Showing 105001 words to 108000 words out of 120086 words

Chapter 36 - ABINDA AKE GUDU

30 Oct 2024

2589

dadin adduar sosai har bazai iya kwantatawa ba "nagode Matar Jikamshi amma hakan bazai hanani ramawa ba idan na dawo." Daga haka ya fita itama ta tashi ta kimtsa tazo ta fara nafila. Bayan ta idar da sallolinta zama tayi tana ta mika godiyarta ga Allah. Hakika ta sami babban rabo da Allah Ya nufeta da yin aure duk da abubuwan da suka faru a rayuwar ta. Mata irinta nawa ne suke cikin tashin hankali da muguwar kyama. Kuma wasu da gaske sun tuba amma hakan bai sa mutane raga musu ba. Ta san dai komai bazai taba gogewa kamar bai faru ba amma duk da haka auren da tayi yafiye mata komai. Ta auri irin mijin da kowace mace zata so kasancewa dashi. A take ta yanke shawarar neman izininsa na yin azumi duk ranakun litinin da alhamis domin neman karin kusanci da Allah da kuma tuba.
*****

A nan ya dawo ya sameta tana kuka da addua. Ya zauna a gefenta suka karasa tare sannan ya kuma bata baki akan ta cigaba da hakuri da rayuwa. Daga hira ya dawo da maganar rama cizo. Ta soma bashi hakuri yace bai san zance ba. Daga baya yace "nuna min inda bakya so a jikinki sai na rama a nan"

"Gaskiya ina son ko'ina"

Dariyar mugunta yake mata don yaga tsoro take ji. "To bari na saukaka miki. Rinka nuna min inda kika fi so, duk inda kika bari karshe shine ba kya so din. Sai ki bar min nayi yadda na ga dama".

Asmau ta hau tunani gashi ya kureta akan gado. Duk inda tasan ana jin zafin cizo ta fara lissafawa a cikin zuciyarta. Yace ita yake jira tace "to bakina nafi so"

Col. Ishaq ya dan bata rai "ni kuma nan ne bana so sosai a jikinki. Kinga sai na rama a nan ba sai munyi nisa ba"

Daga nan bai bari ta motsa ba bare ta gudu....
*****

Shi ya fara tashi wurin goma ya kalleta. Bacci take sosai kamar wata 'yar yarinya. Allah Sarki Asmau, duk wata matsalarta ta wuce a wurinsa. Yadda ta iya jajircewa akan aurensa duk da matsalarsa yasa yake jin sonta sosai a ransa. Zaiyi nasa kokarin sosai wurin kyautata mata. Duk wani gata da miji zaiyiwa mace shima zai kokarta. Baya son ko kadan suyi nadamar auren juna. Yadda take tunanin yayi mata alfarma shima hakan yake ji. A hankali ya fita daga dakin don kada motsinsa ya tasheta. Yasan ba karamar gajiya ta tara ba tun kafin a fara bikin. Ga ta biki ga rashin bacin kirki a nasa gidan.

Kitchen ya shiga wanda ya cika store din da kayan abinci tun kafin a kawo gara. Sauran kananan abubuwa da mace ke bukata na kitchen ya bawa Safiyya kanwarsa kudi yace ta tabbatar idan an gama jere ta sayo su ta ajiye. Ai kuwa ta siyo su kwai, kayan miya da 'yan tarkacen da ba'a rasa ba duk ta ajiye a inda ya kamata tun jiya. Su Shemau ta tarar suna karasa aiki lokacin da ta kawo kayan. Ya duba ya sami abubuwan da yake bukata ya fito dasu. Addua yake kada Asmau ta tashi sai ya gama komai. Ya dade da koyon girki a wajen Hajiyarsu. Ko ta koreshi daga kitchen sai ya dawo yace tayata zaiyi. Ita tana haka saboda namiji ne kuma dan fari shi kuwa ko a jikinsa. Har babansu yace ta rabu dashi. Ga amfanin koyon girkin yazo. Da Asmau idonta biyu kila tayi masa dariya ko kuma ta hana shi. Wata hira da suka taba yi ta fada masa abinda tafi son ci da safe ya tuna. A lokacin dama tunaninsa yayi mata shi ranar farkon aurensu.

