Showing 45001 words to 48000 words out of 132995 words
dake sauya salon fita da shiga.
Cikin tsuke fuska yace.
“Bakwa ganine, yanzu idan da nabi takanku fa?”
“Kayi hakuri dan Allah!” Salman ya fad’a asanyaye.
Itakuwa Jannart sai ayanzu ta bud’e idanunta, Yayinda gaba daya jikinta ke kakkarwa.
Hannu tasa ta dafe ƙirjinta.
Rayyern kuwa y’ar gajerar tsaki yaja, batare kuma daya sake ce musu komai ba ya juya ya nufi inda kayayyakinsa suke.
Yana zuwa kuwa ya zauna akan wata kujerar silver mai daukar mutun uku,
Sunkuyowa yayi tare da bud’e jakan daya shigo da ita ya zaro bottle water, b’alle murfin goran yayi, kana ya soma zubawa akan tarin sumar dake kansa wanda yake jin zufa na tsastsafo mishi.
Jin da yayi baisamu gamsuwa bane kuma yasashi karkad’a gashin kannasa dan yadda ruwan zai taɓa fatar kansa, wanda hakan yasa har ruwan dake kan nasa ya watsu akan fuskar Jannart.
Salman dake tsaye kuwa dan matsowa yayi, tare da gaishe da Rayyern d’in.
Batare kuma daya dago ba ya amsawa Salman d’in atakaice.
Idanu Salman yayiwa Rayyern dake tsaye, alaman ta gaishe shi.
D’an k’aramin bakinta ta turo gaba tare dasa hannunta ta goge ruwan daya watsa mata, kana asanyaye tace.
“Ina wuni.”
Shiru yayi bai amsa taba, tare dayin kamar ma baijita ba.
“Ina wuni.”
Jannart d’in ta sake fad’a akaro na biyu.
still shiru yasakeyi kamar baijita ba.
“Kibashi hakuri.”
Salman dake tsaye ya fada kasa-kasa.
Karamin bakinta ta sake turowa, cikin kuma wata irin murya mai kama da shagwab’a, sakalci, sanyi da kuma tsoro tace.
“Kayi hakuri please, ranan nayi maka b’arna amma bada sanina nayi hakan ba, Dan Allah da Manzonsa kayi hakuri.”
Idanunsa yadan lumshe saboda jin ta had’asa da sunan Allah da Manzonsa ne kuma, yasashi gyaɗa mata kai alaman yayi.
“Nagode.” Ta fad’a asanyaye.
Shikuwa Salman ganin hakanne ya sashi dan matsowa, cikin neman alfarma yace.
“Dan Allah ranka ya dad’e tambaya mukeyi.”
D’ago Kai Rayyern din yayi ya kalli Salman din afakaice.
Batare kuma dayace komai ba ya maida kansa k’asa tare da ɗaukan ɗan karamin towel ɗin dake gefe ya fara goge suman kanshi zuwa wuyanshi da fuskarshi da sajenshi da ruwan ya jiƙa.
Salman kuwa ganin hakanne yasashi Kallon Jannart, wanda gaba d’aya mood dinta ya sanja,tun lokaci da taga kamar dokin zai takesu ta soma sakin wani irin numfashi sama-sama a hankali.
Wanda da dukkan alama kuma tsoritan da tayi dazunne yakeson tayar mata da ciwon ta.
Sanin yanda ciwon keyi mata idan ya tashi ne kuma yasa, Salman din cewa.
“Subahanallah Jannart ciwonki ko?.”
Kai ta gyaɗa mishi cikin jawo ajiyan zuciya da take son yi.
Cikin kula ya nuna mata gefen Rayyern dan babu wata kujerar a nan kusa dasu.
"Maza ga waje ki zauna.”
Ya kare maganan yana meyi mata
Nuni da d’an gefen Rayyern, wanda kuma dama wajen zaman daya rage din bai wuce na zaman mutum daya ba sabida ya ajiye tarkacensa a wajan zaman mutun ɗaya gashi kuma a ɗaya wojen.
