Showing 60001 words to 63000 words out of 68854 words

Chapter 21 - AHALINA Complete Hausa Novel

23 Aug 2025

290

Mami mun wuce and kace mata na gode da private jet ɗin,"
"Okay princess safe j and ki kula da kanki.
Sallama sukayi ta kashe wayan ,kallan Mami wadda ke faman smiling Papa yayi yace sun wuce fa.
Licking lower lips ɗinta tayi tace "ina jinta ai har da baka saƙon godia kayi mun ita mai baba shes feeling big enough' da kirana ko,its Okay Next time idan urgent abu 'ya kamata ka bata PJ na huta da formalities"
Dariya yasa ya tashi zuwa gareta,hugging ɗinta yayi ta baya 'ya ɗora habarsa a kafaɗarta yace"im smelling jealousy,"
Dukan wasa ta kai masa tace "piss up ina da aikin yi a ƙasa ai nagama baban Aiki anan tunda na baka ka ƙoshi"
Dariya yasa yana mai faɗin ban gama ƙoshi ba cos jiya nayi mafarki wai na ganki da baby bump wanda fassaransa yana nuna mun su Autayanki yan uku zasu samu ƙani ko ƙanwa,
Juyowa tayi tana mai saka hannunta a gefen kuncinsa kana tayi kissing gefen kumatunsa tace "dream on baby boy"
Da haka ta fita dan sauka cikin asibitin.
Shafa kansa yayi yana mai taba gurin da tayi kissing nasa yace "that was really close,"murmushi yayi ya sake sipping ruwan da ta zuba masa a cup sannan ya mara mata baya.
***
Tunda Nadiya ta saka ƙafarta Ghana jikinta ke bata Ahmed yana tare da ita,amma a ina?
Kawar da tunaninsa tayi ta mayar a hankalinta wajen meeting ɗin da tazo na haɗaka da suka ƙulla tsakaninta da kamfanin ,sosai meeting ɗin 'ya ɗauki lokaci cos it was a very long process,bayan gamawansu suka fito tare da Naomi da sakatariyarta wadda hannuta ke ɗauke da takardu da kuma files,
Suna tafiya batayi Aune ba sai ji tay An rungumeta ƙam inda a lokaci ɗaya sautin ƙarar mutum biyu ta karaɗe gurin,ɗaya ƙarar Abun ƙaunarta ne wanda a wannan lokacin take rungume tsam a jikinsa yayin da ɗaya ƙarar ta macece wadda bata ɗauka ba,sulalewwar da yayi zuwa ƙasa itace ta fargar da Nadiya abunda ke faruwa,
Binsa tayi da sauri tana mai fashewa da wani irin kuka tana mai kiran sunansa,
Budurwar da tayi stabbing ɗinsa wadda hannunta ke ɗauke da wuƙar da ta chaka masa ta cire ce itama tayi kansa da gudu tana mai faɗin"Evans No,you cant do this To me,please".
Hakaɗeta Nadiya tayi ta ɗan jirkintasa gefe yarda ba zai ƙwanta kan ciwan dake ta faman zubar jini ba ta saka ɗanƙwalinta ta danne inda jinin ke fita ta kalli Naomi wadda ta duburburce tace"Naomi ambulance ".
A ruɗe Naomi ta fara kiran Ambulance ,
Ganin Yarinyar da tayi aika aikan na neman guduwane Sakatariyar Nadiya Haleems ta ruga da gudu gareta tana mai faɗin"you're going no where bitch".
Ƙokarin magana Ahmed ke san yi wanda Nadiya ta lura tace"stay still Ahmed please,I've got this,baza ka mutu ka barni ba ,not now insha Allah".
Cikin lokaci ƙanƙani Ambulance yazo aka ɗaukesa akayi asibiti dashii ,kuka kawai Nadiya keyi tana tsoran rasashi a wannan gurbin na rayuwarta da take ganin Babu wani ɗa namiji da zata iya rayuwa da shi bayan shi ,
Koda Haleems tazo tare da yan sanda biyu tazo waɗanda suka zo tabbatar da zargin da ake akan yarinyar mai suna Thelma,neman magana da Nadiya sukayi amma basu samu ba domin kuwa hankalinta baki ɗaya yana ga Ahmed ɗinta wanda har yanzu Babu wanda ya fito domin sanar masu da halin da yake ciki,tana wannan tsaiwar jiran tsammanin iyayensa suka zo a ruɗe wanda abun ya faru akan idanun wani da yasan mahaifinsa,
Cike da balai mahaifinsa yayi kanta yana mai faɗin"there is the evil and bad luck that is trying To ruin my child,"
Ganin yayi kanta da fitina ya saka matar sa saurin riƙesa tana mai fadin"My husband calm down,"
Cike da balai yace "don't tell me To calm down, shes the root of all This."
Ita dai Nadiya babu abunda ta iya faɗi illa addua da take faman yi a zuciyarta na nema masa sassauci.
Likitan da ya shiga masa aikin ne ya fito ,da sauri Nadiya ta nufi garesa tana mai faɗin"Doctor how is he?"
Kafun likitan ya bata amsa Mahaifin Evans ya tako gurin ya jannyeta yana mai cewa Doctor ɗin"Doctor how is My son,im his father,talk To me".
Kallansa likitan yayi kana ya kalli Nadiya yace"sai dai a godewa matarsa cos da bata kawosa da wuri ba da yanzu wani labari ake inda aka godewa Allah bai rasa jini da yawa ba,"