Tana can tana baccin gajiya ya da fa masu indomie da attaruhu, albasa da caras yadda tace tana so. Ya dafa kwai ya yanka a gefe da cucumber sannan ya hada musu tea a cups ya zuba a tray.

Shi kadai yake murmushi har yaje dakin. Tana nan inda ya barta. Ajiye tray din yayi ya zauna kusa da ita ya janyota jikinsa. Ta bude ido kenan zata yi magana ta kula da agogo. Shadaya harda rabi. Ta zaro ido tana kokarin tashi."Subhanallah haka nayi ta bacci, ka dade da tashi ko? Ko breakfast ban hada maka ba. Bansan wane irin bacci nayi ba yau"

Duk ta damu ko kadan ba haka taso ba. Amare da take jin labari sun riga mazansu tashi sun hada musu abinci ita gashi rana ta fito tana bacci. Zaunar da ita ya sake yi "duk kin wani tada hankali kamar wadda tayi laifi. Bacci kuma ai dole kiyi, ko kin manta baki sami damar yi ba jiya"

Asmau ta ji kunya, duk inda zai dauko maganar da zata kunyatata ya iya. Ta sake yunkurin tashi sai ta ga tray din abincin har tiriri yake, sai lokacin ta farga da kamshin dake tashi taji cikinta na kukan yunwa. Idonta ne ya ciko da kwalla da ta ga yadda ya tsara komai kamar ba hirarsu ne sati daya kafin biki. Fadawa tayi jikinsa "Jikamshina nagode" tana jin wani sabon sonsa a ranta.

Wannan farincikin yake son gani daga gareta kuma ya samu. "Kije kiyi brush kada yayi sanyi. Idan kuma godiyar zaki yi zan baki goyon baya. Kinsan ana son yawan godiya" yana magana yana daga mata gira ta tashi da sauri tana dariya ta shige toilet.

Kafin ta fito wayarsa ta soma kara ya dauka ganin maigadinsa ne.
"Sir baki ne suka zo har mota biyu. Na bude musu?"

Col. Ishaq yaji kamar ya fita ya kori ko su waye. Shi fa yana mamakin wannan dabiar ta hausanmu. Ayi komai na hidimar biki da mace wai amma gari na wayewa sai su zo ganin amarya. Ko ganin gulma kamar yadda yake kiran ziyarar. Ai dai a bari ko azahar ayi. Amma yanzu ko shabiyu batayi ba ace an zo gidan sababbin aure ai ba'a so zaman lafiya ba. Bare a lokaci irin wannan da ya gama tsara yadda zai kasance idan sunci abinci da amaryarsa.
"Ina fata ba a gabansu ka kirani ba"

"Eh Sir, ina daga ciki ne"

Rai a bace yace "to ka fita kace wayata a kashe take kuma nayi umarni kada ka bude sai da izinina"

Ya ajiye wayar da yaji Asmau zata fito. Akan gadon suka ci duk kunyarta ta ajiye a gefe suna bawa juna a baki. Yadda ya kyautata mata itama haka take kokarin yi masa. Shaf ya manta da batun baki sai da Asmau ta fita kitchen zata mayar da kwanukan Hajiya ta kira shi. Ko gaisuwarsa bata amsa ba ta fara fada akan lallai yasa a bude gate ga baki nan 'yan uwansu ne da wasu daga gidansu Asmau duk sun hadu a bakin gate maigadi yaki budewa. Ba'a son ransa ba yace to tare da bata hakuri. Da Asmau ta dawo tace masa zata je tayi wanka.

"Nazo muyi tare?"

Ta fito da manyan idanunta "rufa min asiri"

"Nine sirrin naki Matar Jikamshi. Bakya bukatar rufe min komai. Kije kiyi amma idan kika dade zaki ganni"

Ta fita shi kuma yayi waje daga shi sai dogon wando da jallabiya. Bazai fada mata da baki ba yasan rudewa zatayi ta fara komaina gurguje. Abinda baya so kenan shiyasa ya kyaleta ma tayi wankan. Bayan ya bawa maigadi umarnin ya bude musu ya bude kofar falon ya koma ciki.

