Showing 189001 words to 192000 words out of 200116 words

Chapter 64 - A RUBUCE TAKE (KADDARATA)

ta sake ta taba musu.

Tsantsar baqinciki da bacin rai ya hana hafsat din magana har suka isa asibitin aka sauketa,taso bar musu yaran duka amma nawwara taqi sai mimi ce tabi widad din.

Abinda bata sani ba kwata kwata yara basa damun widad,hasalima ita din mayyar yara ce,ko hana mimi zuwa tayata kwana da takeyi hakan baya mata dadi kwata kwata,ita kadai tasan yadda taji,baya ga dan uban tsoron dake bibiyarta harda kewar yaran.

Kamar ko yaushe zama yayi a waje ya jirasu har aka gama,wannan karonma mimi ta samu albarkacin widad din,an wanke mata kan tsaf,yarinyar sai murna take tana shafa sumartata tana kallon widad

"Anty ashe da dadi" sarai widad ta fahimci me take nufi,tana nufin kanta yayi mata sawai,kuma ta tabbatar iska mai dadi yanzu tana shiga kan.

Tunda suka iso gidan,tun basu shiga ba gaba daya aka saukar mata da bacin rai da baqinciki,taji kamar ta cewa abbas don Allah kada ya shiga ya koma da ita,haka ta dinga qoqarin dannewa har ya saka kan motarsa cikin gidan.

Tana tsaye daga bakin window tana hangen komai dake faruwa cikin gidan,don haka tana hangen sanda ya ajjiyeta ya koma,ta jijjiga kai tana sakin labulen falon.

Da daren ranar ta dinga tsoron kada abinda ya faru xuwanta na qarshe bauchi ya sake maimaita kansa,idan ta runtse ido saita bude,ba motsin komai ko alamu na faruwar wani abu,daga baya tayi dukka addu'o'inta don haka ta samu relief sosai,saidai gidan gaba daya taji ta tsaneshi,tsananin tsana ta gasken gaske,a lokacin taji bata da wata buqata data wuce tabar gidan,bata da wata buqata data wuce ta ganta ba cikin gidan ba,haka ta dinga yawo tsakanin falonta zuwa bedroom,sai tayi kamar zata fita saita koma bakin qofa ta zauna ta fashe da kuka,kusan awa uku tana a wannan halin kafin daga bisani bacci yayi awon gaba da ita a nan bakin qofar a yashe a qasa.

*W A S H E G A R I*


Yadda parlor din yake fitar da sassanyan qamshi mai dadi,hakanan jikinta yake fidda nashi salon qamshin daban,girkinta ne ko ba girkinta ba,wannan duka bai dameta ba,kusan qamshi da tsafta sun zame mata gaado idan ana gadonsu,tun daga hannun ummu kawo yanzu.

Ita daya ce a parlor din,kwance cikin doguwar kujera mai cin mutum biyu,wani doguwar rigar material onion color ne a jikinta mai gajeran hannu,kanta babu dankwali sai sassalkar sumarta mai tsaho baqi da santsi data dameta cikin robber band,sai qyalli take saboda gyaran kan da taje shekaran jiya, hannunta wayarta ce,sunata hira da balkisa,bata jin dadin zaman ita daya,yau gaba daga ko dauriyarsa mimi ba,abinda bata sani ba hafsat dince ta hanata shigowa kwata kwata,ita kuwa koda wasa batayi gefan hafsat din ba,indai ba dalili bane ya hadasu a farfajiyar gidan,suna iya gama kwanakinsu duka basu hadu ba,hatta da gaisuwa da take zuwa mata a yanzun ta ajjiyeta gefe,idan sun hadu su gaisa,idan basu hadu ba fine,ta bawa bilkisa labari, bilkisan tana ta tsokanarta

"Sanda nace ki daina gani kikayi kamar sabo nayi ko?,yanzu fa?" Dariya kawai tayi,its har ga Allah zafin hafsat takeji,batason ma su faye haduwa,data gayawa balkisa dalili sai da tayi dariya sosai

"Anya widad,anya kuwa?,wannan zazzafar soyayya mai cike da kishin tsiya da akewa uncle?"

"Kishi kuma anty?"