Wani tsaki mahaifin Evans yayi yace "kalli nan likita ita ta jawo komai sannan gyara daya da zan maka shine ita ɗin ba matarsa bace"
Mahaifiyrsa ce ta taka a karo 'na farko ganin Nadiya zata matsa gurin likitan,Kaɗa mata kai tayi tana mai Riƙe mata hannu,cikin wani hawaye da ta kasa tsayarwa dashi tace "Mom zan ganshi koda sau ɗaya ne amma kar kice 'na tafi kamar Dad sannan wallahi ban san 'ya abun nan 'ya faru ba,Eh tabbas 'ya shiga mun ne nice 'ya kamata ace ina kwance a asibititin nan bashi ba,amma da gaske nake ban masan yana gurin da nake ba,da ace na sani bazan taba bari yayi wasa da rayuwarsa ba akaina, "Tsaki Dad dinsa yayi yace "maganar banza,a'i rayuwarsa 'ya daɗe da yin wasa da ita akanki tunda 'ya daina yarda da yesu".
Mr Hans 'ya isa mana,saboda Allah Ina tunanin kana jin likita yace Ba domin ita ba da yanzu wata maganar ake,And da kake maganar ba matarsa bace ina tunanin mun gama maganar nan?
Ita Evans yazaba And nima bana ƙorafi so ya isa hakan ,kallanta ta mayar kan likitan tace "Doctor zamu iya ganinsa?"
Murmushi yayi yace "zaku iya saboda An mayar dashi ɗakin hutu amma 'fa sai dai idan kunyarda bazaku damesa ba wanda ni banga Alamun hakan ba,"
Assuring ɗinsa sukayi kana ya barsu suka shiga amma banda Nadiya wadda kejin kamar tayi ta kurma ihu,
Dafata Haleems tayi tace "ranki ya daɗe ki ƙwantar da hankalinki,insha Allahu zai samu sauki ,baki Naomi tasa tana mai faɗin Insha Allah ki bar kuka haka,"
Goge hawayenta tayi tana mai sake faɗin,"sau ɗaya 'fa nake san ganinsa,."
Suna wannan tsayuwar Mom ɗinsa ta
Fito Takowa tayi ta kama hannunta ta zaunar kana ta goge ɗan guntun hawayen dake idanuntaa tace"kije Nadiya idan ya tashi da kaina zan kiraki a waya kizo,
Wani kukan ne ya sake kwace mata tana mai faɗin "Mom idan ban gansa ba bazan iya samun nutsuwa ba"
Kaɗa mata kai tayi tace"'na sani amma na faɗa miki Babu abunda zai sakaki damuwa domin yanzu ma haka bacci yake ,fushin Babansa yana da yawa sannan a wannan gejin bazai taba barinki kiga Evans ba ,amma na miki alkwari 'yana tashi zan kiraki,"
da kyar ta samu ta lallabata ta tafi amma badan taso ba ,
Danne zuciyarta tayi ta saita kanta ta nufi Police station ɗin da Thelma take bisa Alƙwarin da tama yan sanda aka zata zo,
Tana zuwa Officer ɗin da case ɗin ke hannunsa ta sama wanda ya ke faɗa mata ta riga tayi confessing sannan ta tabbatar da cewa stab ɗin was for you not Him.
Ɗan shiru Nadiya tayi da mamaki kana tace "And Officer i don't even know her Beside i just came to Ghana for business'."
Alfarma ta nema 'na ganinta wanda suka bata Dan kuwa tana buƙatar zantawa da Thelma,
Cikin cell ta sameta tana faman rarraba idanu ,tana ganin Nadiya kuwa ta taso da deadly look tana mai faɗin"ban kashe ki ba yanzu amma ki sani wani lokacin zan tabbatar ban missing target ba,kiyi Addua kar na fita 'yau ko gobe"
Da mutuƙar Mamaki Nadiya take kallanta musamman yarda take gano tsantsar tsanarta a fuskrta wanda ya tabbatar mata zata iya kasheta koda kuwa za'a kasheta ne ita,ajiyar zuciya tayi tace "well dole 'na sanar dake labari mara dadi wanda shine dole zakije prison,sannan magana ta ƙarshe kuwa nasan kinyi abunnan saboda Mad crush akan Ahmed wanda nake mai sake tabbatar miki da cewa zuciyar sa a yanzu tana dukane saboda ni."
Cike da huci Thelma tace "kar ki sake kirasa Ahmed saboda sunansa Evans,sannan ki sani tsafin da kikayi akansa ya koma wancan Addinin da kike taƙama dashi lastly zai kunce kuma bazakiji daɗi ba muddin yabar wannan baƙin tsafin,zai kuma iya iyuwa ya baki zuciyarsa amma ki sani a wuta zaki dawwama saboda ke Kaɗai kika san mai kika masa hakan ya faru,sannan kiyi Addua ban fito ba saboda saina kashe ki "ƙaramar Dariya Nadiya tayi kana ta juya ba tare da tace mata komai ba saboda ta lura kulata ɗin bata lokacinta ne,Dan haka tace ma Officer din,indai ta masu confessing basu buƙatar dogon zaman kotu Dan ta tabbatar prison zataje,
Assuring mata yayi zai processing gobe ya tura su court,haka nan ta koma hotel ɗin da suka kama jikinta baki ɗaya a sanyaye ,wayarta kuwa bata bari tayi nesa da ita ba koda wasa tana jiran kiran mom ɗin Ahmed.

