To saiku zo muyi breakfast ko.”


Kai suka jinjina dukansu, tare da karasawa dining table din suka zazzauna, Jannart da kanta tayi saving nasu.


Bayan sun fara cin abincinne kuma, Riyyam-nsra ya ciro Wayarsa tare, da turawa Mamynsa hotunansu da sukayi yanzun, Ganin Mammyn bata online ne kuma yasa shi danna voice, batare kuma daya gama cinye abincin dake bakinsa ba yace


“Good morning Mammyna, ga amaryar Hamma Rayyern dina kiganta, she’s so cute Mammy kisa mata al'barka, kiyi musu addu'a'n zaman lafiya da samun yan tagwayen yara.”


Yana gama fadin haka yayi sending voice din, tare da ajiye wayartasa ya cigaba da cin abinci.


Mamy da Ramadan kuwa murmushi kawai sukayi, saboda sun San yanda Riyyam yake matukar kaunar mahaifiyarsa sun fahimci duk motsinshi sai ya sanar mata.


Jannart kuwa jin abunda Riyyam din ya fad’ane yasa ta sunkuyar da Kanta k’asa, acikin zuciyarta kuwa ta maimaita abunda Riyyam din ya fad’a.


“Amaryar Hamma Rayyern kiyi musu addu'a'n samun yan tagwaye.”


Ya tabbata kenan cewa, Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara ne mijinta.
Saboda shine kad’ai Rayyern din da tasani acikin gidan, shi dinne kuma wanda suke cewa Hamma Rayyern shine kuma mutumin da baimin mgn in na gaidashi ma bai amsawa ko yaushe fuskarshi kamar ta Yah Junaid.


Share duk wani tunanin dake zuciyar nata tayi, tare da ci gaba da tsakalan abincinta tana ci.


Mamy kuwa ganin Rayyern baisauko ba, yasa tayin tunanin ko bacci yakeyi, shiyasa bata tura ankirasa ba.




Atsanake haka suka kammala breakfast din, dukansu kuma cikin falon suka dawo suka zauna.


Inda Riyyam-nsra keta basu labarai kala-kala, wanda duk mafi yawansu akan TIKTOK ne.




Acan b’angaren Abba kuwa yana kammala yin breakfast d’insa, ya kimtsa tare da bud’e kofar falon nasa ta bangaren baya ya fice, hannunsa rike da key din mota, saboda akwai inda zasuje da Baba Maud’o.


Fitowarsa compound din gidan kuwa, yayi dai-dai da shigowar motar Barrister Kabir.


Ganin motar Barrister Kabir dinne kuma, yasa Abba sakin murmushi, tare da dan tsayawa.


Barrister Kabir kuwa yana gama dai-dai-ta parking din motar ya bud’e murfin ya fito, Fuskarsa dauke da murmushi.


Karasowa yayi tare da bawa Abban Hannu suka gaisa.


Cikin sakin fuska Abban yace.


“Barrister ashe kana tafe, sannu da zuwa, mu isa daga ciki.”


Kai Barrister Kabir ya jinjina, tare da cewa.
“To bari na gaisa da Baba Maud’o.”


Ya k’are maganan yana me mik’awa Baba Maud’o hannu sukayi musabaha.


Bayan sun gaisa da Baba Maud’on ne kuma Abba Yayi masa jagora zuwa cikin gidan.


Ta babban kofar falon kuwa suka shiga, wanda dai-dai lokacin kuwa su Jannart duk suna zaune akan sofa, ita dasu Ramadan.


Da Sallama abakinsu suka kutsa Kai Cikin falon.
Jin sautin muryar Barrister Kabir ne kuma yasa Jannart saurin d’ago kanta.


Ganinsa dinne kuma yasa Murmushin jin dadi bayyana kan fuskarta.


Shima Barrister Kabir din murmushi yayi, tare da karasowa cikin falon ya zauna.