'Yan uwansu ne na Jikamshi masu komawa a ranar sai na Asmau 'yan Wushishi. Sake fitowa yayi da bayan sun shigo an fara hayaniya ana ta gaisawa. Wasu suna ina amarya take. Ai suna ganinsa har 'yan uwan nasa kunya sosai ta kamasu domin kana ganinsa zaka san bai dade da tashi ba. Yayi murmushin keta ganin duk sun daburce da ganinsa a haka suka gaisa, manyan cikinsu ma sunji kunya. A ransa yace gobe ma ku sake zuwa kallon kwakwaf. Basarwa yayi yace "tana shiryawa ne bari na kirowata"

Kafin ya karasa shigewa korido din ya soma jin suna kuskus ana cewa dama ba yanzu suka zo ba sai anjima. Dakin Asmau ya shiga tana kokarin zuge zip din riga. Tana ganinsa ta juya kada ya ga bayan ya shigo ya rungumeta ya zuge mata zip din yace "sarkin kunya kin gama shiryawa, muna da baki a falo"

A rude tace "baki kuma, yaushe suka zo. Ban duba kitchen din ba ko akwai waniz , , zaki abu mai sanyi da zamu bawa baki" tunanin yadda zatayi ta soma.

Dama ransa ya baci da zuwan bakin ganinta yanzu ya sa ya dan manta. Gashi yanzu duk an ruda masa mata. Ita ma bata gamawa sanin kan gidan ba an zo mata mutane sunfi goma.
"Shiyasa tun dazu da suka zo nace kada a bude gate din"

"Sun dade da zuwa? Meyasa kace kada a bude yanzu sai ace laifina ne"

A zatonsa zata ji dadin yadda yayi bai san mu mata mun saba da irin wannan bakin na bayan kai amarya ba. Idan ba'ayi sa'a ba ma kawayenta ke zuwa jin ya aka kwana. Amarya mai bakin aku tayi ta bayani dalla dalla. Gani yayi duk ta damu da bakin da bata san ko su waye ba yace "nayi miki gwaninta shine kike bata rai. To kije wurinsu ina daki idan kun gama"

Asmau taji wani iri. Maganarsa kadai ta sanar da ita ransa ya baci. Ya juya zai fita ta riko hannunsa "kayi hakuri Jikamshina"

Ya danyi murmushi "babu komai akwai lemo a fridge kuma ina jin da cake sai ki basu"

Fita yayi ya barta ta rasa yadda zatayi. Gashi yayi fushi sannan ga bakin da idan bata je ba zasu tafi da ita a baki. Haka ta yafa mayafi ta fita wurinsu. Su a takure ango ya basu kunya ita kuma ta kasa sakin jiki saboda kunyar an shanyasu a waje ga Jikamshinta yana fushi. Basu dade ba suka tafi ko irin leken gidan amarya basuyi ba tunda ansan yana gidan.

Suna tafiya ta koma dakinta ta canja kays zuwa wasu riga da siket da suka fiddo da jikinta sosai. Tasha turare da kwalliya ta tafi bawa angonta hakuri.

Zaune ta same shi akan wata doguwar kujera ta dakin ya gama shiryawa yana waya da alama Mami ce. Tunda Asmau ta shigo ya ganta da kwalliya da kamshin da take zubawa ya nemi fushinsa ya rasa. Hannu ya mika mata alamun ta karaso. Tana ji ya sallami Mami ya dubeta "apology accepted"

Tace tana jindadi "tun kafin na bada hakurin"

"Ganinki ya kori fushin amma ki sani bazan yarda da bakin nan ba. Sati biyu kawai aka bani a wurin aiki. Bazanyi sharing dinsu da bakin nan ba. Anjima zamu hada kaya gobe in sha Allah zamu je Yankari Game Reserve"

Ta sunkuyar da kai ta kara bashi hakuri sannan tace "ko naje na fara hada kayan yanzu?"

Ya ja hancinta "yanzu kuma ai lokacina ne ranki ya dade"
ABINDA AKE GUDU🙆🏽57

Batul Mamman💖





Washegari garau ta tashi kamar ba ita ba. Sai a lokacin hankalin Col. Ishaq ya kwanta ya lallai wani satin ta huta har ta kara samun lafiya.

