Showing 99001 words to 102000 words out of 120086 words

Chapter 34 - ABINDA AKE GUDU

30 Oct 2024

2574

Har kin fini....."

Ya Salaam, bata kara magana ba ta kashe wayar ta fita neman pillow tana dariya. Haka ta dawo ta kwanta don bata samu ba. Shima dariyar kunyar da yasan taji ya gama ya gyara kwanciya yana tuno dan lokacinsu na dazu zuciyarsa na kara nutsuwa da zabin da Allah Yayi masa.
*****

Da safe sai da suka yi breakfast kowa ya shirya aka fara komawa gidan Umma wurin yini. Yau atampa ta saka anyi mata dinkin half-gown da plain zani. Ta kashe dauri ta yafa mayafi irin na kayan. Da ta fito falo guda aka saka amarya da farinjini.

Kujeru aka jera a waje da tabarmi da kafet. Sai ga Ado Gwanja ya iso da tawagarsa. Wannan aikin Sally ne 'yar Yaya Abu da Ab Kura kamar yadda suka saba kiran babbar 'yar Anti Lami. Sun dage sai sun gwangwaje suma a bikin nan. Tun kafin dawowar Asmau zumuncin 'yan uwan ya karu bayan tafiyar Kawu Rabe. 'Yan mata kuwa da su Shemau aka shiga filin rawa. Amarya dai sai janta akeyi amma ko da can bata iya sakin jiki tayi rawa balle yanzu da tun jiya Jikamshinta ya rada mata baya son rawar nan. Idan zatayi ta jira sai su kadai.

Ana ciye ciye biki na ta tafiya aka kira Sabira a waya sai ta fita da gudu tana murna. Anti Bintu tace "ke lafiyarki kuwa"

Sauri take ta karasa waje ta taro bakin tace "Anti Bintu 'ya'yan yayyen Mama ne daga Maiduguri. Mota ce tayi musu tsiya tun shekaranjiya suka so zuwa."

Ta fita ta taro 'yan uwanta tazo ta gabatar dasu wurin amarya Asmau.
"Wannan sunanta Fatima Goni ga kuma Amalus sai Halima Wasagu da Feey. Cousins dina da nace miki suna son zuwa biki"

Asmau fuska a sake ta gaisa dasu tana godiya da suka sami damar zuwa. Daga nan aka cigaba da taro har yamma.

Sai da magariba ta gabato aka sallami mai waka iyaye suka kira Asmau cikin dakin Hajjo. Jikinta ya gama sanyi ta shiga dakin suna zazzaune. Hajjo ce a tsakiya ga Mama Yalwa, Umma, Anti Bintu, Yaya Abu da Anti Lami don kara irin tasu harda Yaya Tagwai da Uwargida basu nuna mata kyama ba.

Nasiha ce suke mata wadda tasa ta kuka kamar an bude famfo. Hakuri ne kowacce take mata nuni dashi domin shine jigo a zaman aure duk son da kuke yiwa juna da miji to sai an kai zuciya nesa. Zama ne ake fatan yi har karshen rayuwa. Suka dora mata da ta jure ta kawar da kai ga dukkan maganar da zata ji musamman daga dangin miji. Haka Allah Ya kaddara mata dole ne kuma sai an sami masu yi mata wannan gorin. Hakuri, ladabi, biyayya, tsafta da iya girki kuma sai ta dage. Ishaq yayi mata karamci da yake sonta a haka ya aureta. Ta zage damtse ta kyautata masa.

Kowa ya fadi nasa Asmau tayi kukanta son rai. Bayan ta fita daga dakin ba jimawa Zubaida tazo ta kirata dakin Yassar. Abin mamaki Uwargida ce a dakin Zubaida ta rufe kofar. Sake bawa Asmau hakuri tayi da taso bata mata rayuwa
"idan naje muka gana da 'yan uwana zan koma Azare ne. Gidan nan ba zan barshi a cigaba da sabon Allah ba. Da kika ganni babana Limami ne. Da kuruciya muke sauka. Ina da ilimi na daidai gwargwado. Zanyi amfani dashi wurin bawa matan dake gidan shawara da koyar dasu sannan su koma gaban iyayensu. Ba ido gareni ba kada ayi abinda bazan gani ba. Za'a raya gidan da bautar Allah in sha Allah"

