Showing 12001 words to 15000 words out of 120086 words
naji tana yi shiyasa nace da shirinta ta fito."
Dan murmushi Uwargida tayi sannan ta zaunar da Asmau a kusa da ita
" ke amarya ce ko?" Ta fada tana daga gira.
"Irinku yawanci mijin ne bakwa so sai ku gudu. Shiga duniya ba da ka ake yinsa ba. Dole ki fara ta wani wurin. Kamar yadda na fada miki ko wurin zama ki samu nan gaba idan kika shafa kika ji babu abinda zaki ci nasan zaki fara sana'ar da bata tsufa. A lokacin zan taimaka miki da kayan aiki wato maganin mata sannan na hadaki da kilayen(client). A tsarin gidan nan duk wadda tayi ciniki a gida ko a waje zata bani kaso goma a ciki. Sauran bayani dai sai kin shigo hannu. A lokacin kuma zan saka miki suna. Ni nan babu ruwana da sunan kowace yarinya na gaskiya."
Yarinyar dake tsaye a gefe tayi tsaki "haba Mama tace ba abinda ya fito da ita ba kenan ko dole ne?"
Bulayi ya kalleta yana dariyar shakiyanci "ustaziya Zubaida kenan, kina nan da halinki na korar mana alheri".
Baki ta murguda masa Uwargida tace " yanzu ma fadan da nake mata kenan ya kamata ta ajiye girman kai ta rungumi sana'ar da na haifeta kuma na raineta a ciki shine ta fara min rashin kunya na bige shegen bakin."
Asmau ta sake kallon yarinyar sai taji tana sonta. Murmushi tayi mata yarinyar ta mayar sannan Uwargida ta umarceta da ta nuna mata daki daya cikin wanda babu kowa. Babu yadda Asmau ta iya dole ne ta nemi muhalli kafin tasan yadda zata fara gudanar da rayuwa. Shiyasa ta bi bayan Zubaida. Wani daki ta bude duk yayi kura. Zubaida tace bari na kawo tsintsiya. Bata dade ba ta dawo da yake akwai wutar nepa ta kunna fitilar dakin. Sai da ta taya Asmau shara da goge kura suka karkade yamushasshiyar katifar dakin da babu zanin gado. Bayan sun gama Zubaida ta fita sai gata ta dawo da tuwo wanda aka fara ci da ruwa a kofi.
Tana murmushi tace "Allah Yasa ki iya ci dazu na fara ci Mama ta fara damuna na barshi. Don girman Allah da Ya haliccemu kada kiyi karuwanci. Gidan nan har mace ta nemi mace anayi."
Asmau ta karbi tuwon da murna taci tayiwa Zubaida godiya sannan ta kara tabbatar mata da cewa da zarar komai ya daidaita barin gidan ma zatayi.
Zubaida tace "idan babu damuwa ki fada min abinda ya raboki da gidanku".
Ajiyar zuciya Asmau tayi "in sha Allahu gobe zan fada miki tarihin rayuwata".
Zubaida sai murna take. Har ta fita ta dawo da sauri "ina kara tuna miki kada kiyi sana'ar matan gidan nan. Mata da yawa da farko haka suke cewa sai an kwana biyu su fi kowa lalacewa. Ni ma ba don bani da wurin zuwa ba da tuni na bar gidan nan."
A haka suka yi sallama. Da Zubaida ta koma dakinsu har ta kwanta addu'a take yi Allah Yasa bakuwar nan kada tayi halin matan gidan. Bata da wani ilimin addini amma tasan cewa sana'ar da ta tashi taga mahaifiyarta tanayi bata da kyau..
Washegari shayi da bredinta ta dauka zata fita daga dakinsu Uwargida ta kalleta tayi murmushi.
"Zuby tawa kenan, da kinga bakuwa kin rinka rawar kafa kenan ke a dole sai kinsa ta koma gidan iyayenta. Rayuwar duniyar nan ta wuce tunaninki fa. Ki sani duk wadda kika gani a nan to abinda ya korota yafi nan muni."
Zubaida ta gallawa Uwargida harara ta fita. Kai tsaye dakin Asmau ta wuce. 'Yan matan gidan suna ta mata dariya don sun saba ganin irin haka a wurinta idan taga bakuwa.
Da sallama ta shiga dakin. Asmau na gyangyadi a zaune. Kyamar katifar yasa bata kwana a kai ba. Kusan kwana tayi tana koke-koke da addu'o'i. Cike da farincikin ganin Zubaida ta amsa mata sallama.
