Showing 21001 words to 24000 words out of 76019 words
zuwa can to ko zaka min dole ne? Sahil ya furta ransa a bace.
Me machine yace ni a wa! bani kudi na kawai,Sahil ya bashi kudinsa ya wuce shi kuma ya nufi kasan gada.
Mata da maza ne a wajen ga karuwai nan iri iri wasu a nan suke badalar su idan Allah ya taimaki mace ta tara kudi ko ta hadu da me kudi sai ta kama gida a wata unguwar ta koma shike nan taci gaba ita.
Sai faman kallon Sahil suke yi,ga maza nan wasu duk sun bar kayansu a wajen sun tafi neman kudi,Sahil ya tsaya yana ta kallon wajen in banda kazanta da wari babu komai a wajen,kamar zaiyi amai ga kudaje na dole wanda kazanta ta kawo su ta dole.
Sahil gajiya yayi da tsaiwa ya tsallaka gefen wasu flowers yayi fitsari,ashe ba a fitsari a wajen sai gani yayi 'yan sanda sun zo sun kama shi,daya a ciki da rashin mutunci yazo yana kiransa da Aboki zai mari Sahil hannun dan sanda baras ya balle ihu ya saki ya tsuguna a wajen,Sauran su tunaninsu kuskure ne yasa Oga ya karye,suka fincike jakar Sahil a jikinsa,duk yana kallon su bai ce kala ba,cikin yan sandan su biyar daya a ciki ya rataya jakar a kafadarsa ya cakumi kugun Sahil yace muje Office suna masifa ya jawo Ogansu ya karye,Sahil ya kalle su yace ku jani ku kaini Office din,Suka fisgo Sahil amma suka ji gam gam kamar sun taba jikin katanga,sai da suka hadu su hudu ko zasu iya daukan Sahil amma gam gam a tsaye,kuma yana motsa jikinsa yana komai amma sun kasa,tsorata suka yi,wanda ya rataya jakar Sahil ya fara kokarin cire jakar zai bashi abarsa amma jaka taki ciruwa.
Yayi yayi ya cire jakar ya kasa,sauran suka tayashi amma taki ciruwa,Sahil suka dawo suna roka Oga please....hannu Sahil ya daga musu yace na yafe muku kuje kawai,wanda jaka taki ciruwa a kafadarsa ya kwabe fuska zaiyi kuka yace Sir....Sir....please....yana nunawa Sahil jakar ya fara sheshekar kuka,Sahil ya barsu a cikin rana ya juya zai tafi ai binsa suka yi da gudu,me jaka yana faman tiri tiri da ita ya rike Sahil tare da durkusawa a kasa yana bashi hakuri yana rokonsa, wanda ya karye kuwa yana yashe a kasa rike da hannunsa yana ta ihu da danasani.
Sahil hannu yasa ya janye jakarsa a kafadar dan sanda sai gashi dansanda ya mike yana murna suna godewa Sahil,Sahil yayi tafiyarsa ya barsu.
A haka ya dinga garari a gari idan ya gaji ya samu waje ko jikin bishiya ya zauna ya huta,ga ruwan sama ko yaushe sai dai ya nemi wajen fakewa.
Bashi da inda zai kwana gashi ruwa zai iya tsinkewa komai dare,tafiya ya dinga yi har ya samu sabon gini kango ne an rufa shi kofa da window ba a sa ba,ciki ya shiga ya ajiye jakarsa a nan sai da ya huta sosai sannan ya samu ya fita ya nemi abinci ya siya ya dawo ya zauna ya cinye abinsa ya sha ruwa pure water,a nan ya kwanta bacci ya kwashe shi wurin duk yashi da siminti.
Islaha ce kwance tana ta tunani ko Ina zai je oho,mikewa tayi tana kwance ta zuba tagumi a hankali ta mike ta dauki wasu kudi ta saka rigar ruwanta a saman doguwar rigar atamfarta wata maroon ta fito.
