Showing 123001 words to 126000 words out of 132995 words

Chapter 42 - TUBALI Book 1 Complete Document by GARKUWA

22 Aug 2025

143

kallonsa yayi ga Jannart, wanda take zubawa Mamy juice na pineapple and Orange din da tayi, kanta ak’asa yake, domin tun shigowar Rayyern din bata ma d’ago kanta ba.


“Nasara miki Aunty Jannart, wallahi kin iya dafa abinci sosai, tunda na shigo Nigeria banci fancake mai dadin naki ba, please kullum kina yi manashi kinji..”
ya k’are maganar yana me rausayar da kansa gefe, alaman rok’o.


Jannart kuwa da har yanzu kanta ke k’asa murmushi tayi, batare kuma da tace komai ba, ta zuba musu shaka a cup shida Ramadan.


Mamy kuwa Rayyern dake tsaye yana Kallon wani waje daban ta kalla, still kuma cikin kulawa tace.


“Babana zokaci abinci kaji, ka daina zama da yunwa.”


Kansa ya d’an girgiza alaman “A’a.”


Batare kuma daya ce komai ba, ya zagaya ta gefensu, kaitsaye ya nufi hanyar steps din da zai kaishi zuwa sama, ko kusa kuwa bai kalli inda Jannart take ba, impact baisan da cewar tana acikin falon ba.


Mamy kuwa da kallo ta bisa, harya soma haurawa saman stairs dinne kuma ya Dan tsaya, tare kuma da juyowa ya kalli Mamyn nasa yace.


“Mamy Abba fa ya shigo, yana side d’insa.”


Kai Mamyn ta jinjina, Yayinda shikuwa Rayyern din kaitsaye ya haura sama.


Jannart kuwa har dai zuwa yanzu ta kasa d’ago kanta, saidai jin alaman tafiyarsa yasa ta sauk’e b’oyayyar Ajiyar zuciya.


Mamy kuwa food flask din abincin ta d’auka, bayan ta mik’e tsaye ne kuma tace.


“Barin kaiwa Abbanku nasa abincin.”


Bayan ta wuce sashin Abban ne kuma, Jannart din ta d’an gyara zamanta, tare da d’ago kanta, ta kalli babban tv’n dake cikin falon, inda taga tv channel dinsu, wato Arewa24 suna haska film din, Nisan Kwana.


D’an maida hankalinta ga tv’n tayi, Yayinda su Ramadan kuwa har yanzu cin abincin nasu yaki k’arewa, santi kawai sukeyi, shakan da ta had’a kuwa tas suka shanye shi.


Acan b’angaren Rayyern kuwa yana shiga cikin falon nasu, jacket din dake saman rigarsa ya cire, tare kuma da karasawa gaban fridge dinsa, bud’e murfin fridge din yayi.


Hade da d’auko babban kwalban chocolate d’insa, wanda saboda tsabar sanyi harya fara daskarewa.


Murfin kwalban ya b’alle, tun kafun ya zauna kuwa ya saka spoon acikin kwalban, tare da d’ebo chocolate din ya soma sha.


Idanunsa ya lumshe, alokacin da yaji zakin chocolate din na mamaye bakinsa.


Cikin nutsuwa kuma ya zauna akan daya daga cikin kujerun falon, bayan ya daura kafafunsa akan rug ne kuma ya ci gaba da Shan chocolate d’insa.


Yana girgiza k’afa alaman yana enjoying mood dinnasa.


Mamy kuwa Koda ta isa part din Abban, zaune ta sameshi a falon, ganinta ne kuma yasa Abban sakin murmushi.


Kana cikin sakin fuska yace.


“Banyi tunanin zuwanki yanzu ba ai, naga kaman yaran naki sun rik’eki da zance saboda daga nanma inajin tashin maganganunku.”


Murmushin Mamyn tayi, adaidai lokacin da take k’arasowa gabansa ta durk’usa, kana muryarta atausashe tace.


“Barka da dawowa.”


“Yauwa, kuma sannunku da dawowa, fatan kunyi sayyaya lafiya?”