CHUCHUJAY ✍️
[3/13, 10:57 PM] Chuchujay✍️: https://chat.whatsapp.com/DgTUlodRcp2AHM4rmfKTqK
AHALINA

(Siblings of different fathers)

Book two 'in Aure uku series.

EPISODE 5⃣7⃣◼5⃣8⃣

Tun da Nadiya tayi sallar asuba bata koma ba,zumuɗinta kawai taji kiran mom ɗin Ahmed wanda har baƙwai na safiya bata kirata ba wanda tana da yaƙinin cewa 'ya tashi koda kuwa sau ɗaya ne,ganin shirun da kuma fargaba yana neman karta 'ya sakata tashi ta shirya wuraren takwas na safe ta nufi asibitin ita Kaɗai cos ta riga da tasa Haleems da Naomi booking ɗin jirgi su fara gaba domin ita kam a yanzu bata ga ta tafiya ba sai taga ƙwal uwar daka domin kuwa ko me za'ayi sai tagan shi,

Kai tsaye ɗakin da aka kwantar dashi ta nufa kamar wata munafuka tana Addu'ar Allah yasa babu kowa a ciki,kwance ta tarar dashi a kan cikinsa idanunsa a lumshe,tunanin yana baccine ya sakata takawa a hankali ta zauna kan kujerar dake facing ɗinsa,idanunsa dake lumshee ta zuba ma ido kana ta sauke idanun tana mai faɗin"Alhamdulillah ko yanzu Dad yazo ya koreni ai ƙwalliya ta biya kudin sabuli tunda har na samu na saka ka a idanuna,"

A hankali ta kamo hannusa tana mai kallan bandage ɗin dake bayan sa,lokaci guda idanunta suka ciko da ƙwalla,cikin karyayyiyar murya tace"Why?"Mene ya saka ka zabi daka ji ma kanka ciwo akan ni naji,wanene ya faɗa maka idan kai kana kwance a maimakona zanji daɗi ,i Just hope nice abun nan ya sama ba kai ba saboda baka chanchanci haka ba ko kusa ko misali.

Goge hawayen dake faman mata reto a kumatu tayi tace"ka warke da wuri cos dolene zanyi scolding ɗinka na ƙarba mun stab da kayi bada izinina ba"

Batayi Aune ba sai ji tayi ya shafa hannunta da ta riƙe nasa dashi yace"Why don't you scold me Now My love".

