Showing 102001 words to 105000 words out of 120086 words
gama kissing dinta ya sanya yatsansa a saman bakinta. Tana kallonsa da fuskarta mai hawaye "ba karya kika yi min ba game da rayuwarki. Nasan komai kuma duk da haka Allah Ya sanya min sonki a zuciyata. ASMAU yarda da kaddara shine cikar musulunci. Abinda kika rasa bazai taba dawowa ba. Tunda kinsan baki da iko akansa babban abinda zaki yiwa kanki gata dashi shine hakuri da dangana. Mata da yawa suna aure a irin wannan yanayin kuma wasu sai kiga asirinsu ya rufu. Ke da naki ya fito fili kin zama misali ne ga sauran mata. Kinyi nadama kin tuba, kuma wannan ake nema daga dukkan musulmin kwarai. Allah Ya kara kare sauran mata daga haduwa da fadawa irin wannan sharrin."
Wani kukan mai karfi yazo mata tace "wallahi sau daya ne...sau daya tsautsayi ya fada mana. Ka yafe min don Allah."
Rungumarta yayi sosai a jikinsa duk dauriya irin tasa sai da yaji hawaye ya zubo daga idonsa. Ya Allah Ka nesanta mu daga tarkon zina. Mai zubar da kimar mai kima, ta zubar da girman babba, ta wulakanta mai daraja. Idan aka yita Allah zai iya yafewa wanda ya tuba amma wallahi tayi tambari kenan a rayuwar wanda yayi.
A daidai kunnenta yace "Ashe duk yadda nake fada miki ina sonki baki taba yarda ba tunda har kike kokwonto a yau. Ban taba karyata zancenki ba. Da kinso tun ranar farko zaki iya cewa Safina ba 'yarki bace kuma zan yarda. Fatana Matar Jikamshi shine mu kasance ma'aurata har a aljannah." Ya kwantar da ita akan pillow yana kallon fuskarta
"A daren yau nake so na goge miki duk wata damuwa da kika tsinci kanki a baya. Ina so na zama farincikinki. Ina so tarihin Asmau da Ishaq ya fara. A yau nake son rubuta kaina a zuciyarki. Ki yarda cewa kema abar so ce kuma da yardar Allah zakiyi rayuwar aure cikin jindadi kamar kowace mace. Abu daya kawai nake bukata yanzu daga gareki"
Maganganunsa sun sanyaya mata zuciya. Tsoron da take ji na zata wayi gari taga canji daga gareshi saboda rashin cikarta yasa ta kuka.
"me kake so"
"Kice kina son mijinki"
Sai da ta kalle shi tayi murmushi sosai sannan tace "I love you Ishaq, I love you Jikamshina. Ina sonka mijina"
Ya riko fuskata a tafin hannuwansa ya matso da ita daidai da tasa yana mata wani irin kallo.
"Lokacina da kika cinye kina kuka zaki fara biya yanzu"
Kokarin guduwa tayi ya janyota ya danne tare da rufa musu bargo.
Amarya da ango....asuba ta gari.
_Mrs Othman Maman Jannah gaisuwa mai tarin yawa gareki_
ABINDA AKE GUDU🙆🏽55
Batul Mamman💖
Juyi Asmau tayi wanda yasa ta bude ido. Cikin na Col. Ishaq suka sauka da yake ta kallonta. A kwance take shi kuwa ya dora habarsa akan hannunsa daya ya zuba mata ido tana ta bacci. Ba karamar kunya taji ba tayi kasa cikin lallausan bargon da suka rufa dashi. Yana murmushi ya bude mata fuska tare da cewa
"Na tasheki da kallo ko, duk laifinki ne da kika sa nake jin dama tun ranar da muka fara haduwa aka daura mana aure."
Bai san irin yadda take jin kunyarsa ba. Ta rufe ido tana noke kai. Jin kanta take a takure kamar tayi tsuntsuwa ta gudu. Dama ya tabbatar da wuya yaji tayi magana. Duk da burinsa kunyarta ta ragu idan suna tare amma ya lura kamar karuwa tayi. Matsowa yayi daidai kunnenta yace "zaki iya tashi muyi sallah?"
A hankali ta gyada masa kai sannan tace cikin wata karamar murya "asuba tayi?"