Tana ta duba Sahil unguwa unguwa bata ganshi ba,ta nufi kasan gada inda marasa galibu suke tafiya taje ta duba ko ina babu shi,ta sake hawa machine tayi ciki ta kangon da Sahil ke kwance ta wajen ta wuce haka ta gaji da nemansa ta koma gida cikin dare.
Washe gari ma da wuri ta tashi ta gama ayyukanta ta sake fita nemansa duk inda tasan yan cirani na zama sai da taje bata ga Sahil ba,har sai da ta kwashe 5days kullum sai ta fita nemansa,shi kuma yana cikin kangon sai dai ya fito ya siyi abinci ya koma.
Kudinsa ya kare bashi da ko sisi babu kudin siyen abinci,Sahil sai da ya kwana ya yini bai ci komai ba ruwa ma a wani pampo ya samu ya sha,zama yayi a cikin kangon yace gwara na koma gida kawai wannan ciranin bazai yuwu ba babu riba a cikinsa,gwara na kira Sahil ya turo min kudi na koma naci gaba da bauta bazan iya ba.
Please call me ya yiwa Sohail nan take Sohail ya kira shi,yace ya lagos din ko ta samu ne? Sahil yace Allah ya tsinewa lagos wlh gwara arewa mutum yana cikin mutunci da sutura,ni dawowa zanyi gida ka nemo kudin mota ka turo min,Sohail yace da wuri haka? Yace ai gwara ka dawo gashi me shago ta zama kawar mu,Sahil yace nemo kudi ka turo min jira nake yau na kwana na yini ba uwar da naci kaje ka roki Adnan a bani kudi dan Allah yunwa zata kashe ni.
Sohail wayar ya kashe ya nufi bedroom din Adnan yayi knocking Adnan sai da ya gama yangarsa ya bude kofa sanye cikin gajeren wando,yana ganin Sohail ya bata rai,Sohail yace dama dan Allah kudi za a turawa Sahil zai dawo gida,Adnan ya kece da dariya ba shiri ya dinga dariyar mugunta harda shakewa yace yaji wuya,ina neman kudin? shi a dole me zuciya,ai ba abinda zai samu dama na fada muku ku hakura da rayuwa ku zauna ku dinga bautar mu kunki ji,baku da gata amma ku kunki yarda shi a dole zaiyi kudi to sai yayi kudin mu gani idan yana da kwakwalwar tara kudi.
Sohail yace arziki dai na Allah ne,Adnan yace au nasiha zaka min? Kai ka isa kayi min fada kana talaka? Me yasa baka yiwa kanka fadan ba ka zama me kudi,kayi tunani me kyau akanka ka zama me kudi in ka isa,amma ina me kudi ai kuwa nine nake da hankali da tunani,talaka ai bashi da hankali tunda ya kasa yin hankalin yin kudi.
Sohail yana jinsa yace hmm bani kudin na tura masa to,Adnan yace sai nan da 2weeks,bashi da kudin abinci fa Yaya dan Allah ka bani na tura masa dan Allah.....Adnan yace wlh na rantse sai nan da 2weeks kuma ko ka kira Daddy bazai bayarba sabo da komai naku yana hannunmu an dawo da rikon ku hannun mu.
Sohail juyawa yayi ya tafi kawai ya wuce bedroom dinsa yana rufe kofar ya jingina da jikin kofar ya zame ya zauna a kasa hawaye ya fara zubarwa sosai yana kuka,ya daga hannaye sama yana rokon Allah yace Allah kaga halin da muke ciki Allah ka fitar damu Allah ka bani kudin da zan turawa Sahil,ya zauna yana addua yana kuka,ya dade a haka ya wanke fuskarsa sanna ya fito.
Maheera ya gani tana Gyara kujeru ta kalle shi taga alamar kuka yayi.
Murmushin karfin hali yayi ya zauna kawai ya zuba tagumi,Maheera zama tayi a kujera daya suna Facing juna tace Sohail lafiya? Me suka yi maka? Sohail ya kwashe labari ya fadawa Maheera yace kuma Sahil yana can ya kwana baici komai ba a kango yake kwana,Maheera tace to kwantar da hankalinka jiya Zayna ta bani dubu talatin tace na siyi kayan sawa ta gaji da ganina cikin tsumma wai kyankyamina take yi a haka,Sohail yace a hakan kika yi kalar kyankyami? Maheera ta daga masa kai tare da furta haka tace.