Sun cigaba da harkokinsu cikin kwanciyar hankali ya karbo mata form din Jamb suka cike tare sai jiran lokacin jarabawa. Bayan sati daya Walida ta kirata ta sanar da ita zata kawo mata ziyara da neman shawara. Dadi ya kama Asmau ta shiga dakin Jikamshinta ta fada masa ta same shi ya mike akan gado yana baccin gajiya ko uniform dinsa bai iya cirewa ba. Daga taje ta zuba masa abinci kafin yayi wanka sai bacci. Asmau ta tsaya tana kallonsa cike da tausayi. Babu abinda baya wadata su dashi ita da Amatullah. Ji tayi a ranta inama zata haifa masa da ko 'ya mai kama dashi. Yana da tsayi da girma kana ganinsa kaga soja. Bata gajiya da kallon mijinta abin alfaharinta, komai nasa yayi mata. Fuskarsa kullum bata rabo da yi mata murmushi, idan kaga ya hade rai to yana wurin aiki ne. Amma duk da haka mutanen dake karkashinsa suna yabonsa da kirki da iya jan mutane a jiki. Col. Ishaq mutum ne mai jama'a, a irin zamansu da kyautatawarsa gareta haihuwa ce kadai tasan zata yi ta faranta masa rai sosai. Hawaye taji ya zubo mata tayi saurin sharewa kada ya gani hankalinsa ya tashi.

Wayarta ta saita a kansa ta kashe flash light ta fara daukarsa a hoto. Sai da ta gaji don kanta ta juya zata fita taji ya tade mata kafa ta fado a kansa. Da farko ta tsorata sai kuma ta fasa bayan taji yadda ya riketa a jikinsa. Ta dube shi idanunsa har lokacin da alamar bacci ya sake kwantar da kansa ya rufe ido. Tace
"Tun yaushe ka tashi?"

Bai bude idon ba yace "tun da kika shigo kina kare min kallo mana. Ko nayi miki kyau ne"

Tayi murmushi tana shafa sajensa "kullum ma kyau kake min Jikamshina. Musamman idan kasa kayan nan kamar kada ka fita"

Yaji dadin abinda ta fada. Kamar yadda mata ke son a yabe su haka maza suke so suma matansu su yaba musu. Wayarta ya karba ya daukesu selfie suna yiwa juna murmushi. Bayan ya dauka yace "Matar Jikamshi kinyi kuka ko"

Asmau tayi saurin kai hannunta wurin idonta zata goge sauran hawayen da tayi lokacin da take tsaye yana bacci.
"Abu ne ya shigar min ido fa"

"Uhmm uhm Matar Jikamshi kada mu fara yiwa juna karya. Na kuma san halinki da saurin kuka. Fada min me kika saka a ranki."

A nutse yake kallonta ta sake shige masa tana jin wani hawayen na kokarin zuba.
"Kawai ina tunanin abinda zanyi maka ne na faranta maka rai sosai. Kayi min komai a rayuwa har bana jin akwai matar da tayi dacen abokin rayuwa kamar ni. Har kunyarka nakan ji a raina in ga kamar bana yi maka abin da ya dace"

"Babu abinda nake so daga gareki da baki bani ba. Kin bani Asmau da duk abinda Asmau ta mallaka. Adduata kullum Allah Ya bamu zaman lafiya mai dorewa."

Ta amsa da amin hawayen da take boyewa suka gangaro. Ba su suka fito ba sai da Amatullah ta dawo daga islamiyya lokacin an kusa kiran magariba.
*****

Bayan ya tafi aiki da safe sannan Amatullah ta tafi makaranta ta gama gyaran gida ta dora abinci. Walida na son alala shiyasa da tayiwa Jikamshi nashi abincin ta gyara wake tayi musu alala mai cike da dafaffen kwai da ta yanka kanana da kayan hadi. Kafin ta iso ta gama komai da zatayi har da juice din kwakwa da ayaba.

Sai da tayi wanka Walida ta iso suka zauna hira. A hirar ne suna cin abinci Walida take neman shawararta akan abokin Col. Ishaq wanda shina soja ne kuma likita a nan asibitin barrack dinsu. Sunansa Hussaini, yana da mace daya da yara hudu. Asmau dadi ya kamata tace "ashe dai da gaske yake, Walida ki amince ni dai a dan haduwarmu a fuskanci mutumin kirki ne kuma mai addini. Yazo gidannan tare da Jikamshina yayi min tambayoyi a kanki. Dama shiru nayi sai kinji daga bakinsa."

