Showing 117001 words to 120000 words out of 120086 words
tace "Anti Asmau ko zaki tambayar min su Umma na koma motarsu"
"Wani abin ne ya faru kike son canja wurin zama?"
Shiru tayi sai kuma ta soma hawaye. Nan da nan hankalin Asmau yayi mugun tashi. Shi kuwa Yassar hannunsa rawa ya soma yi ya sami gefen hanya yayi parking din motar. Asmau tana ta tambayar me akayi mata sai ji tayi Yassar yace "Bilkisu"
Ta dago kai idanunta sun kumbura sunyi jawur.
"Idan ba cewa zakayi kana sona ba ka rabu dani. Allah zai bani wani"
Asmau ta hangame baki cike da mamaki. Rashin kunya a gaban masoyi ta yarda gadon gidansu Jikamshi ne. Anya Bilkisu bata manta tana bayan motar ba. Allah Yasa ma Amatullah tayi bacci.
Yassar yace "kema kinsan ina sonki don Allah ki share hawayen kinga a hanya muke"
Ta murguda masa baki "a haka ne kana sona tunda ka tafi ba waya ba text sai na gaji na nemeka. Kuma kaki fadawa kowa balle a fara shirin bikinmu sai iya zuwa bikin wasu"
Asmau ta shiga tafa hannu a hankali tace "Bilkisu kwantar da hankalinki naji komai muna dawowa in sha Allah magana zata je gaba kinji ko. Kinsan Yassar din ne akwai tsoron mata"
Dora hannu Bilkisu tayi a kanta tare da jan mayafi ta rufe fuska. Wallahi ta manta da Asmau a motar. Haushi Yassar dinta ya bata tun bikin su Asmau da ta samu yace yana sonta bai kara waiwayenta ba.
A nasa bangaren shima wata matsananciyar kunya yaji. Ko Bilkisun ba don baya sonta yake kin nemanta ba. Shi bai san me zai rinka fada mata ba a waya ko text. Shiru suka yi su biyun Yassar ya tayar da mota Asmau tana ta dariya. Abu yayi dadi zumunci zai kara kulluwa tsakaninsu. Tsabar murna a lokacin ta turawa Jikamshi text tana fada masa. Shi dinma ya nuna farincikinsa sosai yace sai sun dawo. Bilkisu dai har aka isa Jos bebiyar dole ta zama.
Ansha biki Zulaiha ta sake bawa Asmau labarin yadda suka kare dasu Zinaru dama ta sanar da ita a waya. Asmau tace ina ma tana wurin ta ga idanun Zinaru mai son kudin tsiya. Daga nan suka koma hirar cikin Asmau da kuma Alh Najib da yake jiran Zulaiha ta gama iddah. Ita dai tace bata da ra'ayin aure tasha wahala a wancan ga yara har shida waye zai dauketa tare dasu. Shawara Asmau ta bata kada ta bari dama ta kubuce mata wurin yiwa babanta biyayya.
Ranar Asabar da sassafe suka dauko amarya suka taho Kano da ita. Washegari akayi dinner sannan aka wuce da ita Shanono inda zatayi sati sannan su tafi Zamfara da angonta.
Ranar da suka dawo Col. Ishaq kamar ya cinye Asmau. Kwanaki uku kawai ji yake kamar ya dade sosai basa tare. Itama tayi kewarsa domin kuwa duk kulawar da take samu bata kai tasa ba.
*****
Cikinta na da wata shida ya fara siyayyar kayan baby. Wani lokacin yaje da ita wani lokacin kuwa sai dai taga ya shigo da kaya. Tun daga gadon yara (cot), kayan sawa da duk wani abin amfani ya tanada. Ita har gajiya tayi da cewa ya barsu haka. Mutum mai shekarunsa zaiyi haihuwar fari sai dai a zuba ido.
Wata rana ya dawo daga aiki a gajiye yake fada mata ta hada kaya jibi zasu tafi Port Harcout an tura shi aiki na wata daya. Amatullah sun fara hutu sai a kaita gidan Umma kafin su dawo. Asmau ta zauna ta hada musu kaya washegari suka kai Amatullah gidan Umma sannan suka je yiwa Hajiya sallama.
Tunda ya fara bayanin abinda ya kawo su Hajiya ta dakatar dashi.
