Showing 99001 words to 102000 words out of 132995 words

Chapter 34 - TUBALI Book 1 Complete Document by GARKUWA

22 Aug 2025

133

magana amma kuma yau gashi wata tasashi yayi ta magantuwa.


Da kai kawai Rayyern din ya amsa masa, batare daya zauna acikinsu ba kuma kaitsaye ya wuce part d’insa.


Wanka yayi tare da dauro alwalan sallan magriba, bayan ya kimtsa kansa acikin wasu kaya marar nauyi ne kuma, ya fito inda dukansu suka had’a hanya wajen zuwa masallaci.


Koda sukaje masallacin kuwa kamar Koda yaushe basu dawo ba saida aka Sallame sallan Isha.


Suna dawowa gidan kuwa suka samu Mamy ta had’e musu lafiyayyen dinner, hakan yasa duk suka k’arasa kan dining table din suka zazzauna.


Yau din kuma Riyyam-nsra ne da kansa ya amshi Mamy wajen yin saving dinsu, shida kansa ya zubawa kowa abincin banda Abba da Mamy ta zuba mishi nashi, sannan da kansa ya had’awa Hamma Rayyern din tea.


Bayan ya kammala had’a musu ne kuma, kowa ya soma cin abincinsa, anutse Abba ya d’ago da kansa ya kalli Rayyern cikin jinjina da kuma ya bawa yace.


“Tabbas hirar da akayi da kai yau, tayi armashi da kuma ma’ana, sannan shawarwarin daka bayar shawara ne masu kyau, gaskiya na jinjina maka,”.
Sai kuma ya ɗan tsagaita kana ya ɗan kalleshi tare daci gaba da cewa. “Amma da kashawarce ni kafun hakan, To fa da bazakaje ba.”


Zazzafan tea din dake bakinsa ya had’iya, kana cikin yin kasa dakai yace.


“Kayi hakuri Abba nima banaje Dan son raina bane, naje ne kawai saboda nayi musu alk’awari, sannan banason wanda aka bawa kwangilar nema na din ya rasa aikinsa, kamar yanda manyansa suka bashi zab’i.”


Kai Abban ya jinjina, batare kuma daya ja zancen yayi tsawo ba yace.


“Shikenan To Rayyern Allah ya taimaka ya tsare min kai.”


Da Ameen duk suka amsa.


Bayan sun kammala cin abincinne kuma, kaitsaye Rayyern din ya wuce daki’n sa.


Yayinda Ramadan da Riyyam kuwa suka dawo Cikin falon suka ci gaba da hirararsu, daga karshe ma game suka had’a, suka soma yi.


Ganin hakanne kuma yasa Abba da Mamy wucewa sashinsu.


Rayyern kuwa yana shiga dakinnasa kwanciya yayi, Cikin mintuna kad’an bacci yayi nasaran daukarsa.


Acan falon kasa kuwa Ramadan da Riyyam, duk kowannensu saman kujera ya d’ale ya kwanta, su kansu ba zasu iya sanin tayaya nema bacci ya kwashesu ba, kowannensu da abun buga game din ahannunsa, haka sukayi bacci kasancewar dare ya nisa.


A sashin Jannart kuwa yau tun 9 tayi baccinta mai cike da nutsuwa, Yayinda takejin zuciyarta wasai babu sauran wani fargaba.




Washegari.


Friday.


Tun tashinsa karfe 7 ya gama shirya kansa, saidai shigarsa ta yaudin ta banbanta dana kullum.


saboda wani riga da wando mai Taushin gaske ya saka ajikinsa, sabanin suit daya saba sakawa akowacce rana.


Sosai kayan Yayi masa kyau, musamman daya daura boyfriend jacket mai kyau akan kayan.
Wasu bakaken shoe masu tsada da watch ya daura a tsintsiyar hannunsa .


Bayan ya gama kimtsa kannasa ne kuma, ya dauki wayarsa tare da duba sakonnin da suke ta shigo masa ta Twitter, saboda yanda duniyat Twitter din ta Dinke da hotunansa, gaba daya shi kawai ake watsawa, da kuma bayani akan hirar da akayi dashi.


