Showing 93001 words to 96000 words out of 132995 words
da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.
Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
By
*GARKUWAR FULANI*
D’an gyara zamanta tayi, tare da sake fuskantar cameras din dake shooting fuskarta.
Ajiyar zuciya ta d’an sauke tare da nemo jarumtarta dake suɓuce mata,
cikin Taushi da kuma amon muryanta zakin tace.
“Assalamu Alaikum Masu kallonmu, sannunmu da arzikin sake saduwa, acikin shirinmu mai farinjini wanda mukeyi Domin farincikin ku, wato Bak’onmu na Mako, To ayau dai shirin namu ya gam da katar yayi babban kamun gayyato muku wani babban bak’o, wanda nasan idanuwanku suna cike da dokin ganinsa. Wannan bako kuwa ba kowa bane face. Dr...!”.
Sai ta kuma datse sunan tare da sakin murmushi.
Wanda hakan yasa kab masu kallo suka ɗokanta da son jinnwayene baƙon makon.
Mayafin kanta ta ɗan gyara tana mai jin harshen ta bazai iya furta sunansa ba, cikin nitsuwa ta tare da lumshe taci gaba da cewa.
“Sanannen mutumin da sunansa yayi shuhura acikin kasarmu Nigeria dama wajenta baki daya, nasan da yawan masu kallo basu tab’a Ganin wannan bak’on namu ba.
Dan yauce rana ta farko daya amsa gayyatar wata kafar sadarwa ta jarida, da TV. Alhamdulillah sai namu a yau.
Kasancewarsa Babban Doctor kuma babban d’ankasuwa da duniya ke damawa dashi, saboda haka yau dai gamu gashi, zakuma mu haska mukushi, inda zai fayyace mana koshi din waye.”
D’an tsagaitawa da maganan nata, tayi tare da juyowa Ahankali ta fuska ce sa.
Cikin muryarta mai taushi tace.
“Doctor barkanka da zuwa, barkanka kuma da shigowa cikin wannan tasha tamu mai Al'barka, da fari dai munaso ka gabatar da kanka ga masu kallonmu.”
Numfashi ya d’an sauk’e, batare kuma da wani sakin fuska ba, ya dago da kansa ya d’an kalli cameran a fakaice, cikin muryarsa da ako yaushe yake kara bayyana asalin wanene shi yace.
“Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara.”
Ya k’are maganan atak’aice, Cikin kuma halin nitsuwa.
Kai Jannart din ta jinjina, tare da hade yatsunta awaje daya, cikin tsananin kwarewa da sanin makamar aikinta tace.
“Masha Allah to Dacta, yanzu dai ka gabatar da kanka awajen al’umma, saura kuma mu shiga cikin shirin namu ka'in da na'in,.
Dai-dai lokacin kuma aka ɗan ɗauke fuskokinsu aka sa ɗan sautin tambarin tashar Arewa 24 din.
Kana aka dawo dasu.
Cikin nitsuwa ta ɗan kalleshi a fakaice kana a hankali tace.
“Shin amatsayinka na cikakken Likita, wanda kasa keji dashi, wacce irin shawara zaka bawa al’umma dan kula da lafiyarsu da matakan kariyar riga-kafi?.
Sannan kuma ya kake Ganin irin yanda al’amarin k’asarnan yake, ma’ana irin halin da al’ummar k’asar take ciki, da kuma irin k’alubalen da muke fuskanta more Especially wurin kiwon lafiyar kananan yara da mutanen karkara da tsofaffinmu, Sannan wani irin hanya da kuma mataki zamu bi, Domin mu samu nasara akan yaƙar cututtukan dake addabar al'ummar ƙasar mu?
Then menene matsalarmu aharkar malaman kiwon lafiya?”.
Kanshi ya ɗan kauda gefe tare da yamutsa fuska, ɗan gajeren tsaki yaja.
Ji yadda yarinyar nan take zuba babu ƙaƙƙautawa kamar carbi ya tsinke ko numfashin bata ja.
Ta wani jero min tambaya kusan goma, a dungule.
Ni Radio ne ko ni parrot ne da zan iya haka.
Duk yayi tunanin cikin second 5.
Numfashi ya ɗan fesar kana cikin haiba da dakewar murya yace.
“Privet Hospital!!!
Sune matsalan kiwon lafiyar kasarmu.
Domin sune suke dak’ushe asibitocin gwamnati, har suke zama ba masu inganci ba.”
Ya fad’i maganan kai tsaye, batare kuma da wani dar ko shakka ba.
