Showing 111001 words to 114000 words out of 132995 words
gidanmu gidan duniyar leshi, atamfa shadda, material da sauransu. Sai kun zo. Muna maraba da kai a kowanne gari kake.
GARKUWA COLLECTION! Siyan nagari mayar da kudi gida!
By
*GARKUWAR FULANI*
https://chat.whatsapp.com/IM6PrgYNy9s6lP0aXmBkaN
Samun zafafan saukakan kayayyakin zamani na mata tun daga kan leshi, shadda, atamfa, material, jaka da takalmi, hijab..... da dai sauransu akan farashi mai sauki da rahusa sai a kamfanin Garkuwa collection. Bama wannan kadai ba akwai kayan order da muke yi shi ma duk a cikin rahusan da saukin kudi. Ba mu tsaya nan ba ina kuke yan kasar *NIGER* albishirinku kuma kuna iya siyan kayanmu ya isa gareku cikin aminci ba tare da bata lokaci ba. maza yan’uwa ku garzayo ku gane wa kanku wannan rahusar da kuke jin labari. Kayanmu ko a kasuwa ba zaka samu farashinsu ba. gidanmu gidan duniyar leshi, atamfa shadda, material da sauransu. Sai kun zo. Muna maraba da kai a kowanne gari kake.
GARKUWA COLLECTION! Siyan nagari mayar da kudi gida!
Mamy ta kira sunansa da d’an k’arfi, wanda hakan yasa shi dawowa daga duniyar tunanin daya fad’a.
D’ago da kansa yayi Ahankali ya kalli Mamy’n, da ta tsare shi da ido.
“Mamy yaushe kika shigo?”
Ya tambaya da dan mamaki akan fuskarsa.
“Tayaya zaka san lokacin dana shigo, bayan kanason takurawa rayuwarka, dason sawa kanka damuwa akan abunda kasan ya zama wajibi akanka.”
Mamyn ta fad’a.
Longoɓar da kansa yayi, kamar zaice wani abu kuma saiyayi shiru.
Mamy kuwa Ajiyar zuciya ta sauk’e, had’e da cewa.
“Idan akwai magananin zazzab’i awajenka, ko paracetamol ne ka bani, Jannart ce jikinta duk ya d’au zafi.”
Jin abunda Mamyn ta fad’a ne kuma yasashi d’ago kansa ahankali ya kalleta, fuska ya kwab’e kana cikin muryarsa mai kama da shagwab’a yace.
“Ni kam Mamy bani da wani magannin zazzab’i.”
Harara Mamyn ta watsa mishi tare da gyara tsayuwarta tace.
“Taya zaka cemin babu bayan bakaje ka duba ba.”
Sake langwabar da kansa yayi, still yace.
“Mamy nasan fa babunne, kuma yanzu ni bana ajiye magani, saidai ko ki tambayi Ramadan.”
“Katashi Kai kaje ka karb’omin maganin awajen Ramadan.”
Mamyn ta fad’a adake.
Jin hakanne kuma yasa shi mik’ewa jiki asanyaye, ya nufi dakin su Ramadan.
Yana zuwa kuwa ya samu Ramadan da Riyyam-nsra kowannensu na rike da waya ahannu.
Ko Kallon kirki baiyi musu ba, ya tsaya tare da d’age kansa sama, kana yace.
“Ramadan bani paracetamol.”
Da mamaki Ramadan yake kallonsa, kamar zaiyi magana kuma saiya fasa, kaitsaye ya bud’e wani Dan box maganin zazzab’i ya ciro ya mik’awa Rayyern din.
Yana karb’a kuwa ya fice, inda ya samu Mamy abakin k’ofa ya mik’a mata.
Amsan maganin Mamy tayi, batare da tace masa komai ba kuma ta juya ta sauk’a k’asa.
Shikuwa d’akinsa ya koma, zuciyarsa cike da takaici.
Domin shi sai yanzu ne ma yakejin haushin yarinyar da aketa kira da Jannart din.