Asmau taji dadi sosai haka ma Zubaida. Uwargida tace "Asmau ina so ku saurareni da kyau. Nasan sana'ata ba mai kyau bace kuma ina ta rokon Allah gafara. Amma ina son sanar daku wasu 'yan sirrikan rike miji da muke amfani dasu a da muna raba mata da mazansu muna aikata haram. Wannan abin idan kunyi a gidan miji riba zaku samu da lada. Ku zama marasa kunya amma ba tsiwa da fitsara ba. Duk abinda miji yake so kiyi masa kada yaje nema a waje. Wani kinkime jiki da hijabi a dakin miji sai a sallah ko kunyi baki. Ku zauna da kayan da zasu ganku da kyau suji suna sha'awarku."

Zubaida da Asmau sai kunya aka fara sunkuyar da kai. Uwargida da taji sunyi shiru tace "kunga ni babarku ce. A bariki nayi amfani da wannan banga riba ba saboda aikin haramci ne. Amma ku gwada a gidan aure wallahi miji sai ya yaba muku. Da ajiye kunya mu kyautata musu muke raba auren soyayya. Matan hausawa kamar munfi kowa kunya. Muyi a waje sannan a gidan auren ma miji yana binki kina nokewa wai ke kin girma. Ai kullum ku nuna musu kamar yau kuka fara kasancewa tare. Sunayen soyayya na zamani samo ki kira abinki. Wani maigida ko baban wane an wuce wurin. Idan miji bai zo da kansa ba ke ki nemo shi. Hanyoyi gasu nan barkatai. Ku dan matso kada aji daga waje ace Uwargida zata bata ku. Allah Ya gani sharrin irinmu nake guje muku. "

Ai kuwa su Asmau sunji batu a bakin Uwargida. To dama kunya a wurin irinsu sai a hankali. Baro zance kawai take Zubaida ta gama jin kunya. Ko da ta gama bayani sai dai su kalli juna suyi murmushi.
*****

Wanka Asmau tayi saboda ance masu daukar amarya suna hanya. Amatullah kamar tasan ba da ita za'a tafi ba yau ta like mata. Da kyar da dabara Shemau ta hadata da yaranta tasa Yassar yayi saurin kai mata su gidanta. Nan da sati biyu sai a dawo da ita lokacin itama Asmau ta saba. Ana fita da ita kuwa Asmau tasa kuka. An rabata da Ama ji take gara kawai a bata ita su tafi tare. Da kyar tayi shiru ta shirya cikin wani material mara nauyi riga da skirt. Fuska tasha kwalliya sosai ga katon mayafi har ka ta lulluba. Jammu cikin kawayen Shemau ita ta matso kusa da Asmau ta damka mata wani abu kamar zuma kadan a kofi. Asmau ta dan dago kai ta kalleta.
"Nasan kin sha abubuwa da yawa shiyasa na zuba miki kadan. Kinsan yadda muke da Shemau kanwa na daukeki. Na bata sauran za'a ajiye a gidanki."

Wannan kayan idan batayi da gaske ba cikinta sai ya baci. Kowa da nasa kuma duk abu daya ne. Suna son daga darajarta a wurin miji. Kafa kai tayi ta shanye tsumin. Jammu tayi dan murmushin jindadi. Tasan nan gaba Asmau sai ta nemeta da kanta. Sirrinsu ne na Sokoto.
******

Dirar motoci aka ji wanda yayi daidai da faduwar gaban Asmau. Shikenan ta zama matar aure. Auren da ta fitar da rai ashe tana da rabonsa. Gashi zata bar Umma ta kama rayuwar ibada.

Su Mami ne suka zo daukar amarya da wasu 'yan uwansu manya. Da aka tashi fita da kyar aka bambare Asmau daga jikin Umma, ita ma Umma kukan take. Su Anti Bintu ma da Mama Yalwa sunyi nasu kukan. Motoci sunfi goma daga bangaren ango banda na dangin amarya masu motar gida da ta haya. Mata ne kawai suka cika gidan. Biki yayi albarka. Mutan Jikamshi sun dauki amaryarsu Asmau.

