Showing 1 words to 3000 words out of 120086 words
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Arewa hausa novels
Novels villa
Duniyan novels
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
And
Cool novel, makeup an
d cooking)
WHATSAPP NO:
+2347039625239
ABINDA AKE GUDU 🙆🏽 1
Batul Mamman💖
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Daki ne cike da 'yan mata sai hayaniya suke yi. Wasu suna saka kaya wanda ya kasance atampa ce ja mai adon baki, wasu kuwa kwalliya suke yi a gaban madubi. Wadanda basu sami wuri a gaban madubin ba da na jikin hodarsu suke amfani ana ta fentin fuska cikin nishadi.
Suna wannan hirar da shewa wata mace da bazata wuce shekaru talatin ba ta shigo da katon cikinta ita ma irin atampar jikinsu ta saka tayi kwalliya daidai gwargwado cike da damuwa ta soma magana.
" don Allah kuyi sauri ku fito ku ake ta jira. Umma sai fada take min babu amarya babu kawayenta. Kun dai san tayi ta kashedi akan African time".
Wata cikinsu wadda da alama ta gama nata shirin tace "kiyi hakuri Anti Shema'u yanzu zamu fito".
"Babu wani yanzu zaku fito. Ina Asma'un?" Ta fada tana dube dube.
Can gefen gado ta hango kanwar tata ana rangada mata kwalliya irin ta amare tayi kyau sosai. Kusa dasu Shemau ta koma ta sake nanatawa mai kwalliyar tayi sauri ta gama a fito da amarya. Ita dai Asma'u har yayarta ta gama magana bata ce komai ba saboda kada ta bata kwalliyarta. Wannan rana ce mai matukar mahimmanci a rayuwarta. Ranar kamunta da mutumin da take ganin tamkar babu irinsa a duniya.
Har Shema'u ta fara tafiya tayi saurin dawowa da sauri ta sake kai idonta gaban rigar jikin amarya. Daure fuska tayi " duk amaryar duniya idan ana bikinta rama takeyi saboda zulumin barin gida da sabuwar rayuwa banda ke Asmau. Dubi yadda rigar nan ta sake matse ki duk kirjinki ya fito ta sama".
Hannu Asmau tasa ta rufe jikinta saboda yadda 'yan uwa da kawayenta na dakin suka maido da kallonsu gareta. Shemau ta cigaba da magana "ki tabbatar abinda zaki yafa ya rufe miki kirji don bani da amsar bawa Umma idan ta fara fada." Daga nan ta fice tana mamakin irin wannan jiki na kanwarta. Dama can ita mai jikin kiba ce....
******
Farfajiyar gidan ta gama cika da mata inda aka kawata wani bangare da ado irin na gargajiya domin zaman amarya. Ga kujeru da tebura wurin yayi kyau sosai harda turaren wuta na tsinke da na garwashi aka kunna sai kamshi ke tashi.
Mai gabatar da taron mace ce ta nemi kowa yayi shiru saboda amarya zata fito. Mai kida ya canza salon kidansa da wanda ya dace da amarya aka fara ita da kawayenta suka fito suna taku daidai.
Sunyi matukar kyau da burge mutane da irin salon fitowarsu. Aka dauki tafi, masu hoto kuwa na camera da na waya suka fara aikinsu. Haka suka rinka tafiya har suka karasa inda zata zauna. Autarsu ce Aina'u 'yar kimanin shekaru sha uku a tsaye da mafici irin na kaba yayarta na zama ta soma yi mata fifita a hankali. Hakan ma ya kayatar da mutane.
Hajiya Bara'atu dake zaune cikin 'yan uwanta da kawaye har 'yar kwalla sai da tayi. Gashi cikin ikon Allah karo na biyu kenan da zata aurar da daya daga cikin 'ya'yanta. A hankali tace " Allah Ka jikan Alhaji" bai rayu yaga auren 'ya'yansa ba bare yaga jikokin da suka fara tarawa.
Daga nan fa aka soma shagalin biki inda aka bukaci dangin ango su fito domin kamun amarya. Suna tahowa Asma'u ta bawa Walida aminiyarta wayarta ta rada mata a kunne ta dauketa a hoto idan ana fesa mata turaren kamun. Walida tace "uhmm su Asmau an iya soyayya. Nasan sarai Abubakar zaki turawa".