Mamy kuwa kaitsaye kitchine ta nufa, bayan ta d’auki abincinne kuma ta wuce sashin Jannart.
Jannart kuwa dai-dai lokacin ta fito daga wanka, bayan tayi wankanne kuma ta sake maida doguwar rigar da ta cire.
Tana tsaka da maida hijab dinta ne kuma, Mamy ta shigo hannunta dauke da cup da kuma plate din indomei.
Akan wani Dan stull Mamy ta ajiye cup da plate din, tare da duban Jannart din Cikin kulawa tace.
“Yauwa Jannart kinfito ko, ga abinci nan kici, sai kisha magani saboda naji jikinki akwai zafin zazzab’i.”
Kai Jannart din ta Dan sunkuyar kasa, kana aladabce tace.
“Mamy nakoshi.”
“A’a kam Jannart, saboda kefa na shiga kitchine na dafa abincin nan, saboda haka ki zauna kici, kada kiyimin gardama kinji, koso kikeyi na barki haka, Allah ya kama mu kefa amanace awajen mu, zo maza ki zauna kici.”
Mamyn ta fad’i haka cikin matukar kulawa.
Wanda hakanne kuma yasa Jannart din karasowa, ta zauna akan lallausan sofan dake malale agaban gadon.
Abincin Mamy ta ajiye mata, Ahankali kuma ta soma tsakuran abincin tana kaiwa bakinta.
Kasancewar kuma da gaske bata wani jin yunwa sosai ne, yasa bata wani ci abincin sosai ba, saidai tea din da Tasha har fiye da rabin kofin.
Dan matsar da plate din abincin tayi gefe, tare da yiwa Mamy alama akan ta koshi.
Hakanne ko yasa Mamy b’are maganin ta bata tasha.
“Ki kwanta to ki huta, Dan Allah karki sakeyin kuka kinji Jannart, kinga shine ya haddasa miki wannan zazzab’in.”
Mamy ta fadi haka tana me daukan plate da cup din abincin.
“To Mamy.” Jannart din ta fad’a, tana me mikewa tsaye ta haura saman gadon ta kwanta.
Murmushi Mamy tayi saboda a iya yaudin kawai ta yada da hankali,da kuma biyayyar da yarinyar take dashi.
Cikin kula tace.
“A'a Jannart tashi kiyi addu’a kinji, kada bacci ya daukeki batare da kinyi addu’a ba.”
Aikuwa da d’an hanzari Jannart din ta tashi zaune, hannayenta ta hade waje guda, falaq,suratul nass, da kuma suratul Iqlas, k’afa uku uku, kursiyu da amarasulu sai kuma Hasbiyallahu la’ilaha illahuwa, alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim, k’afa 7, sai kuma suratul Khafirun kafa uku shima.
Bayan ta shafa ne kuma ta koma ta kwanta.
Mamy kuwa cike da farincikin samun ya kuma surkuwa ta gari, ta ragewa Jannart gaba daya hasken wutan dake dakin.
Bayan sunyiwa juna saida safe ne kuma Mamyn ta juya ta fita.
Bayan ta maida plate and cup din kitchine ne kuma, kaitsaye Mamyn dakin Abba ta nufa.
Koda taje Zaune ta sameshi akan gado.
Zama ita dinma tayi agefensa, kana cikin tausasa murya tace.
“Tabbas Rayyern ya samu mata, yayi dace da yarinyar arziki mai ladabi da biyayya”.
Cikin jin daɗi Abba ya juyi ya fuskanceta yana mai jinjina kai alamun gamsuwa.
Ita kuwa Mamy cikin girmamawa tace.
“Toh amma Alhaji meyasa ka umarceni dana kaita wancan dakin, bayan ganan sashin Rayyern.”
Murmushi Abba yayi, tare da maida kallonsa gareta yace.
“Nace ki kaita wancan part dinne Saboda, sai anyi gyara a b’angaren Rayyern kafun ta koma can.