Mamaki tayi domin gani take kamar yanzu ta rufe idonta ta fara bacci. Kamar yasan me take tunani yace "kina mamaki ne? Bayan kin cinye daren da kuka da ....."
Da sauri ta rufe masa baki kafin ya fadi abinda yayi niyya. Ai kuwa ya ciji tafin hannunta a hankali ta cire shi daga bakinsa ta saki kara tana kwabe fuska zata yi masa kuka. Dariya ya fara da yaga da gaske kukan zata yi harda guntun hawaye ya kama hannun yana hurawa.
"Yi hakuri my darling Asmau, matar soja bata kuka. Matar Jikamshi kuma ba raguwa bace"
Kyale shi tayi yana rarrashinta ta daidaici kafadarsa sai saukar cizo yaji. Ta soma dariya da taga ya shige shi sosai ai kuwa suka fara kokawa yana cewa sai ya rama. Ga tsoron kada ya rama din da gaske ga dariya tana cinta. Tun yana zai rama har ya koma yana kallon yadda take dariya da hawaye a idonta. Ji tayi ya rungumeta a hankali
"Allah Yayi miki albarka Matar Jikamshi. Yadda kike faranta min nima Allah Ya bani ikon yi miki haka."
Nutsuwa tayi ta dena dariyar tana cewa amin ga adduarsu sai ga kiran assalatu. Col. Ishaq yayi saurin tashi
"Kinga zaki sa mu makara ko? Na tashi da niyar nayi shirin zuwa masallaci sai na tasheki ne"
"Ka tashi dai kana cin zalina daga zuwana gidanka"
"Haka ma kika ce? Ji yadda kika cije ni fa. Ki zauna cikin shiri idan na dawo zan rama."
Sai da ya fito daga bandaki ya saka doguwar riga zai tafi masallacin dake bayan layinsu yazo inda take kwance don bazata tashi yana dakin ba yace "ki kular min da kanki sai na dawo" ya kusa bakin kofa yaji tace
"Allah Ya tsare min kai Ya dawo da kai lafiya"
Yaji dadin adduar sosai har bazai iya kwantatawa ba "nagode Matar Jikamshi amma hakan bazai hanani ramawa ba idan na dawo." Daga haka ya fita itama ta tashi ta kimtsa tazo ta fara nafila. Bayan ta idar da sallolinta zama tayi tana ta mika godiyarta ga Allah. Hakika ta sami babban rabo da Allah Ya nufeta da yin aure duk da abubuwan da suka faru a rayuwar ta. Mata irinta nawa ne suke cikin tashin hankali da muguwar kyama. Kuma wasu da gaske sun tuba amma hakan bai sa mutane raga musu ba. Ta san dai komai bazai taba gogewa kamar bai faru ba amma duk da haka auren da tayi yafiye mata komai. Ta auri irin mijin da kowace mace zata so kasancewa dashi. A take ta yanke shawarar neman izininsa na yin azumi duk ranakun litinin da alhamis domin neman karin kusanci da Allah da kuma tuba.
*****
A nan ya dawo ya sameta tana kuka da addua. Ya zauna a gefenta suka karasa tare sannan ya kuma bata baki akan ta cigaba da hakuri da rayuwa. Daga hira ya dawo da maganar rama cizo. Ta soma bashi hakuri yace bai san zance ba. Daga baya yace "nuna min inda bakya so a jikinki sai na rama a nan"
"Gaskiya ina son ko'ina"
Dariyar mugunta yake mata don yaga tsoro take ji. "To bari na saukaka miki. Rinka nuna min inda kika fi so, duk inda kika bari karshe shine ba kya so din. Sai ki bar min nayi yadda na ga dama".
Asmau ta hau tunani gashi ya kureta akan gado. Duk inda tasan ana jin zafin cizo ta fara lissafawa a cikin zuciyarta. Yace ita yake jira tace "to bakina nafi so"
Col. Ishaq ya dan bata rai "ni kuma nan ne bana so sosai a jikinki. Kinga sai na rama a nan ba sai munyi nisa ba"
Daga nan bai bari ta motsa ba bare ta gudu....