Asmau ta juya ido tana fari "ke kuwa an hana bawan Allah ganin iyalinsa dole na taimaka masa da hoto". Dariya duk suka yi sannan aka cigaba da biki.
******
Ana soma kiran sallar magriba aka gama taron shiyasa dama Haj Bara'atu ta rinka nanata musu banda African time. Sallah aka tafi a gabatar harda amarya wadda ta gaji sosai. Dakinta suka nufa ita da kawayenta suka yi tasu sallar. Tana idarwa aka fara yi mata tayin abinci, kafin a kawo ta dauki wayarta ta turawa Abubakar hotunan kamu.
A lokacin yana tare da abokinsa Qasim. Shi dai Qasim gani yayi Abubukar ya dan matsa ya fara waya. Murmushi yayi don yasan da wa ake wayar. Hira suke yi sosai yana fada mata yadda tayi kyau da kuma rashin jindadinsa da aka hana shi zuwa wurin kamun.
Karshen gado ta koma ta rungume waya suna ta hira. Tun ana cewa ta sauko ga abinci har suka gaji suka dena. Ba su suka gama wayar ba sai da ya fara jin kiran sallar isha daga masallacin gidansu wanda suma su Asma'u shi din suke ji. Sallama suka yi tare da alkawarin zai kirata anjima.
Tana saukowa daga kan gadon ta dafe cikinta "yunwa nake ji kamar na kwana ban ci abinci ba"
Walida ta dan harareta "abincin ai ba jiranki zaiyi Juliet. Ni nayi tsammanin a irin soyayyarki da Romeo din naki baku san yunwa ko kishiruwa ba idan kuna tare".
"Nasan ba wani abu ke damunki ba sai tafiyar da rabin ranki Babangida yayi gashi ba kya samunsa a waya sosai" Asmau ta fada cikin tsokana ai kuwa Walida ta jefeta da pillow tana fada. Babangida yaron gidansu Walida ne irin almajiran nan marasa kunya gashi ya kware wurin kaiwa matar babansu gulmar duk abinda take yi shiyasa ta tsane shi. Har kusan daya na dare 'yan matan suka kai suna hira sannan bacci ya dauke su. Wasu akan gado wasu a katifun da aka shinfida a kasa.
Cikin bacci Asma'u taji wayarta na kara ta dauka cikin magagi. Tana ganin sunan mai kiran ta wartsake.
Cikin taushin murya yace " Asmy na tasheki daga bacci ko?"
Sai a lokacin ta kula karfe hudu da kwata na dare sunfi wata daya yana tashinta a irin wannan lokacin dama.
Ta dan shafa idanu "babu komai Yayana yau mun so mu makara ma".
"To a tashi ayi a nemi kusanci da Allah. I love you Asmy."
Murmushin da yake so a gareta tayi sannan tace "me too Yayana".
Bayan ta ajiye wayar tashi tayi ta fita ta tafi bandaki ta dauro alwala. Nafila tazo ta fara yi sannan ta dukufa istigfari kamar yadda suka sabarwa kansu ita da Abubakar har aka kira assalatu. Sake kira yayi ya tabbatar idonta biyu sannan ya tafi masallaci ita kuma ta tashi 'yan matan dakin ta tayar da tata sallar.
*****
Yau ta kama alhamis babu wani taro da za'ayi a gidan sai karfe bakwai da rabi da za'ayi dinner da daddare.
Qasim yazo har gida ya sami Abubakar tare da takardar da aka bashi ta canjin wurin aiki da karin matsayi. Abin takaici ana bukatar lallai yaje ya gabatar da kansa a sabon ofishin da aka tura shi a Zamfara kafin litinin mai zuwa. Abubakar ya taya shi murna sai dai sunyi bakincikin bazai sami dinner da daurin auren abokin nasa ba. Abubakar duk ya shiga damuwa Qasim ya rinka kwantar masa da hankali.
Abubakar yace "yanzu tunda ka zama ACP Qasim to sai ka nemo mana mata musha biki."
Dariya Qasim yayi "wace mata zan nemo bayan kasan albashin dansanda har yanzu bai taka kara ya karya ba."