Kadafa ki manta fa amaryace, Koda cewar auren ba dan shiri bane, amma yana da kyau a inganta mata komai nata”.
Da sauri tace.
“Eh gsky hakane kam”.
Ɗan gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“Sannan kuma baki ga dan naki bahagon yaro bane, kwata-kwata na kasa gane inda ya dosa, Sam bai fahimci abunda muke nuna masa ba, atakaicema gani yake kamar takurasa mukeson yi.
Bayan haka kuma ganan Ramadan shima yana saman.
To dole yanzu zai dawo k’asa, kafun adai-dai-ta komai ta koma side din nasu.”
Kai Mamy ta jinjina cike da gamsuwa.
Kasancewar ta gaji ne kuma yasa ta zame ta kwanta gefensa.
Acan b’angaren Rayyern kuwa, akwance kawai yake amma duk zuciyarsa babu dadi.
Ak’alla saida ya kwashe sama da 50mn kafun bacci b’arawo ya iya satan shi.
Jannart kuwa tun fitan Mamy ta lumshe idanunta.
Yayinda tunani kala-kala ke yawo aciki kwakwalwarta, akaro na farko kenan tun tashinta izuwa yanzu, da zata kwana awani gida sab’anin nasu dan ko gidan Barrister Kabir Daddy bai taɓa barin ta ta kwana ba sai kuma asibiti.
Tunani ne fal zuciyarta, saidai kuma kamar yanda tayiwa Mamy al'ƙawari, batayi kuka ba, da taimakon maganin zazzabin da tasha ne kuma bacci ya dauketa.
Yayinda acan gidan Alhaji Idi Sale Dakata kuwa, kowa ya kwana sharbar bacci batare da tunanin Jannart bata cikin gidan ba, Domin wasu daga cikin mutanen gidan har da gwartin su, saidai banda Junaid Wanda ya taso sad’ab sad’ab ya nufi d’akin Jannart din, saboda gaba daya ya kasa bacci.
Daya rufe idanunsa Surar Jannart dinne keyi masa gizo, shiyasa yazo domin rage zafin abunda ke damunsa.
Koda ya karasa kofar dakin nata, kaitsaye ya tura kansa ciki.
Saidai kuma rashin ganinta da baiyi acikin dakinba, yasa shi cije labbansa, lokaci daya kuma ya raya cewar ko tana toilet Murmushin mugunta yayi, tare da nufan toilet din kaitsaye.
Tura kofar yayi batare daya jira komai ba kuma ya soma zare belt din wandonsa, saboda ya gama targetting yana ganinta zai Afka mata, amma kuma saidai meye?
Wayam haka yaga toilet din, ba alaman ma anshigesa tsawon sama da 1hour.
Tsuka yaja tare da fitowa, yana kwafa haka ya fice daga cikin dakin, cike da takaicin rasa damar da yayi.
Badan ransa yaso ba haka ya koma sashinsa ya kwanta a tunaninsa ko tana dakin Mom.
*Washegari*
8:00 am dai-dai Mom ta gama kammala musu breakfast, wanda kuma har zuwa tsawon wannan lokacin ba taga Jannart ta fito ba.
Hakanne kuwa yasa bayan ta gama setting dining table, kaitsaye tatafi izuwa dakin Jannart din.
Koda ta isa bakin kofar knocking ta fara yi, har na tsawon mintuna 2 kuwa bataji ko motsin za’a bud’e kofar ba, hakan yasa Ahankali ta tura kofar d’akin, tare da kutsa kanta ciki.
“Jannart! Jannart!!” Momyn ta kira sunan Jannart din, saboda rashin ganinta da tayi adakin.
Jin shiru ne kuma yasa Momyn juyawa ta fita, saboda atunaninta ko Jannart din tana cikin toilet ne.
Kaitsaye dining table ta dawo, tana zuwa kuwa, Daddy da Abdull suma suka fito suka zauna.
Momyn ce tayi saving dinsu, tana cikin saving dinnasu ne kuma, Junaid ya shigo cikin falon, yana fito, daga shi kuma sai t shirt da gajeren Wando.