Mamy kuwa da murmushi akan Fuskarta tace.


“Barrister sannu da zuwa”.
Cikin jin daɗi ganin yadda Jannart ta dan sake a cikinsu yace.
“Barka dai Hajia ya bakuwarku?".
Murmushi Mamy ta ɗanyi tare da cewa.
“A'a ai mu bamu da bakuwa, mu duk nan yan gidane”.
Murmushi sukayi baki ɗayansu.
Ita kuwa Mamy juyowa tayi ta kalli Jannart daketa murmushi tace.
“Jannart kawo masa ruwa ko.”


Mik’ewa Jannart din tayi, Tana murmushi, taje ta kawo masa ruwa da kuma ragowan drinks din da ta had’a, harma da sandwich din.


“Abbana sannu da zuwa.”
Ta fad’a cikin tsananin farin cikin da ta samu kanta aciki, tare kuma da ajiye masa dan tray din da ta Hado ruwan agabansa.


“Yauwa Jannart sannu.”
Barrister Kabir din ya amsa yana murmushi, tare da juyawa suka gaisa da Mamy.


Ramadan da Riyyam ne kuma suka gaidashi, fuska asake ya amsa musu.


Jannart kuwa sabida tsananin jin dadin ganinsa, dan matsowa kusa dashi tayi, tare da manna kanta jinin hannun kujerar da yake zaune a kai, cikin yanayin rauni tace.


“Abba Ina kwana.”


Murmushi Barrister Kabir din, yayi cikin jin dadin yanda ya ganta yace.


“Lafiya k’alau Jannatuwa, ya kwanan bak’unta.”


Kanta tad’an sunkuyar kasa, fuskarta dauke da dan murmushi tace.


“Alhamdulillah Abba, yasu Aunty Dijat Hafeez,da Hafeeza”.


“Alhamdulillah suna lfy”.
Ya bata amsa yana kallonta.
Cikin nitsuwa tace.
“Ayya Abba da kazo min da Hafeeza.”


Murmushi Barrister Kabir din yayi, tare da dubanta yace.


“Uhummm Jannart kenan, waya gaya miki yanzu, bayanni akwai wanda zai na kawo miki ziyara.”


Fuskarta ta dan shagwabe, cikin sanyi tace.


“Ayya Abba yanzu har Aunty Dijat dasu Hafeez babu mai zuwa, ba wanda zaizo wajena kenan.”
Kai Abbansu Rayyern ya jinjina tare da cewa.
“Shima ai zamu hanashi zuwa sai naga kin saki jikinki kin dena zama kina tagumi da zubda hawaye”.
Da sauri tace.
“Abba na dena”.
Yar dariya sukayi kana
Barrister Kabir yace.
“Ato kin dai ji kam ko”.
Turo dan karamin bakinta gaba tayi, wanda hakan yasa Mamy, Ramadan da kuma Riyyam duk sukayi murmushi.


Adai-dai lokacin kuwa Rayyern wanda fitowarsa daga part d’insa kenan, ya soma saukowa daga kan steps din, cikin shigar wani lallausan yadi mai kalan mobile blue mai masifar taushi da sheki wanda akayi masa dinkin half jamfa da kuma, wando pencil, sosai kayan sukayi masa masifar kyau yanayin kalarsu ya kara hasko farar fatarshi ta fito ras,
Hular damanga farace a amsa mai ratsin Nobel blue ɗin.
Yayinda kwantacciyar sajen dake kan fuskarsa ke zuba sheki har wani dauke ido yakeyi.
Sai takalmin toms Noble blue dake kamarsa.
Kamshi kawai yake zubawa, yanayin yanda yake takun nasa kuwa cikin dan sassarfa alamun sauri yakeyi.


Yayi kyau matuk’a, Daddaɗan kamshi da kuma jin sautin takusa ne kuma yasa, duk suka kalli steps din.