Kashe data dinnasa yayi, tare da juyawa ya nufi k’asa kaitsaye.


Anan cikin falon ya samu su Abba, harma da Riyyam nsra wanda yake ta hamma da alama bacci bai ishesa ba.


Dan Koda asuba ma Abba ne daya fito yagansu kwance afalo, shi ya tashesu tare da saka su agaba suka wuce masallaci.


Karasowa yayi ya zauna akan dining table din, bayan kuma Mom tayi saving dinsa ne, ya soma cin abincin atsanake, saidai kuma bai wani ci sosai ba, ya mik’e tsaye.


Yaudin ma dai atare suka fita shida Ramadan, saidai kuma Riyyam-nsra ya dage kan cewar, tare zasu tafi Hospital shida Ramadan.
Hakan kuwa akayi inda Ramadan din ya dauki Riyyam din suka wuce Hospital, shikuwa Rayyern dama yau ba Hospital din zaije kaitsaye ba.


Bayan anwangale musu gate din gidan sun fito da tsalatsalan motocinsu ne, kaitsaye su Riyyam suka wuce Hospital, shikuwa Company’n sa ya nufa.


Koda ya isa company din kuwa ya samu, ma aikata madasa in juna suna ta aikinsu, Domin yau din injunan da zasuna had’a kwalaye da buhuna ake kafawa amazauninsu.


Sosai ya jinjina kansa ganin yanda aikin nasu ke tafiya yanda ya kamata.


Kasancewar kuma akwai aikin da zaiyi ne yasa, kaitsaye ya haura sama inda Office d’insa yake.


Acan gida kuwa Baba Maud’o na zaune yaji karan horn din mota, atunaninsa ko su Rayyern dinne suka dawo, hakan yasa ya wangale gate din gidan.


Barrister Kabir kuwa dake cikin motar, kaitsaye ya shigo da motar tasa cikin gidan.


Bayan ya gama dai-dai-ta parking din motar tasa ne kuma, ya bud’e ya fito, saidai kuma ayau din bashi kad’ai yazo ba, atare dashi akwai Dr.Sajo.


Karasowa wajen Baba Maud’on sukayi tare da bashi hannu sukayi musabaha.


Baba Maud’o kuwa fuska asake ya amsa musu, sannan kuma da kansa yayi musu iso zuwa cikin gidan, har cikin babban falon kuma ya kaisu.


Ganinsu ne kuma yasa Abba fadada fara’arsa, tare da sawa Mamy tayi musu tarba maikyau.


Bayan sun gaggaisa ne kuma, Barrister Kabir ya gyara zama, tare da Kallon Abban ya gabatar masa da Dr. Sajo.


Haka dai suka Dan tattauna, agame da abunda suke shirin had’awa.
Bayan kuma sunyi tattaunawa mai tsawo ne, suka yanke shawara akan cewar yau Idan an sauk’o daga sallan Jumm’a za’a daura auren.


Da wannan batun sukayi sallama.


Inda Abban ya rakosu har waje, bayan sun tafi ne kuma ya zauna anan awajen Baba Maud’o suka d’an soma tattauna wasu batu.




Acan Office din Rayyern kuwa. Ganin 11:30 am ne yasa shi mik’ewa. Tare da barin duk wani abu da yakeyi.


Kaitsaye kasa ya sauko, saboda yanason sake komawa gida saboda yin shirin zuwa masallaci.


Koda ya shiga motar tasa kuwa cewa Hadi yayi su wuce gida.


Take kuwa kaitsaye suka nufo gida.




Koda ya dawo gidan, wanka ya sakeyi inda ya shirya kansa cikin riga da wando da kuma babbar riga, ta hadaddiyar getzner’n da ak’alla kudinta ya haura sama da 100k, sosai kayan sukayi masa kyau kasan cewar kalarsu lemon green ne kana zaren da aka watsawa garen su kuma shudi ne da fari da baƙi sosai sukayi mishi kyau, musamman daya kafa hulan zanna bukar blue color Kansa, ga kuma wani tsadadden takalmin toms suma blue da agogo daya saka, Tabbas yayi kyau kwarai.
Domin shigar tasa bawai gama gari bace, shigace ta musamman, wacce ta kara bayyana kyau da kwarjininsa.


