Showing 15001 words to 18000 words out of 76019 words
ta sake saki tace amma yau naji dadi come ba zato Sohail yaji anyi hugging nasa,ido ya zaro da sauri ya janye jikinsa tare da ja baya yace mene haka? Sahil fa baya nan,to wlh shima sai kin masa na rantse.
Ido Maheera ta zaro tana murmushi tace Sahil din? Sohail yace ke ba a wasa damu na fada miki sai kin masa shima ya hade rai,Maheera tace to never mind zan masa shima amma ai kaine abokina Sohail ka gane?
Ni bazan gane ba kawai malama zamu yi fada,Sorry to zan masa shike nan?
You promise? ya sake tambaya,tace yeah,yatsa ya mika mata yace mu kulla,ta kawo nata suka kulla ta furta shima sai an yiwa Sahil? yace kamar da kasa.
Juyawa yayi zai tafi ta ruko shi tace na sallameka ne? Ban gane ba sai ma kin sallame ni? Ke mace fa ni baza ta juya ni ba in fada miki gaskiya 'yar nan, Maheera tayi dariya tace to fa,har ya tafi ya dawo yace na fasa tafiya zo muyi game?
tace wacce iri ba kayan game a nan.
Wasan yar buya buya zamuyi,okay ka bari sai gobe idan naje test sai muzo muyi kaga ko Oga ya kama mu kawai korata zaiyi shike nan.
Sohail yace no ba a haka kuyi rabuwar mutunci basai munyi ba tunda baya so.
Okay tace kawai,kallo ya fara kare mata yace wai mene wannan a kirjin ku?
Sam Maheera bata gane ba,yace gashi nan tulu tulu ana gani.
Maheera fuskewa tayi duk da taji kunya tace shi kuka sha kuka girma,yace Allah sarki na Mama yana kabari yanzu ina tunosa ke ya akayi naki chakare chakare ita kuwa Umma Nadia nata kamar na tsohuwar saniya wacce yunwa ta kamata.
Maheer ta dinga dariya ba shiri tace Umman taku guda?
Sohail yace ke bafa ita ta haife mu ba Na Mama yana Kabari nata me kyau ne Daddy ma ya dinga ta yashe baki idan tana wajensa ya dinga ta dariyar dole hahahaha ranar girkin Mama,Allah ko ni sai na iya Auren Mamata.
Dariya ta sake kama Maheera tace ashe ta hadu dai?
Yace tab ke kin isa ma kice shekarunta 47, Mamanmu ta iya sa kaya ko wanne wanka kyau yake mata ga kamshi,gata da mutunci ke Mama fa duniya ce,akwai uwar data kai tamu ma,Maheera tace Mamata fa? Sohail ya bata rai yace ko uwarki bata kai Maman mu ba.
Da sauri Maheera ta kalle shi tace zagina kayi fa Sohail,yace to ba uwarki bace? Uwarki mana nace bata kai tawa ba,nifa in kika takura min zan iya miki dukan tsiya.
Maheera tace ni din?
Kwalla ce ta cika masa ido tab da ya tuno da Mama Asmau.
Maheera tace sorry mene abin kuka? Yace baza ki gane bane... baza ki gane ba ina ta so na baki labarin damuwa ta sai kice baza kiji ba labari na akwai jira kafin a saurara,tsaki ya ja ya fice yayi tafiyarsa .
Maheera ta tsaya kamar gunki tana mamaki.
Bata yi tunanin zata ganshi ba washe gari ba
Sai gashi da yamma ya sha farar shadda tana shining ba karamin kyau yayi ba ka rantse wani me kudin gaske ne,ga kyau,ita kanta Maheera tsayawa tayi tana ta faman kallonsa,hannu daya a aljihu ya shugo yace ya garin me shago? Tace lafiya lau tana murmushi.
Hannunta ya riko yace zo mu tafi.
hararsa tayi tace bazan je ba shine jiya kayi fushi?
Yace ni din? Yana nuna kansa da yatsa yace me nayi jiyan?