“Lafiya lau Alhamdulillah, munsayo duk wasu abu da suka dace gacan kayan ma acikin falo, ko kuncesu ba mu yi ba.”


Mamy ta amsa tana me kokarin zuba masa fried rice acikin plate.


Abban kuwa Kai ya jinjina cike da gamsuwa, kuma yace.


“To Allah ya Amfana.”


“Ameen.” Mamyn ta amsa tana me ajiye masa plate din abincin agabansa, hade kuma da zuba masa juice, and fancake.


Juice din Abban ya d’auka ya d’an kurb’a, cikin rashin son tauyeta kuma yace.


“Kije ki gama da yarannaki ko, ni Idan yaso kyaji dani anjima.”


“To.” Mamy tace tana murmushi, kana kuma ta mik’e ta fice daga Cikin falon.


Koda ta dawo falon,harsu Ramadan sun kammala cin abincin.
Inda Riyyam da kansa ya tartare wajen,. Tare dakai plates din da suka b’ata kitchine.


Mamy kuwa zama tayi tare da jawo kayyyakin da suka sayo.


“Jannart zokiga kayayyakin da muka sayo.”
Mamyn ta fad’a tana me bubbud’e kayan.


Inda ta fara ciro wasu tsala tsalan laces, da kuma atamfofi masu kyau, Hadi da materials da shadda laces.


Jannart kuwa ganin yanda kayan suke da kyau sosai ne yasakata sakin murmushi, tare da cigaba da Kallon kayayyakin da Mamyn ke fitowa dasu.


Bayan Mamyn ta faka su laces din agefe ne kuma, ta soma ciro had’add’un Turkish, and Dubai abayas and kimonos, masu kyau da tsadar gaske, kasancewar kuma abayas din irin new design dinnan ne yasa suka dauki hankalin Jannart.


Mamy kuwa sauran shoes bag and vails, da kuma sauran abubuwan da suka sayo duk ta nunawa Jannart, kana cikin kulawa kuma tace.


“Jannart ga kayayyakin naki, Allah yasa sunyi miki.”


Murmushi Jannart din tayi, tare da d’an sunkuyar da Kanta, tana kallon datsassun abayas masu masifar kyau da laces din cikin sanyin murya kuma tace.


“Komai yayi, nagode sosai Mamy Allah Ya saka da al'khairi.”


“Ameen Summa Ameen Jannart, ba komai ai yiwa kaine.”


Mamy ta amsa, tana me zaro wayarta, inda ta dannawa number’n, tailor din da ta amince da k’warewar sa kira.


Bugu biyu kuwa tailorn ya d’auka, bayan sun gaisane kuma Mamy ta shaida masa cewar tanason ganinsa.


Kasancewar yasan inda Naira take ne kuma, yasa take yace.


“Toh Hajjajo. Ganinan zuwa.”


Kashe wayan Mamy tayi, tare da Kallon Jannart cikin kulawa tace.


“Yauwa Jannart wani irin dinkuna kikeson ayi miki, kinsan ku y’an matan zamanin nan yanzu baku cika son riga da zani ba.”


Sadd’a kai k’asa Jannart din tayi, ladabce tace.


“Ni Mamy komai akayi ma inasawa.”


Murmushin Mamyn tayi tare da cewa.


“Shikenan To bari tailan yazo.”


Nan dai suka shiga d’an tab’a hira, Yayinda Riyyam-nsra da Ramadan keta jan Jannart din da hira.


Suna nan azaune kuwa, cikin abunda bai wuce 15mn ba saiga tailorn yazo.


Bayan sun gaisane kuma Mamy ta basa, k’atuwar ledan da ta Ware kayayyakin dinkin aciki, kana cikin sakin fuska tace.


“Fahad ga y’atanan dan Allah kayi mata dinkuna masu kyau, way’anda zasu sake fito da ita sosai, sannan kuma akan kari muke buk’atar kayan.”


Murmushi Tailan da Mamyn ta kira da Fahad yayi, kana Cikin bata girma yace.


“Insha Allahu Hajiya za’ayi mata dinki dai-dai da zamani, kafun nan da sati biyu kuma zaku samu dinkin Insha Allah.”