Jannart kuwa kasancewar dama ta gaji da tsayuwa kuma ga numfashin ta dake fizga ne yasa, batare da ta musa ba ta zauna awajen sanin in ta zauna zai iya dai-dai-ta.
Shikuwa Salman ƙara matsosu yayi.
Tare da sake maimaita maganarsa ta dazu.
“Dan Allah ranka ya dad’e tambaya mukeyi.”
“Inaji.”
Rayyern din ya fada agajarce, nan ma saboda yaji Salman din ya hadashi da Allah ne.
"Dan Allah wani mutum muke nema".
Uhum ya kuma cewa a taƙaice.
Gyara tsayuwa Salman yayi tare da cewa.
" Sunan shi Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara.
Shi muke nema, munje Hospital d’insa ne aka tabbatar mana da cewa Lallai-Lallai yana nan, shine muke tambaya dan Allah koka sanshi?”
Ad’an fakaice Rayyern din ya kalli Salman, saidai kuma cikin halin nuna ko inkula yace.
“Meyasa kuke nemanshi me zai muku? Wa yace muku yana nan?.”
Jannart dake dan haki ne taja ajiyan zuciya ta fizogishi da ɗan ƙarfi kana tace.
“Mitssss mutun sai rashin gsky, gaba ɗaya ya wahal damu."
Ta wutsiyar idonshi ya ɗan kalleta a fizge.
Ita kuwa ci ga da cewa tayi.
"Nemansa kawai mukeyi, wallahi daga yanzu kuma ni nagaji,
Dan bazan zauna inyi ta neman wani can ƙato baƙi mummuna mai ƙaton tumbi ba dan yayi kuɗi yana jin kansa waya masan TUBALI kuɗin nashi ko na haram ne shiyasa yake tsoron yin ido huɗu damu ƴan jaridu.
Kada ya gaza amsa mana tambayoyinmu."
Numfashin ta fesar a hankali jin ya dai-dai ta.
Salman nata jujjuya mata kai ina bata ganiba bare tasawa bakinta linzamin.
Tsaki ta ɗan ja tare da ci gaba da cewa.
"Mutumin nan ya wahalar damu sosai, na farko dai shiba kudi ba, amma na lura kudi yafi saukin samu akanshi.”
Alama Salman ya mata akan tayi shiru, da yin gyaran murya.
hakanne kuwa yasa tayi shirun.
Shikuwa Rayyern tunda ta fara maganan yake kallonta ta wutsiyar idanunsa baki cai-cai.
Salman kuwa gyara tsayuwarsa yayi, tare da fadin.
“Mu yan jarida ne kuma ma’aikatan tashar Arewa24, munzo nanne domin samun daman yin hira dashi, Lallai kuma muna da buk’atar ganinsa.
Domin rashin samun tattaunawa dashi ɗin, dai-dai yake da rasa aikin mu.”
Fuska Rayyern din yadan tab’e tare da cewa.
“Uhummm.” Atakaice.
Jin hakanne kuma yasa jikin Salman yin sanyi, still cikin yanayin dake bayyana damuwarsa yace.
“Dan Allah In dai kasan hanyar da zanbi wajen ganinsa ka taimaka min, Banason rasa aikina, inason aikina sosai, Dan Allah Idan ka sanshi, ko kuma kasan inda zan sameshi ka fad’amin, domin da wannan aikin kad’ai na dogara, dashi ne kuma nake ciyar da iyalaina da iyayena, dan Allah ka taimaka kada in rasa aikina.”
Tabbas Salman ya karyo lagonsa tunda ya hadashi da Allah da kuma nuna masa aikin shine mafogararsa, Idanunsa yadan lumshe ahankali, batare kuma daya kalli daya daga cikinsu ba yace.
“Naji badamuwa amma dai yanzu kam bayanan, Zan gaya masa idan ya amince shikenan, zan kawoshi har cikin tashan Arewa24 din kuyi mishi duk tambayar da kukeso.”