Bayan ya gama kimtsawa ne kuma, ya feshe jikinsa da turare tare da sauk’owa k’asa, saboda jiyo hayaniyar Ramadan da kuma Riyyam da yayi, wanda suma sun shirya ne tsab, Cikin sabin getzners dinsu, masu kyau.


Kallonsu Riyyam din kawai yayi kana a takaice yace.
“Ka kwaso kayanka ka dawo nan, ka dena kwana a hotel”.
Ya ƙare mgnar cikin bada umarni.
Cikin yanayin ba zata jin mgnar Riyyam-nsra ya kalleshi da alamun zaiyi mgn sai kuma yayi shiru.
Ganin tuni ya fice batare kuma daya ƙara ce musu komai ba.
kaitsaye ya fice daga cikin falon.
cikin sauri-sauri kuma ya nufi motarsa saboda bayason rasa hud’uba.


Bayan ya fita daga gidanne kuma suma suka fito inda suka shiga motar Ramadan daketa murna da farin cikin mgnar Hamma Rayyern ɗin nasu.
kaitsaye masallacin Alfruq’an suma suka wuce.


Acan gidansu Jannart kuwa hakanan tun tashinta yau din takejin zuciyarta na yawan tsinkewa, ga kuma wani irin faduwar gaba da takeji akai akai.


Sai-dai rashin sanin takamaimai abun yi, yasa ta fara ambaton sunan Allah a cikin zuciyarta.


Barrister Kabir kuwa, bayan yayi shirin zuwa masallaci, yau din ko motarsa bai dauka ba, da kafansa ya fito inda ya tako har bakin titi, taxi ya tara, tare kuma da yiwa mai taxi din bayanin inda zai kaishi.


Wanda kuma bako Ina bane face masallacin dake gefen gidan Dr. Sajo.


Koda mai taxi din ya saukesa a masallacin, kaitsaye wajen Dr. Sajo ya nufa, atare sukayi sallan Jumma’a, bayan sun idar da sallan ne kuma, Dr. Sajo ya fito musu da mota.


Kaitsaye suka nufi unguwar Nassarawa GRA.


Yayinda acan masallacin alfurq’an kuwa, bayan an sallame sallan jumma’an, Ramadan da Riyyam-nsra suka sulale, kaitsaye basu zame ko inaba kuwa sai kasuwa, saboda kafun su fita Abban ya basu kudi yace su sayo masa huhun goro da kuma katton katton na mintuna.


Sudai haka suka je suka sayo batare da sanin na meye bane.


Koda suka dawo gida, anan cikin falon Abban suka jibge huhun goron da kuma mintunan da suka sayo.


Dawowarsu kuwa yayi dai-dai da isowan su Barrister Kabir da kuma Dr. Sajo.


Inda Abba da kansa yazo yayi musu iso zuwa babban falon k’asa.
Bayan sun zazzauna ne kuma ya fita ya kira Baba Maud’o, inda yace.


“Baba Maud’o ka shigo, yau abun na musamman za’ayi acikin gidannan, Insha Allah yanzu za’a daura auren Rayyern.”


Idanu Baba Maud’o ya d’an fitar, lokaci daya kuma yaji wani irin farinciki ya lullub’e sa, wanda hakan yasa Cikin matuk’ar jin dadi yace.


“Masha Allah lokaci yayi kenan, yau dai Ranar Rayyernu ta tsaya, To Allah yasa hakan shine mafi alkhairi.”
Da “Ameen.” Abba ya amsa.


Dai-dai lokacin kuma suka shigo cikin falon shida Baba Maud’o.


Acan waje kuwa yanzu motar Rayyern din ke isowa, Jin sunyi horn ba a bud’e musu bane kuma, yasa Hadi fitowa da kansa ya bud’e musu gate din suka shiga ciki.