Dai-dai lokacin kuwa ya gama sauk’owa.
Ganin Barriter Kabir da yayi ne kuma, yasa shi ɗan yamutsa muskarshi.
“Kai wannan menne irin mutum ne mai masifar nacin tsiya mutun kamar maye!.
Wannan jaraba har ina, toh yanzu kuma Meya kawoshi da sanyin safiyar nan, kamar mai binmu bashi.”
Yayi mgnar zuci tare da kwaɓe fuska yana mai k’arasowa cikin falon.


D’an rusunar da kanshi yayi, cikin naɗe murya can ƙasa yace.


“Barka da zuwa Barrister.”


“Yauwa Barka Dr. Rayyern.”
Barrister Kabir din ya amsa masa, cikin sakin fuska.


Rayyern din kuwa dan matsawa gefe yayi, tare da zama akan kujera dake gefen Ramadan.


Ganin hakanne kuma yasa Abba kallonsa, cikin kulawa yace.


“Rayyern fita zakayi ne.”


“Eh Abba”.
Ya bashi amsa a takaici.
Cikin tsaresa da ido Abba yace.
“Ina zakaje”.
Ya ƙare tambayar da alamun son cikekken bayani ina zaije me kuma zaiyi.


Hannunshi ya ɗan d’ago.
Tare da saidashi kan wuyanshi.
Ya ɗan shafa wuyanshi har zuwa kan ƙeyarsa kana a hankali yace.
“Inason zanje company ne, saboda P.A yamin waya, wai akwai wani inji da ba’a gane kansa ba, like dai baya aikin daya dace kana Engineer bello yana can yana jirana shima.”




Kai Abban ya jinjina, kana cikin gamsuwa yace.


“To Allah Ya bada sa’a.”


Da “Ameen.” Ya Amsa.


Barrister Kabir kuwa, ledan dake hannunsa ya mik’awa Jannart dake zaune akasa, cikin kulawa yace.


“Jannart ga waya nan na sayo miki, akwai new sim acikinsa, bayan number na kuma bansa miki numbern kowa ba, sannan kada ki fara amfani da laptop dinki yanzu, kina dai charging nasa amma kada ki yi using dashi,domin hakan zai taimaka wajen gujewa duk wani shaida.”


Karb’an ledan da yake mik’o mata din tayi, cikin jin dadi tace.


“Nagode sosai Abba Kabir Allah ya kara budi.
Amma fa jiya Abba ma ya sayamin sabuwar waya.”


Ta kare maganan tana meyi masa nuni, da Wayar dake hannunta.


Barrister Kabir din kuwa murmushi, yayi cikin jin dadi yace.


“Masha Allah waya tayi kyau sosai, Allah yasanya al'khairi ya kuma saka da alkhairin.”


Da “Ameen.” Duk suka amsa, saidai banda Rayyern wanda ya kawar da kansa gefe yana kallon Riyyam-nsra daketa lallatsa woya ya kifa kai har kamar zai hade goshinsa da wayar haka yasa ya tsareshi da ido yana nazartarsa.
Dan ko kasa inda take dinma bai kalla ba sai dai yana jin amon muryarta.


Barrister Kabir kuwa Mikewa tsaye, yayi tare da Kallon Jannart din, cikin tausasa murya yace.


“To Jannart ni zan wuce, dama sakon da nazo kawo miki kenan.”


Murmushi Jannart din tayi, cikin sanyi tace.


“Abba ka gaida gida, ka gaishemin da Aunty Dijat dasu Hafeeza.”


“Zasuji Insha Allah.” Abban ya fad’a, tare da juyawa yayiwa Mamy sallama.


A gaida gida Mamyn tayi masa, sannan suka fice shida Abba.


Ganin hakanne kuma Yasa Rayyern ma mik’ewa tsaye.


“Rayyern katsaya kayi breakfast tukun kafun ka fita, gacan abinci akan dining.”


Cewar Mamy tana me kallonsa.