Jannart kuwa Kai ta d’an jinjina, tare da sake rik’on wani farin card dake hannunta, saboda acikine duk wani tsare tsaren tambayoyin da zatayi masa suke.
Kanta ta d’ago daga Kallon takardar da takeyi, still kuma Cikin muryarta da akoda yaushe take fitar da daddad’an sauti tace.
“To Dakta. munji abunda kace. Kuma al'umma zata iya gamsuwa da hakan.
Toh amma kamar wani mataki za’abi, Domin asamar da ingancin asibitocin Gwamnati da kiyaye lfy?.”
Numfashi ya ɗan fesar a hankali kana yace.
“Dole gwamnati ta tsaya ta gyara asibitotin ta, ta ingantasu hade da kawo nagartattun kayan aiki, da kuma kwararrun ma’aikata, baya ga haka kuma ta rika biyan likitotin isassun kudaden da zasu iya biya musu bukatunsu, saboda mafi akasari acikin kasar bawai Nagartattun Doctor’s dinne bamu da suba, kawai dai basa samun yanda suke sone, hakanne kuma yasa suke fita wasu k’asashwn suje su fara aiki Acan, ko kuma kowannensu saiya zaga gefe yaje ya bud’e asibitin kanshi, saboda baisamu yanda yake so a gwamnati ba, wannan dalilin yasa ayanzu asibitocin gwamnati suka lalace suka zama kara zube,, Domin anriga da ancire Tubalin abunda aka gina asibitin akai haka yasa duk mai ƙarfi da yar wadata bazaibi ta kan asibitin gwamnatin ba, wanda kuma da al'ummar ƙasa aka ginasu.
Sannan yana da matukar muhimmanci ga iyayen yara suke kula da tsabtar jikin raya da muhalli da abinda zasuci domin shine babban rigakafi.”
Ya k’are maganan yana me gyara zaman necktie din dake wuyansa.
Sosai yayi masifar kyau yadda yake dan jujjuya fararen yatsunshi
Inda Jannart kuwa ta ci gaba da cewa.
“To Doctor yaya za’ayi agyara matsalar Government Hospitals din domin in ƙantasu ta yadda al'ummar ƙasa zasuje garesu da kekkyawan yaƙini!?.”
Dan muskutawa yayi still kuma cikin rashin tsoro ko fargaba cikin yaƙinin da Kekkyawar manufa yace.
“To Da farko dai asibitotin gwamnati abunda zai gyarasu abu maisauki ne!?”.
Da sauri ta ɗan fuskanceshi tare da cewa.
“Duk da lalacewar da sukayi gyaran mai sauƙin ne? Ta yaya ko kuma ta ina gyaran zai fito da sauki!?”.
Cameras din ya ɗan kalla kana ya gyara zamanshi tare ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya cikin masakaicin amo yace.
“Idan har gyara akeso ta yadda zasu in ƙanta tofa dole daga kan, Shugaban k’asa, Governors, Ministers, senator's har zuwa kan ciyamomin kana kama daga Sarki, Waziri, Galadima, Wambai, Chiroma, Durbi, Garkuwa, Ɗan buram, Majidadi, Ma'aji, dama duk wasu masu fad’a aji, na siyasa da masarautun gargajiya. suyi kokarin daina zuwa asibitotin kudi, ko fita kasashen waje Dan duba lafiyarsu, su tsaya su ingata asibitotin Gwamnati, ta hanyar dasu kansu asibitotin zasuna basu Kekkyawar kulawa,
Ya zama asibitin da Sarki zaije.
To shi fadawan sarki zasuje.
Kana asibitin da shugaban kasa zaije ya zama shine na talakawa, ta hakane zai sa shugabanni su san halin da asibitocinsu suke ciki, da inƙancin likitocin da kayan aikin.
Haka zai sa a kula da in ƙancin asibitocin.
Domin duk wani asibitin gwamnati matukar akwai ingantattun Doctor’s da kayan aiki da watar tsabtacewa.
Toh dai-dai yake da duk wani asibitin kudi, hakanne kuma zaisa asibitotin kudin su dakushe, su durkushe.
saboda yawnacinsu bawai anginasu Dan taimakon al’umma bane, anginasu ne kawai saboda neman kudi irin na yaki haram yaki halal, tayanda talaka bazai tab’a amfana dasu ba sai dai su cika aljihunsu.”
Da sauri Jannart ta juyo ta kalleshi.
Ido cikin ido sukayi da juna,
Bakinshi ya taɓe tare da yimata wani irin munafukin harara, hakane yasa tayi saurin yin ƙasa da kanta
Kai ta jinjina, cike kuma da gamsuwa da kalaman nasa tace.