“Yauwa to Allah yasa, yanzu za’a baka size dinta ne, ko zaka gwada ta?”


Mamyn ta fad’a tana me Kallon Jannart da kanta ke sunkuye.
Kanshi ya ɗago ya ɗan kalli Jannart kana yace.
“A’a basai na gwada taba, ai naganta kuma Insha Allah zanyi mata komai yanda ya dace.”


Fahad din ya kare mgnar yana sake harhad’a kayan waje daya.


Mamy kuwa kaita jinjina cike da gamsuwa tace.


“To nawa ne kudin dinkin naka.”


D’anjim Fahad din yayi, saboda shi kansa baisan nawa zaice ba, kasancewar kayan suna da yawa, dole sai ya nutsu ayi total tukunna.


Fahimtar hakanne kuma yasa Mamy mik’ewa tsaye, tare da cewa.


“Kad’an jirani inazuwa.”


Kaitsaye sama ta haura, tana shiga cikin falon saman kuwa ta hango Rayyern zaune, ya daura kafarsa daya kan d’aya, Yayinda idanunsa kuwa ke lumshe, sai kuma goran swan dake rike a hannunsa.


“Rayyern.”
Mamy ta kira sunansa.


Jin sautin muryar Mamynnasa ne kuma yasashi bude idanunsa.


Tare da gyara xamansa yace “Mamy.”


“Na’am tunanin mekakeyi?” Mamyn ta tambaya cike da kulawa.


Kansa ya dan juya, kana cikin sanyi yace.


“Babu komai Mamy, kawai dai nagaji ne.”


“Da kyau.
dama kudin dinki nazo karb’a awajenka, yanzu na kira taila kuma yazo, zai tafi da kayayyakin da muka sayo zaije ya dinkosu.”


Mamyn ta fad’a tana me tsaresa da idanu.


Wanda hakanne kuma yasashi shagwab’e fuska, tare da karyar da wuyansa gefe, kana akasalance yace.


“Eyyah Mamy ai duk kun kwashemin y’an kud’ad’ena, kuma fa bana da wani kudi sosai, sannan ba atm dina yana hannunku ba naga shima yadda kuka yasheni kamar ba gobe.”


Murmushi Mamy tayi, saboda tasan maganar cewa ma bashi da kudi ba gaskiya bane.
Sai dai al'adarsa ce bai cika son almobazaranci ba, yana fadin hakanne kawai saboda kaucewa mgnar da suke ta lika mishi


“Cash mukeso yanzu ba wai transfer ko wani abuba, tailor ne yazo, ko atm card din kakeso mu bashi yaje ya cire?”


Cewar Mamyn.


Rayyern kuwa da sauri ya kalleta tare da cewa.
“Atm card na din zaku bawa wani, uhumm lallai Mamy abun ya magaga”. shi bawai kudin bane bayason bayarwa, a'a kawai dai shi ayanda aka lika masa auren ne baiso ba, saboda dama yasan dolene sai antakurasa akan hakan.
Ita kuwa Mamy ido kawai ta zuba mishi.
Mik’ewa tsaye yayi, tare da nufan d’akinsa, kaitsaye gefen bedside drawernsa ya nufa, Koda ya ya karasa bud’e drawern yayi ya d’auko, bandir din kudi, Rafa daya inda kuma kowani Rafa daya 50k ne.


Juyowa yayi ya dawo falon, tare da damk’awa Mamyn kudin.


Cikin shagwab’a da kuma turo baki yace.


“Mamy gashi yanzu a barni in huta ko. Kuma a kamo min ATM na kin san Ramadan ba mutuncine dashi ba, in ya samu kudi.”


Karb’an kudin Mamy tayi, batare kuma da ta sake ce masa komai ba, ta juya ta fice daga cikin dakin.


Koda ta sauko kasa, duka 50k din ta bawa Fahad.


Da ya tashi tafiya ne kuma ta had’ashi da Hadi ya kaisa har zuwa babban shagonsa.




Sauran kayan da suka rage din kuwa, Mamyn da kanta ta Taya Jannart suka shigar dashi, can cikin bedroom din Jannart din.