Walida tace "wato ko kunyata ba kya ji kike cewa Jikamshinki"

"Don ma kada kice abin yayi yawa ne na tsaya a nan. Kinsan yadda nake ji dashi kuwa. Hmmm Jikamshi mijin Matar Jikamshi" tana magana tana kashewa Walida ido don tsokana. Ai kuwa ta kai mata dundu ta kauce suka saka dariya.

Walida tace "to ya batun matarsa? Kinsan yadda muke da Anti bana son harkar kishiya. Ko shekara batayi ba a gidanmu Abba ya saki Mama. Auren shekara tara ya iya yi mata saki uku lokaci guda."

Asmau tana tausayin Walida ta wannan fannin. Bata tashi tasan soyayyar mahaifiya ba kamar yadda suka sani ita da nata 'yan uwan. Tsakaninta da babarta sai anyi hutu. Shima babanta baya bari ta dade "Walida ba duka aka zama daya ba. Munje gidansa suma sun zo mana nan. Ni dai ina ganin kamar tana da kirki gaskiya duk da idan aka ce kishiya yanzu sai tunaninmu ya sauya. Ki dage da adduar neman zabin Allah. Idan mijinki ne sai kiga mun sha biki cikin kwanciyar hankali. Kada ki bari tsoron abinda baki da masaniya akansa ya sakaki ki amincewa da shi. Baki san inda alkhairinki yake ba"

"In sha Allah zan dage da yin istikhara. Allah Yasa yankewar zaman nawa a gida tazo. Nima nayi auren nan na huta da gorin Anti"

"Ke ba'a cewa haka, aure ai saboda Allah ake yinsa ba gorin kowa ba. Da baki samu da wuri ba ai ba laifinki bane. Auren wuri ko rashinsa jarabawace wallahi"

Murmushin yake kawai Walida tayi tace "Kada ki manta na girmeki da fin shekara. Ni fa ina jin kamshin shekara talatin. Gorin dangi anyi anyi har na saba dashi"

"Masu shekaru arbain suce me Walida? Nayi tunanin yanzu ke mai iya bawa wasu shawara ce idan kika duba rayuwarmu. Kowane bawa mace ko namiji akwai hanyar da Allah ke gwada imaninsa. Fatanmu kada Allah Yasa mu kasa hakuri har mu fadawa shirka."

Sun cigaba da hirarsu Asmau ta soma jin zuciyarta na tashi. Da gudu ta tashi ta tafi toilet din cikin falon ta rinka kwara amai kamar kayan cikinta zasu fita. Walida duk ta gama tsorata ta dafe mata baya tana sannu. Hirar da basu karasa ba kenan sai da ta sani nutsuwa Walida tace "ke kuma aka ake yi sai dai idona ya gane min. Meye nufinki da, wato sai ya fito na gani kamar kowa." Ta kalli saitin cikin Asmau "dan albarka ko yar albarka Mama Walida na gaisuwa. Wannan aman nasan so kake nasan da zamanka. Ranka ya dade dan soja"

Asmau tayi murmushi mai ciwo. Ina ma dai gaske ne, "Walida ba ciki bane wallahi, kwanakin nan wake baya zama a cikina. Rannan ma daga cin kosai sai amai"

"Ban gane ba ciki bane, gashi kince wake na saka ki amai. Kin gwada ne kinga babu?"

"Babu amfanin gwajin nasan babu"

Walida bata gaskata ta ba tace "kina tsarin iyali ne, me ya kaiki daga aure ki fara da bin tsarin nan na sai an gama amarci"

Asmau tace "kema kinsan bazan soma ba"

"To mene ne, Asmau kinsan dai zaki iya fada min. Ni na iya karanta miki nawa sirrin amma ke..."

Ganin bata ji dadi ba Asmau ta fada mata komai game da Col. Ishaq
"Wannan sirrinmu ne daga mu sai iyaye muka sani."

Sosai Walida taji tausayin Asmau. Su kuma kullum sai sun hadu da wani

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login