Aljihun doguwar rigarta ta duba tace gashi sai nayi mata karya nace tela bai dinka min kayan ba,dama dubu talatin a zamanin nan wanne kaya zata siya min na kirki kuma a garin Abuja sai dai atamfa karama da gwanjo. Sohail ya karbi kudin yace na gode Maheera,tace to ba gashi Allah ya rufa asiri ba ai dai ko a trailer ya dawo kamar yanda ya tafi.
Murmushi yayi sai yanzu hankalin Sohail ya kwanta ya fice da sauri ya nemi POS ya turawa Sahil kudin,ya kira shi a waya ya sanar masa,Sahil ya mike yana murna cikinsa ba komai ya fito daga kangon zai nemi me POS ya cire kudin,yana fitowa Islaha tana zuwa wajen a kafa tana ta dube dube tana nemansa,ido biyu suka yi ta ganshi ya rame sosai yayi busu busu da siminti ,Murnar ganinsa tayi tace ina ka shiga dan Allah Sahil yau nafi kwana shida ina nemanka
Sahil ya kalle ta yace ina nan wajen ai yanzu ma fita zanyi kika zo ina zan samu me POS? Kudi zan cire na siyo abinci,Islaha tace zo mu tafi,bayan ya cire kudin suka wuce wajen cin abinci, a nan suka zauna yace ke me zaki ci? Islaha zuciyar Sahil na birgeta yanda yake kula da mace,tace a koshe nake,ai daga gida nake fa,yace to lemo fa? tace zan sha to ta dauki nasa ta sha,yana cin abincin yana kallonta yace kika sa min baki a lemo na bazan sha ba,sai kace kazama ta dauke tace to siyi wani bari na shanye wannan din,lemonsa ya kwace yasa aka kawo mata wani.
Wani matashi ne ya zauna in banda kallon Islaha ba abinda yake,Sahil ya kalli matashin yace kai dauke idonka,Saurayin yace ai da gani budurwa ce baka da ikon hanani kallonta,Sahil ya kalli Islaha a fusace yace ke kika bashi dama ya kalle ki?
Islaha tace ni kaga nace ya kalle ni.
Idan kin san na iskanci kike nema kiyi magana tunda sana'arki ce,Islaha tana zaune ta share zancen tace nifa da zan samu wani aikin a wani gidan barin gidan Aunty zanyi.
Sahil ya kalleta kawai ya gama cin abincinsa ya mike tare da furta nifa Abuja zan koma gidanmu na fasa neman kudin bazan iya ba,Islaha tace da wuri haka dan Allah karka tafi,.
Ke da Sohail aka haifo ni bada ke ba.
A ina gidan naku yake a Abuja? Address ya fada mata,tace number waya please wlh kana da hankali kai nutsatse ne,dariya Sahil yayi yace tab ni din? dan baki san yanda ake cewa bani da hankali bane,ai har mahaukata ake fada mana,amma ai ni na sani me hankali ne,ya bata number wayarsa daga wajen ya mata sallama ya wuce Tasha a kafa yake tafiya.
Yana cikin tafiya a titi wata mota me bala'in tsada ta gaske ta fara wala wala a titi kamar zata yi hatsari Allah yasa ya ganganre kasa a hankali yayi parking a gaban Sahil.
Wani dattijo ne fari da alama bahaushe ne sabo da yana ta waya da hausa sannan kayan jikinsa shadda ce me tsadar gaske,agogonsa da takalmi duk masu tsada ne sosai,gaban motar ya bude yana tunanin kiran me gyara sai Sahil ya tambaye shi yace Baba gyara motar ta samu ne? Yayi murmushi ya kalli Sahil sannan ya furta yaro kana gani karambani yasa nayi tuki da kaina amma bana driving sabo da ido na baya gani sosai ma.