"Qwarai da gaske" ta jima a ranar tana son gane banbanci tsakanin kishi da kuma abinda takeji akan hafsat din.

Sake gyara kwanciyarta tayi tana jin yadda gaba daya cikinta yake a cushe,duka cikin kwanakin nan bata jin dadin cikinta da jikinta sam,sai tajishi kamar a kushe,mararta babu dadi,amma saita danganta hakan da rashin zuwan period dinta da take saka ran ko yaushe zata iya ganinsa,tun tana lissafi da xuba ido harma ta share taci gaba da harkokinta hadi da cewa cikin ranta

"Wai meye ma don baizo ba zan damu?,nima na huta da takurarsa" har zata gayama abbas saita fasa,tana tsoron kada yace suje asibiti,daga nan ace sai anyi allura.

Tsayawa tayi da replying massage din da takeyi sanda sassanyan sound din data sama wayarta na musamman saboda shi ya shigo

"Baby uncle" shine sunan da tayi saving dashi, qaramin murmushi ya kubce mata saman fuskarta,bata gajiya da ganinsa,duk sanda zata bar kwana sassansa hafsat ta karba tana jin raunin zuciya sosai,tana jin kamar ta riqeshi ya barta tayita kwana,amma bata iya hakan.

Karbar jakarsa data gani daxun hafsat tayi ta kuma bishi sassansa ya fado mata a rai,saita tura baki sannan ta daga wayar a shagwabe tayi masa sallama.

Hannu yasa ya buda qaramar qofar dake jikin sashensa,wadda take bullo dashi zuwa parking lot na gidan,shi daya yake amfani da ita time to time,ya soma takawa a hankali yana fita daga sassan,sanye cikin wani yadin kaftan na maza,qafarsa sanye da lafiyayyen baqin half cover na maza qirar kamfanin aldo mai asalin kyau da tsada,kansa babu hula sai gyaran da yasha,komai nashi fes yana zuba qamshin nan nasa mai aji da daukan hankali.

Ya tabbata don hafsat bata nan ne,don bayan ta ajjiye masa abinci ta fita sashenta,kafin ta dawo ya shirya ya fito ko abincin bai tsaya ci ba,don gida zashi,akwai dan zama da zasuyi meeting shi da yayansa da yayyensa mata.

Idonsa ya lumshe,wani abu na tsarga masa sanda tayi masa sallama da shagwababbiyar muryarta,kwanaki biyun da zai cikashe a yau ba tare da ita ba sun masa mugun nisa,jinsu yake kamar shekaru biyu

"Kina ina baby?"

"Ina parlor"

"Okay,ki sameni ta qofar bayan part dina,fita zanyi"

"Okay sir" yadda ta fada cikin shagwaba da kuma salo na girmamawa dole yabar murmushi saman labbansa,ya zare wayar ya jingina da motarsa da ya saka sale ya wanketa kusan tun safe,idanunsa akan hanya yana jiran fitowarta.

Dakinta ta shiga tayi fitsarin daya cika mata mara,tana ta mamakin yawan fitsarin da takeyi yanzu akai akai,har ta gota madubinta ta dawo da baya,ta dauki turarenta ta sake fesawa sannan ta dawo parlor din ta zura slipper dinta ta fito ba tare data nema dankwali ba.

Tar harabar gidan take da wadataccen haske,wannan ne ya bashi damar hangota tun daga nesa,ya zuba mata idanu kamar ko yaushe yana kallonta,wani abu mai sanyi yana ratsa zuciyarsa,canji yake gani daga widad din da gasken gaske,murjewa takeyi tana sake ninka kyau da farinta

"Fatabarakallahu ahsanul khaliqin" ya samu kansa da furtawa yana shafa qirjinsa da hannunsa saitin zuciyarsa.

Dab dashi ta tsaya,ta langabe kai tana kallonsa, murmushi ya saki yana gyara tsaiwarsa,irin wannan kallon nata,duk sanda ya gani yasan zaisha rigima ne

"You look so good baby.....You look so cute,bansan yadda zan fasalta miki ba" dan murguda masa qaramin bakinta kadan tayi

"Duk ban yadda da wannan dadin bakin ba, kwalliyar ka kaima yau tayi yawa,ina zakaje?" Mamaki da dariya suka tuqeshi,yau itama zata rama kenan?,gefe daya kuma tana nufin kada ya fita yaje wajen wata?.