Da mamaki Rayyern yake Kallon bakuwar motar dake fake afarfajiar gidan nasu, yayinda daga gefenta kuma motar Usman PA ne wanda yazo babu jimawa, kuma shima ya shigo yana can cikin falon Abban.


Ahankali ya bud’e murfin motar ya fito, Yana fitowa dinne kuma, Abba ma ya fito daga cikin falo, Kallon Rayyern din yayi, lokaci guda kuma ya hade fuskarsa, cikin tsare gida, ta yanda yasan Rayyern din bazai samu daman tambayarsa wani abuba yace.


“Hadi ka shigo daga ciki, kaima Rayyern ka biyoni.”


To Hadi yace tare da rufawa Abban baya, shima Rayyern din haka cikin daurewar Kai yabi bayan Abban nasa.


Suna shiga cikin falon kuwa, yaji zuciyarsa tayi wani irin harbawa, saboda yanda yaga mutane atare.


Daya bayan daya yake bin kowannesu da kallo, Koda ya sauke idanunsa akan Barrister Kabir, ji yayi wani irin abu ya tsarga mai.


“Oh My God meye kuma wannan mutumin ya sake zuwa yi agidan mu? Waishi bazai tab’a fahimta bane, nace masa ban shiryawa auren yartasa ba banasonta wai ko ana dole ne ai gaggawa dai bata da kyau.”


Yayi maganan azuciyarsa, tare da yin kicin kicin da fuskarsa.


Gudun kada yaji wata magana ta taso ne kuma yasa, cikin nitsuwa.
Ya ɗan motso ya gaidasu a mutunce.
Kana sauri-sauri ya soma kokarin haurawa sama.


“Rayyern zo zauna.”


Muryar Abba ta katse shi daga tafiyan da yakeyi, wanda kuma hakan yasa dolensa ya dawo cikin falon.


Zama yayi akusa da Abban nasa, tare da dago kansa ahankali yace.


“Abba Lafiya kuwa, meke faruwa?”


“Lafiya kalau sai alkhairi.”


Abban ya fad’a yana me d’an gyara zamansa, tare da fuskantar Baba Maud’o, cikin mutumtawa Hadi da karramawa yace.


“To Baba Maud’o kaine babba amatsayinka na babba kuma Kai ya kamata ka fada mana wanda zai zama waliyin Rayyern.”


Murmushi Baba Maud’o yayi, cikin muryar tausasawa yace.


“Kai ne zaka waliyancesa Alhaji, ai babu damuwa Dan uba ya waliyanci dansa.”


Baki Abban ya bud’e daniyar cewa wani abu, amma kuma saiya fasa saboda wani tunani daya fado cikin zuciyarsa.


Ajiyar zuciya yadan sauke tare da gyara zamansa yace .
“To shikenan ba matsala, wanene waliyin amarya?.”


“Gashi nan.”
Barrister Kabir ya fad’a yana mai nuna Dr Sajo, yana me fuskantar sauran mutanen dake cikin falon kuma da kyau.


Kai Abba yajinjina tare da juyawa ya kalli Rayyern.


Cikin yanayin dake nuna babu alaman wasa acikin magana ko fuskarsa yace.


“Rayyern kawo sadaki.”


Wani irin karya wuya Rayyern yayi, lokaci daya kuma ya narke fuska cike da tsananin mamaki yace.


“Sadaki kuma Abba? Sadakin menene, nifa...”


Ganin wani kallon da Abban ya watsa masa ne yasa shi yin shiru, tare da sunkuyar da kansa k’asa, asanyaye yace.


“Abba yanzu ba kudi ajikina, a daga auren sai na samu kudin.”
Cike da mmkin mgnar tasa Abba yace.
“Eh munsani fa baka da kuɗi.
Amman kada ka damu ko transfer ne kayi mana.”


Saurin dagowa yayi ya kalli Abban nasa, lokaci daya kuma ya kwab’e fuska, Murya araunace yace.