Zubaida na zama ta mika mata abincin ta karba da godiya taci. Sannan ta tambayeta inda ake samun ruwa domin taimama tayi da asuba tayi sallah.
"Meye kuma taimama?" Zubaida ta tambaya.
Asmau tayi mata bayani. Zubaida ta gamsu sannan ta sanar da ita kowa a gidan siyan ruwa yake yi. Dole sai ta siye duk wani abin amfani sannan ta tanadi kudin hayarta domin anjima kadan Uwargida zata bukaci ta kawosu. Bayan duk ta gama jin bayanin gidan ne Zubaida tayi mata tuni akan alkawarinsu na jiya.
Asmau tayi murmushi mai ciwo sannan ta fara sanar da Zubaida dalilin watsewar farincikinta.
*FARKON LABARI*
Alh Shu'abu Yahaya sunan mahaifinsu Asmau. Iyayensa duk 'yan Kano ne kuma a nan cikin Kanon suka tashi. Su biyar ne a gidansu shine na biyu. Babbar yayarsa suna kiranta Yaya Abu sai shi sannan mai binsa Rabe sai Lami da Garzali.
Babansu mazan kawai yake sawa a makaranta. Saboda haka Shu'aibu yayi karatu har matakin digri inda ya karanci Agric Science harkar aikin gona. Shi mutum ne mai saukin kai da kirki shiyasa mahaifinsu yake ji dashi. Sauran 'yan uwansa kuwa kusan duk halin Hajjo mahaifiyarsu suka debo na fada da sa ido.
Lokacin bautar kasa aka tura shi makaranta a wata karamar hukuma a jihar Niger mai suna Wushishi. A can ya hadu da Bara'atu tana ajin karshe na sakandire. Farkon haduwarsu duk da baya koyar da 'yan ajinsu soyayya ta kullu a tsakaninsu. Abu kamar wasa har lokacin komawarsa gida yayi inda yayi mata alkawarin turo iyayensa. Dama a hannun kawunta take ita da kanwarta Bintu marayu ne ko kadan basa jindadin zama da matar kawun.
Da ya koma Kano ya sanar da iyayensa Hajjo ta dage indai tana da rai danta bazai auri banufiya ba. Duk 'yan Niger mayu ne a cewarta. Ita a son ranta ya auri 'yar kanwarta. Akayi ta jan zance ita da mahaifinsu shi kuma ya dage Shu'aibu sai ya auri wadda yake so. Rigima sosai akayi sai bayan wata biyu iyayensa suka je Wushishi. Lokacin Bara'atu har ta fitar da rai. Ba wani dogon lokaci aka saka bikin ba gashi ko aiki bai fara ba. Wurin hada lefe yasha wahala Bara'atu ta bashi kudi cikin kudin gadonta ya cika ya siya mata kaya masu kyau. Haka aka yi biki aka kawo amarya Kano ita da kanwarta Bintu saboda bazata iya barin kanwar a hannun matar kawunsu ba ta cigaba da azabtuwa.
Wani bangare aka gyara musu a cikin gidan iyayensa suka tare a ciki. Zaman lafiya sosai suke yi da mijinta sai dai a wurin Hajjo da 'yan uwansa tana ganin wulakanci mara misaltuwa. Daga ita har kanwarta basu da sunan da ya wuce Mayya. Gashi dama duk suna da idanuwa Tubarakallah.
Duk wani aiki na gidan ya dawo wuyansu amma bata taba korafi ba. Kullum Shu'aibu sai dai ya bata hakuri lokacin yana ta fafutukar neman aiki. A haka ta samu ciki har sau uku yana barewa saboda aikin wahala.
A karo na ukun ne da safe Hajjo ta shigo taga Bara'atu bata sha kunu da kosan da ta aiko mata dashi ba wanda babansu Shu'aibu ne ya tilasta mata dama.
Fuska babu walwala tace "Au baku karya ba har yanzu saboda ki jawo min fada wurin Malam yace bana kula dake?"
Daga kwance inda take saboda rashin kuzari Bara'atu tace "Kiyi hakuri na koshi ne".
Hajjo tayi dariya "yo ba dole ki koshi ba, kunyi kalaci da jikana ke da kanwarki. Ai Shu'aibu ya gama janyo mana masifa. Nan gaba kadan ma mu zaku bi ku lamushe."