“Tabbas maganarka tatafi Kan hanya mai kyau, sai-dai kuma amma baka ganin yin hakan zai dakushe mutane da dama, musamman ga masu privet hospital kamar yanda ka fad’a!!!.”
Kansa ya d’an girgiza, sannan kuma akaro na farko da tun zamansa awajen ya dago kansa da nufin ya kalleta da kyau dan tambayar da tayi masa.
Saidai ko secan daya bai dauka yana kallontan ba yakau da kansa gefe.
In don’t care manner yace.
“Hakan ba wata matsala bace ai, Domin bani da yakinin cewa yin hakan zai tauye musu hakkinsu”.
Da sauri ta kuma cewa.
“Toh kuma kake bada shawara a rushe asibitocin?”.
Wani irin kallo ya ɗan watsa mata.
Sabida ta mishi tambayar cikin gajin haƙuri irin nasu na ƴan jaridu.
Dan bata tsaya taji ya dasa Ayaba.
Koda yake haka suke.
Yan jaridun suna jin daɗin jefowa mutun tambaya kamar sauƙawar aradu ko kuma titsiye.
Cikin tsare fuska yace. “Dama meyake sawa su bude nasu asibitotin?”.
Ya mata tayarma tare da tsareta da ido.
Yar-yar haka taji tsikar jikinta na tashi.
Haka yasa da sauri ta kauda kanta gefe.
Shi kuwa kai ya jin jina tare da cewa.
“Baki sani bako?
To bari in gaya miki...”
Ya kare mgnar yana mata hararan ƙasan ido kana yaci gaba da cewa.
“Dama rashin samun isasshen abunda zasu rufawa kawunansu asirine, saboda sometimes acikin asibitotin Gwamnatin, gwamnati bata biyansu al'bashi akan kari, baya ga haka kuma bata basu isassun al'bashin da zasu dauki nauyin iyalansu sabida gwamnatin tayiwa malaman jinya dana makarantu riƙon sakainar kashi Alhamdulillah gwarama wannan gwamnati da muke ciki.
Duk da haka ana buƙatar ƙari.
Domin duk lokacin da Gwamnati ta fara biyansu isassun al'bashi, To ba wani abu da zaisa suje su bude privet Hospital toh ko sunje sun buɗewama wa zai je musu in dai asibitocin gwamnatin nada inkanci , Domin ak’asarnan ba yawan asibiti muke da bukata ba, ingancinsu kawai shine abun buk’atar mu, tayanda talaka da maikudi da fulanin daji zasu samu gamsashshiyar kulawa, batare da nuna wani banbanci ba!!!.”
Ajiyar zuciya Jannart ta sauk’e, kana kuma cikin yanayin nutsuwa tace.
“Mungode sosai Dr. inafatan kuma Gwamnati zataji shawarar daka bada kuma tayi aiki dashi, yanzu kuma zamu shiga babi na biyu. wanda ya shafi b’angaren kasuwanci kafin mu dawo nan a likitance.
Yah Salam shine abinda ya faɗa a ransa.
Sabida ya lura yau bakinshi sai yayi tsami sabida magantuwa da wannan fitinenneyar yarinyar take sashi.
Kamar a tsakiyar kanshi yaji ta kuma cillo mushi tambaya.
“Shin Dakta wacce irin shawara zaka bayar, agame da yanda sha’anin saye da sayarwa ya zama acikin k’asarnan, misali ta yanda ayanzu kayan abinci yayi tsada sosai, akullum wasu daga cikin yan kasuwa k’ara farashin kayansu suke, rayuwa tayiwa talaka tsada, manyan y’an kasuwa da kamfanoni sun had’e kai da baki waje daya, Koda yaushe farashin kaya hauhawa yake, tayaya ne za’a samawa al’umma sauk’i, musamman manoma, wanda sune ma suke noma abincin amma kuma Idan ya shigo kasuwa sai yazo yafi karfinsu, shin wacce shawara zaka iya bawa manoma?.”
Numfashi ya dan fesar ta bakinsa, saboda yanda yaji labbansa sun soma gajiya da yawan motsasu da yake.
Hakanne kuma yasa batare daya dago ya kalli ko cameran ba, saidai atausashe yace.