"A dai rinka godewa Allah" Abubakar ya fada yana saka takalmi. Har bakin mota ya raka Qasim. Dukkaninsu basu ji dadin zuwan canjin aikin a wannan lokacin ba.
******
Kwalliyar Asma'u ta yau har tafi ta jiya. Kawaye da 'yan uwanta kowa yayi irin nasa adon. Anti Shema'u, 'yarta Mimi da Aina'u kayansu iri daya. Mazan gidan su biyu suma shadda suka saka iri daya.
Suna gama shiryawa motar ango tazo daukar amarya. Shima kayansa ya dace da nata. Tun a gida ake daukarsu hotuna haka a wurin dinner din. Abin ya kayatar saboda komai anyi shi cikin nutsuwa irin na 'yan boko. Duk motsin Asma'u idon Abubakar yana kanta suna hada ido sai suyi murmushi. Soyayya ce da ta samo asali tun farkon tarewarsu Asma'u a unguwar su Abubakar shekaru tara da suka wuce.
Sai wurin shadaya da rabi aka tashi daga taro kowa ya tafi gida. Wani abokin Abubakar ke tuka motar suka ajiyeta a gida sannan suka wuce.
******
Washegari Juma'a gidan commissioner kamar yadda duk 'yan unguwa suka sakawa gidansu Abubakar sun tashi a makare saboda gajiyar da suka kwaso a wurin dinner da kuma sanyin da aka tashi dashi.
Mahaifinsu Alh Adamu Matawalle tsohon dan sanda ne har commissioner ya taba yi. Da taimakonsa Qasim ya sami aiki ma. Matarsa daya Yalwa wadda suke kira Mama. Su shida ta haifa. Babban danta sunansa Abdulhalim yana da mata daya da 'ya'ya biyu sai mai binsa Nasiba itama tana gidan nata mijin. Abubakar ne na uku amma kannensa mata biyu Sadiya da Suwaiba duk sunyi aure. Su biyu suka rage shi da autansu Umar.
A gaggauce suka tashi domin baifi awa daya da rabi ya rage musu ba lokacin daurin auren ya yi. Mata suka tashi aka shiga kitchen saboda abokan Baba kamar yadda suke kiran mahaifinsu a gidan zasu ci abinci idan an taso daga wurin daurin auren. Ga samari 'yan uwa da suka kwana a gidan su ma shiyasa aka yi ta layin shiga wanka a bandakuna biyun dake bangaren maza. Da gangan suka ki barin Abubakar ya fara shiga a cewarsu shi ango dole a jira shi.
Baifi minti talatin ya rage ba Umar ya fito daga bandaki kumfar jikinsa bata gama fita ba Abubakar ya shiga ya rufe kofar da mukulli.
Sauran samarin babu wanda ya tsaya cin abincu suka fita dama wurin daurin auren babu nisa daga gidan ko a kafa zasu iya karasawa kofar gidan kakan Asma'u tunda bayan layi ne.
Duk an gama taruwa iyaye suna daga cikin katon soron gidan sauran mutane suna daga waje duk an cike layin. Alh Adamu ya kira Abdulhalim yana tambayarsa ina Abubakar. Abdulhalim yace "inajin yana waje kasan halinsa da kunya karshenta ya ki shigowa."
A waje kuma abokansa ke tambayar juna ko ya shige ciki ne domin basu ganshi ba.
Babu wanda ya saka damuwa a ransa har aka gama daurin auren kowa yana tunanin yana wani wurin.
A can gidansu kuma Haj Yalwa ce ta kira wata yarinya cikin 'yan uwansu tace ta duba mata kowane bandaki na gidan ta dauko bota a cika su da ruwa a ajiye a waje saboda abokan Baba. Idan sunci abinci zasu yi shirin sallar Juma'a.
Yarinyar tayi ta zagaye tana dauko buta. Kofar bandakin dake cikin dakin Umar ce ta kasa budewa sai ta koma ciki ta fadawa Nasiba. Tare suka dawo suka yi ta kokarin budewa suka kasa ga ruwa kuma ya fara fitowa ta karkashin kofar bandakin. Nasiba ta saka kunne jikin kofar taji alamun famfo yana zubar da ruwa. Mama suka sanarwa tace a samo wani ya balle kofar saboda kada ruwan bangaren ya kare tunda tanki ne. Abu ya hada da mata suka kasa budewa ga ruwan yana yawa.