Farinciki da tsananin jindadi ne ya lullub’e cikin zuciyar Jannart da Salman.
Cikin bayyana zallan jin dadi Salman yace.
“Mungode sosai ranka ya dad’e, mungode kwarai, saidai amma dama ka sanshi ne?”
Kansa ya jinjina tare da cewa.
“Eh nasanshi uban gidanane zan gaya masa Insha Allah kuma zaizo zan roƙeshi in gaya masa uzurinka bisa tausayawarsa kan kada ka rasa aikinka da kake kula da ilanka zaizo in Sha Allah.”
Murmushi Jannart dake gefe tayi, tare da lumshe idanunta saboda wani irin sanyi da taji acikin zuciyarta sai kuma ta ɗan gyara zamanta.
Shikuwa Salman cikin tsananin jin daɗi yace.
“Sir! Nagode! Nagode!! sosai!!! Dan Allah kayi mishi magana, ni kuma zan tsumayeka har zuwa nan da y’an wasu kwanaki, wallahi Banason rasa aikina yau kuma saura kwana takwas za'ayi hirar dashi ranar Alhamis na sama.”
Kai Rayyern din ya jinjina, tare da sake cewa.
“Insha Allah zaizo.”
“Ka tabbatar zaizo?”
Jannart da nutsuwa ya dan fara sauka azuciyarta ta fad’a.
Dan juyawa yayi ya watsa mata harara, cikin zuciyarsa kuwa cewa yayi.
“Oho bansani ba shegen baki.”
Salman da farinciki ya cika zuciyarsa kuwa, cewa yayi.
“Mungode sosai amma dan Allah in ba matsala ka bamu numbern ka saboda idan zaizo din musani.”
Kansa yadan girgiza, cikin kuma rashin sabonsa da yawan magana yace.
“No kai dai ka bani taka numbern.”
To Salman yace Cikin gaggawa kuma ya bashi numbernsa.
Mikewa tsaye yayi fuskarsa cike da farinciki yace.
“Alhamdulillah Jannart taso mutafi Insha Allah yanzu kam na samu full confidence.”
Yayi maganar yana me soma tafiya, saboda tsananin farincikin da yake ciki kuwa bai majira Jananrt dinba.
Jannart kuwa ganin Salman din ya soma tafiya ne yasa ta mik’ewa tsaye itama.
Tashin nata kuwa yayi dai-dai da juyowan Rayyern inda ya sauke idanunsa Akan bayanta.
Da sauri ya rumtse idanunshi da ƙarfi tare da kame jikinsa sabida yadda yaji tsikar jikinshi na mimmiƙewa yana tashi tsaye.
Sabida a bunda ya gani ajikinta.
Yadda yaji tsikar jikinshi na tashi ne ya kuma sashi buɗe idanunsa.
Damatsan hannunsa ya kalla gaba ɗaya tattausan gargasar jikinsa ta miƙe tsaye.
Ita kuwa Jannart taku ta farayi da nufin bin bayan Salman wanda haka yasa ta ƙara matsowa gabanshi tana takun dake juya kyawawan mazaunanta.
Fuskarshi ya kuma yamutsawa.
Tare da saurin kawar da kansa gefe.
“Meye haka?”
Ya fad’a azuciyarsa yana mai jin kamar ana tsikarinsa
Jannart kuwa da batasan komai ba, ahankali ta soma dan takawa.
"Ta yaya mace zata kasa sanin ranakun al'adar ta? Ko ta kasa kimtsa kanta har ya fito ya ɓata mata sutura?".
Yayiwa kansa tambayoyin a jere.
"Miteeeew". Ya kuma jan gajeren tsaki.