“Ni wayata ba charge, amma muje sama da Ramadan dakina in bashi kuɗin ya kawo muku.”
Ya ƙare mgnar yana yunƙurin tashi.
Alamun guduwa da yake son yi.
Murmushi ɓoye Abba yayi tare da danne kafaɗarsa kana yace.
“Zauna”.
Cikin kwaɓe fuska yace.
“Abba Kudin zan bashi”.


Ya k’are maganar tamkar zai zubda hawaye.
Cikin tsare fuska yace.
“Ina kuɗin suke?”.
A sanyaye yace.
“Cikin bed side drower”.


Kallon Ramadan Abba yayi kana cikin, bada umarni yace.


“Ramadan jeka ɗebo kudin koma nawane kawosu.”


“To“ Ramadan din yace, tare da mikewa cikin sauri ya haura sama.


Inda Rayyern kuwa ya bishi da Harara kasa kasa.


Mintuna biyu kacal kuma saiga Ramadan ya dawo da bandir din yan dubu dubu, na dubu dari biyu, Dan kowani bandir dubu dari ne.


Mik’awa Abban nasu yayi.
Tare da komawa ya zauna.


Abba kuwa duka dubu dari biyun din ya mik’awa, Dr Sajo tare da cewa.


“Ni Alhaji Bashir Muhammad ina nemawa, d’ana Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara auren yar wajenka Jannart Idi Sale Dakata, akan sadaki naira dubu dari biyu.”


Karb’an kudin Dr Sajo yayi, tare da gyara zamansa cikin mutumtawa yace.


“Ni Dr Sajo Umar, na bawa danka Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara auren yata Jannart Abdulkarim Saleh Dakata akan sadaki naira dubu d’ari biyu.”
Daga nan kuma sukayi duk abinda ya dace na tsarin daurin aure bisa koyarwar musulunci.


“Alhamdulillah! Alhamdoulillah!! AURE Ya D’auru jama’a muyi salati goma ga Annabi.”


Cewar Baba Maud’o, cikin tsananin farinciki.


Adai-dai lokacin kuwa Rayyern ya rumtse idanunsa da karfi, tare da dafe dai-dai saitin zuciyarsa cikin rudu hadi da bugawar zuciya Ya......!










*Dan Allah ki saya ki karanta littafina na kuɗine special Group 1k ƙaramin group 500 yawan posting ne banbancinsu, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, in ba halin turawa ta account ki sayi katin MTN ki kofi number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp.*












By










*GARKUWAR FULANI*








Danne jajayen labb’ansa.
“Innalillah wa innailaihi rajiun.
Oh ni Rayyern wannan wacce irin rayuwace? Wannan wanne irin ƙaddara ne mai tafe da jarababbe .ayataccen kuma lik’akk’en aure ne, shikenan dai ni.
Bani da freedom din kaina, dolen-dole sai an sako min wata acikin rayuwata!!!.”
Yayi maganar azuciyarsa, yana mejin tamkar ya mike tsaye, yace sam shi baiyarda da wannan auren ba.


Su Abba, Ramadan, da kuma Riyyam-nsra, kuwa gaba d’aya farinciki ne ya lullub’e zuciyoyinsu, more especially Ramadan da ayanzu yake Ganin shima ya samu chance na auren Rayhanna’n sa.


Baya ga haka kuma abun farinciki ne awajensu ace yau Hamma Rayyern din nasu yayi aure.


Barrister Kabir kuwa idanunsa ya lumshe tare da soma sauke ajiyar zuciya akai akai, Lallai yasan cewa yau din ya bawa Jannart Garkuwa, da kuma mafakar da babu wani mahaluki daya isa ketare ta, Allah Sarki Jannart marainiyar Allah, akullum Allah shike zama gatanta.


Dr. Sajo ne ya gyara zama, tare da somayin addu’a, bayan ya kammala addu’an ne kuma yace.


“Ina rokon Allah madaukakin sarki daya sanya al'barka da kuma al'khairi mai tarin yawa acikin wannan auren, Allah ya kade duk wata fitina da zata kunno Kai, Kai kuma Rayyern Allah Ubangiji ya baka ikon sauke nauyi da kuma hakkin dake kanka.”