“Shawarar da zan iya bawa Manoma itace, duk wani manomi Idan har ya noma abunda zaici, To kada yayi gangancin saidawa, har sai ya tabbatar daya ware ishashshen abincin da zai isheshi, har na tsawon wata shekarar da zai sake noma wani abincin, kafun nan sai yazo ya saida wanda zai sayar, saboda gudun kada ayi gaban mai haƙar rijiya. kai ka noma ka gama shan wahala, sannan kuma ka tattara ka sai dashi lokacin da yake araha, bayan y’an wasu watanni sai yayi tsada, ga kuma wanda kake dashi ya riga ya k’are ga damuna ta sako sama ruwa ƙasa ruwa, fita nemowar ma wata rana sai ya gagara, kaga kenan nakan daka saida shi zaka sake zuwa ka saya, akan farashi mai masifar tsada, kenan Kai Manomi kaine ka wahala a banza.
Sannan kuma ya kamata manyan kamfanoni su dinga tausayawa talakawa, su daina yi musu irin wannan hawan k’awaran, zuwa su sai abincin manoma tun yana gona basu shigo dashi gari ba su kuma manoma ku farga da wannan sagegeduwar da akeyi muku.
Sannan kuma su manoman kansu, su daina sayarwa masu manyan kamfanoni abincinsu tun yana gona, saboda wasu tun abunda suka noma yana yabanya suke saida shi, atunaninsu ko da ace abun da suka noma din baiyi kyau ba ko sanadin fari ko tsuntsaye ko kwari ko tsutsa, su dai sun samu kudi, da yawan mutane basu san al'barkar dake cikin kayan gonansu ba, saboda haka yana da kyau, ka dinga girbe abunka kana gyarawa da kanka, ka kididdige abinda ka samu ka ware na buƙatunka kafun ka mik’ashi ga wasu, sannan kuma duk wani manomi yayi kokarin saida abincin daya noma, akan farashi mai kyau, saboda ko yaya guminsa ya keci.
Domin shi kadai yasan wahalar daya sha wajen noma ta, sannan yanzu Idan akayi dubi, gaba daya manoma da talakawa su suke shan wahala, musamman Idan aka shiga cikin damuna, haka komin ruwa da iska zasu tsaya neman abunda zasu rufawa kansu asiri suyi noma dan ciyar da al'umma duk kudinka fa, in manomi baiyi noma koda kuɗin ka bazaka samu abincin ba, shin zakaci kuɗin naka ne!!!?. Sannan ku kuma y’an kasuwa da kamfanoni masu karawa kayan abincinsu kudi, ba komai kuke ciba face *RIBA* haramtacciya, wanda kuma kowa yasan hakan ba abubane mai kyau bane, ga wanda suke sayan abinci su b’oye sai yayi tsada su fito dashi, suma duk Allah naganinku, kuma Allah da kansa baya tausayawa wanda baya tausayin na kasa dashi.”
Kai gaba daya mutanen dake boye abayan cameras din suka jinjina, hatta MD da kansa shima ya samu cikakkiyar gamsuwa da bayanan da suka fito daga bakin Dr. Rayyern din.
Ba kuma a iya cikin tv station din ba, har acikin gaba daya k’asar tamu, mutane da yawa dake Kallon Live Program din sun samu cikakkiyar gamsuwa, Yayinda kalaman Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din ya ratsa zuk’atansu, ciki kuwa harda mafiya yawan manoma da suke kallon shirin, sabida Tashar Arewa 24 TV tayi zarran birni da ƙaune suna kallonta maza da mata manya da yara.
Adai-dai lokacin kuma Abba Kabir zaune yake agaban tv yana Kallon shirin, shi kansa ya gamsu da kalaman Dr. Rayyern din, saidai kuma sosai zuciyarsa ta cika da tsananin mamakin, ganin da wanda Jannart din ke hira yau.
Acan babban falon gidansu Jannart din kuwa, Alhaji Idi Sale Dakata, Dr. Lukman da kuma Alhaji Abdu Tababa ne, zaune sun zubawa babban TV plasma din dake cikin falon idanu.
Wanda kuma yanzun akayi musu kira na musamman, akan su kunna tashar Arewa24 Dan Ganin hirar da akeyi da Dr.Rayyern din.
Hakance kuma ta kasan a wurare da dama yadda wasu ke kiran wasu manyan ƙasar suna shaida musu su kunna tv tashar Arewa 24 TV suga program ɗin da akeyi da Dr Rayyern Mai-nasara.
Jin abubuwan da Rayyern din ya fad’ane kuma, yasa Alhaji Abdu Tababa yin k’wafa, kana cikin takaici yace.