"Daga nan zuwa parking lot mutun nawa zata sa suga jininta, maza nawa zasu ganta a haka, yanzu ita in an barta wai mai hankali ce ko? Waɗanne irin iyayene gareta da zasu barta kara zube da irin wannan shigar, na tabbatar da suturarmu ta hausa fulani tasa baza'a gane lalacewar kayan jikinta da wuriba kamar wannan tsukekken farin wondon pallozo ɗin ko ya ɓata mata jiki hijabinta zai kareta."
Yayi kalaman a saman harshensa.
A hankali ya ɗan juyo ya kalleta tana mai ci gaba da tafiya.
"Ko ba komai musulmace yana da kyau ta suturce kanta".
Ya faɗa yana kallon yadda take jujjuyawa tamkar Wahainiya.
Sai-dai bai wuce taku goma tayi ba zuwa sha biyu.
Taji muryarsa ta ratsa dodon kunnenta.
Inda yace “Stop.” Cikin wata irin kakkauran murya.
Aikuwa cak ta tsaya saidai kuma Sam ta kasa juyawa ta kalleshi.
Shikuwa Rayyern fuskarsa ya sake had’ewa, tare da yamutsaawa dan ji yake tamkar zaiyi amai kana ahankali ya juyo ya kalli alkyabbar shi dayake gefenshi.
A hankali yasa hannunshin ya d’auki alkyabban.
Ya tashi tsaye kana ya fara taku a nitse.
Har lau bata juyoba kuma bataci gaba da tafiya ba.
Salman kuwa juyowa yayi ya zuba musu ido.
Kauda kansa gefe yayi lokacin daya kara taku ɗaya ya iso kusa da Jannart ɗin.
Ƙara matsowa yayi kusa da ita yana mai ware alkyabbar.
Kanshi ya ɗan ronkofar cikin yamutsa fuska yace.
“Duk wata Macen da tasan ciwon kanta, bata yawo a haka kamar yanda ke kike yi, sannan mata da yawa suna sirranta kansu, amma ke kina bayyana kazantarki in kika sani nayi amai bazan yafeba.”
Cike da mamaki ta ɗan juyo yana kallonshi.
Hakan ya zama kamar irin hirar masoyane irin ana kallon juna nan.
Wani saurayi ne dake can ta bayane yana kallonsu ta cikin raga,
Ya zaro wayarsa da sauri ya fara ɗaukar su hoto, domin ya gano ƙanwar Junaidu ce.
Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara harara ya watsa mata tare da cewa.
"Mitssssss Ni ki dena kallona ko in tsokale idanun".
Ya fad’i maganar yana me zagayeta tare da dago alkyabban ya d’aura mata akan K...!
Fawal beauty parlor sunai muku albashir da bude gidan Mata wato kigyara da kanki👩🏻🦰 da cewa suna gabatar da aiki na zamani kamar su gyaran jiki, spa kenan gyaran fuska wato facial,gyaran Kai, hair style , gyaran kafa pedicure,gyaran hannaye, manicure kitso,lalle ja da bakki,ba'a barsu abayaba suna saida kayan gyaran aure, turaruka,man shafawa, suna kwalliya wato makeup,turaren wuta, humrah,kulaccham dama abunda Baku sanshiba wato maida tsohuwa yarinya akankanin lokaci😄iya kudinka iya shagalinka💃kudai ku hanzarta zuwa ga wannan gida na mata zallah (FAWaL BEAUTY PARLOR)
Address: Main gate na fire service jimeta, opp sixty plaza.
kada kubari abaku labari😍 munai muku maraba a koda yaushe Mata yan kwalisa mace sai da gyara , yar uwa bora ba sunanki kizama mowar mai🏨 da taimakon FAWAL BEAUTY PARLOR 👩🏻🦰da kudinki qalilan kifita sab abunki ki baza kamci mai kama jiki.