Au ka manta? Yace na manta kuma har ga Allah har ya manta ma,sai da ta tuna masa yace Oh ya share zancen kamar ba shi ba.
Mikewa tayi suka fito,zata rufe shagon ya karbe key din yana cewa kawo kamar namiji mace tana wahala haka Mama bata irin haka,ai ana taba ki kice wash zan mutu.....harda gwadawa! dariya Maheera ta fara yi ba shiri har ya gama rufe shagon yace muje
Juyawa tayi tana rataya handbag dinta,yace kawo handbag din na rike miki ki daina wahala zaki yi muscles kamar na maza ki bubbude.
Jakar ya karba ya rike a hannunsa suna tafiya suna hira,yayi hauka yayi hankali a haka har suka je gidan su.
Maheera kanta ya kusa bugawa ganin irin unguwar da suke da layin da suke balle uwa uba gidan nasu tamfatsetse na gani na nunawa sa'a,tace a nan kake zaune? duk bata kawo gidan uban Sahil da Sohail bane,tunaninta ma yaran riko ne ko 'yan uwa.
Sanda suka shiga Maheera tana ta kalle kalle ya kalleta yayi dariya yace kinga gida me kamala ko? Yana dariya yace ai kamilallen gida ne wannan ba ballagazin gida ba irin naku,nasan gidanku ballagazin gida ne.
Maheera tayi dariya tace kaima ai ba naku bane,bai ce mata komai ba,yace muje na nuna miki kitchen din,In kin gama girkin ki shirya a dining sai na kira su masu gidan su dandana.
Haka ya fisgi hannunta ya jata ko ina na gidan sai da ta dinga hakkin sosai yanda yake fisgarta sai hakki take da nishi, da sauri yana nuna mata ko ina har katafaren kitchen din katon gaske komai akwai ciki,ya nuna mata komai da kayan sarrafawa,kin gane? tace ae naga komai da nake bukata akwai,yace yawwa to fara girkin ni bari naje na gyara dakin Adnan da na Ibrahim kafin nan kin gama,ta furta ba damuwa,ya juya ya tafi.
Farfesu ta fara yi na naman rago sannan ta tsara fried rice lafiyayya taji hadi da su hantar rago da naman kaza,sannan ta hada couslow da lemo ingantacce ta shirya a Dining, har da potatoe ball tayi da kwai da nama a tsakiya.
Tana gama shiryawa a dining ta zauna a palo tana kallon tv,sai taji karar takalmi me tsini ana sakkowa daga sama ,Kamshi na mamaki ya mamaye palon.
Zayna ce take sakkowa ta sha wata material gown ready made abinta golden ta tsula kyau,kana gani kasan taji hutu da kudi ba karya,Maheera tsabar tsananin kyawunta yasa duk inda mace takai bata isa ta fita ba sai dai daiku tunda a duniya baka rasa wanda ya fika dole ne wannan.
Zayna wani kallo ta bi Maheera da shi sama da kasa ta ganta sanye cikin material silk black me adon flower pink sai dan mayafi siriri data dora a kanta,takalminta normal dai na talaka me dan kyau gashi nan dai,sai dai kyawun Maheera ya tsoratata amma ganin mijinta yana da class kuma sannan yana sonta gashi ma shi sai me kudi yake kulawa sai kawai ta fuske a ranta tasan itama me kyauce komai da namiji ke nema wajen mace tana da shi.
Maheera mikewa tayi tsaye da sauri tace good day Ma,Zayna ta wuce Dining kawai ta zauna ba tare da ta wani amsawar kirki ba,Ibrahim ne ya fito yayi arba da Maheera ya bita da uban kallo ya dauke kai ya wuce Dining ya zauna,shima tace Good day Sir, har tana risinawa,hannu kawai ya daga mata,Adnan ne ya fito shima yana zuba kamshi ya hade cikin kana nan kaya masu tsada blue, ko kallo Maheera bata isheshi ba ya zauna a Dining,sai ga Sohail shima ya fito sanye cikin gajeren wando da riga singlet da bocket da mopper a ciki ya hada uban zufa.