Dole suka hakura har Allah Yasa aka fara dawowa daga wurin daurin auren. Lokacin duk sun tsince kayan dake kasan dakin saboda ruwa. Umar na shigowa Mama ta hau shi da fada shi bai ma san laifin da yayi ba sai da tace yaje ya bude kofar bandakin shi. Yayi mamakin jin kofar a rufe ya saka iya karfinsa ya soma dukanta. Babu kowa a dakin sai shi kadai don Mama tace babu mai taya shi gyarawa. A bugu na hudu kofar ta bude yayi tozali da abinda yayi matukar razana shi.
Abubakar ne kwance cikin ruwan da ya hade da jini daga kasan kansa ga sabulu can a gefen kafarsa ta hagu alamun zamewa yayi.
ABINDA AKE GUDU 🙆🏽 2
Batul Mamman💖
Lokaci guda Umar ya gigice jikinsa ya hau bari. Da sauri ya shiga bandakin ya zauna cikin ruwan kusa da Abubakar sannan ya daga kansa ya dora a kan cinyarsa. Da kyar ya iya cewa "Yaya".
Babu wata alamar motsi a tare da Abubakar. Umar ya shiga jijjiga shi yana kiran sunansa. Duk da haka Abubakar bai motsa ba. Iyakar tsorata Umar yayi don ji yake kamar zuciyarsa zata buga. Wasu zafafan hawaye ya soma yi a hankali yace "Yaya Abubakar ka tashi an daura auren."
Nan ma dai shiru yaji. Tunaninsa gabadaya ya kulle ya rasa me zaiyi ya taimakawa dan uwansa. Da sauri ya tashi ya fara kokarin daga shi ya fitar dashi daga cikin ruwan, amma yayi masa nauyi domin duk jikinsa a sake yake. Ya sake gwadawa yaji tabbas bazai iya ba sai ya tashi ya fita tare da rufe dakin da mukulli.
Duk wanda ya ganshi da kaya a jike ga alamun jini a gaban sabuwar shaddarsa da tasha dinki sai ya tambaye shi ko lafiya. Babu wanda ya bawa amsa ya wuce dakin Mama.
A tsaye ya ganta a gaban mudubi tana saka sarka. Kafin yayi magana ta juyo da sauri saboda ganinshi da tayi ta mudubin. Gaban rigarsa ta nuna tare da zuwa gabansa ta tsaya "Umar me ya faru? Ciwo kaji garin gyaran bandakin? "
Maimakon yayi magana kawai sai ya rungumeta yana kuka mai tsuma zuciya.
*****
Duk akwatunan kayan Asmau an gama hadasu a wuri guda. Daya daga ciki ta bude ta dauko wata atampa zata saka Aina'u ta shigo dakin da gudu sai haki take yi.
"An daura auren. Daga yau dakin nan ya zama nawa ni kadai" ta fada iyakar karfinta tana murna. Tana gama fadar abinda ya kawota ta sake ficewa da gudu.
Su Walida suka soma guda suna yiwa Asmau tsiya. Harda masu yi mata wakar ta zama dauko riga....ta zama dauko hula....ta zama dauko wando....
Duk baki irin nata jikinta sai da yayi sanyi ta kasa biye musu kamar yadda ta saba. Ji tayi zuciyarta tana bugawa da karfi har abin ya bata tsoro kawai sai ta soma kuka. Hankalinsu ya fara tashi. Walida ce ta rungumeta maimakon ta bata hakuri itama sai ta fara kukan. Wata 'yar kanin baban su Asmau ce tace "haba Walida maimakon ki bata hakuri sai ki biye mata. Yau ai ranar farinciki ce ba kuka zakiyi ba. Ki tashi kiyi nafila ki godewa Allah da Ya nuna miki wannan rana."
Jiki a sanyaye Asmau ta saka kayanta ta dora hijab ta tayar da sallah.
*****
Gaban Mama ya fadi ta dan ture Umar daga jikinta. Ta soma kokarin daga masa riga ta ga ko ciwo yaji ya zubar da jini da yawa haka.
"Mama jinin Yaya Abubakar ne".