"Babu inda zaka je min da ita da wannan cikin. Wa kuke dashi a can da zaka kaita cikin arna ka ajiye. Idan haihuwa tazo yaya zaku yi?"
Yace "Hajiya akwai musulmai kuma da sauran lokacin haihuwar har maje mu dawo"
"Kasan Allah babu inda zata je. Ko dai ka fasa tafiyar ko kuma ita ta zauna a nan ko can hotoro. Wannan karon ba kyaleka zanyi ba irin yadda ka tabayi min har na bari kuka koma gida"
Asmau kanta na kasa Col. Ishaq yaki shiru don ba karamar cuta bace gareshi tafiyar wata daya babu matarsa. Hajiya ta dage harda kiran Umma. Itama Umman tace abinda ta gani kenan da suka kai mata Amatullah sai dai batayi magana ba. Hajiya tace ta gama magana shawara na garesu. Jiki babu kwari suka tafi gida.
Asmau tayi ta bashi baki akan yayi hakuri ya dena nuna bacin rai amma ya kasa.
"Matar Jikamshi wata daya ba sati bane. Ta yaya zanyi kwanakin nan ni kadai bayan na riga na saba da yin komai tare dake"
Idonta na shirin zubo da hawaye tace "kayi hakuri kaima kasan abinda ta fada domin amfaninmu ne. Bazaka iya fasa tafiyar ba? Wallahi bana son kayi min nisa"
Kuka ta soma yi ya rungumeta "bani da yadda zanyi ne. Umarni ne daga sama"
A ranar ko kadan basuyi bacci ba sai aikin rarrashin juna. Tayi ta masa kuka har muryarta ta dashe. Bayan ya dawo daga sallar asuba ya hada mata kaya a wani akwatin. Ko abincin kirki sun kasa ci haka suka fita ya kaita gidan Umma ya wuce office. Daga nan dreba ya kaisu airport su hudu suka tafi. Harda Hussaini wanda idan sun dawo za'ayi bikinsa da Walida.
Sai da ya kusa sati sannan ta warware ta dena zaman daki. Umma tayi dariya kawai. Safe, rana da dare aiki yana yi masa sauki sai waya. Kafin su kwanta kullum sai anyi video call yana kallonta da cikinta da kuma princess dinsa.
****
Kwanci tashi saura kwana biyu ya dawo gida. Ita da Sabira suka je ta tayata gyaran gidan domin tayi nauyi sosai. Harda kitso da kunshi Jikamshi zai dawo. Ranar da zai dawo kuwa karfe tara na safe ta gama shiri zata tafi gida. Umma ta rinka ja mata rai tana dariya a ranta yadda Asmau take ta kallon agogo. Sai goma da rabi ta fito ta ajiyeta a gida ta wuce office. Amatullah tana gidan Nasiba tana karasa hutunta.
Karfe daya taji motarsa ta bude kofa da sauri. Col. Ishaq ya tsaya yana kallonta. Ciki yayi girma sosai. Ita ma shi take kallo har wani jiki ya danyi ta fasa rungumeshi taja da baya. Rufe kofa yayi yana binta "haba Matar Jikamshi kada kiyi min rowar kanki. A tausayawa bawan Allah"
"Shine kayi kiba duk da baka gani na ko"
Ya janyota yana murmushi "yau 'yan rigimar suna kusa ne? Bayan wata daya not even a kiss sai korafi zan samu. Bari na koma tunda bakiyi murnar dawowata ba"
Kin sakinsa tayi ta rungumeshi sosai tana kuka "bazaka kara tafiya irin wannan ka barni ba. Kullum da kyar nake bacci"
Yayi kissing dinta yana kallon fuskarta "na sani my sweet Asmau. In sha Allah next time kafata kafarki."
Daki suka je zai shiga wanka yaga tana dan runtse ido ya tambayeta ko meye tace kafarta ce ta dan rike. Ranar sallah kawai ke fitar dashi daga gida. Kowa yana kokarin nunawa dayan irin yadda yayi kewarsa. Makale suke da juna kamar ranar aka kawo masa ita. A haka kuma tana ta dan jin ciwo daga mararta zuwa baya amma tana cijewa don tasan akwai wurin sati uku kafin lokacin haihuwarta.