Sahil yace bude motar na duba maka to,Dattijon yace thank you ya bude gaban mota yace ka iya gyara ne? Sahil yace a'a zan gwada dai ko zan samu sa'a,Dattijon yace to Alhmdllh gwada mu gani gaba daya taki tashi ma mutuwa take a hanya.
Sahil yayi tabe tabensa ya gama yace shiga ka kunna mu gani,Dattijon ya shiga ya kunna ta tashi normal,yaji dadi yace ta dawo dai dai amma da har wani kuka take yi,Sahil yace ta warke ai baza ta kara yin komai ba,amma ka dinga kiran Engineer suna mata service akan lokaci.
Dattijon yace na gode ya zaro kudi da yawa yan dubu dubu ya mikawa Sahil,Sahil yace ka barshi akan dan wannan sai ka bani kudi bana bukata,Dattijon dai yayi ta godiya yace sunana Alhaji Isah Danjuma,Sahil yayi murmushi kawai ya juya zai tafi,Dattijon Alhaji Isa yace zo na rage maka hanya mana ina zaka je?
Sahil yace aini bako ne ma zan koma gida da kaina,Alhaji Isa yace ko kana cikin masu zuwa cirani? Sahil yace kamar ka sani.
Okay Okay da alamarka kayi karatu?
Na dai fara University aka cire mu sabo da bamu da kokari bama ganewa mu dakikai ne.
Dariya Alhaji Isa yayi yace kana da kokari mana gashi ka gyara min mota ai kasan me kake yi tabbas,karka damu muje gidana ni ka kwanta min a rai zan taimaka maka karka yi rayuwar da wasu suke zuwa suna zubar mana da mutunci hausawa.
Sahil cewa yayi na gode Alhaji a wajen Allah nake nema,Alhaji Isa yace ka taba ganin anyi ruwan kudi a duniya duk adduar ka? Sahil yace idan Allah yaga dama fa ni yayi min ruwan kudin? Ni Inshaallah Allahruwan kudi za ayi min daga sama!
Alhaji yace ba a ja da ikon Allah amma duk da haka na gode,Sahil ya juya yayi tafiyarsa yana cewa haka kawai ka cuce ni za ayi min ruwan kudi.
Tasha ya wuce ya shiga wata trailer din zuwa Abuja,rana tsaka sai ganin Sahil suka yi ya dawo a rame yayi duhu yayi futu futu,Adnan da Ibrahim suna palo suka dinga sheka dariya harda buga kafa,Zayna ce ta sakko itama daga sama ta hau dariya tace masu zuciyar neman kudi.
Sohail ne ya fito tare da janye Sahil suka wuce bedroom dinsu,Sohail yace duk ka rame sai da na fada maka karka tafi,ya fita yaje kitchen ya kawowa Sahil girki,Sahil ya zauna yaci ya koshi yace Alhmdllh Allah ka raba mu da cirani.
Sohail yayi dariya,Sahil ya shiga toilet ya dinga wanka sai da ya dade yana abu daya haka ma brush duk da yana yi kullum amma na yau na musamman ne.
Yana fitowa sai gashi fes da shi ya canja kaya masu kyau,jakarsa kuwa gaba daya kayan ciki ya zuba a washing machine ya sake wanke su,jakar ma ya wanke ta du ya shanya sannan yayi sallar Azahar.
Sohail yace tashi muje kaga Baby Maheera kawar mu,kwanaki ta rungume ni sai ta maka kaima dama nace sai ta dauki Alkawari.
Sahil yace Good hakan yayi muje,fitowa suka yi gidan ba kowa da Alama mutanen gidan sun fita,a kitchen suka iske Maheera cikin riga da skert yan kanti,Maheera tace barka da zuwa Sahil tana murmushi,Sohail yana gefe,tace ya hanya? barka da dawowa,kaci abinci kuwa? Ta tambaya tana murmushin birgewa,Sohail kawai sai yaji ai bai kamata ace Sahil ta yiwa haka ba,amma sabo da kar Sahil yaji haushi sai ya wayance yace kin fiye dariya da yawa da murmushi,saukinta ma Sahil kika yiwa amma wannan surutun da kike ba birgewa a ciki,kin fini son dan uwa nane da zaki zauna kina surutu? Ki tsaya a matsayinki,abinci dai yaci na kula da abina karki kawo mana iyayi kice ke zaki kula da shi.