Jin maganar tayi har tsakiyar kanta. Jinin Abubakar kuma? Abubakar din da ta tabbatar yana tare da abokansa yanzu suna shirin zuwa wurin reception din da zasuyi. Cikin rashin fahimta tace "wane irin jini? A ina kaga Abubakar din?"
Umar yace "yana toilet dina ya suma".
Mama bata jira ya sake magana ba ta fita daga dakin da sauri yana binta a baya. Matan dake cikin gidan suna ta tambayar abinda ke faruwa. Ganin basu tsaya basu amsa ba suka bi bayansu.
A kofar dakin Umar suka tsaya ya saka mukulli zai bude kofar Abdulhalim ya shigo yana fadan Abubakar ya bar mutane suna ta cigiyarsa har Baba sai da yayi ta fada. Umar dai bai kula shi ba ya bude kofar Mama ta ture shi ta shiga da gudu. Inda ya barshi a kwance suka sake samunsa.
Abdulhalim ya karasa gabansa da sauri yana tambayar Umar me ya faru. Da taimakon Umar suka dora shi a kan gado daga shi sai dogon wando a jikinsa. Mama ta fada kanshi tana jijjiga shi tana kuka.
Matan dake kofar dakin suma suka soma kukan. Nan da nan aka kirawo 'yan uwansa mata. Abdulhalim ya kira wani abokinsa likita da yazo wurin daurin auren ya bukaci ya karaso gidansu da gaggawa. Dakin duk ya rude da kuka duk da har yanzu basu san ainihin me ya same shi ba. Sai da Abdulhalim yayi da gaske ya iya sawa suka fita.
Cikin mintuna kadan likitan ya karaso. Yayi mamakin ganin angon kwance jini har ya soma jika zanin gadon. Umar ne yayi masa bayanin yanayin da ya tsince shi a ciki. Abdulhalim yace "bari mu saka shi a mota mu tafi asibiti. Bana so mutane su ganmu. Zanyi kokarin kawo motata baya sai a fita dashi." yana gama magana ya fita.
Kabiru ya duba kan Abubakar inda ya fashe sannan ya taba kirjinsa da tsintsiyar hannunsa. A razane ya dago kai Mama ta kalle shi da jajayen idanu tace "ya cika ko?"
Yadda ta tsare shi da idanu bai isa yayi mata karya ba. Sunkuyawa yayi ya sake bincika shi sosai sannan cikin murya mai rauni yace "Mama sai dai muyi hakuri....".
A take ta zube a jikin Abubakar a sume. Su Suwaiba sai kuka suke yi suka dagata. Kabiru ya fara kokarin taimaka mata. Kuka kowa na dakin yake yi sosai. Tun kafin Abdulhalim ya karaso yaji sautin kukan ya shigo a guje. Umar ya fara hangowa durkushe yana kuka ya shigo ya tarar Kabiru yana danna kirjin Mama. Wani irin numfashi taja sannan ta bude ido da kyar.
Mikewa tayi tana kuka ta koma bakin gadon inda har ansa gefen zanin gadon an rufe Abubakar. "Allah Ya jikanka Abubakar. Na yafe maka duniya da lahira. Allah Ya sa mutuwa hutu ce gareka."
Ana amsawa da amin kuka yana karuwa.
Duk dauriya irin ta Abdulhalim shima kukan yake yi ya kama hannun Kabiru suka fita. Suna fitowa ya fara hango kawunansa da sauran abokansa da na Abubakar. Wurinsa suka taho suna tambayarsa ina ango. Bai iya cewa komai ba sai hawayen da yake zubarwa. Kabiru ne ya iya basu amsa ya sanar dasu halin da ake ciki. Gabadaya farfajiyar gidan ta rude da addu'a. Tashin hankali mara misaltuwa aka tashi dashi. Abubakar ya rasu daidai lokacin daurin aurensa.
Maza sai kai kawo suke yi cikin dan kankanin lokaci labari ya isa kunnem Alh Adamu wanda dama suna hanyar shigowa gidan da abokansa. A gigice ya shigo ya wuce dakin Umar inda su Yalwa suke da sauran 'ya'yansu. Suna ganinsa kuwa su Nasiba suka rungume shi suna kuka. Duk wanda yake gidan sai ya tausaya musu wannan tashin hankali da suke ciki.