Hannunsa ya goge da karamin towel ya karaso wajen Maheera yana murmushi yace kiyi serving nasu cikin rada yayi maganar.
Maheera ta karasa da sauri tana cewa kuyi hakuri" nan take ta fara serving nasu har ta gama,suka ga girki sharr tun a ido ga kamshi.
Ibrahim ne ya riko hannun Maheera zata juya yace zo ki canja min Spoon 'yar kauye.
Tsoro Maheera taji akan idon Sohail aka yi,daga haka Sohail kawai idonsa ya canja ya nufi Ibrahim gadan gadan ya sa baki a saitin keyarsa ta baya ya gartsa masa cizo sai da wajen ya fashe,Ibrahim ya saki kara da ihu ya mike zasu yi kokawa da Sohail!
Adnan yayi sauri ya rike Ibrahim yasan yana hada jiki da Sohail sai buzunsa karfinsu ba na mutane bane,yace kyale shi kai zaka biyewa mahaukaci,abin kullum karfi yake fa sun fara duka da cizo nan gaba sai tsince tsince a bola suna bin yara da gudu.
Zayna ta tabe baki tace yo ni da suka ce zasu aure ni su biyu ma.
Sohail yace in Allah ya yarda baza ki haihu ba,mahaifarki ta mutu a haka zaki gama aurenki,Adnan yace ameen da sauri kayi addua me kyau dama ni bana son haihuwa, Zayna kamar zata yi kuka tace da Sohail mahaukaci karya kake,Maheera tana ta kallo ta gaji ta janye Sohail tace relax mana ta jashi suka koma gefe suka zauna,Sohail yace da Sahil ne ya rikeki da sauki bazan damu ba ai wannan ba yi bane,kawai a rike mutum idan kika masa ciki fa,Maheera ta danne dariyarta,tace au ba ma shine zai min cikin ba nice zan masa? Ina ka taba ganin namiji ya haihu?
Sohail yace ke wancen kwarto ne tsaf zai iya haihuwa,tayi murmushi kawai tana boye dariyarta.
Kallonta yayi yace ki dinga rufe wannan chakare din naki ni bana son ganinsa duk sai gani ake ta yi Mama fa Hijab take sawa idan zata fita ba a ganin nata,badan ma mama ce ba ai sai nace miki bata da Chakare din nan.
Amma ke kowa sai gani akeyi haba Allah za a daina ce miki Classy girl me shago kawai yafi dacewa dake,Maheera ta rufe bakinta sabo da dariya.
Can gefe kuma su Zayna sai kwasar girki suke yi me shegen dadi suna ta ci,Adnan cikin santi ya kira Maheera da hannu,ta karasa a nutse yace aikinki yayi kyau na daukeki aiki,zan dinga biyanki dubu dari,tana murna tayi ta godiya abinta yace gobe ki dawo nan da zama ki fara aikinki,ga Sohail nan zai nuna miki room dinki,tace na gode Sir na gode ta juya ta fice.
Ibrahim sai duri yake ko kala bai ce ba,itama Zayna haka.
Maheera ta fice daga gidan tana ta murna,Sohail ya biyo bayanta yace dama na fada miki zaki samu baki yarda dani ba gashi kuma,tace na yarda ai yanzu na gode sosai Sohail,yace ki daina gode min ni,muje to ka rakani,yace a'a na gaji ni bacci zanyi,tace to bye,ya juya abinsa ya tafi itama ta wuce gidan da take kwana gidan wata kawar Maman su,matar tana auren me rufin asiri a Abuja,itace ma ta samowa Maheera aiki ganin halin da suke ciki a suleja ta kawota gidanta Abuja ta samo mata aiki,matar yaranta uku yare ce kuma na Igala,tana da kirki ga tausayi.
Gida Maheera ta koma tana murna ta samu wacce suke kira da maman Rahmat a palo,maman Rahmat tace yau ya naga yarinya ta tana murna?