A motarsu daga wanda yake ja wani soja ne abokin aikin Col. Ishaq sai Walida a gaba. A baya kuma Yaya Abu ce da Mama Yalwa suka saka Asmau a tsakiya.

Gida ne flat mai kyau tun daga waje ga filawoyi sun fito ta saman katanga. Gate din a bude yake da yake bazai dauki motoci sama da uku ba dole aka bar wurin da za'a shigo da motar amarya. Tun a nan zaka san anzo gidan amarya saboda kamshin dake tasowa daga ciki. Wannan aikin su Shemau, ne da Rashida, Sabira da Suwaiba. Mata sai son barka ake gida yayi kyau sosai. A cikin falon aka kai Asmau wurin wasu mata iyaye ga Col. Ishaq ta bangaren Hajiya da babansu. Anyi barkwanci suka kare da nasiha. Babu mai iya tanka Asmau domin sun sha gargadi a wajen iyaye maza. Col. Ishaq yana da kwarjini basa son bata masa, ihsani ya sami tangarda.

Daga nan aka wuce da ita dakinta wanda Umma tayi namijin kokari wurin sayan kayan kawata shi. kanta a rufe yake tana hawaye har aka zaunar da ita a bakin gado. Wata da tace gidanta na jikin na Asmau mai suna Husna tazo ta dan bude fuskar amarya tana murmushi
"Masha Allah amarya Allah Ya bada zaman lafiya. Idan kina da matsala ki rinka nemana. In kina so ma ni kullum sai na shigo na taimaka miki."

Ainau dake gefe tayi dariya, Husna baki san wannan angon ba.

Sai da aka hada da magiya aka samu matan suka fara fita. Gidan ba babba bane sosai. Daidai mata da miji da 'ya'yansu. Gida ya watse sai makusantan Asmau. Har lokacin bata bude fuskarta ba.

Walida tace "kinga ki tashi kiyi sallar isha in da hali kiyi wanka ki canza kaya. Kinsan saboda mutane dakin yayi zafi gaki a kunshe cikin mayafi"

"Nima abinda zan fada mata kenan. An taho da kayanki sai ki sami 'yar rigar bacci mai kyau ki saka"

Asmau bata san lokacin da ta bude lullubin tana kallon Zulaiha ba harda harara. Dariya suke mata sosai Zulaiha tace "meye na hararata, ki tashi ko na tonaki wallahi"

Zubaida tace "don Allah tona" sauran suka rinka naci ita kuma Zulaiha tana ta ja musu rai. Da yake yau bakin yayi lakwas Asmau bata ce komai ba ta shiga inda aka nuna mata bandakin dake cikin dakinta. Sai hamdala take, ko a toilet ba karamin kashe kudi aka yi ba. Duk kayan toilet Abdulhalim ne yayi mata su. Wanka tayi da alwala ta mayar da rigarta akan tawul din. Tana fitowa duk an ragu sai yayarta Shemau. Za'ayi sirri na 'yan uwa ta nuna mata inda ta ajiye kayan gyaran da aka bata a wata drawer
"Don Allah kada ki rinka yi musu shan koshi. Komai sama sama yafi ko don kada ki sha wanda zai illata ki. Ga wannan kuma ki saka"

Asmau ta karbi kunshin ledar da Shemau ta bata. Doguwar riga ce abaya amma ruwan madara. Rigar ta tsaru karshe da mayafinta. Bude baki tayi zata fara godiya da dan hawayenta Shemau tace "indai tayi miki kyau shikenan. kiyi sauri ki shirya kiyi sallah kada ango yazo kina daure da tawul. Mu zamu tafi ga Zulaiha nan da Walida sune kawayen naki dama. Sabira da mijinta bai kamata ta zauna ba."

Shemau bata fita ba sai da Asmau tayi sallah ta shirya. Wani turare mai maiko ta bata ta fara shafawa kafin aje ga sauran. Kamshi ne zai tarar da Jikamshi.

Bayan tafiyarsu daga ita sai su Walida suka dawo falo don ba'a son wannan zuwa har uwar daki da abokan ango. Alamun bude gate ya sa hankalin Asmau tashi. Mayafinta ta gyara kafin su shigo. Su hudu ne harda angon. Biyu abokansa da kaninsa Ismail. Bata iya ganin kowa sai muryoyi da take ji. Ba wasa suka tsaya yi ba nasiha ce dai da addua. Sai a lokacin taji muryar maigidan nata yace Amin. Daga nan suka tashi yace akwai dreba zai ajiye su Zulaiha. Abokin nasa mai dauko amarya yace shi zai je. Ashe Walida ce ta dauke masa hankali.