“Amma dai wannan yaron anyi d’an iska, mai tsaurin ido, kujifa abunda yake fad’a, wai gwamnati ta rushe asibotin kudi ta inganta nata, Lallai yaron nan bashi da tsoro.”
“To shi nashi asibitin na uban meyene, shegen yaro mai jajayen kunnuwa.”
Cewar Dr. Lukman da yakejin kansa kamar ya kurma ihu yayi fiffige yaje ya shaƙo wannan yaron.
Yayinda Alhaji Idi Sale Dakata kuwa ya rumste idanunsa, saboda shi ayanzu ko son Ganin yaron bayayi, hasalima gaba daya tunaninsa ya tafi ne akan yanda zai ga bayan Rayyern din, saboda al'ƙawari ne da yayiwa kansa cewar saiya b’atar da yaron daga Doron k’asa.
Acan cikin tashar ta Arewa24 kuwa, Jannart ce ta sake gyara zamanta, batare kuma da ita ma ta d’ago kanta ta kalli Dr. Rayyern MAI-NASARA dinba tace.
“Toh Doctor mu dan koma baya.
Kaba da shawara akan cewar aduk’ar da asibitotin kudi, a tada na Gwamnati, ta hanyar zuba ingantattun likitoti da kuma kayan aiki, To irinku fa masu asibitotin kudi yaya zakuyi kaida ire-iren ka masu privet Hospital's, kodai kuma zaku dawo aiki a asibitotin Gwamnati ne! Ku watsar da naku asibitocin!!?.”
Cikin gamsuwa da yarda da kai yace.
“Kwarai kuwa, saboda ai hakan bawai gazawa bace, Indai muka had’e hannu da Gwamnati dan musamar da ingantaccen kulawa ga al’umma, To mu hakan kamar alkhairi ne agaremu, ba kuma najin hakan zai tauyemu ko ya ragemu da wani abu.”
Ya fad’a atak’aice saboda ya fara gajiya da amsa tambayoyin yarinyar mai shegen baki cai-cai surutu tuni yawun bakinsa sun kafe.
Hannunshi yasa ya ɗan shafa sajenshi har zuwa kan lips ɗinshi sabida ji yayi kamar bakinshin yayi tsawo ne da surutu.
Jannart kuwa, again cikin sanin makamar aikinta tace.
“Amma kamar baka goyon bayan duk wani privet hospital, in na fahimceka.
Kuma naga kaima kana da naka hospital din, wanda kuma bana gwamnati bane, ya akayi to hakan ta kasance? meyasa baka had’a hannu da Gwamnatinba!? kun ingata Koda asibiti daya ne!!!?”.
Wannan Tambayar ta saka duk magautan
Dr. Rayyern Mai-nasara dake Kallon tv suka saki Murmushin mugunta, saboda atunaninsu yarinyar ta kawosa makura inda bazai iya amsa tambayoyin nata ba Alhaji Idi Saleh Dakata kuwa.
Saida yaji tamkar ya shiga TV ya goya ɗiyar tasa Jannart, sai yakeji kamar dan su tayi mishi wanna tambayar dan ta kure musushi.
Dr Lukman kuwa hannunshi ya dunƙule tare da jinjinawa Jannart harda yimata alamar kiss dan masifar daɗi.
Ita kuwa Jannart batama san sunayi ba, kuma bada wata manufa tayi tambayarba sai dan dacewar hakan tunda tasan yanada asibitin.
Shikuwa Rayyern ko ajikinsa baiji wani abu ajikinsa dangane da tambayar da Jannart din tayi masa ba, hasalima Dan gyara zamansa yayi, cikin kuma kwarin guiwan da ako yaushe yake tare dashi yace.
“Banyi karatun likita Dan yin aiki akarkashin wani ba, asali Tubalin karatuna shine Idan na kammala na raya asibitin, dake gine tun kan zuwata duniya.
saboda amfanar al’umma, bawai iya mai kudi ba kawai harda talakawa, saboda babu wani wanda, asibitin Mai-nasara Hospital yafi karfin zuwansa, koda kuwa bashi da karfi, Mai-nasara Hospital muna da foundation na taimakawa marassa karfi dashi mukeyin dukkan taimakon daya dace, sannan kuma Mai-nasara Hospital bawai irin asibitotin nan ne da kowa ya sani ba, Ina da confidence akan Hospital dina, ako ina kuma zan fada batare dajin na fadi ba daidai ba!!!.”
Kai Jannart ta jinjina, saboda ayanzu kam amatsayinta na y’ar jarida ta gamsu da duk kalaman mutumin, musamman da ta fahimci with full confidence yake magana, ba