Cikin kulawa kuma haka Mamyn ta Taya ta suka shirya duka sauran kayan acikin wardrobe, kayan shafa kuwa anan kan dressing mirror Jannart din ta jere su.


Bayan sun kammala komai ne kuma, suka sake dawowa nan cikin main falon.


Zama sukayi inda Riyyam da Ramadan kuwa suka shiga sana’arsu ta buga game, ganin yanda Game din ke dadi ne kuma yasa, Jannart maida gaba daya hankalinta garesu.


Mamy kuwa kallonsu take fuskarta d’auke da yalwataccen murmushi, saidai kuma ganin yanda hankalinsu duk ya tafi akan game dinne yasa, ta mik’ewa.
Anutse ta nufi sashin Abba.


Ahankali ta tura kofar dakin ta shiga, bakinta dauke da sallama.


Abba dake rike da wani littafi na Tafsir, ne ya amsa mata sallaman tare da d’ago kansa ya kalleta.


Itakuwa Mamy fuskarta dauke da murmushi ta k’arasa shigowa cikin falon, cikin muryar dake nuna tautasawa tace.


“Allah yasa bankatseka daga abunda kakeyi ba.”


Murmushi Abban yayi, cikin fadada fara’ar dake kan fuskarsa kuwa yace.


“Sam baki katseni ba, kamar kinsan cewar kuma dama ina nemanki.”
Abban ya fad’a yana me jawo wata leda dake gefensa.


Mamy kuwa k’arasowa inda yake zaunen tayi, tare da durkusawa ta zauna agabansa.


Abba kuwa Ledan dake hannunsa ya mik’a mata, atausashe yace.
“Waya ce wannan d’azu na sayowa Jannart ita, ki kai mata, duk na sha’afa shiyasa d’azu da kika shigo ban baki ba.”


Murmushi ne ya bayyana akan fuskar Mamy, cikin farinciki kuma tace.


“Kai Masha Allah, amma gaskiya Jannart zataji dadin hakan, Allah ya kara bud’i.”
Mamy ta fad’a tana amsar ledan.


“Ameen.” Abban ya amsa, Yayinda ita kuwa Mamy ta mik’e, tana fad’in.
“Bari nakai mata wayar na dawo.”


Abban kuwa Kai ya jinjina alaman “To.”


Haka Mamy ta fito daga sashin Abban fuskarta d’auke da murmushi, ta karaso nasu sashin.
Har yanzun kuwa su Jannart na zaune.


Akusa da Jannart din Mamyn ta zauna, kana cikin tausasawa tace.
“Jannart ga sak’o inji Abbanku.”


Jin hakanne kuma yasa Jannart, d’ago Kai ta kalleta, tare kuma dasa hannayen ta bibbbiyu ta karb’i ledan, da Mamyn ke mik’o mata.


Ahankali ta warware ledan, tare dasa hannunta ta zaro kwalin dake cikin ledan.
Idanunta ta d’an zaro waje, saboda Ganin kwalin waya da tayi, kirar Samsung Galaxy S21 ultra.


“Wow Samsung galaxy S21 ultra, gaskiya Abba yanaji dake Aunty Jannart.”
Riyyam-nsra ya fad’a, Cikin nuna jin d’adinsa.


Jannart din kuwa, itama tsananin farinciki ne ya bayyana akan fuskarta, wanda saboda jin dadin kyautan da tayi ne kuma yasa, har hakwaranta suka bayyana alokacin da take murmushi.
Cikin tsananin jin dadi, da kuma nuna yaba kyautar da Abban yayi mata tace.
“Nagode sosai Mamy Allah ya kara arziki, ya kuma kara rufa asiri, Allah ya jik’an magabata.”


“Ameen Ameen Jannart, ba komai ai duk yiwa kaine, yanzu ke tamuce komai mukayi miki basai kinyi mana godiya ba.”
Mamy ta fad’a ciki kulawa.


Jannart kuwa rungume wayartata tayi, cikin jin dadi da kuma duk’ar dakai tace.


“Mamy nagode sosai, kuma inason yiwa Abba godiya.”