Fuskarsa ya d’an ya mutsa, tare da Kallon agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa, adan kasalance yace.


“Mamy banajin yunwa sosai, kuma Idan na tsaya break zan makara, saina dawo kawai ki ajiyemin lunch.”


Ya k’are maganan yana me nufar hanyar fita daga falon.


Wanda hakan yasa Mamy da Ramadan suka Bishi da kallo, Mamy kuwa har cikin ranta tana mamakin, yanda Rayyern din yake tafiyar da rayuwarsa, gaba daya sam cin abinci bai damesa ba sai dai wasu lokuta isasshen lokacin zaman cinnema yake rasawa, shiyasa idan ya tara yunwar tofa in ya samu ya ya zauna zaici da dama.


Rayyern kuwa Koda ya fito compound din gidan, ya samu tuni harsu Abba da Baba Maud’o sun tafi, Yayinda shima Barrister Kabir Yayi nasa tafiyar.


Motarsa ya shiga, Yayinda Hadi ya jasa suka fice daga Cikin gidan.


Acan falo kuwa, har Rayyern din ya fice Jannart bata iya sake dago Kai ta kalleshi ba, saboda tun Kallon farko da tayi masa, taji zuciyarta na bugawa, wanda kuma batasan dalilin hakan ba.


Bayan fitan nasa ne kuma ta d’ago kanta tare da Kallon Mamy, ad’an ladabce tace.


“Mamy yau me zamu dafa da rana.”


Murmushi Mamyn tayi, kana atausashe tace.


“A’a Jannart yau kam kihuta, ina nan zanyi komai, basai kin wahalar da kanki ba wannan fa aiki nane!!!.”




“Mamy ba wahalar da kai bane zanyi, na saba ko agida ma duk ranar da babu aiki Ina taya Momy duk wasu aikace-aikace gida, Dan Allah Mamy ki bari Ina tayaki ki dena cewa na bari.”


Jannart din ta fad’a cikin tausasawa.


Hakanne kuwa yasa Mamy jin sanyi acikin zuciyarta, saboda tasan Itakam tayi sa’ar suruka.


“Shikenan Jannart babu damuwa, na baki wuk’a da nama ki dafa mana duk abunda kikeso.”


Mamyn ta fad’a cikin sakin rai.


Riyyam nsra kuwa, cikin dokin cin abincin Auntyn tasa yace.


“Yauwa Aunty Jannart muje kitchine din, ni yau da kaina ma zantayaki aikin, amma mezaki dafa mana me dadi haka?”


Murmushi Jannart din tayi, tare da cewa.


“Muje zaka gani.” Yanayin yanda tayi maganan tana me mikewa tsaye ne, yasa Riyyam din rufa mata baya suka shiga kitchine.


Shida kansa yayi mata wanke wanke, Yayinda ita kuwa tayi greetting kwawa, saboda abunda ta tsara zata dafa musu shine.
Coconut rice, and onion sauce, sai kuma gas meat mai kayan kamshi, da salad cream, ab’angaren drinks kuma, Banana Milk shake zatayi musu.


Anutse ta fara aikinta, Yayinda Riyyam keta yi mata hira, daga gefe guda kuwa yana tayata da y’an wasu ayyukan, kama daga kan yanke yanke zuwa yan kananun abubuwa masu sauk’i dai.


Haka dai sukayi aikin cikin nutsuwa, almost 1hour kuwa ta kammala komai, tare da jeresu akan dining table.


Gaba d’aya gidan kuwa haka ya gauraye da kamshin girkinta.


Bayan sun kammala jere komai a dining table dinne kuma, ta kunna boner tare dasa turaren wuta mai dadin kamshi.


Mamy kanta ta yaba da aikin Jannart din, bayan sunyi sallan azahar ne kuma, suka zo kan dining table din sukaci abincin.