Kallan idanunsa tayi da sauri ,har a lokacin a kulle suke,dukan wasa ta kaimasa tana mai faɗin"so idanunka biyu you silly lover"

Ɗan sautin ƙara yasa wanda ya ruɗata nan take ta duka tana mai faɗin im sorry,

Dariya yasa sosai har Adam Apples ɗinsa 'na motsawa gwanin shawa'a,hannunsa ya miƙa mata yace"help me up,"Babu musu ta taimaka masa ya zauna tana mai kaffa kaffa da ciwansa gudun kar ya fama.

Hannunsa ya ɗora kan gefen gadon yayi mata alama da tazo ta zauna,

Zama ɗin tayi tana mai goge guntuwar kwallar dake gefen idanunta ,alama yayi kamar zai kama hannunta sai kuma ya fasa,kular da tayi da gesture ɗinsa ne ya sakata murmusawa tana mai kama hannunsa tace "ka riga ka taba and 'na tababata a yanzu baka da lafiyan bad thoughts,yar karamar dariya yayi kana yace "Ina mutuwar sanki Nadiya,A yarda nake jinki a zuciya zan iya karba miki stabs ko mai adadin yawansu ,zan iya mutuwa domin ki sannan da ace za'a dawo mun da rayuwata a sake maimaitawa zan sake mutuwa a dominki,'na sani im a public figure wanda nake da mad crushes waɗanda nasan they will kill for me musamman ma a yanzu da mutane da dama ke ganin kin jani astray saboda 'na zabi addinin musulunci ,amma mene ?

Abun da nake san ki sani wanda shine ,"zan kula dake a ko wanne hali,zan baki tsaro a duk inda kike muddin Babu tsaro a wannan gurin,zan soki da dukkan rayuwata ,a wannan abun daya faru na sake samun gamsuwa da kaina 'na cewa tabbas ina buƙatar ki kusa dani,Ina san ki zamo mallakina matata,zan baki duk wani kulawa da ya kamata ace Namiji ya bawa matarsa ,sannan na gama yanke shawarar binki ƙasarki inda nasan nan hankaliki zaifi kwanciya,idan kuma ba Nigeria ba ki zabi ko wacce ƙasa kike so zan biki mu gina rayuwa mai tsafta a tare domin duk inda kike nan ne ƙasata"

Saurin goge hawayenta tayi kana tace"shi yasa ai ka ƙwana biyu baka kirani ba,"

Murmshi yayi mai kyau yace "aiki yasa ban kiraki ba shima kuma Babu yarda zanyi ne ,Ina samun lokaci kuma da sauri na bibiyi schedule ɗinki na dawo Ghana gareki na ƙarba miki rauni ya sarauniyata"

Tsintar kanta tayi da yin ƙasa da kanta cike da kunya saboda maganar da tayi domin kuwa tama rasa abun faɗa ne duba da yarda kalaman sa suka sace mata zuciya,

Hannun sa yasa ya ɗago habarta yace "ai kuwa ki cire kunyar nan ki kalleni,cos bana san kunya tsakani na dake,Babu kunya sai soyayya,"

Ɗankwace fuskarta tayi tace "da gaske kake zaka bini duk kasar da nake so,?idan kuma su Dad basu amince ba fa?,

Ni ban so ne yau a wayi gari na zama silar rabaka da iyayenka ,nice mace kuma nice nake da Alhakin binka duk wata ƙasa da kace nan kake so ,idan kana nan ni gidana a nan gurin yake"

Yasan Babu wata kyauta da zai bata da ya wuce aje ta a ƙasarta dan shi kan sa yana buƙatar chanji na gurin zama,cikin ƙwantar mata da hankali yace"Nine zan zauna dake ba iyaye na ba ,sannan Aurena dake ba shine yake nufin na butulcewa maganarsu ba ko kuma na juya masu baya dole da amincewarsu a ciki domin ni ke nake so kuma ke na zaba dan haka suma ke zasu zaba,sannan nima Ina buƙatar chanza guri wanda ke nake so ki zaba.

Faɗaɗa murmushin ta tayi tace"Nigeria"

Tafa hannayensa guda biyu yan mai darawa ganin yarda ya sakata nishaɗi kana yace "deal and done yanzu abu guda ɗaya ya rage wanda shine Aurenki dan Allah muyi Aure."