Da “Ameen.” Duk suka amsa amma banda Rayyern wanda yakejin kamar yasa musu kuka, Dan takaici, Yayinda acikin zuciyarsa kuwa yace.


“Ni babu wani nauyi daya hau kaina.”


Barrister Kabir ne kuma ya d’an kallesu, kana. Cikin taushin murya yace.


“Nagode Kwarai da irin karamcin da kukayi mana, kun amince damu, sannan kuma kun karb’i auren y’armu da daraja, nagode Kwarai abu na karshe kuma da zan rokeku dukanku shine, Dan Allah wannan magana ta daurin auren ya zama sirri atsakaninmu, Domin nima dole ce ta sani yin hakan.”


Kai duk suka jinjina, Yayinda Abba Kuwa ya gyara zamansa tare da fuskantar Barrister Kabir din yace.


“Karka damu Barrister, nayi maka al'k’awarin bayan mu babu wani wanda zaisan da batun auren, haka kuma babu wanda zaisan da zaman Jannart acikin gidannan.”


Kai Barrister’n ya jinjina cike da gamsuwa, Yayinda Abban kuwa ya dawo da kallonsa gasu Ramadan din, cikin tsare gida yace.


“Dukanku ku tashi ku bamu waje.”


Aikuwa Rayyern kam dama kaman jiran hakan yakeyi, Domin bakin Abban ko gama rufewa baiyi ba ya mik’e zumbur, Da sauri Abba ya kalleshi har ya buɗe baki zaice banda kai.
Sai kuma kawai yayi shiru ya bishi da ido har ya haura sama.


Ramadan kuwa hannun Riyyam-nsra ya kama, suka nufi side d’insa, Tabbas suna cikin farinciki, amma daga wani b’angare tsananin mamakin yanda auren Hamman nasu ya kasance sukeyi, auren bazata, auren da ba tsammani kuma auren sirri auren shaidu goma.


Suna shiga cikin side din Ramadan din ne kuma, Riyyam-nsra ya zaro wayarsa, Yayinda shi kuwa Ramadan kaitsaye ya wuce toilet.


Riyyam kuwa numbern Mammynsa ya kira, bugu biyu kuwa ta d’auka, bayan sun gaisa ne kuma Riyyam din, ya dan jujjuya ya kalli kofar shigowa data Bathroom, tare da karyar da wuyansa gefe, bakinsa cike da tarin maganganu kala-kala yace.


“Mammy kinsan me yake faruwa?”.
Da sauri Mammy ta jujjuya mishi kai tare da cewa.
“A'a sai ka faɗa!”.
Numfashi ya ɗan fesar kana a hankali yace.
“Yau ɗinnan a yanzun nan aka d’aurawa Hamma Rayyern aure.”


Idanu Mammyn ta d’an zaro cike da tarin mamaki, tace.


“Aure kuma Riyyam, wanne irin aure haka?.”
Gyara zamanshi yayi tare da sauke nannauyan numfashin yace.
“Aure dai da kika sani Mammy irin dai wanda ake daurwa tsakanin mata da miji”.
Lumshe ido tayi cike da al'hini tace.
“Ikon Allah”.
Shi kuwa Riyyam-nsra ci gaba da cewa yayi.
“Mammy kinsan meye ma kuwa? acikin falo fa aka daura auren, kuma kwata-kwata bamu wuce mu goma ba, wa y’anda aka daura auren agabanmu”.
Da sauri tace.
“Toh wannan wanne irin aurene meke ɓoye a ƙasa, tabbas akwai manufar auren!”.
Da sauri yace.
“Uhumm ai baki sani, bama Mammy Hamma Rayyern fa bayason auren wallahi Mammy, karki ga yanda ya had’e fuska, kamar zai daki babu.
Domin shi kanshi baisan cewa za’a d’aura masa aure yau ba.”


Ajiyar zuciya Mammy’n ta sauke, cikin yanayin mamaki kuma tace.


“To Riyyam Allah Ubangiji yasan hakan shine mafi al'khairi, ya kuma basu zaman lafiya

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login