Showing 81001 words to 84000 words out of 200116 words

Chapter 28 - A RUBUCE TAKE (KADDARATA)

yana mata magana cikin hikima akan ya kamata ra gyara dakin yaran dama nata dakin da kyau,baki ta tura,shi kome qoqarinka me yasa sai ya cika gyara?,sai yayi challenge naka?,duka ba hidimar dafa masa abinci ke cinye mata lokacin ba?,ita sai taji har ta qagu ya koma Kaduna,ta yadda zata samu ta miqe qafarta da kyau.

Tana gama sallar isha'i ta shiga wanka saboda tuna alqawarin data daukarwa anty deena,data fito ta shirya cikin kayan bacci kai tsaye,wasu riga da wando ne kalan pink da suketa burgeta cikin kayan lefanta,dama Allah Allah take ta sakasu,tana gamawa ta maida hijab dinta tabi lafiyar gado tana hamma,yau ma a nan dakin zata kwanta tare da latifa,idan suka kwana tare sai tayita jin kamar ummu.

Dai dai sanda take rufe bakinta sabida doguwar hammar bacci da taketa saki latifa ta turo qofar dakin,shigowarta kenan bayan ta maida kwanukan da sukaci abinci daki

"A'ah,me zan gani?,yauma?" Ta fada tana kama baki,sai widad din ta waiwayo tana dubanta

"Me nayi?"

"Ke da zaki wuce ki tafi dakin mijinki?"

"Dakin miji kuma umma latifa?,kamar wata 'yar iska?" Tayi maganar tana maida kanta saman pillow ta dora da cewa

"Yanzu da kanki kike cewa ma naje dakin wani" dariya taso qwacewa latifan,lallai da gasken gaske wauta da quruciya sun yiwa widad din yawa,saita qaraso gefan gadon ta zauna tana qoqarin fahimtar da ita.

Sam widad din ta gaza kai hankalinta kan abinda take nufi,sai ma tubure mata da tayi kan babu inda zata,dai dai lokacin hafsat tazo kiranta tazo suci abinci,nan ma tace ta qoshi ba zata ba,ran hafsat din ya mata dadi,amma duk da haka a gaban latifa dashi kansa abbas din saita nuna bataso haka ba

"Rabu da ita,yi serving dina" ya fada kansa tsaye sanda yake dan diban abincin kadan kadan yana baiwa nawwara a baki,wadda tayi dare dare saman cinyarsa,saita soma zuba masa abincin,amma bata rabu da zancan ba,don lallai ta nuna masa ita ba'a son ranta ba,har sai da yace

"Will you keep quiet madam?,ko sai na saka gum dina na rufe miki bakin?" Ya fada yana jifarta da hararar wasa

"Kai bakasan na fika farinciki da haka ba" ta fada cikin ranta,amma a zahiri bakin nata taha ta rufe,bata sake tashin zancan ba.


*********sannu a hankali kwanaki suka fara tafiya,widad cikin gidan har a sannan tana matsayin baquwa,baquwar dake ganin kulawa da damuwa daga idanun hafsat,harma taje ganin matuqar kirkinta fiye dana ja'afar,yadda su mimi ke kiranta da mommy haka nan itama take kiranta dashi,tana mata kallon da takewa anty madina ne,tana kallonta a matsayin uwa ko wata babbar yayarta,gefe guda kuma sabo ne ya shiga tsakaninsu dasu mimi da nawwara,musamman mimin,a nan sassanta suke kusan yini.

Idan ka samu widad din dasu mimi zakayi tunanin yayace da qannenta,kusan ko yaushe suna tare,sosai suke debe mata kewa,idan lokacin da zasu shiga kitchen yayi ita da latifa zasu shiga tare,to amma kusan fiye da rabin hankalinta yana kan yaran,don haka ba wani abun arziqi take tsaiwa ta koya ba.

Ta bangaren abbas shima tana masa kallo daya ne,matsayin uncle muhsin take kallonsa,saidai wani bangare na zuciyarta haka kawai yake cika da tsoronsa,ta kasa sakewa dashi kwata kwata,babu fashi,a kullum zai shigo da safe yaji basu da matsala,ya sake dawowa da dare ya tabbatar da komai lafiya,zaman cin abinci dasu kuwa ko sau daya bata taba yarda ta zauna din ba,hakan yana yiwa hafsat dadi matuqa,yadda yarinyar je tattare kanta waje daya,take kuma dari dari da komai nasa,wannan shike haska mata lallai komai zai tafi mata a sauqi.