Cikin dare suna bacci taji ciwon ba mai daukewa bane ta tashi ta fita a hankali. Ita kadai take ta kai kawo a falo ciwo yana ta gaba gaba har taji tafiya tana neman gagararta. Da jan kafa ta dawo dakin ta zauna a bakin gado. Sai da ta zauna ta fara cewa "Jikamshina" ta kira sau uku yana baccinsa. Wani ciwo taji sosai bata san lokacin da tace
"ISHAQ" da karfi ba.
Tashi yayi ya rasa daga ina take kiransa. Ciwo yayi ciwo ta sake cewa Ishaq, fitila ya kunna ya ganta a bakin gado sai gumi take. Ya rude sosai yace me kike yi a nan.
Tambayar ma haushi ta bata ta cije dai tace "nakuda nake"
Rigarsa ya nema ya saka ya fara neman mukullin mota. Ciwo na cinta tace "Jikamshina bazan iya tashi ba. Haihuwar ta matso. Ka dauko sabuwar reza a waccan drawer din"
Ya zaro idanu a tsorace "inyi me da reza?"
Tana wash wash tace "yanke cibiya"
A take jikinsa ya fara rawa.
"Kiyi hakuri na kaiki asibiti don Allah kada ki haihu a gabana wallahi bazan iya gani ba suma zanyi. Ko ta awaki bana son gani" yadda yake maganar kasan a tsorace yake sosai.
Durkushe yake a gabanta ta daure ta rike masa hannu "Jikamshina kafin muje asibiti ko wani yazo zan iya haihuwa. Ka daure ka duba min ko baka son baby din"
Jikinsa a sanyaye yace "ina so"
Wani nishin ciwon ta gama sannan tace ya dauko rezar. Yaje ya dauko ya dawo gabanta ya zauna tare da mike kafafu. Yana zama yaga ruwa yana fito mata ya dago kai a razane.
"Ruwan jikinki zai kare don Allah ki bari na kira ko Hussaini ne"
Jin bata amsa ba ya dan dago "Asmau kina jina"
Idonta a rufe ta gyada kai "faya ce ta fashe kada ka damu"
Yana kallon yadda take famam cije lebe tausayinta ya kama shi. Babu inda baya rawa a jikinsa idonsa a rufe yake ya fito da reza sai kyalli take amma bai san me ma zaiyi da ita ba. Sai da tace ya bude idonsa ya rinka gani ta kusa haihuwa.
Budewar yayi ya juya gefe tare da rike mata kafa yana ta faman cewa "push Matar Jikamshi, push, yauwa gashi nan kin kusa ko? Push, push nasan zaki iya"
Ji tayi kamar ta haure shi da kafarta don takaici. Wai push ga uban ciwo gashi ya kasa yi mata abin kirki. Sake cewa push yayi ta ce cikin bacin rai
"Idan ka sake cewa push wallahi zan haureka"
"Au toh, bansan ba'a fada ba. Naji haka akeyi a tv. Yanzu me kike so?"
Gumin fuskarta ya goge mata sannan tace "addua zaka rinka yi min kuma *ka bude ido ka kalli yadda baby zai fito* kada a sami matsala"
Ya rinka gyada kai tana magana. Ita ke fama da ciwon kuma ita ke fada masa yadda zaiyi. Daga lokacin addua ya rinka karanto mata itama tana yi. Can yaji ta fara nishi ya sake cewa push ai kuwa ta kai masa hauri da kafa. Ji tayi ta tsani kalmar gabadaya. Yana kallo kan baby ya fara fitowa sai ji tayi ya fara kiran sallah. A yanayin da take ciki babu halin dariya. Da yaga abin na gaske ne yace "na shiga uku in hade miki kafarki kada kiji ciwo."
"Kashemu zakayi ne? Ka tara hannu kada ya fado a kasa" Ta fada da kyar.
Yace "toh, ita rezar ina zan yanka miki?"
Tunani tayi kada yayi mata karin da bata shirya masa ba tace "ajiyeta a gefe tukunna" wai tana wannan yanayin yake damunta haka.
Ya ajiye ya mika hannu ya cigaba da kiran sallah tana nishi har Allah Ya taimaketa baby ya fito tare da mahaifa sai kukansa taji. Da jinin da komai Col. Ishaq ya rungume dansa yana hawayen farinciki. Asmau nuna masa yadda zai yanke cibiya sannan ta mayar da kai ta dan kwanta tana mayar da numfashi.