Maheera ta bata labarin samun sabon aikinta da salary dinta,ta bata labarin Sohail,Maman Rahmat tace Alhmdllh sai dai zanyi missing zaki barni na daina cin girki me dadi amma na tayaki murna Allah ya taimaka ya bada sa'a,a kula sosai a tsare mutunci,sai kiyi waya ki sanar da yan uwanki da Mamanki ko?
Maheera tace ae anjima da dare zan kira su,kema ki kira Oga fadlu ki sanar masa ya nemi wani ko wata,Maman Rahmat tace yanzu kuwa zan sanar masa inshaallah,Yaran Maman ma suna tayata murna" tashi tayi ta shige bedroom tana cewa thanks.
Washe gari da safe da wuri Maheera ta hada wasu kayanta a akwati me kyau ta tafi gidan su Sohail,har kofar gida me taxi ya sauke ta,knocking tayi dake Sohail ne ke bude gate basu da me gadi,shuru ba a bude ba sai da ta gaji ta turo karamar kofar ta jikin gate sai taga ta bude kawai ta shugo.
A compound ta hango Sohail yana zaune a kujera ya harde kafa daya kan daya yana ji ana knocking bai kula gate din ba,tana shugowa ya bude idonsa da yake a lumshe ya kalle ta kawai,ta karaso inda yake tace Hey,Hey shima yace sannan ya wani tafi dogon tunani sai da ya jima a haka tana tsaye tana kallonsa sannan yayi zumbur ya mike yace oh wai kece?
Akwatin ya fisge a hannunta yace idan an hanaki daukan heavy abu bakya jin magana kawo muje ciki,ta bishi tana murmushi suka shiga ciki ya nuna mata bedroom hadadde kamar dakin amarya yace ga room dinki,tace na gode Sohail,ya hade rai tare da furta ki daina min godiya ki godewa Allah,tace ai ina gode masa yace wannan ke ta shafa,kije ki ma matar gidan girki kafin 5pm suma su Adnan kiyi musu nasu,Maheera tace to ta mike ta wuce kitchen.
Tana tsaka da girkin Sohail ya shugo sanye da jallabiya wata fara dangalalliya duk kaurinsa a waje fari kal me dauke da kwantaccen gashi me kyau yace yana kallon Maheera ya aikin? Murmushi tayi tace Alhmdllh
Yana murmushi yana sosa gashinsa ya furta ko na tayaki?
tace a'a na gode,zai kara magana tace jeka kawai karka jawo min a koreni a aikin nan suce wani abu muke yi ka rufa min asiri,Okay....okay...ya furta yana kallonta ya juya ya fita ya barta tana aikinta, kamshin girkinta ya cika gidan,tana gamawa ta shirya dining Sohail yana can yana wanke mota.
Maheera sai da ta tambayi Zayna ko za a miki wani abu Hajiya? Zayna tace no sai anjima ki dora abincin Ogana, okay tace,taje kitchen ta kwashe ragowar a plate da Spoon ta fito har inda Sohail ke wanke mota,tace ga abincin naka,yace harda ni? tace ae mana,yace ki daina dafawa dani kar su gani suji haushina ke 'yar aikin su ce ba 'yar aikina ba,to yanzu dan kaci abinci sai ya zama matsala? Yace hmm kawai......Adnan ne ya shigo da motarsa wata benz me shegen tsada,a idonsa yaga Maheera tana mikawa Sohail abinci,mantuwa yayi ya dawo gidan shima.
Fitowa yayi a nutse cikin suits me tsada yana danna waya,yana zuwa inda suke tsaye ya dakawa Maheera tsawa sai da ta firgita,yace ke waye ya dafa abincin da kike bashi? jikinta ya hau mazari tace ni..ni...nice na dafawa Hajiyanka shine da ya ragu na bashi.
hannu Adnan ya sa ya fatalar da plate din a hannun Maheera,abincin ya watse a wajen a kasa ya furta look daga yau ke ba yar aikinsa bace,ni na daukeki aiki ni kadai zaki yiwa aiki tare da matata da kanina,idan ba haka ba zan koreki a aikin,idan yana son yaci abinci ga kitchen ya dafa da kansa.