"Wajen hajajju zani ranki ya dade,na rantse babu inda zani daga nan" yadda ya rantse mata din yana daga hannuwansa sama alamun surrender ya bata dariya,ta tuntsire da dariya shima yana tayata,kafin daga bisani ya gyara tsaiwarsa yana dubanta

"Me zaki kaima yaa baraka na gudunmawa?" Fararen idanunta dake dimautar dashi ta juya sannan tace

"Na baka zabi,ko zabamin kome kaga ya dace,sai nakai din" folding hannayensa yayi yana kallonta, sosai ta bugeshi kimarta tana sake cika masa zuciya,sai ya tuna yadda sukayi da hafsat dazun da safe,kai tsaye ta nuna kudi zai bata,ya bata din kuma ta karba abinta,yasan halinta farin sani,bashi da tabbacin kuma zata kai abinda yakai kimar abinda ya batan,kansa ya jinjina ya buda baki zaiyi magana,saidai kafin yace komai hafsat ta bayyana a wajen from no where,daga shi har widad babu wanda yaga tahowarta bare isowarta wajen,tana isowa kuma babu inda ta nufa sai kan widad gadan gadan,batayi wata wata ba tasa hannu takai mata shaqa tana fadin

"Yau sai kinci ku******mar ubanki,zaki gane ke qaramar 'yar iska ce" cikin sauri da kuma tsananin tsoro widad din ta kauce,saita sake kai mata cafka,dai dai sanda abbas yayo kanta yana daka mata tsawa

"Ke hafsa,meye haka?,kina da hankali kuwa?,me kike yi haka" ko sau daya bata nuna ma ta jishi ba bare ta dakatar da abinda take shirin aiwatarwa,burinta kawai ta cimma widad din ta ida nufinta,cikin wani irin zafin nama ya isa garesu ya kuma shiga tsakiya yana duban hafsat din cikin wani irin mummunar bacin rai da zaka jima baka ganshi kan fuskarsa ba.

*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Page 98

"Matsa daga gurin nan hafsa tun raina bai baci ba" ya sake fada cikin kausashiyar murya,shammatarsa tayi sai kawai ga hannunta jikin widad,ta shaqeta sosai tana dura mata ashar,kai zaka dauka mahaukaciya ce sabon kamu.

Cikin qasa da second biyu,cikin wani irin bacin rai fushi da kuma qarfin hali itama widad ta shaqetan

"Ya salam" abbas din ya fada da qarfi yana kama hannun hafsat ya fincike daga jikin widad,sannan ya janye widad din gefe yana riqe da hannunsa tsam cikin nata

"Wuce cikin gida tun kafin raina ya gama baci!" Ya fada a tsawace

"Bazan wuce ba,ba inda zani, wallahi wallahi yau saina koyawa yarinyar nan hankali don ku****mar ubanta,ni za'a dinga rainawa hankali ana cin amanata?"

"Ba ubana kike zagi ba,naki kika zaga wallahi" widad ta fada cikin bacin rai,tana jin kamar abbas ya saketa ta sake komawa kan hafsat din.

Sake yunqurawa tayi a zafafe jin raddin da ta mayar mata

"Ni kike gayawa haka?,ka barni nayi mata dan banzan dukan da ba zata sake magana ba" kafin ta qaraso ya buda qofar bayan sashensa ya sanya widad wadda itama takeson qwacewa ya maida qofar ya rufe sannan ya juyo yana kallon hafsat da idanunsa da suka canza launi saboda bacin rai,ranshi a mugun bace yace

"Ki shiga hankalinki, banason rashin mutunci da hauka"

"Nice mara mutunci?,nice kuma mahaukaciya?,ai dole ka fadi haka,kun hada kai kuna cin mutuncina,kuna cin amanata,Allah ya isa wallahi ban yafe ba,Allah ya isa na" ta fada da qarfi,saidai......tun kafin ta kammala rufe bakinta ya kwasheta da wani kyakkyawan mari a kuncinta.