Maheera tace kuka ce ni kawar ku ce duka na ma tuna da alkwarin Hugging da muka ajiye yau ga Sahil yazo shima ayi masa,Sohail yace ba yau ba sai ya huta ya gaji yanzu,Sahil yace da Islaha ce ma tayi mana nata zai fi dadi,Sohail yace wace Islaha?
Sabuwar kawace nima na yo mana ita Allah ta hadu tafi wannan ma Maheera din,Sohail yace kai anya kuwa zata kai wannan? Ta kai wannan hankali? Sahil yace tab Islaha dai bata da hankali ita can na tsinceta tana duniyanci,yarinyar nan ta dinga nuna min barikanci,ni Sahil zata yiwa bariki Allah ya kamata ai,Yanzu ma da zan taho harda kuka,Sohail yace ubanta ne kai to da zata yi kuka,ga Maheeran mu.
Maheera tana jinsu tana ta dariya tace ayi maka hugging dinka ko? Sohail yace ance sai gobe ba yanzu ba,muje dan uwa kyaleta tayi aikinta,ka daina kulata sosai sabo da kar a koreta a aiki,Sahil yayi dariya dan shi bai gane nufin Sohail ba yace to ni dama ai ban fiye magana ba.
Fitowa suka yi Islaha anya ta kai wannan kuwa Sohail ya sake tambaya dan abin ya tsaya masa ance zata fi Maheera,Sahil yace sai ka ganta kawai za dai suyi kai daya da wannan din sai dai kamar Islaha din ta fita cola shape,Sohail yace ji karya kai yunwar lagos ta kashe ma ido.
Sahil yace fatar Islaha zam flour suluf suluf,Sohail yace uhm ita wannan din ance maka garin masara ce fatarta? Libis take itama,Sahil yayi dariya yace naga rayuwa a kira Maheera na bata labarin Lagos,Sohail yace ni yafi cancanta ka bawa domin nine jininka,fafur Sohail yaki yarda.
Zuwa dare Maheera ta fito kallo palo ta samu sai Sahil da Sohail kawai,Sohail ya ganta cikin kayan bacci doguwar riga har kasa me dogon hannu,yace me kika fito yi? Tace kallo mana,Koma daki kiyi baccinki,ba a so mace ta dinga kaiwa tsakiyar dare har 10 ta wuce tana kallon aikin banza shedanu zasu shigeta koma ciki.
Maheera tace kallon bazan yi ba haba Sohail fuska ya bata ya kalleta ransa a bace juyawa tayi ba shiri ta koma ciki,Sahil yace mace sai da muzurai ka birge ni.
gobe zamu je ka rakani muyi sabon aski cewar Sahil"
Sohail yana kallo yasan askin Sahil ya lalace amma sai yace ai askin ka fes yake bro,ba sai kayi ba,ni ya kamata nayi sabo kalli nawa fa duk ya lalace kai kuwa fess kake kana taba gashinka zai lalace.
Sahil yace baka isa ba sai naje ya zaka barni na dawo kazami,bakin ciki zaka fara min? Sohail yace Allah ya kiyaye ni nayi maka bakin ciki Sahil im sorry muje taren.
Washe gari suka yo askin su iri daya gashi yaji gyara,Sohail Allah Allah yake kar Maheera taga Sahil,sai kuwa suka sameta a palo tace kaiiii mashaallah kunyi kyau yan biyu na rasa wa yafi kyau ma,Sahil ya harareta dan me zaki yabe ni ke mama ce? Maheera baki ta bude tace daga abin arziki? Sahil yace ae bana so a yabe ni,Sohail yace yawwa a kyale mu yana hararar Maheera suka wuce.
Maheera tace