To hakanan duk yadda latifa zata lallabata taje sashensa kona awa daya ne sai ta dawo taqi,sai tayi mata kamar bata ji ba,ta kwanta ta hau barcinta,tare suke kwana da latifa din a daki daya,gado daya,wannan yana debe mata kewar ummu qwarai da gaske.

*******A nutse cikin takun nan nashi dake nuna zallar karsashi da lafiya da tsiyayyar qirar jikin da yake dashi yake takowa zuwa harabar gidan,kunnensa maqale da waya yana amsa kira,hannunsa daya riqe da key din motarsa.

Sanye yake wani yadin kuftan mai kyau da daukar ido,anyi masa aikin hannu mai tsadar gaske,sosai kayan suka zauna masa,abbas din ba daga baya ba wajen iya saka manyan kaya,kowacce shiga daukansa takeyi,saika gaza tantance wadanne kaya ne suka fi masa kyau.

A hankali ya zare wayar daga kunnen nasa yana katse kiran, hankalinsa yana kaiwa kansu, suna daga gefan farfajiyar gidan,mimi ce da widad,widad din na daga zaune gefan wata tukunyar fulawa,sanye take da wata doguwar riga mai santsi mai dogon hannu,tana hade da hula ne daga bayanta,bata saka hular ba,tadai saketa,lallausan gashinta mai santsi da tsaho yana matse cikin qaramin band,jelar ta buya ta bayanta,fararen qafafunta na slipper blue din slippers,color din dake matuqar fidda hasken fatarta.

Mimi kedan garo mata ball,itama tana daga zaunen sai ta sanya qafarta ta maida mata,yau din tunda ta tashi bata da wani cikakken kuzari,shi yasa ma tace wa latifa ba zata shiga kitchen kallon girkin yamma ba,itama bata matsa mata ba,ta barta suka fito da mimi din,wadda hafsat ta tafi unguwa ita da nawwara,ta barta a nan,don qememe taqi binta,ba kasafai ta fiya damuwa da bin hafsat din unguwa ba,tafison zama da widad.

Idanunsa ya janye dsga kanta ya nufi parking space,yana hangosu har sannan ta cikin mirror din,shi kansa a yau sai yaga babu wannan kuzari da kazar kazar din daya santa dashi,idanunsa ya kuma daukewa yana rufe motar ya tayar da ita ya fice daga gidan a hankali.

A nutse yake tuqinsa kamar kullum,yana tafiya yana lura da abubuwan dake faruwa saman hanya,gidan hajiya ya nufa kai tsaye,don dama a yau din can yayi niyyar zuwa,sai dare kuma ya tsara zai fita daga unguwar.

A hanya ya tsaya ya siyama hajiyan abubuwan da yasan tana sha'awa kamar yadda ya saba,sannan ya wuce,mintuna qalilan ya iso unguwar tasu.

Tun daga farkon layinsu matasan da suka ankara da shigowar tasa suka biyo bayansa, mutum ne shi mai matuqar kirki tausayi da kuma taimako,wannan ya sanya masa farinjini sosai ga al'ummar unguwar,kamar ko yaushe,bai shiga gida ba sai da ya gama sallamarsu.

A bakin qofar dakin hajiyan ya duqa ya cire Black cover shoes din dake qafarsa mai matuqar tsada da kyau,sannan ya yaye kyawawan labulayen falon dattijuwar bakinsa dauke da sallama.

Su biyu suka amsa sallamar,hajiyarsa da kuma yayarsa yaaya bara'atu,fuskar hajiyan kwance da fara'a tayi magana

"Tun dazu akacemin kana qofar gida,a raina nace qila jama'a ne suka riqeka" yana qoqarin zama a gabanta saman carfet yace

"Sune hajiya,da qyar na qwato" ya qarasa maganar tsadadden murmushin sa kwance saman fuskar sa yana duban mahaifiyar tasa,saita jinjina kai

"Ma sha Allah,mafi alkhairin mutane shine wanda yake amfanar da mutane,Allah ya qara tsare mana ku a duk inda kuke"

"Ameen ya hayyu ya qayyumu" ya amsa,yaaya bara'atu tana tayashi.

Sai da suka fara gaisawa da hajiyar sannan ya gaida yayar tashi,yana tambayarta mai gidanta,sannan suka shiga hira,kafin hajiya ta kira muneera ta kawo masa ruwa da lemo.

"A qoshe nake hajiya alhmdlh,saidai kafin na wuce"

"To shikenan muneera jeki", tsaiwa tayi ta gaidashi cikin girmamawa,sannan ta koma kitchen taci gaba da aikinta.