Kafun tayi magana aka turo ƙofar,turus Mom ɗinsa tayi bayanta ƙanwarsa Mercy sai Dad dinsa wanda ya shigo yan mai faɗin Oge"

Saurin tashi Nadiya tayi tana mai zazzare idanunta kamar An Kaɗa jaba a buta,kame kame ta fara kana tace "Good morning"

Takowa Mom ɗinsa tayi tana mai sakin fuskarta tace "yarinyata Good morning,kafun na kiraki kunzo ashe,wannan soyayyar taku sai Allah"

Ƙasa tayi da kanta cos She's appeared To be desperate wanda bazata ƙaryata ba She's desperate ɗin ,dafa kafadarta Mercy tayi tace "A fili ma kinfi kyau akan hoto,gaskiya yayana ya iya zabe,"

Murmushi kawai Nadiya take bangare guda kuma tana satar kallan Dad ɗin Ahmed wanda ya zauna kusa dashi yana mai tambayarsa 'ya jikinsa,

Ɗaukar jakarta ta tayi tana mai faɗin"bari na wuce mom"

Kamo hannunta tayi tace"im sure baki karya ba dan haka ki zauna kuyi beakfast ke da Evans,"

Rasa ƙaryar da zata gilla tayi dan haka cikin saurin Ɗaukar yanayin tace"ai Ina azumi ne"

Sanin nauyi ne ya saka bazata zauna ɗinba yasa Mom cewa ,"its Okay ki dawo da rana ki kula dashi cos nida Dad din sa zamu fita and Mercy Nada rehearsal na rawa,and make sure kin masa abinci mai daɗi ya koshi,Ina san naga idan kunyi Aure zaki kula dashi .

Cike da zumuɗi ta mata godiya inda gogan yake ta kallanta kamar zai cinyeta da ido,ta masu sallama tana ƙokarin fita muryar Dad ta katseta inda yake faɗin"ki kira mutanenki zamu zo muyi maganar Aurenku,

Kamar a mafarki haka taji zancen nasa,cike da murnar da ta kasa boyewa ta fara masa godiya domin ta fahimci ya amince da ita ,sannan a wannan gejin tasan Allah ne kawai zai hanata da Ahmed mallakar juna a matsayin mata da miji.



***********

A bangaren Hafsa da Abdallah kuwa soyayyace suka tsakanin junansu mai tsafta da aminci,tunda ta koma gidan Aunty shatuh shima ya ɗaura ɗamara domin bama ya kunya ko tsoran wani yasa suna san juna tunda ba haramci suke Aikatawa ba domin kuwa ya gama gamsar da kansa akan muddin idan ba Ba wata kadaraba Allah ya tsara masu daba To shifa yayi mata.

Kamar kullum a yarda yake zuwa gidan Aunty shatuh yauma haka yazo,taba hira yayi da Antin nasa amma bai ga Hafsa ba,kasa jurewa yayi yace "Aunty wai nikam ina hafsa ta shiga cikin daren nan?"

Murmushi tayi tace"Nazata ai bazaka tambaya ba ,To taje gidan Innarta zata kwana biyu,"Dan turus yayi sannan yace"amma jiya ma munyi waya da safe amma bata faɗaa mun ba,"

Yar dariya Aunty shatuh tasa tace"Abdallah na kenan,To ai yanzu bata ƙarkashinka tukunna ,"

Sinarr da kai yayi yace"Aunty ba wai haka nake nufi ba fa,"Dariya tasa tace "nasani ai nima,yanzu dai ba sai ka tsaya tambayata mai ya faru ba ga nan address ɗinta zan baka sai kaje.

Murmushi yayi yace "nasan gidan ai ,kin tuna na taba kaita,tsokanarsa ta fara ,Babu bata lokaci ya tashi 'ya gudu"

Koda yaje gidan ya jima yana kiran layinta bai sameta ba,yana wannan ƙokarin ya hango muhammadu ya aikasa 'ya kira masa ita,

Koda muhammadu 'ya sanar mata charaf inna tace kaje kace 'ya shigo tunda bazata fito fili ta faɗamun ba ko ta haɗani dashi,

Kafun tace wani abu muhammadu 'ya koma yi masa iso,da gudu ta faɗa ɗakinta domin kimtsawa,bayan lokaci kalilan kuwa sai ga Abdallah nan bisa jagorancin Muhammadu,

Cike da maraba inna tayi masa iso zuwa matsakaicin falonta ,da fara'arta ta amshesa tana mai yi masa maraba maraba kana ta ƙara da cewa "Hafsatu ba zai fito

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login