Saidai kuma Jannart din bata wani ci abincin sosai ba, ayanda Mamy ta fahimta kuwa shine, Jannart din irin Rayyern ce, kwata kwata basu dauki cin abinci serious ba sai dai tasan shi Rayyern in ya zaunawa abincin bai mishi da wasa ko dan yakan dade baici bane, ta lura ita kuma Jannart irin mutanen ne da zasuci kaɗan yanzu anjima su kuma cin kaɗan.


Bayan sun kammala cin abincinne kuma suka dawo falo, hira suka Dan tab’a, lokacin da Ramadan da Riyyam suka fita yawo ne kuma, Jannart ta tashi ta koma side dinta, tana kwanciya afalonta kuwa bacci ya dauke ta.


A can gidan Alhaji Idi Saleh Dakata kuwa.
A gajiye ya dawo gida, daga Tashar Arewa 24 TV da yaje, yanzu ya samu MD da kansa ya mishi bayanin ɓacewar Jannart da kuma hukuma da suka shiga lamarin kana yasa gidajen Rediyo su cekinta su kuma ya bawa gidan tv nasu cekiyar gaggawa.
Daga nan kuma asibitin Dr Lukman ya wuce inda anan sukayi tattaunawa mai yawa kana ya nufo gida.
Da sauri Mom tabi bayanshi.
Tana cewa.
“Alhaji anji lbrin Jannart kuwa?”.
Da sauri ta matsoshi ganin yadda ya dafe kanshi da hannaye bibbiyu yana mai jujjuya kanshi.
Kana ya tafi lu alamun zai fadi.
Cikin tsananin tashin hankali da kidima Mom ta saki ihu tare da isowa gareshi ta tallabeshi murya na rawa take kwarmawa Abdul kira.
da gudu Abdul ya shigo cikin tashin hankali tace.
“Abdul kira min Barrister Kabir Abbanku kace Daddynku ba lfy”.
Kafin ta ƙare mgnar kuma Alhaji idi Saleh Dakata ya sake gaba ɗaya naushin ya jata suka tafi kasa bisa carpet.
Ganin haka ne yasa Abdul gigicewa tare da zaro wayarsa ya kira Barrister Kabir.
Wanda shi kuma lokacin ya fito daga gida shi kenan.
Koda Abdul ya gaya masa abinda ke faruwa.
A firgici ya dauko ya wuce asibitin Dr Sajo ya dauko shi.
A gidan Alhaji Idi Saleh Dakata'n kuwa, suna cikin gigin suka jiyo muryar Dr Lukman yana sallama hakane yasa Mom sakin dogon numfashi tare da cewa.
“Dr ka shigo, kayi sauri shigo ka taimaka mana Alhaji zai fadi”.
Jin hakane yasa Dr Lukman kutsa kai cikin main falon nasu da hanzarin.


Daga nan shida Abdul suka tallabeshi suka a mota suka wuce asibitin Dr Lukman din.


Suna tafiya ba jimawa.
Barrister Kabir da Dr Sajo suka iso.
Bayan Ashiru ya musu bayanine suka nifi asibitin Dr Lukman ɗin.




A nan gidansu Rayyern kuwa.


Bacci Jannart tayi sosai dan Koda ta tashi tayi sallan la’asar sake komawa tayi ta kwanta.


Ahaka dai har magriba.




9:30 pm dai-dai ya shigo gidan, wanda kuma tun fitan da yayi da safe sai yanzu yake shigowa.


Da sallama abakinsa ya tura kofar main falon ya shigo.
Jin da yayi ko ina shiru babu alaman motsin kowa ne, yasa kaitsaye ya wuce sama, saboda yasan zuwa yanzu su Mamyn nasa sunyi bacci.


Yana haurawa saman kuwa, anan cikin falonsu ya samu Ramadan da Riyyam, ko wannensu rungume da waya ba abunda sukeyi sai chatting.
Kana ga TV a kunne tashar Arewa 24 TV.
Yayinda su basuma san me akeyi a TV'n

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login