*****
Shi ya fara tashi wurin goma ya kalleta. Bacci take sosai kamar wata 'yar yarinya. Allah Sarki Asmau, duk wata matsalarta ta wuce a wurinsa. Yadda ta iya jajircewa akan aurensa duk da matsalarsa yasa yake jin sonta sosai a ransa. Zaiyi nasa kokarin sosai wurin kyautata mata. Duk wani gata da miji zaiyiwa mace shima zai kokarta. Baya son ko kadan suyi nadamar auren juna. Yadda take tunanin yayi mata alfarma shima hakan yake ji. A hankali ya fita daga dakin don kada motsinsa ya tasheta. Yasan ba karamar gajiya ta tara ba tun kafin a fara bikin. Ga ta biki ga rashin bacin kirki a nasa gidan.
Kitchen ya shiga wanda ya cika store din da kayan abinci tun kafin a kawo gara. Sauran kananan abubuwa da mace ke bukata na kitchen ya bawa Safiyya kanwarsa kudi yace ta tabbatar idan an gama jere ta sayo su ta ajiye. Ai kuwa ta siyo su kwai, kayan miya da 'yan tarkacen da ba'a rasa ba duk ta ajiye a inda ya kamata tun jiya. Su Shemau ta tarar suna karasa aiki lokacin da ta kawo kayan. Ya duba ya sami abubuwan da yake bukata ya fito dasu. Addua yake kada Asmau ta tashi sai ya gama komai. Ya dade da koyon girki a wajen Hajiyarsu. Ko ta koreshi daga kitchen sai ya dawo yace tayata zaiyi. Ita tana haka saboda namiji ne kuma dan fari shi kuwa ko a jikinsa. Har babansu yace ta rabu dashi. Ga amfanin koyon girkin yazo. Da Asmau idonta biyu kila tayi masa dariya ko kuma ta hana shi. Wata hira da suka taba yi ta fada masa abinda tafi son ci da safe ya tuna. A lokacin dama tunaninsa yayi mata shi ranar farkon aurensu.
Tana can tana baccin gajiya ya da fa masu indomie da attaruhu, albasa da caras yadda tace tana so. Ya dafa kwai ya yanka a gefe da cucumber sannan ya hada musu tea a cups ya zuba a tray.
Shi kadai yake murmushi har yaje dakin. Tana nan inda ya barta. Ajiye tray din yayi ya zauna kusa da ita ya janyota jikinsa. Ta bude ido kenan zata yi magana ta kula da agogo. Shadaya harda rabi. Ta zaro ido tana kokarin tashi."Subhanallah haka nayi ta bacci, ka dade da tashi ko? Ko breakfast ban hada maka ba. Bansan wane irin bacci nayi ba yau"
Duk ta damu ko kadan ba haka taso ba. Amare da take jin labari sun riga mazansu tashi sun hada musu abinci ita gashi rana ta fito tana bacci. Zaunar da ita ya sake yi "duk kin wani tada hankali kamar wadda tayi laifi. Bacci kuma ai dole kiyi, ko kin manta baki sami damar yi ba jiya"
Asmau ta ji kunya, duk inda zai dauko maganar da zata kunyatata ya iya. Ta sake yunkurin tashi sai ta ga tray din abincin har tiriri yake, sai lokacin ta farga da kamshin dake tashi taji cikinta na kukan yunwa. Idonta ne ya ciko da kwalla da ta ga yadda ya tsara komai kamar ba hirarsu ne sati daya kafin biki. Fadawa tayi jikinsa "Jikamshina nagode" tana jin wani sabon sonsa a ranta.
Wannan farincikin yake son gani daga gareta kuma ya samu. "Kije kiyi brush kada yayi sanyi. Idan kuma godiyar zaki yi zan baki goyon baya. Kinsan ana son yawan godiya" yana magana yana daga mata gira ta tashi da sauri tana dariya ta shige toilet.
Kafin ta fito wayarsa ta soma kara ya dauka ganin maigadinsa ne.
"Sir baki ne suka zo har mota biyu. Na bude musu?"