Tana ji ya fita rakiya ta kasa bude mayafin bare ta tashi. Lokacin da ya rufe kofar gidan kuwa zuciyarta ba karamin harbawa take ba. Anyi an gama yau ga Asmau a matsayin matar Ishaq.

Motsi da kamshinsa taji a kusa da ita ta sake kankame mayafin. Shiru bata ji ya zauna ko yayi magana ba. A hankali taji an bude gaban mayafinta ya shigo da kansa ciki. Ashe a gaban kafafunta ya durkusa. Zatayi baya yasa hannu ya zagayeta ga mayafinta ya rufe su sai kamshin turaruka da numfashinsu. Babu abinda zata iya yi sai kawai ta rufe idonta cike da kunya.

A hankali yake mata magana "Kinyi kyau Matar Jikamshi, yau so nake kamshinki ya rikita ni shiyasa zanyi ta like miki"

Sake runtse ido tayi tana jin wata irin kunyarsa tana karuwa a zuciyarta. Ya dago kanta tare da matso da bakinsa kusa da nata ga hancinsu yana gugar juna
"Ko na daukeki ne?"

A nutse ta bude ido suka sauka cikin nasa. Murmushi tayi masa yaji gabadaya ta hargitsa masa lissafi. Irin wannan farincikin a karkashin inuwar aure halattaccen zama kawai Allah Yake sako shi. Bai dena kallonta ba ya rike mata hannu suka tashi. Mayafin ya cire ya ajiye a kan kujerar ya karewa rigarta kallo. Shemau ta iya zabe. Sai a lokacin ita ma ta kula da kayansa. Yau ma harda babbar riga a shaddarsa ruwan madara kamar kayan jikinta. Hular kuwa a kasa ta ganta kusa da inda take zaune. Yana rike da ita har suka je dakinta.
"Shiga ki jirani naje nayi wanka. Kunyarki nake ji da nace ki rakani. Amma kiyi alwala kafin na dawo" Yana kashe ido tana sunkuyar da kai. Sai da ta shiga ya wuce yana murmushi.
*****

Da abin sallah ya shigo harda mayafinta na falo sanye da kayan bacci riga da wando. Ya shimfida musu abin sallar tana kallonsa sannan ya nuna mata alamun ta tsaya suyi sallah. Kira'ar Jikamshinta ta tafi da ita don nutsuwa da bawa harufa hakki. Raka'a biyu suka yi sai shafai da wutri sannan ya shiga jero addua da larabci kamar bazai dena ba. Bayan ya kai karshe suka shafa ya dawo gabanta ya dafa kanta ya sake wata sannan ya tashi zai nade abin sallar. Karatun Uwargida ta tuna ta dan matsa a kunyace ta karba ta ninke. Ya ji dadin hakan kuwa sosai.

Fita yayi daga dakin ya dawo yace ta biyo shi. Falo suka koma ya ajiye mata snacks, nama, juice da youghurt.
"Wanne kika so"

Jikinta duk ya fara sanyi ta ce ta koshi. Yayi murmushi wannan salihancin duk zatayi ta gama ne.
"Ni zanci kinga ya kamata ki zauna a kusa dani har na koshi ko"

Tace "uhmm" kamar wadda ta tauna flagyl bisa kuskure. Centre table din na gabansa ta zagayo zata zauna a kusa dashi kawai ya janyota kan cinyarsa tare da yi mata rikon da bazata iya gudu ba.
"kada kice min kunyata kike ji kin san ni dai bani da ita indai a kanki ne. Kema kuma haka nake so ki zama."

Ta rausayar da kai gefe guda tana kokarin zillewa.
"Idan ba kya so muci abincin sai mu koma inda muka fito ni bani da matsala."

Tace "To bari na matso da plate din ni ina jin yunwa"

Hancinta yaja yana dariya "ace sai da dabara zan samu kici abinci."