Gamai buka contact CEO FAWaL BEAUTY PARLOR kan 09033901035 or 08078809930 sai kunzo, our time services from 8:am to 7pm, Monday to Saturday/ Sunday 10am to 6pm🪞🎁🛒🛍️🤝🏻
*By*
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*TUBALI*
PAGE 12
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
*FREE PAGE ne*
*Littafin TUBALI na kuɗine special Group 1k ƙaramin group 500 kacal 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU,sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276. Ko kuma katin MTN*
Fawal beauty parlor sunai muku albashir da bude gidan Mata wato kigyara da kanki👩🏻🦰 da cewa suna gabatar da aiki na zamani kamar su gyaran jiki, spa kenan gyaran fuska wato facial,gyaran Kai, hair style , gyaran kafa pedicure,gyaran hannaye, manicure kitso,lalle ja da bakki,ba'a barsu abayaba suna saida kayan gyaran aure, turaruka,man shafawa, suna kwalliya wato makeup,turaren wuta, humrah,kulaccham dama abunda Baku sanshiba wato maida tsohuwa yarinya akankanin lokaci😄iya kudinka iya shagalinka💃kudai ku hanzarta zuwa ga wannan gida na mata zallah (FAWaL BEAUTY PARLOR)
Address: Main gate na fire service jimeta, opp sixty plaza.
kada kubari abaku labari😍 munai muku maraba a koda yaushe Mata yan kwalisa mace sai da gyara , yar uwa bora ba sunanki kizama mowar mai🏨 da taimakon FAWAL BEAUTY PARLOR 👩🏻🦰da kudinki qalilan kifita sab abunki ki baza kamci mai kama jiki.
Gamai buka contact CEO FAWaL BEAUTY PARLOR kan 09033901035 or 08078809930 sai kunzo, our time services from 8:am to 7pm, Monday to Saturday/ Sunday 10am to 6pm🪞🎁🛒🛍️🤝🏻
Kafad’anta wanda ya sauk’o ya rufe bayanta.
Batare kuma daya sake cewa komai ba, ya juya fuskarsar nan amurtuk’e.
Bottle water da kuma phone d’insa ya d’auka, kana ya zo ya wuce ta gefenta.
Itakuwa Jannart Idanunta ta rumtse da k’arfi, tare dasa hakwaranta ahankali ta cije lips d’inta.
“Duk wata macen da tasan ciwon kanta, bata yawo ahaka kamar yanda ke kikeyi, sannan mata da yawa suna sirrranta kansu, amma ke kina bayyana k’azantarki.”
Ta maimaita maganar daya fad’a mata d’in, wanda yasa tajin zafi har acikin zuciyarta, cikin kuma k’unan rai da b’acin ran kalaman nasa da wata iriyar fitinenneyar kunya mai masifar kashe ido da jiki tace.
“Waye shi da har yake fad’amin irin way’annan bak’ak’en maganganun, meya gani ajikina haka? Sannan akan me zai rufamin wannan abunnasa me shegen mayataccen k’amshi?.”
Ta fad’i maganar tana me d’an zame alkyabba’n ajikinta, dare da juya bayanta ta kalli jikinta, saboda tanason sanin mai ya gani ajikinta da har zai fada mata irin wannan maganan.
Karab kuwa Idanunta suka sauka akan jinin, dake jikin farin wandon ta, wanda da alama kuma daga jikinta jinin ya fito.
Idanunta tad’an zazzaro waje cike da mamaki da wata sabuwar kunya tace.
“What period dina kuma? Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un Period at this time, Oh My God!!”
Ta fad’a da d’an k’arfi, cikin kuma muryar dake bayyana tsananin takaicinta, saboda Sam bata tab’a tunanin period din nata zaizo a irin lokacin ba, kasancewar tasan da sauran lokacin daya rage masa, har na tsawon kwana uku kafun yazo.
“But amma why yazo yanzu? Meyasa Meyasa?”
Tayiwa kanta tambayar tana me b’ata fuska, domin sam bataji dadin abunba, cikin sauri kuma taja alkyabban daya rufa mata din ta sake rufe jikinta.