Col. Ishaq yaji kamar ya fita ya kori ko su waye. Shi fa yana mamakin wannan dabiar ta hausanmu. Ayi komai na hidimar biki da mace wai amma gari na wayewa sai su zo ganin amarya. Ko ganin gulma kamar yadda yake kiran ziyarar. Ai dai a bari ko azahar ayi. Amma yanzu ko shabiyu batayi ba ace an zo gidan sababbin aure ai ba'a so zaman lafiya ba. Bare a lokaci irin wannan da ya gama tsara yadda zai kasance idan sunci abinci da amaryarsa.
"Ina fata ba a gabansu ka kirani ba"
"Eh Sir, ina daga ciki ne"
Rai a bace yace "to ka fita kace wayata a kashe take kuma nayi umarni kada ka bude sai da izinina"
Ya ajiye wayar da yaji Asmau zata fito. Akan gadon suka ci duk kunyarta ta ajiye a gefe suna bawa juna a baki. Yadda ya kyautata mata itama haka take kokarin yi masa. Shaf ya manta da batun baki sai da Asmau ta fita kitchen zata mayar da kwanukan Hajiya ta kira shi. Ko gaisuwarsa bata amsa ba ta fara fada akan lallai yasa a bude gate ga baki nan 'yan uwansu ne da wasu daga gidansu Asmau duk sun hadu a bakin gate maigadi yaki budewa. Ba'a son ransa ba yace to tare da bata hakuri. Da Asmau ta dawo tace masa zata je tayi wanka.
"Nazo muyi tare?"
Ta fito da manyan idanunta "rufa min asiri"
"Nine sirrin naki Matar Jikamshi. Bakya bukatar rufe min komai. Kije kiyi amma idan kika dade zaki ganni"
Ta fita shi kuma yayi waje daga shi sai dogon wando da jallabiya. Bazai fada mata da baki ba yasan rudewa zatayi ta fara komaina gurguje. Abinda baya so kenan shiyasa ya kyaleta ma tayi wankan. Bayan ya bawa maigadi umarnin ya bude musu ya bude kofar falon ya koma ciki.
'Yan uwansu ne na Jikamshi masu komawa a ranar sai na Asmau 'yan Wushishi. Sake fitowa yayi da bayan sun shigo an fara hayaniya ana ta gaisawa. Wasu suna ina amarya take. Ai suna ganinsa har 'yan uwan nasa kunya sosai ta kamasu domin kana ganinsa zaka san bai dade da tashi ba. Yayi murmushin keta ganin duk sun daburce da ganinsa a haka suka gaisa, manyan cikinsu ma sunji kunya. A ransa yace gobe ma ku sake zuwa kallon kwakwaf. Basarwa yayi yace "tana shiryawa ne bari na kirowata"
Kafin ya karasa shigewa korido din ya soma jin suna kuskus ana cewa dama ba yanzu suka zo ba sai anjima. Dakin Asmau ya shiga tana kokarin zuge zip din riga. Tana ganinsa ta juya kada ya ga bayan ya shigo ya rungumeta ya zuge mata zip din yace "sarkin kunya kin gama shiryawa, muna da baki a falo"
A rude tace "baki kuma, yaushe suka zo. Ban duba kitchen din ba ko akwai wani abu mai sanyi da zamu bawa baki" tunanin yadda zatayi ta soma.
Dama ransa ya baci da zuwan bakin ganinta yanzu ya sa ya dan manta. Gashi yanzu duk an ruda masa mata. Ita ma bata gamawa sanin kan gidan ba an zo mata mutane sunfi goma.
"Shiyasa tun dazu da suka zo nace kada a bude gate din"
"Sun dade da zuwa? Meyasa kace kada a bude yanzu sai ace laifina ne"
A zatonsa zata ji dadin yadda yayi bai san mu mata mun saba da irin wannan bakin na bayan kai amarya ba. Idan ba'ayi sa'a ba ma kawayenta ke zuwa jin ya aka kwana. Amarya mai bakin aku tayi ta bayani dalla dalla. Gani yayi duk ta damu da bakin da bata san ko su waye ba yace "nayi miki gwaninta shine kike bata rai. To kije wurinsu ina daki idan kun gama"
Asmau taji wani iri. Maganarsa kadai ta sanar da ita ransa ya baci. Ya juya zai fita ta riko hannunsa "kayi hakuri Jikamshina"
Ya danyi murmushi "babu komai akwai lemo a fridge kuma ina jin da cake sai ki basu"
Fita yayi ya barta ta rasa yadda zatayi. Gashi yayi fushi sannan ga bakin da idan bata je ba zasu tafi da ita a baki. Haka ta yafa mayafi ta fita wurinsu. Su a takure ango ya basu kunya ita kuma ta kasa sakin jiki saboda kunyar an shanyasu a waje ga Jikamshinta yana fushi. Basu dade ba suka tafi ko irin leken gidan amarya basuyi ba tunda ansan yana gidan.