Bayan ta gama fadanta ta fita Bara'atu babu abinda take yi sai kuka. A wannan yanayin Shu'aibu yazo ya sameta. Hakuri ya bata kamar kullum tare da kyakkyawan albishir na cewa ya sami aiki a jami'ar Ahmadu Bello ta Zaria a matsayin lecturer matakin farko. Kuma har da gida aka bashi. Murna a wurin Bara'atu ba'a magana.
Kafin su tattara su koma Zaria ne mahaifinsa ya fara cuta yana ta ramewa. Hajjo tasha kuka tana rokon Bara'atu akan ta sakar mata kurwar miji.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽12
Batul Mamman💖
*BAYAN SHEKARA DAYA*
Anti Bintu tazo Kano wurin yayarta yawon arba'in. Tunda tazo kullum sai sun fita kasuwa siyayyar kayan amfanin gida. Duk wani kudin Bara'atu na albashi, kasuwanci da abinda ta samu na gado ta hada shi a gini da zuba kayan bukata a sabon gidan. A lokacin falo da dakuna biyu kawai ta gama sai kitchen amma bahaushe yace da babu gara ba dadi. Hatta sutura da Hajjo ke yi mata gorin bata siyawa yaranta duk ta siya. Dama tara kudin take sai ta gama da abinda yafi mahimmanci.
Sai da ta gama shirinta tsaf sannan wata juma'a bayan su Asmau sun dawo daga makaranta tasa sukayi wanka duk ta basu sababbin kaya sannan ta hada sauran 'yan kayansu suka tafi dakin Hajjo. Duk yaran mamaki ya ishe su ina Umma zata kaisu sun kwashe duka kaya.
Kwadon zogale take ci yaran Rabe suna zaune suna wasa a gefenta tana dariya. Shigowar Bara'atu da 'ya'yanta yasa ta hade rai.
Dan Rabe na biyu sarkin gulma ya ruga ya fadawa babansa ga Anti Bara da su Jafar zasu fita yau sunyi kwalliya. Daga shi sai dogon wando haka ya fito da sauri jin kwaf.
Bara'atu na dauke da jaririyar Bintu tace
" Hajjo albarkacin zaman tare a yafemu Allah Yayi zamu tashi"
Zaro ido sukayi ita da Rabe. Shi a son ransa idan Bara'atu ta gaji da takurata da akeyi ta yarda da aurensu. A ranar ma zai saki Sagira.
"Ina zaki kai min yaran da kike cewa zaku tashi? Idan tafiya zakiyi ke kadai dai ga hanya nan."
"Ba nisa zanyi ba Hajjo, nan layin gidan sabon kwamishinan 'yan sanda zan koma. Cikin ikon Allah na kammala gini na."
Ashar Rabe ya fara saki sannan yace "kika kammala wane ginin? Waye ya baki filin da kudin ginin?kada ki raina mana wayo wani saurayin kika yi kuke zaman....."
Katse shi tayi kafin yayi barambarama gaban yara.
"Fili dai tare muka siya da wannan da kuke ciki ni da babansu Yassar. Ina sana'a ina aiki. Allah Ya buda min gashi nayi gidan kaina. Wannan da kuke ciki kuma har abada ku sani cewa gidan marayu ne. Allah SWT kuma Yace wanda yaci dukiyar marayu tamkar yana ciwa cikinsa wuta ne."
Hajjo ta bata rai "nufinki mune 'yan wutan..Bara'atu ki kiyayeni wallahi. Kuma idan kika fita da yaran nan to ki sani babu ni babu su."
"Ai aikin gama ya gama. Yara dai ke kika haifi babansu saboda haka jininki ne. In Allah Ya yarda zasu rinka zuwa gaisheki tunda ba nisa mukayi ba."
Daga haka suka fice Rabe yana binsu a baya yana kiranta.
*****
*Sabuwar Rayuwa*
Wannan tashin nasu shine ya kara kiyayya tsakanin iyalan mariyayi Shu'aibu da gidan Hajjo. Kamar yadda ta fada duk juma'a bayan masallaci take tura yaran gaishe da Hajjo. Manyan kullum sai sun dawo rai a bace ko da hawaye a idonsu. Amma hakan baisa ta dena turasu ba saboda tasan su din dai suka rage musu dangin uba.
Rayuwa sabuwa suke yi cike da 'yanci da jindadi. Bara'atu ta dage wurin bawa yaranta tarbiya. Sannan tana nuna musu soyayya irin wadda bazata sa su sangarce ba. Shakuwa mai karfi ce a tsakaninta da 'ya'yanta.