"Nace sai yaushe zaka koma kadunan ne ango?,ko cin amarcinne bai qare ba?" Yaaya bara'atu ta fada tana gyara zamanta sosai cikin lausasan royal chairs din hajiyar.

K'aramin murmushi ya subuce masa,banda yaaya bara'atun babu wanda zasuyi irin wannan maganar dashi

"Jibi nake saka ran wucewa,hutun da suka bani ya qare"

"Sun kyauta ma ai, duka duka yaushe ka koma kadunan ma,Allah ya sanya albarka sun kyautata maka kam"

"Sosai hajiya" ya furta yana gyada kansa.

"Tafiya dai ta kama hafsat zuwa yanzu,tunda dai ai ba zasu tattare gaba dayansu su zauna anan kai kana can ba" anty bara'atu ta sake fadi tana dubansa,duk da bata da tabbacin samun cikakkiyar amsa daga gareshi,ta sani ba kasafai ya fiya son hirarraki irin wadan nan ba.

Kaman hajiyan ta fuskanci bashi da niyyar yin magana din,sai tayi amfani da wannan damar ta isar da saqon da take ta son isar masa din

"Hafsat ai dama bauchi ta zaba,widad itace abokiyar tafiya Kaduna,ita ta riga ta yankewa kanta hukunci,bana jin kuma zata janye" tsaf ya gama karantar saqon hajiyan,saidai can qasan ranshi yana tunanin yadda zai dauki rigimammiyar yarinyar da bata da maraba dasu mimi har zuwa wata uwa duniyar da sunan matarsa

"Amma hajiya sai nakega ba zataji dadi ba,daga zuwan wata sai a tafi da ita ita kuma tana zaune?"

"A'haaannn,to daa waye yayi mata?,ita ta yankewa kanta wannan hukuncin,ta kuma bada zabin ya samo mai zama dashi,meye laifi yanzun dukka a cikin wannan lamarin?" Shuru bara'atun tayi,sai ta dan jinjina kanta

"Allah ya sawwaqe" .

Shigowar fanteka ya tasheshi,ya miqe yana zuba hannayensa a aljihun wandonsa

"Bari na danje bayanmu na dawo"

"Allah ya kiyaye,sai ka dawo" hajiya ta fada kanta tsaye,tashin da yayi yayi mata,don batason wata magana sam a gaban fantekan,tunda ta karanci inda ta sanya gaba.

Ba haka fanteka taso ba,amma saita rakashi da yaqe tare da addu'ar a dawo lafiya.

*Arewabooks:Huguma*

KI KULANI miss xoxo

DAUDAR GORA Billynabdul

RUMBUN K'AYA hafsat rano

IDON NERA Mamuhghee

A RUBUCE TAKE huguma

_sinkin labaran dake dauke da dukkan wasu nau'ikan salo da kuke so_

_masoya ku biya kudinku ta wannan hanyoyin_

0022419171
Maryam sani
Access bank

Saiku tura shaidar biya ga
+234 903 318 1070

*Masu katin waya ko VTU zaku tura ta nan*
09166221261

*Al'ummar nijer +227 96 09 67 63


*Thanks for choosing us*=?%?=?%?=?%?=?%?=?%?=?%?

*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)

Page 42



Sanda ya dawo gidan babu kowa sai hajiyan tashi,nan yayi zamansa bayan ya fito daga sallar isha'i,yana cin abinci tana qara masa suna hirarsu

"Nidai don Allah zan riqo alfarma guda daya a wajenka abbas" tayi zancan tana ajjiye dan bowl din data qara masa miya,sai ya tattara mata hankalinsa gaba daya,har yana ajjiye spoon din hannunsa

"Hajiya badai alfarma ba,saidai umarni ko?"

"Ko alfarma koma umarni,nidai burina ka cika......don Allah ka kula da yarinyar nan kamar yadda zaka kulaa da hadiyya da kuke fito ciki daya" kai ya jinjina,can qasan ransa yana jinjina tarin qaunar da hajiyar kema yarinyar

"Na daukar miki alqawari hajiya"

"To Allah ya taimakeka,yaci gaba da dafawa al'amuranka"

"Ameen ya raheem,Allah ya qara lafiya da nisan kwana" sai ta bishi da murmushi kawai,kafin ta amsa masa da ameen.