Cak wuta ta dauke mata,yayi mata mugun ba zatan da bata taba tunanin zai iya aiwatar wa ba,itace yau abbas ya daga hannu ya mara saboda widad?

"Stupid!" Ya fada yana huci,wani irin fincikar jikinta tayi tana dosar qofar

"Wallahi yau sai na daketa naga abinda zakayi" dab da zata qarasa ya isa gabanta yana nuna mata hanya,amma burinta ta qarasa ta bude qofar ta fiddo widad

"Ka matsa ka bani waje azzalumi kawai"

"Kibar wajen nan hafsa na gaya miki"

"Saina shiga,saina shiga azzalumi" wani lafiyayyen marin ya sake sauke mata hagu da dama,gaba daya sai wuta ta dauke mata,taci burki tana kallonsa kamar wata zararriya riqe da kumatunta

"Don kina iskanci da rashin mutuncinki kina ganin kamar bazan iya daukan mataki a kanki ba kin yaudari kanki,sassauci na da dauke kan da nake miki inason na zama mafi alkhairi ne ga iyalinsa,amma ke gaba daya tosashiyar kwanyarki ta kasa gano miki hakan,to wallahi wallahi kinyi na farko kinyi na qarshe,bazanci gaba da dauka ba,ki bacemin daga wajen nan tun ban bi ta kanki ba!!!" Ya fada da wata irin rugugin tsawa,ba hafsat dake tsaye a wajen ba,hatta da widad dake daga cikin falon saida cikinta ya juya, tsoron sosai ya kamata,ta koma ta zauna saman daya daga cikin kujerun dake dab da qofar,karin farko da taji sautin fushi da bacin rai daga gareshi kenan.

"Ko meye zaka ce, kuma ko me zakayi bazan fasa fadin cutata da kakeyi da cin zarafina ba,yarinya qarama ta mallakeka sai yadda tayi dakai,sai abinda tace,kanata zalunta ta,bazna yafe ba wallahi,sai Allah ya sakamun,kai da ita dukanku bazan yafe muku ba" cikin fushi ya sake daga hannu sai kuma idanunsa suka sauka kan cikinta,ya janye hannun yana qoqarin hadiye fushinsa,bai taba dora hannu a kanta ba sai yau,sai ya kama hannunta ya saita mata hanya yana gaya mata cikin tsawa ta bace masa a wajen.

Jinta take kamar ba'a tsaye take saman qafafunta ba kamar akan iska take haka ta juya ta fara barin wajen, hannunta har yanzu akan kuncinta,idanunta na malalar hawaye masu zafi da quna,yau ita abbas ya mara?,wannan shine mummunan abun tarihi na farko daya faru a iya zamansu da ba zata mance dashi ba.

Ido ya zuba mata cikin fushi har ta bace a wajen,sannan ya juya ya bude qofar,wanda tuni widad dake zaune saman kujera ta miqe tana dakon isowarsa,saidai zuwa yayi ya wuceta abinsa yana wani irin huci,kaman zai zauna akan kujera amma sai ya kasa,ya dinga kai komo widad din tana kallonsa tana kuka qasa qasa

"Shut up" ya fada mata da wata irin tsawa data sakata qanqame jiki waje daya hadi da runtse idanunta,bayason jin kukanta ne kwata kwata,tana qara hasala masa zuciyarsa ne ba tare data sani ba,a cikin yanayin da yake kuma a yanzun bazai iya lallashinta ba,sai kuma ya koma ya zauna bayan ya sakar mata tsawar,jikinsa yana mutuwa,qaramin sautin kukanta yana sake ratsa falon.

Kusan minti talatin suna a haka,ta kasa shuru shi kuma ya kasa lallashinta,sai da suka doshi minti arba'in sannan ya miqe ya fice,ba jimawa ya dawo dauke da hijab dinta da wayarta ya miqa mata,sannan ya isa gaban freezer dinsa ya ciro ruwan gora mai sanyi ya bude ya miqa mata,tasa hannu ta karba tana satar kallonsa,idanunsa ba'a kanta yake ba,wani gurin daban yake kalla,sai takai ruwan bakinta ta fara sha,ya fara sauka cikin cikinta yana ratsa qirjinta dake suya,yana kuma rage mata radadin da takeji.