Juyawa yayi ya kalli Sohail yace ka dakko abin shara ka share nan kayi clearing komai ya ja tsaki ya juya abinsa ya wuce ciki.
Maheera tace ikon Allah haka kake shan wahala? Murmushi Sohail yayi yace rayuwa kenan ya za ayi ko a jikinsa ma taga ya dakko abin shara ya share wajen tas ya tattara plate din ya maida kitchen.
Maheera tana ta kallonsa cike da tausayinsa,yace kina ta kallona zan dafawa kaina karki damu.
Jikinta a sanyaye ta koma ciki gaba daya tausayin Sohail ya kamata duk tunaninta dan aiki ne suka dauke shi a gidan.
Daddy Ali ne ya kira Adnan ya sanar masa cewar zaizo Abuja wani aiki zai kawo shi amma a ranar zai koma kano ba zama zaiyi ba,Sohai ma bai sani ba washe gari Zayna a kitchen ta samu Maheera tace ke Maheera kike ko wa? kiyi abinci lafiyayye da wuri before 2pm surikina zai shigo,Maheera tace Alright ma.
Ta fara girke girkenta Sohail ya sameta yace yau girki da wuri? Wai surukin Madam ne zaizo,Sohail baki ya tabe yace na sani ai,sun fada maka ne? Yace sai sun fada min ma,ko sunanki ai ji kika yi na fada miki to ko basu fada min ba na sani yana hanya yanzu ma.
Maheera bata karyata shi ba,kira Sohail yaji Ibrahim yana kwala masa kamar zai fasa gidan,Maheera tace jeka ana kiranka,fitowa yayi da sauri,Ibrahim yace kawo min glass of juice,Sohail ya koma ya kawo masa lemo glass cup,yana karba yace jeka dakina zaka ga wani note book green ka dakko min shi sauri.
Sohail ya wuce sama da sauri har hadadden dakin Ibrahim yana dubawa ya hango notebooks guda uku daya green,daya blue,daya grey color,Sohail ya dauki daya ya duba yace wanne ne green din a haka ya daga sama yana karewa ko wanne kallo,blue din ciki ya dauka yace yesss....wannan shine green ya fito ya kawo.
Ibrahim takaici ya kamashi yace wannan yayi kama da green? shine green din? Sohail yace idonka baya gani wannan ai shine green,wannan color din itace ta dace da green haba Yaya kalli ko idon naka computer ta fara kashe shi,uwarka ce computer din ai.
Sohail ya furta ai kuwa da mun huta sai muyi ta danna ta ba ruwanmu muyi game muyi kallo,computer uwar mu guda ai sai game kawai,tsaki Ibrahim ya ja cike da takaici ya fisge littafin ya tafi da kansa ya dakko abinsa.
Sohail ya bi littafin da kallo yace wannan ne green? blue fa ka dakko,Ibrahim yace Sohail dan Allah tafi ka bani waje just go....
Sohail ya nuna hanya yace na tafi kake nufi?
Ibrahim bakar magana ya fada yace a'a ka zauna nace,Sohail ya dawo palo ya zauna tare da harde kafafu yace na gode Yaya yana dagawa Ibrahim gira kamar dan iska,Ibrahim yace kai Sohail karuwa ka gani a nan a zaune? kana wani daga min gira kamar dan iska yaga karuwa.
Sohail ya sake kashewa Ibrahim ido yace ai mu idan iskanci zamu yi karyar karuwa ta kama kafar mu,dariya Ibrahim yayi ba shiri,yace gaskiya haukarku shahararriya ce, Sohail yana jinsa yace Yaya Ibrahim jiya Allah kaje kayi iskanci da wata mace sunanta Bilkisu,mamaki ya kusa kashe Ibrahim,yace a gidan uwarka?
Sohail yayi murmushi yace Allah kayi Sex da wata kuma shine na farkonka ta rinjayeka,ka cuci kanka tunda kakai wannan shekarun baka taba yin iskanci ba sai jiya,duk shekarun da ka kwashe kana hakuri sun tashi a banza fa.
Ibrahim ya hade rai yana muzurai yace kai