“Bakomai Jannart, taso muje to sainayi miki iso zuwa wajennasa ko.”
Cewar Mamy tana me mik’ewa tsaye.


Ganin hakanne kuma yasa Jannart itama mik’ewa tsaye, tabi bayan Mamyn, Yayinda tabar wayar nata awajen Ramadan, wanda tuni harya cirota ya kunna, domin shikansa wayar tayi masa kyau.


Mamy kuwa ahankali ta murd’a handle din kofar falon Abban, tare dasa kanta ciki, hakanne kuma yasa Jannart dake biye da ita, itama ta shiga bakinta dauke da sallama.


Abba dake zaune kuwa, ganinsu ne yasashi fad’ad’a fari’arsa, cikin sakin fuska yace.


“A’a Jannart.”


Murmushi Jannart din tayi, tare da k’arasowa dan nesa da Abban, ta durk’usa tare da zube guiwowinta ak’asa, kanta ta duk’ar k’asa, cikin muryar dake nuna girmamawarta agaresa tace.


“Abba naga waya, nagode sosai, Allah ya kara budi da arziki, ya jikan magabata.”


“Ameen summa Ameen Jannart, idan kina buk’atar wani abu ki sanarwa Mamynku, kinji kada kiji nauyi ko kunyarmu, muba iya surukanki bane kawai mu matsayin iyaye muke a gareku.”
Abban ya amsa, yana murmushi.


Itama Jannart din murmushi tayi, tare da mik’ewa cikin sakin fuska, ta fice daga cikin dakin.


Direct falo ta dawo, zama tayi akan sofa, tare da karb’an wayan nata ta soma dud dubawa.
Sosai wayar tayi mata kyau, musamman da colourn wayan ya kasance bak’i.


Hira suka dan tab’a dasu Ramadan, din kafun daga bisani ta tashi ta shiga ciki.
Kasancewar tana danjin gajiya ajikinta ne kuma yasa, kaitsaye toilet ta wuce tayi wanka.


Bayan ta fito ne kuma ta shafa, daya daga cikin mayukan da Mamy ta seyo mata, tare da binjikinta da Body spray mai dadin kamshi.


Direct wardrobe dinta ta bud’e, daya daga cikin dogin rigunan da Mamyn suka sayo mata ta saka ajikinta, kamar kuwa tun can dominta akayi rigar, saboda yanda rigar ta zauna mata d’as ajiki.


Dai-dai lokacin kuwa aka soma kiraye kirayen sallan la’asar, kasancewar kuma tayi alwala tun acikin toilet shiyasa kawai hijab dinta ta zura tare
da tada sallan, bayan ta idar ne kuma ta kwanta.


Acan cikin gidan kuwa Rayyern tunda ya shiga daki baifito ba, sai yanzu da yaje yayi sallan la’asar, still kuma sake dawowa gidan yayi, tare da komawa daki yayi kwanciyarsa, kasancewar yau din weekend ne shiyasa yakeson morewa hutunsa.


Su Ramadan kuwa Koda sukayi sallan la’asar, cikin gari suka kutsa shida Riyyam.


Haka dai sukayi wunin wannan ranar.
Mamy na mai jan Jannart a jiki sosai, ba laifi kuma ta ɗan sake.


Washegari


Acan gidan Alhaji Idi Sale Dakata kuwa, tashin hankali kam sun shigesa k’arara sun wuni sun kwana cikinsa, musamman awajen Alhaji Idi Sale Dakata, dako zaman kirki ya kasa yi, hankalinsa amatukar tashe yake, badon komai ba kuwa, face sanin da yayi cewar, b’acewar Jannart babban tashin hankalinsu ne, haka kuma kaman wani kalubale ne dake fuskantarsu, wanda ba zasu tab’a iya tsaidashi ba kwana yayi baiyi bacciba a wannan daren.


Mom kuwa tayi hawaye har saida idanunta suka bushe, gaba daya ta shiga damuwar rashin Ganin Jannart din, Yayinda duk wani zarginta ta d’aurashi akan Junaid, saboda sanin da tayi cewa, ba k’aramin aikinsa bane sace Jannart din.