Da dan rungume a jikinsa ya zagayo ya rungumeta sunyi kace kace dasu.
"Allah Yayi miki albarka Asmau. Allah Ya sakawa iyayenmu da alkhairi"
Baby din ya bata yana ta canyara kuka ya dauki wayarsa lokacin biyar da rabi ya kira Hajiyarsa. Cikin bacci ta farka ganin mai wayar ta tashi a gigice. Tana dauka ta jiyo kukan jariri. Col. Ishaq yace "Hajiya mun haihu"
Bakinta ya kasa rufuwa don murna tace "kun haihu ko ta haihu"
Yana ta murmushi yana kallon Asmau da dansu yace "wallahi tare muka yi komai muna gida. Saura wankan ne ban iya ba"
Hajiya ko tambayar me aka haifa bata yi ba ta tashi cikin sauri ta tafi dakin Bilkisu ta tayar da ita tace ta kira mata Dahiru shine gidansa yafi kusa da nata yazo ya kaita gidansu Asmau. Da yazo suna hanya tana addua Allah Yasa haihuwar babu matsala.
Ai kuwa sun sha kallo don da dansa a kafada yazo ya bude musu kofa lokacin an fara kiran asuba. Hajiya tayi saurin karbar baby din tace maza yaje yayi wanka. Ko da ta shiga kitchen ya dora ruwa a manyan tukwane biyu akan gas cooker.
Wurin da Asmau ta haihu ya gyara shi tas ya dauke kafet din ya fito dashi waje. Hajiya ta yaba masa duk da bata fada ba. Asmau ta gani tana dauko robar wankan baby. Tana jin muryar Hajiya kunya ta kamata. Hajiya tace Bilkisu ta juyo mata ruwan tayi wanka ita kuma zata yiwa baby. Anjima kuma da kanta zata yiwa maijego.
Kafin takwas na safe Asmau maijego da jaririnta sunyi fes. Col. Ishaq kuwa baki har kunne. Tare da Hajiya suka je asibiti aka yi mata allurai aka basu magani suka dawo gida. Lokacin su Umma suka zo gida ya cika da yan uwa.
Col. Ishaq shima jegon yake don kuwa daki ya shige yana baccin gajiya saboda irin aikin karbar haihuwa da yayi.
Shi da 'yan uwansa sun nunawa Asmau gata sosai. Amatullah an dawo gida sai murna tayi kani. Kayan barka lodi guda su Mami suka kai gidansu Asmau.
Ranar suna aka shirya walima gagaruma aka ci aka sha yaro yaci suna Abdallah. Su Zulaiha, Rashida, Zubaida, Walida da Ma'u matar Qasim sun sha hidima.
Daren ranar Asmau tayi wanka ta fito ta sami su Ainau suna ta hade mata kayan barkan da ta samu. Hawaye ne ya ciko mata Shemau tace " zaki fara ko."
"Amatullah nake tunani, lokacin da na haifeta babu mai kaunarta. Ita nata uban ma bai san da ita ba har ya koma ga Allah. Ko pant bata dashi sai da Allah Ya hadamu da Zulaiha ta bata kayan Ali. Bazan taba mantawa da bambancin dan zina da dan aure ba. Allah Ya yafe mana" sai kuka yaci karfinta. Su Shemau sunji tausayinsa suka rinka bata baki.
Washegari Col. Ishaw yace tazo ta ga wani abu a waje. Mota ce mai kyau ya siya mata. Bata san lokacin da ta rungumeshi a wurin ba don murna.
*****
Duk abinda miji zaiyiwa mata Col. Ishaq yana wadata Asmau dashi. Ta bangaren yara kuwa duk yadda yake matukar son Abdallah hakan bai hana shi cigaba da nuna tsantsar kulawa ga Amatullah ba. Asmau bata taba ganin wani abu daga gare shi da zai sa taji ya ware Amatullah saboda ba tasa bace ko kuma yanayin haihuwarta. Shiyasa a kullum bata gajiya wurin saka shi a adduarta.
Abdallah na da wata uku Yassar ya dawo daga short service dinsa ya dage shi fa aure yake so. Ga ginin da Umma take yi masa da saura amma haka ya hada har da nasa 'yan kudin kafin aiki ya kankama. Bilkisu ta kunno shi sosai akan maganar aure kuma ya zama irinta. Dama zama dasu Jikamshi sai an koyi hali. Iyaye dai sunyi murna kuma an saka rana.