K’arasowa dining table din yayi, batare daya gaisar da kowanne daga cikinsu ba, cikin iskancinsa irin na wasu masifaffun sojoji yace.
“Ina Jannart?”
D’agowa duk sukayi suka kalleshi.
Sanin halin rashin mutumcinsa ne kuma yasa Mom tace.
“Yanzu na dawo daga dakinta banganta ba, tun safe kuma bata sauko ba, amma Ina tunanin ko tana toilet ne.”
“Bawani bata gidan nanne ma gaba d’aya, y’ar iskar yarinya, jiya ma da dare ai naje dakinta amma bansa meta ba, wallahi Idan na kamata sainaci Uwarta.”
Baki Momy ta tab’e, tare da kallonsa cikin yanayin mamaki tace.
“To kai meya kaika dakinta da dare?.”
“Oho bansani ba, munafurci kawai.”
Junaid din ya fad’a kaitsaye, babu wani shakka ko shayi.
Duk da Abba yana jinsa kuwa, haka yayi shiru bai tanka masa ba, saima Kallon Momyn da yayi, yace.
“Kije ki duba toilet din, ko me ta keyi kice mata ta bari, injini tazo mu yi breakfast.”
“To.” Momyn tace, tare da juyawa tasake nufan dakin Jannart din.
Tana zuwa ta tura kofar, but still Jannart bata ciki, da d’an mamaki Momy ta karasa jikin kofar toilet din, tare da kasa kumnenta.
Waiko zataji karar ruwa, saidai bataji komai ba, hakan yasa Momyn ta tura kofar tana me kiran sunan Jannart.
Saidai meye, idanunta ba abunda suka gane mata, domin kuwa Jannart bata cikin toilet din.
Mamaki ne ya kama Momyn, saboda Sam bata taba tunanin Jannart bata cikin toilet din ba.
Juyawa tayi cikin sauri ya dawo falo.
“Alhaji Jannart fa batanan, na duba bata dakinta kuma bata bayan gida.”
Cak Alhaji Idi Sale Dakata yatsaida duk wani abu da yakeyi, cikin yanayin mamaki had’i da razana yace.
“Bangane mekike cewa ba, wannan wani irin maganar banza ce, tayaya zakice bata dakinta kuma bata bayan gida, wannan gashi anan dinma batanan, To ko tana dakinki ne?”
Kai Momy ta girgiza da sauri, tare da cewa.
“A'a wallahi bata dakina, tun Safe ma banga sauk’owarta ba, zaiyi wahala ace ma tana dakina.”
“Kije ki duba ta yanzu.”
Dadyn ya fada cikin bacin rai.
Hakan yasa da sauri Momyn ta juya zuwa dakinta, kamar yanda ta zata kuwa hakanne, domin Jannart bata cikin dakinta.
Dawowa falon ta sakeyi, tare da Kallon Daddyn tace.
“Alhaji Jannart fa bata dakina.”
Idanu Daddyn ya zazzaro waje, Abdull kuwa da mamamki yace.
“Ha’a To Ina Aunty Jannart ta shiga ita da yawo ma bayinsa takeyi ba, amma bari na duba compound ko Garden ko tafita shan iska.”
Yana gama fadin hakan ya mik’e ya fita.
Kaitsaye garden dinsu ya nufa amma baiganta ba, hakan yasa ya dawo, fuskarsa dauke da damuwa yace.
“Daddy banganta ba.”
Kwafa Junaid yayi, tare dasa hannayensa a aljihun wandonsa, cikin bakar muguntan dake cinsa yace.
“Nifa Tunjiya na fada muku banganta ba, maybe yawon iskancinta ma ta tafi, dama ai ta saba tafiya kwanan gida.
Rijiyace kowanni dan iska yana iya zuwa ya zira gugansa yaja ruwa son ransa.”
Idanu Momy ta rumtse saboda har acikin zuciyarta bataji dadin bakar maganar da Junaid din ya fada akan Jannart d’in ba.