Washegarin tarewarsu suka shiga makota domin gabatar da kai. Lokacin da suka shiga gidan Kwamishina Mama Yalwa tayi musu tarba ta karramawa. Dama sun saba da Umma. Duk yaranta suna gida ta kirasu ta gabatar dasu ga 'yan uwansu kamar yadda ta fada musu. Abdulhalim, Nasiba da Abubakar dai duk sun girmesu amma suma sunyi kokarin jansu a jiki.
Bayan 'yan kwanaki ne Mama Yalwa taje gidan Umma take sanar da ita Baba yace ta rinka turo su Asmau ana yin magariba masallacin gidansu akwai Malamin da yake koyar dasu Sadiya karatun Qur'ani zuwa karfe tara.
Umma taji dadi sosai,duk da suna zuwa islamiyya amma wannan ma zai taimaka kuma ba nisa suka yi da gida ba.
_Asmau S. Yahya_
Ranar farko da zasu je makarantar kowa yana doki banda Asmau. Haka take da tsoron mutane. Duk gidansu ita ce ta kasa sakewa da yaran Mama.
Kowa ya shirya ta kwanta ciwon cikin karya saboda taji ance kowa karatunsa shi kadai malam zai biyawa. Yadda zata yi karatu a gaban su Suwaiba ne yake kara tsorata ta. Umma na ganinta tasan ciwon karya ne. Da rarrashi ta lallabata suka tafi suna idar da sallar magriba.
Cikin gidan suka fara zuwa suka gaishe da Mama sannan suka fito waje. Suwaiba 'yar Mama ta hudu ita ce kusan sa'ar Shema'u amma duka ita da Sadiya sun zama kawaye da Shema'un. Tare suka fito zuwa masallacin Asmau na bin bayansu rike da hannun Aina'u.
Malam Hadi yana zaune tare da Abdulhalim, Abubakar da Umar. Suna zuwa gaishe shi suka yi kowa ya sami wurin zama. Sai da ya gama da manyan sannan yaji karatun su Suwaiba. Daga nan ya fara jin inda su Asmau suka tsaya yace kowa sai ya biya surar karshe inda ya tsaya.
A nan ake yinta ana zuwa kan Asmau da ta fuskanci idanu sun dawo kanta tana yin Bismillah sai hawaye. Malam yace ta barshi ya gama da sauran .Shema'u tayi tsaki tace " malam wallahi ko a islamiyya haka take yi sai taji bulala take kawo hadda."
Murmushi yayi "ni bana duka kinji Ma'u. Bari na gama da kannenki sai ki biya min."
Hatta Aina'u sai da ta karanta suratul Ikhlas amma ana dawowa kan Asmau sai kuka. Jafar yace Ummansu tace a zaneta idan bata yi karatu ba.
Tunda ta fara kukan farko Abubakar yake kallonta. Dariya abin ya bashi sai da yaga taki denawa ta soma bashi tausayi.
Malam Hadi yayi har ya gaji taki karatu sai kuka da rawar murya. Yace kowa ya fita banda manyan yayye. Suna tafiya ya nuna mata Abdulhalim da Abubakar
"Waye a cikinsu kika yarda zakiyi karatun a gabansa tunda kin kasa a wurina."
Tana daga kai suka hada ido da Abdulhalim ya hade rai. Da shine malamin zaneta zaiyi fes baya daukar rainin hankali. Da sauri ta nuna Abubakar. Malam Hadi yace "to Sadiq ka kwatanta gaskiya ka ji karatun. Ke kuma gobe ki tabbatar zakiyi a gabana ko na samo bulala".
Da haka suka fita saura ita da Abubakar.
Fuskarsa a sake ya fara tambayarta "shekarunki nawa Asmau?"
"Shahudu"
"Ashe ma kin girmeni da shekara takwas"
Ta dan saki fuska amma muryarta bata dena rawa ba "so kake kace ka girmeni da shekara takwas dai"
Yayi murmushi dama so yake ta saki jikinta "Haka ne, ni yanzu ina level two a BUK ina karanta computer science. Ke fa?"
"SS1 nake a science class. Likita nake son zama" yadda take maganar yasan ba karamin son hakan take ba.
"Very good, sai dai bakiyi kama da likita ba saboda tsoro yayi miki yawa. Likitoci kuma basu da tsoro".
Yana kallon bata ji dadin maganarsa ba ya sake yin murmushi.