Suna tafiya ta koma dakinta ta canja kays zuwa wasu riga da siket da suka fiddo da jikinta sosai. Tasha turare da kwalliya ta tafi bawa angonta hakuri.
Zaune ta same shi akan wata doguwar kujera ta dakin ya gama shiryawa yana waya da alama Mami ce. Tunda Asmau ta shigo ya ganta da kwalliya da kamshin da take zubawa ya nemi fushinsa ya rasa. Hannu ya mika mata alamun ta karaso. Tana ji ya sallami Mami ya dubeta "apology accepted"
Tace tana jindadi "tun kafin na bada hakurin"
"Ganinki ya kori fushin amma ki sani bazan yarda da bakin nan ba. Sati biyu kawai aka bani a wurin aiki. Bazanyi sharing dinsu da bakin nan ba. Anjima zamu hada kaya gobe in sha Allah zamu je Yankari Game Reserve"
Ta sunkuyar da kai ta kara bashi hakuri sannan tace "ko naje na fara hada kayan yanzu?"
Ya ja hancinta "yanzu kuma ai lok[truncated by WhatsApp]
ABINDA AKE GUDU🙆🏽56
Batul Mamman💖
Bai san irin yadda take jin kunyarsa ba. Ta rufe ido tana noke kai. Jin kanta take a takure kamar tayi tsuntsuwa ta gudu. Dama ya tabbatar da wuya yaji tayi magana. Duk da burinsa kunyarta ta ragu idan suna tare amma ya lura kamar karuwa tayi. Matsowa yayi daidai kunnenta yace "zaki iya tashi muyi sallah?"
A hankali ta gyada masa kai sannan tace cikin wata karamar murya "asuba tayi?"
Mamaki tayi domin gani take kamar yanzu ta rufe idonta ta fara bacci. Kamar yasan me take tunani yace "kina mamaki ne? Bayan kin cinye daren da kuka da ....."
Da sauri ta rufe masa baki kafin ya fadi abinda yayi niyya. Ai kuwa ya ciji tafin hannunta a hankali ta cire shi daga bakinsa ta saki kara tana kwabe fuska zata yi masa kuka. Dariya ya fara da yaga da gaske kukan zata yi harda guntun hawaye ya kama hannun yana hurawa.
"Yi hakuri my darling Asmau, matar soja bata kuka. Matar Jikamshi kuma ba raguwa bace"
Kyale shi tayi yana rarrashinta ta daidaici kafadarsa sai saukar cizo yaji. Ta soma dariya da taga ya shige shi sosai ai kuwa suka fara kokawa yana cewa sai ya rama. Ga tsoron kada ya rama din da gaske ga dariya tana cinta. Tun yana zai rama har ya koma yana kallon yadda take dariya da hawaye a idonta. Ji tayi ya rungumeta a hankali
"Allah Yayi miki albarka Matar Jikamshi. Yadda kike faranta min nima Allah Ya bani ikon yi miki haka."
Nutsuwa tayi ta dena dariyar tana cewa amin ga adduarsu sai ga kiran assalatu. Col. Ishaq yayi saurin tashi
"Kinga zaki sa mu makara ko? Na tashi da niyar nayi shirin zuwa masallaci sai na tasheki ne"
"Ka tashi dai kana cin zalina daga zuwana gidanka"
"Haka ma kika ce? Ji yadda kika cije ni fa. Ki zauna cikin shiri idan na dawo zan rama."
Sai da ya fito daga bandaki ya saka doguwar riga zai tafi masallacin dake bayan layinsu yazo inda take kwance don bazata tashi yana dakin ba yace "ki kular min da kanki sai na dawo" ya kusa bakin kofa yaji tace
"Allah Ya tsare min kai Ya dawo da kai lafiya"
Yaji