Daddy kuwa Wayarsa ya zaro daga cikin aljihun rigarsa, tare da lalub’o numbern Jannart din ya danna mata kira.
The first time akace masa wayan nata, is switch off, da Mamaki Daddy ya sake dialing airtel number dinta, still switch off, wani irin bugawa yaji kirjinsa yayi, cikin sauri yace.
“Junaid je maza ka duba side dina, watakila ko taje gaisheni ne.”
Juyawa Junaid din yayi, Inda kaitsaye ya nufi side din Daddyn, Koda ya karasa baiganta ba, har cikin bedroom na Dad din ya shiga amma babu ko alamarta.
Dawowa yayi yana ta kwafa, yace baiganta ba.
Mik’ewa tsaye Daddy yayi, cikin tsananin tashin hankali ya nufi kofar fita daga falon, batare kuma daya lura ba har tuntub’e yake.
Kaitsaye compound din gidan ya fito, tun daga nesa kuma ya soma k’walla kira.
“Ado! Ado!!”
Baba Ado dake bakin gate wurin Ashiru ne, Jin irin kiran da Alhajin keyi masa ne kuma yasashi tahowa da sauri.
Kallonsa Alhaji Idi Sale Dakata’n yayi, kana cikin dan daga murya yace.
“Jannart ta fita ne?”
Kai Baba Ado ya girgiza kana cikin girmamawa yace.
“A’a Alhaji Jannart bata fita ba, kwata kwata tunsafe Ina zaune anan banga wani ma daya fita acikin gidan nan ba.”
Shiru Daddyn yayi, na yan wasu mintuna, kamar kuma Wanda aka tsikara yasoma k’wala k’iran Guards.
Su kuwa k’attin banzan ma sai yanzu suka tashi daga nannauyan baccin daya daukesu.
Jin kiran da Ogan nasu keyi musu ne kuma, yasa cikin sauri duk suka k’araso.
Kallonsu Daddyn yayi tsab cikin hade fuska yace.
“Ina Jannart, dawa ta fita acikin ku?.”
Kai suka girgiza dukansu, kana suka had’a baki wajen cewa.
“A’a bamuga Jannart ba, mu yanzu ma tashinmu wata kila tana cikin gida.”
“Wani irin cikin gida kuma, bayan babu Inda ban duba batanan, maza ku zagaye duka gidan nan ko zaku ganta.”
Dadyn ya fada cikin bacin rai.
Nan take kuwa guard din suka bazu ako ina dake cikin gidan, amma ko alamar Jannart basu gani ba.
Hankalin Daddy yayi masifar tashi, musamman daya sake kiran wayanta yaji akashe.
Haka ya dawo falon afujajan, Yayinda Momy kuwa ta kasa zaune ta kasa tsaye, saboda abune kaman wasa amma yana neman Zamowa gaskiya.
Kallon Daddyn tayi, tare da Daukar wayarta tace.
“Bari na kira Barrister Kabir.”
Dialing number’n Barrister Kabir din tayi, bugu hudu kuwa Barrister Kabir ya dauka.
Bayan sun gaisa da Momynne kuma, cikin tashin hankali tace.
“Barrister bamuga Jannart bafa, munnemeta sama da kasa acikin gidan nan amma bamu sameta ba, munkira wayarta kuma akashe, Kodai tazo wajenka ne?”
Daga can b’angaren Barrister Kabir ya mik’e tsaye tare da daga muryarsa cikin nuna tashin hankali yace.
“What!! Wannan Wace irin magana ce, Ba’a ga Jannart ba, annemeta anrasa? Ita kudi ce da za’ace annemeta anratsa? Ko kuma ita din wayar hannu ce da za’ace an nemeta anrasa.”
Ya k’are maganar cikin yanayin tsawan, dake nuni da bazai iya tolerating nonsense akan Jannart ba.
Momy kuwa cikin tashin hankali tace.