"Kada ki damu akwai maganin tsoro. Shine ki daure ki rinka magana a cikin mutane. Babu mai yanka ki. Iyaka idan kinyi kuskure a gyara miki. Karatun Qur'ani karfin zuciya yake sawa ba ragwanta ba."
Shiru tayi tana sauraronsa yana ta janta da zance. Sai karshe yace ta biya masa yaji.
Da kyar ta daure hawaye wani na bin wani ta karanta. Kafin tayi rabi kukan ya dauke sai karatun ake ji.
Tana kaiwa karshen surar yayi kabbara sannan ya sake karfafa mata gwiwa wurin bude baki a gaban jamaa.
Da murmushi ta fito suka tafi gida ran Shema'u a bace saboda tasa sun dade.
Tun daga wannan lokacin ko ta fara kukan idan Abubakar yana masallacin sai ta daure. Karshe dai sunanta ya koma Idon kuka saboda kullum sai tayi. Gashi ta tsani sunan.
Haka rayuwa ta cigabar musu har lokacin bikin Nasiba. Gidajen biyu suna ta shiri duk da su Umma basu fi shekara daya a unguwar ba. Haka suka yi bikinsu lafiya kalau kamar dangin juna.
Su Asmau an kara zama 'yan mata. Yanzu tana dan sakewa har ayi hira da ita. Wani lokaci da Umma zata Wushishi gashi basu yi hutu ba a nan gidan Mama Yalwa ta barsu.
Abdulhalim ya tafi bautar kasa Jos yanzu Abubakar ne babba a gidan. Duk da yanayin karatunsa bai hana shi cigaba da zama daukar karatu a wurin malam Hadi ba. Duk cikinsu yafi kowa mayar da hankali akan karatun addini shiyasa Baba yake matukar ji dashi.
Watarana an gama karatu kowa ya fita daga masallacin sai Asmau dake zaune tana kokarin kammala aikin da malam ya bata na fitar da hukuncin (NUUN saakina) a thumunin da ya biya mata ranar saboda washegari test gareta a makaranta karatu take son yi. Abubakar yana can wurin zaman liman yana tilawa aka soma iska mai karfi alamun ruwa zai iya sakkowa a kowane lokaci.
Da dan gudunta ta tashi zata rufe tagogi kafin ta fita saboda kurar dake shigowa. Har ta gama rufewa Abubakar baiyi yunkurin tashi ba. A take kuma aka dauke wuta saboda wata tsawa da akayi mai karfi. A dan tsorace tace
"Yaya Abubakar kazo mu fita kafin ruwan nan ya sauko"
Shiru taji sai numfashinsa da ya kara karfi. Gabansa ta karasa sai dai duhu yasa bata ganinsa sosai. Wayarsa da ta taka ta dauka ta haska shi. Kwance yake numfashinsa yana sama-sama da kyar yake fita. Hannunsa daya kuma yana nuna mata aljihun wandonsa.
Asmau duk ta rikice ta kuma fahimci abu yake so ta miko masa daga aljihunsa. To kuma Umma tayi musu gargadi sosai akan taba maza wannan yasa ta kasa tabashi ta fita da gudu a cikin ruwan ta shiga gidansu ta fadawa Mama Yalwa.
Tare suka dawo har da Suwaiba dauke da irin filtilar nan mai batir. A kwancen dai suka same shi ya hada gumi idanunsa harda hawaye. Mama ta daga kansa ta dora a cinyarta a rude tace "ina inhaler dinka?"
Aljihunsa yayi kokarin nuna mata. Tasa hannu ta dauko ta shaka masa. Asmau da Suwaiba suna tsaye suna yi masa sannu.
Duk da haka numfashin bai dawo daidai ba. Mama tace a fadawa dreba yazo su tafi asibiti. Bayan fitarsu Asmau ta tafi gida ta sanar da Umma abinda ya faru.
ABINDA AKE GUDU🙆🏽11
Batul Mamman💖
Rabe ne ya fito yasha sabuwar shadda sai kyalli take yi. Idonsa a kan Bara'atu da yanayin da ta shiga yayi dariyar mugunta. Don tsabar wulakanci yace
"A'a bazawara kune a garin? Ya hanya?"
Hawaye take yi wani na bin wani ta durkusa a gaban Hajjo
"Nasan har mijina ya rasu baku taba kaunata ba amma Hajjo wallahi cin dukiyar marayu haramun ne. Gidan nan baku da hakki a kansa to a wane dalili zaku zo