Bikin Walida ma ya tashi su Asmau sunyi rawar gani. Sai da aka gama ta fara shirin makaranta an gama komai. Jikamshi ya cika alkawari bai hanata ba. Yarinya ta samu suke tafiya tare tana rike mata Abdallah idan zata shiga aji. Yana da wata tara amma da girmansa ga kamaninsa da babansa kamar yayi kaki. A haka ne wata rana ta tashi da safe da amai ko makaranta ta kasa zuwa. Gwajin farko ta gane ciki ne. Murna a wurin Col. Ishaq kamar cikin farko. Yayi ta tattalin matarsa. Dole ta yaye Abdallah ga karatu. A haka tayi ta fama har ta haifi 'yarta mace wannan karon a asibiti. Yarinya taci sunan Hajiya wato Lubabatu amma suna kiranta Amaturrahman.
*Bayan shekara uku*
Asmau ce tsaye a kofar dakin yaranta suna bacci. Amatullah da Amaturrahman akan gado suna rungume da juna. Shakuwarsu har ta baci. Saboda Amatullah bata iya fadin sunan kanwarta sosai itama idan an tambayeta sunanta sai tace Amatuyyahman. Duk yadda mutum yaso gyarawa sai tace ba haka Yaya take fada ba. Abdallah yana kwance a kan nasa gadon ga kayan wasa sun baza.
Hannuwan Jikamshinta taji ya rungumeta ta baya tare da dora kansa a kafadarta. A daidai kunnenta yake magana
"Tunanin me kike yi Matar Jikamshi?"
Kwantowa ta sake yi a jikinsa tace "ina godiya ga Allah akan ni'imarSa gareni."
Hannunta yaja suka tafi dakinsa ya tura kofar da kafa. Yana juyowa yaga tana hawaye.
"Allah nagode Maka baki da aiki sai kuka. Ni kaina daga haduwarmu zuwa yanzu sau nawa kina sani kukan nan. Yau kuma me ya faru?"
"Ina tsoron ranar da yaran nan zasu tsaneni. Gara gara ma su Abdallah amma Amatullah sai taji ina ma bani bace mahaifiyarta. Me zan fada musu a lokacin da suka kara wayo mutane suka sanar da su mamansu ta taba ciki a waje? Ya zanyi da Amatullah idan ta tuhumeni da gurbata mata asali? Idan suka kyamaceni yaya zanyi da rayuwata?"
Kuka take yi da gaske. Kwantar da ita Jikamshi yayi ya kwanta kusa da ita kanta yana kan kirjinsa.
"Daga ranar da kika ji rasuwar Abubakar da batun cikinki kin taba tunanin zaki kara samun nutsuwa a rayuwarki?"
"A'a"
"To a yanzu Allah Ya kyautata miki rayuwa ko kuwa?"
"Ya kyautata min"
"Ina so ki sani cewa tunanin gaban da baki gani ba babu alkhairi a ciki. *Abinda ake gudu* ya riga ya faru. Adduarmu shine Allah Ya kara karemu daga sharrin shaidan da mukarrabansa. Yara kuma da kike tunani bazasu taba guje miki ba da izinin Allah. Ke dai kiyi iya yinki wurin basu tarbiya da nuna musu so irin na uwa, sauran kuma mu barwa Allah. A karshe Matar Jikamshi, Asma'un Ishaq ina mai kara shaida miki idan duniya zata gujeki in sha Allah bazan taba rabuwa dake ba. Kece Ishaq, Ishaq kuma Asmau. I love you with all my being"
Kara rungumeshi tayi sosai tana hawayen farinciki "I love you too Jikamshina. Allah Ya barmu tare"
Suka ce Amin a tare.
*****************
*ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH*
Ina godiya ga Allah da Ya bani ikon gama wannan labari. Ina fata Allah Yasa mu amfana da abinda yake cikinsa wanda yake daidai. Kuskuren dake ciki Allah Ya yafe min Ya kawar da hankulanmu daga aiki dashi. Allah Ya karemu daga abinda ake gudu.
Godiya mai tarin yawa gareku masoya wannan labari. Hakika kun cancanci yabo domin kun bani kwarin gwiwa sosai. Bazan kama suna ba domin