“Wallahi Barrister bamuganta ba, body guards dinta da masu gadi duk sunce basu ganta ba.”
“Gani nan zuwa.” Barrister Kabir din ya fada agigice.
Tare da kashe wayar.
Bayan ya kashe wayartasa ne kuma ya saki wani irin murmushi tare da juyowa ya kalli Aunty Dijat dake zaune.
“Sakarkaru sai yanzu suka lura da cewar Jannart bata gidan, hmmm da sannu munafukan boye zasu fito fili, kowa kuma zai girbi abunda ya Shuka.”
Dariya Aunty Dijat tayi.
Yayinda shikuwa ya dauki key din motarsa ya fice.
Kaitsaye gidansu Jannart din ya nufa.
Yana isa gidan kuwa ko gama dai-dai-ta parking baiyi ba, ya fito.
Inda Daddy kuwa ke tsaye, gaba daya hankalinsa atashe yake sai safa da marwa yake, Yayinda kuma yake ta balbale guard din da fad’a, tankar zai hausu da duka, sai cewa yake, su je su nemo Jannart duk inda ta shiga ta fita.
Barrister Kabir kuwa agigice ya karaso, hankalinsa amatuk’ar tashe yace.
“Yaya ina Jannart? Waya dauke mana Jannart? Ina kuka kaita?.”
Kai Alhaji Idi Sale Dakata ya girgiza, cikin tsananin damuwar da yake ciki yace.
“Bansani ba Kabir, bansan Ina Jannart tayi ba, munduba ko ina amma babu ita babu alamanta.”
Hannu Barrister Kabir ya daura akai, lokaci daya kuma ya jujjuya idanunsa sukayi jajur, ahaukace ya soma neman Jannart din, tare kuma da soma zagaye cikin gidan yana leka har cikin followers, sunan Jannart din kawai yake kira da iyaka karfinsa.
Daddy kuwa bala’i da tashin hankali ne ke cinsa, cikin zafin nama kuma ya kalli Ashiru.
Afusace yace.
“Ashiru Ina Jannart waya bude mata kofa ta fita, ka fadamin nace ko kuma yanzu nasa bindiga na harbe kanka.”
Yakare maganar atsawace tare dasa hannu kuma ya dauke Ashirun da lafiyayyen Mari.
Kai Ashiru ya girgiza, cikin shanye zafin marin yace.
“Alhaji banganta ba, tun jiya gidannan akulle yake, gaba daya jiyama kowa ya sani bataje aiki ba, tunjiya bata fito ba, ga guards dinta nan suma shaidane.”
Sake hasala Daddyn yayi, Wanda hakan yasa ya sake gallawa Ashiru mari, tare da juyowa ya soma balbale Body guards din.
Cikin fushi yake cewa.
“Aikin banza k’attin banza kawai, angaya muku ahaka kawai na daukeku aiki ne, sokaye kun kwanta bacci sai kace matattu, yan iska kusan duk inda zaku ku nemomin y’ata.”
Barrister Kabir kuwa, zuwa yanzu har muryarsa ta Dishe, saboda yanda yake ta k’wala kiran Jannart.
Gaba daya lokaci daya jikinsa har karkarwa yakeyi, hankalinsa ya matukar tashi, inda yake reaction tankar da gasken gaske shima baisan inda Jannart din take ba.
Cikin kuma tashin hankalin daya nuna yana ciki ne kaitsaye ya nufi dakin Jannart din.
Yana shiga kuwa ya soma wargaza komai dake cikin d’akin, ananne fa kuma idanunsa suka sauka akan wayarta.
Da sauri ya dauki wayar dake kashe ya kunna, batare ma daya jira wayar ta karasa kawowaba ya dawo cikin falon, inda dukansu ke tsaye, cikin kuwa harda Junaid dake zukan shisha.
Wayar nata na kawowa Barrister Kabir ya shiga cikin dialing call dinta.
Aikuwa last sunan wanda tayi waya dashi Ne ya bayyana.
“Yah Junaid”
Idanu Barrister Kabir din ya