Bayan sun gama ta kwashe komai ta kai kitchen din da bata gaji da gani ba tun da su Walida suka nuna mata. Da ta dawo ya kashe duk kayan wuta suka shiga ciki. Dakinta zata shiga yace "muje namu dakin ki saka masa albarka"

"Brush zanyi"

"Can ma akwai duk abinda zaki bukata" hannunta ya kama suka tafi. Ni'imtaccen kamshi da sanyi ne suka doki hancinta. Komai na dakin sabo ne. Dama dakuna hudu ne a gidan. Aka saka mata gado a biyu dayan aka mayar mata karamin falo. Nasa dakin ya dauki hankalinta. Ya shiga bandaki ta tsaya dube dube. Wani bakin abu mai santsi ta gani akan gadonsa ta dauka. Baki ta bude da ta gane ko meye. Rigar bacci ce mai kyau da ta dace da amare.

Tana jin zai fito ta ajiye sai dai ya ganta. Ya zo ya rungumeta ta baya "rigar tayi miki kyau ko? Hmmm nifa ban ganewa kamshin nan naki ba. Ji nake kamar na mayar dake jikina"

Asmau ta janye jikinta kai a kasa. Rigar ya mika mata yace taje ta shirya yana jiranta don yaga taki sakewa a nan. Idan ta wuce minti goma zai biyo baya. Dakinta ta koma tana mayar da numfashi kamar wadda tayi tsere. Sai juya rigar take yi a hannu. Karshe dai ta sake shiri ta saka ta dora zani ta fito.

Daga bakin kofa ya tareta ya dagata sai kan gado. Sai dai kuma yana ajiyeta ta soma hawaye. Zuciyarta tayi mata nauyi sosai. A take ya rude yana tambayarta ko me ya sameta. Duk yadda zaiyi Asmau taki magana sai kuka har yaji babu dadi a ransa. A sanyaye yace
"Kin tuna Abubakar ne? Addua ya kamata kiyi masa ba kuka ba"

Tayi saurin girgiza kai. Idan ya tabata kuma jikinta rawa yake sosai. Ganin taki magana sannan kamar tana tsoronsa sai kawi ya kwantar da ita yaja bargo ya lullubeta tare da yi mata kiss a goshi "kiyi hakuri idan nayi miki abinda bakya so ne. Just sleep bazan dameki ba"

Daya gefen ya koma ya zauna yana kallonta. Asmau ta juya baya tana kuka mai tsuma zuciya da tada hankalin mai saurare. Dole tayi kuka a wannan rana ko taji sauki a ranta. Yana gefe yana jin kukan har ransa amma ya rasa me take so.

Sai da tayi mai isarta yaji tana ajiyar zuciya. A zaune ma yake jingine da pillow yana kallonta ya rage hasken dakin sai fitilar gefen gado.

Baiyi fushi ba ya matso kusa da ita ya sanyata cikin jikinsa. Fuskarta duk hawaye ta matsa kusa dashi itama don kokari harda zagaye hannuwanta a jikinsa ta kwantar da kanta a kafadarsa tana mayar da numfashi.

Hankalinsa ya dan kwanta da yaji ta a jikinsa ya shafa mata kai "kukan me kika yi, dama akwai abinda zai saka ki kuka ki zabi yinsa ke kadai ki kasa fada min?"

Saukar hawaye mai dumi yaji a kirjinsa tace "Jikamshina don Allah da gaske kana sona?"

"Kinfi kowa sanin amsar tambayarki"

Ta dago kanta tana fuskantarsa kunya sosai a tare da ita. Muryarta ce take nuni da rauni da ciwon dake cikin ranta "a yau na kara tsanar kaina da biyewa zuciya, nayi aure a matsayin budurwa amma na dade da rasa wannan darajar. Ban san na gama cutar kaina ba sai yanzu, lokacin da duk wata mace take jin ta isa a wurin mijinta idan ya sameta cikakkiyar budurwa. Na rasa wannan damar, bazan taba yi maka tinkaho da abinda bani dashi ba. Ina jin kunyarka ina jin kamar na cuceka ma...."

Allah Sarki, tausayinta yaji ya kama shi sosai har tasa zuciyar ta raunana ya hanata karasa maganar ta hanyar da yasan dole tayi shiru. Sai da ya

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login