Kusan rabi tasha sannan ta miqa masa,sai ya sake saka hannu ya karba ba tare daya kalleta ba,bakinsa yakai ya shanye sauran yana yin gaba,ya cillar da robar yana cewa

"Wuce muje" bayansa tabi ba tare da tasan ina suka nufa ba,motar sa ya bude tun kafin su qarasa da remote control,ya isa seat din gefan driver ya bude mata ta shiga ya mayar ya rufe,sannan ya zagaya shima nasa bangaren ya shiga ya tayar da motar suka bar gidan.

Lamo tayi cikin motar,ta kwantar da kanta a makarin kujerar tana 'yar sheshsheqar kuka,idonsa ya dinga runtsewa,sautin kukanta yana qonashi da yawa,basarwa ya dinga yi yana zaton zai iya daurewa amma sai ya kasa,tausayinta ya lullubeshi,yadan daki kan motar,sai ya gangara gefan hanya yayi parking ya juyo sosai ya zuba mata ido yana hadiye bacin ransa da qyar

"Why widad.....why.......me yasa kika biye mata?" Idanunta dake jiqe da hawaye ta daga ta kalleshi

"Amma uncle.....itace ta fara fa" kai ya jijjiga

"Na sani,amma kina zaton zan tsaya ne a wajen ina kallo ta cutarmin dake?" Kai ta kada a hankali alamun a'ah

"So kike ki koyi irin abinda takeyi?,kinaso na daina samun walwala gaba daya?" Kai ta girgiza nan ma sabuwar qwalla na sauko mata

"Kayi haquri uncle......am sorry" a hankali ya lalubo hannunta da hannunsa guda daya ya hadesu waje daya yana hadiye wani bacin rai daya tsaya masa

"Am sorry too baby,na miki tsawa,it was not intentionally.......hankalina ne a tashe,raina a bace,banason kema ki koma wani abu daban"

"Bazan sake ba uncle" ta kuma fada hawaye na sake balle mata

"Kina qonani baby doll,kina qona zuciyata,ki daina wannan kukan" ya fadi yana kamo fuskarta cikin hannunsa,tare da zaro handkerchief dinsa ya soma goge mata fuskar cikin wani irin salo na tausasawa da nuna zallar qauna,hausawa sukance gaida mai gaidaka ko bazai amsa ba,ko meye zai mata idan tana cikin bacin rai bai fadi ba,widad ce kadai ke fahimtar ransa a bace yake ko yana fushi,saita tabbatar tayi abinda zai samu sassauci kota saukeshi daga fushinsa,duk da kusan ba itace sila ba.

Saida suka shiga unguwar ta fahimci gidan hajiya ya kawota,bashi da wani solution illa hakan,saboda yasan kwana zatayi kuka ita kadai,babu lallai ta saki jikinta,a nan ne kawai zata sake tayi baccinta.

Mamaki ya kama hajiya lokacin data gansu tare,baice ma hajiyan komai ba ya barta a nan ya koma setting room din qofar gidansu suka shiga meeting din da suka shirya yi din.

Itama batace komai da hajiyan ba,saidai hajiya ta fuskanci sanyi jiki kadan tattare da ita,tanata kallon widad din,canzawar da tayi tayi yawa,ta kasa cinyewa wannan karon bayan sun gama meeting din ya shigo gidan,widad din ta tafi kawo masa abincin da bai samu ci ba tace dashi

"Anya abbas ba juna biyu yarinyar nan take dashi ba?" Ido yadan lumshe yana sakin qaramin murmushi,hasaso 'yar rigimar tashi da ciki kawai yakeyi,inda hakan zata kasance da yafi kowa farinciki,amma fa yasan daru ne za'a shashi

"Banjin haka hajiya"

"Bata amai bata yawu,ba zazzabin dare?" Dan jim yayi sannan ya girgiza kansa

"Babu hajiya"

"To ma sha Allah,Allah ya kawo nagari masu albarka"

"Ameen ameen" ya fada cikin dan jin nauyi.

Muneera ya nema yace ta gyara daki daya widad din zata kwanta a ciki,ba jimawa muneera ta gyara din,don

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login