Lokaci d’aya kuma taji wani irin matsanancin kunya, da takaicin kanta na taso mata, duk da kuwa tasan cewar ba laifinta bane, period dinne ya sanja time wanda ko wacce mace kan iya fuskantar hakan musamman in tashin hankali da tsinkewar zuciya ya riski mutum, amma tayi matuk’ar takaicin ganin jinin period dinta da wani da bata sani ba yayi.
Tabbas taji kunya yanzu da wani idon zata sake kallonshi? kuma shi dinma ayanzu wani irin kallo zainayi mata karo na forko a rayuwarta da taji haushin irin shigar da takeyi.
“Wata macen da batasan ciwon kanta ba, bata iya ankilta kantaba.”
Zuciyarta ta bata amsa atake.
Idanunta ta rumtse cike da takaici.
Dai-dai lokacin kuwa Salman Ya ware idanunshi a kansu tare da dawo da kallonsa gareta.
Fuskarsa dauke da d’an mamaki yace.
“Ha’a Jannart lafiya kuwa kizo mutafi mana..”
Sauran maganar tasance ta mak’ale, alokaci da yaga jikin Jannart din lullub’e da Al'kyabban, da dazu ya ganta agefen mutumin da har yanzu baisan sunanshi ba.
Jannart kuwa fuska tad’an marairaice, kana cikin sanyin jiki ta soma takowa zuwa inda Salman din ke tsaye.
“Jannart wannan Al'kyabban fa? Kin sanshi ne?”.
Salman din ya tambaya, saboda yayi mamakin ganin ya sawa Jannart din da al'kyabban k’warai.
“Shi ne ya bani.”
Jannart din ta fad’a kaitsaye, bisa kuma sanin rashin dacewar Salman din yasan gaskiya abinda yasa yasa mata, shi yasa ta fad’a masa hakan, batare kuma da ta bada wata kofar da Salman din, zaiyi mata wata tambayar ba ta soma tafiya.
Salman kuwa idanunsa ya zuba mata, yana mai Kallon yanda al'kyabban tayi mata matuk’ar kyau duk da tayi mata yawa, saidai kuma Jin tace wancan mutumin ne ya bata, yasa shi jin babu dadi acikin zuciyarsa.
Saidai kuma bashi da ikon bayyana hakan.
Ab’angaren Dr. Rayyern kuwa Koda ya fito daga wajen wasan, kaitsaye Inda motarsa ke fake ya nufa.
idanun y’an tsirarun mutanen dake wajen ke kansa, duk da cewar kuwa basusan shi din asalin waye bane, amma kallo daya zakayi mishi kafahimci cewa mutum ne mai zarra.
Baya ga haka kuma ga tarin baiwar kyau da Allah Yayi mishi.
Tun kafun ya karasa isowa Parking lot din wajen kuwa, Hadi driver’nsa ya fito tare da bud’e masa k’ofar motar.
Yana shiga kuwa driver’n ya rufe k’ofar, tare da zagayawa cikin sauri ya tada motar.
Suna ficewa daga Parking lot din kuwa, su Jannart na isowa.
Nanfa kallo kuma ya dawo kan Jannart, domin al'kyabban dake jikin nata ya k’ara bayyana asalin kyau da kuma kawata shigar dake jikinta da jawo hankalin mutanen dake wurin kanta.
Murfin motar Salman din ta bud’e, tare da zagayawa gidan baya ta zauna, wanda tayi hakanne kuma, saboda idan sunzo shiga cikin gidan tv’n nasu, kada masu tsaronta su ganta, ko kuma wani wanda yasanta .
Salman ma shiga cikin motar yayi, tare da yiwa motar keyi suka fice daga cikin wajen wasan gaba d’aya.
Jin sun hau titi ne kuma yasa ta lumshe Idanunta, tare da sauke wata irin ajiyar zuciya mai karfi.
Lallai ayau din tana cikin tarin damuwa tsananin kunya da kuma takaicin kanta da kanta.
Yayinda acikin zuciyarta kuwa take fatan