Abdull ma gaba daya haka yayi wuni jiya ya kwana yau kuwa tun da safe ya gayawa Yah Azeez abin da ake ciki.
Abinda yayi masifar tada hankalin Azeez kenan. saboda b’atan ƙanaartasa ya daki zuciyarsa sosai.


Haka kuma yau ɗin ma gari na wayewa Alhaji Idi Sale Dakata ya fita, da kansa ya dinga zaga gari waiko zai samu wani labari amma Ina.
Daga karshe dai haka ya dawo gida zuciyarsa duk ba dadi.
Har dare kuwa babu wani labari akan Jannart din.


Yayinda Barrister Kabir kuwa ya buwayesu da zurya da tashin hankali.


Acan gidansu Rayyern kuwa ana idar da sallan isha'i Ramadan da Riyyam suke dawowa gida.
Mamy kuwa bayan ta kammala dinner, har d’aki ta kaiwa Jannart nata zaune ta sameta bisa sallaya tasa hannunta duka biyu ta tallabe h...!












By
*GARKUWAR FULANI*












Habarta tana lallatsa wayarta.
Cikin sauri ta ɗago kanta jin motsin Mamy.


Ita kuwa Mamy ajiye mata tray'n tayi gefenta tare da cewa.
“Ki ajeyi wayarnan haka, kizo kici abinci.
Ga tea kisha da zafinsa mgnin wannan sanyin da akeyi mana”.
Cikin girmamawa tace.
“Toh Mamy sannu ngd”.
Kai ta jinjina kana juya ta fita.


Kasancewar kuma yanayin garin ana busa sanyi mai masifar ratsa jikine, yasa su Mamyn ma basu wani jima afalon ba, suna kammala diner din, kowannensu ya wuce dakinsa.


Rayyern kuwa dama ko saukowa k’asan baiyi ba, abincinsa ma sai Mamy ne tasa Riyyam ya Kai masa daga nan ya zauna gefenshi yanata zuba mishi surutu.
Nan ma baiwani ci sosai ba sabida ya rigada yaci Chocolate ɗinsa shi yasa Riyyam din ya fita dashi.


Duk da cewar yanajin bacci kuwa, bai kwanta ba harsaida ya motsa jikinsa, na kusan tsaeon 1 hour kafun ya kwanta.
Cikin yan mintuna kadan kuwa bacci ya daukesa, saboda duk garin ya dauki sanyi sosai.


Acan b’angaren Jannart ma, da wuri ta kwanta, tare da shigewa cikin lallausan blanket dinta, tana rik’e da wayarta kuwa bacci ya dauke ta.


Washegari.


Kamar kullum kuma Koda yaushe, dukansu atare suka dawo daga sallan Asuba.


Inda suna shigowa kuwa Mamy ta tarbesu da hadin Coffee dinta, mai dadi.


Bayan sunsha ne kuma duk suka miƙe suka wuce sama dan sake kwanciya, Mamy kuwa kaitsaye kitchine ta wuce.


Tare da soma shirye shiryen had’a musu breakfast.


Tana cikin aikin nata ne kuma, Jannart ta fito zuwa main falon.


Sanye take da Hijab ajikinta, Jin motsi acikin kitchine dinne kuma yasa ta, nufar kitchine din kaitsaye saboda tana da tabbacin cewa Mamy ne.


Mamy kuwa dake tsaye, Jin alaman tafiyan mutum ne yasa ta Juyowa da sauri, dai-dai lokacin ne kuma Jannart din ta k’araso bakin kofar kitchine din riƙe da mug din coffee da Mamy ta kai mata.


Murmushi Mamy tayi, tare da fadada fara’ar dake kan fuskarta, atausashe tace.


“A'a Jannart da sanyin safiyar nan me kika fito yi?.”


Kai Jannart din ta jinjina, cikin girmamawa kuwa tace.


“Mamy aikin zamuyi.”


“Da wannan sanyin, a jeki kwanta?”
Mamyn ta fada tana murmushi.


“A'a Mamy aiki da yawa ai bari na tayaki.”
Jannart din ta fad’a tana me k’arasa

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login