Yau din sassan Widad din ya fara isa,saidai latifa na bude masa qofa taja baya cikin girmamawa,har ya sanya kansa sai ya dakata

"Kuna lafiya?,baku buqatar komai?" Ya tambaya,kai ta girgiza,tana tsananin yabawa da irin kulawar da yake nunawa akan widad din

"Lafiya qalau alhmdlh,babu komai"

"Itafa?" Ya tambaya kai tsaye

"Tayi bacci tun dazu"

"Lafiya dai ko?" Ya tambayeta yana dan ritsata da ido,kusan bai taba zuwa ya sameta tana bacci ba,yafi samunta a daki,data ganshi zata fara tattare jiki waje daya,ta kuma sanyawa bakinta kwado da linzami,har sai ya gana zamansa na mintu biyu zuwa uku sannan ya fito

"Eh bata dan jin dadin jikinta ne wai"

"Subhanallah,amma me yasa ba'a kirani an kaita asibiti ba?"

"Ba zazzabi ko ciwon kai bane,kawai bata da kuzadi ne kamar yadda ta saba" sai yadan kada kai kadan

"Allah ya sawwaqe,ammmm..... Please,koda akwai wani damuwa,a kirani ko ta wayarta ne"

"In sha Allah" ta fada cikin girmamawa,cikin ranta tana yaba kulawa da sanin darajar dan adam irin nasa.

Sanda ya shiga falon hafsa a zaune ya sameta,yaran na kwance a wajen saman carfet kowa d'ai d'ai,itama saman carfet din take a zaune,hannunta riqe da waya,plates din abinci ne da abincin da sukaci suka zuzzubar kaca kaca,saman kanta ba dankwali,gashinta dake samun qarancin kulawa qwarai da gaske daure a kyauro.

Idonsa ya dauke daga kanta yana qarasawa wajen yaransa,saita janye qafafunta tana masa sannu da zuwa,qasa qasa ya amsa mata,yana dauke yaran daga qasa ya nufi dakinsu dasu.

A hargitse ya samu dakin kamar ko yaushe,sai a gadon nawwara ya fara ajesu,ya karkade gadon mimi ya maidasu kai,sannan ya gyarawa nawwara nata gadon itama ya maidata kai,bayan ya duba cupboard dinsu ya canza musu wankakken zanin gado,ya tattara karikicen kayan wasansu dake tsakiyar dakin ya killace a drawer dinsu ya hade kayan wankinsu a laundry basket.

Yana gab da kammala mopping na dakin ta turo qofar ta shigo,zuwa yanzu daurin dankwalin ture kaga tsiya ne a kanta,dinkin atamfa ce doguwar riga data bude sosai daga qasa,saidai idan ka kalli kayan sosai a jikinta zakasan ta dan sha jiki.

"Ya daga shigowarka kuma dear?" Ta fada tana jin wani iri a ranta,shi ya fiya qaqale qaqale,banda hakan bataga wani shahararren datti da dakin yayi wanda zai hana mutum yin bacci ba,taga ko daxun kafin ta fita sai data tattare kayan wankin gefe daya,amma shi baima gani ba.

Idanu ya aza mata kafin ya janye yaci gaba da qarasa goge wajen,sai jikinta ya dan mata sanyi daga kalar kallon da yayi mata,don haka ta saki qofar tana qarasowa ciki.

Kafin ta qaraso ya gama,ya ajjiye mopping stick din,sannan ya goye hannayensa da tuni ya nade hannaun rigar xuwa sama yana kallonta,yadda ya aza mata kallon mayatattun idanuwan nan nasa duka sai taji nauyinsa ya sake kamata,don haka ta daburce gaba daya

"Samu guri ki zauna" ya bata umarni kai tsaye,sai tadan ja tunga,gabanta yana faduwa,bata qaunar fadansa gaba daya,yanzun nan zai sanya ka ka rasa abun fadi,bayan tasan bata da kalar kowacce hujja da zata kare kanta da ita,dole ta samu gefan gadon nawwara ta zauna.

Daya daga cikin kujerun dake hade da teburin karatunsu ya jawo,ya ajjiyeta dab ds ita ya zauna akai.

Shuru ya ratsa dakin,tana ta kasa kunne taji me zayace da ita,yayin da shi kuma bai furta komai ba,sai kallo da ya ritsata dashi,kallon dake sake sanyata jin cewa da gaske ita din mai laifi ce

"Hafsat" ya kira sunanta kai tsaye,wanda abune mawuyaci kaji ya kirata din

"Na'am" ta amsa masa ba tare data iya kallon qwayar idanunsa ba

"Ki gayamin me kika nema kika rasa a gidan nan,wanne nauyi ne nawa da bana sauke miki?" Motsawa tayi,kamar wadda ke zaune saman wuta,kasa bashi amsa tayi,har ya gaji da jiranta,sai ya sauke hannayensa qasa ya dafe kujerar da yake kai yana ci gaba da kallonta

"A iya sanina babu wani abu da yayi saura wanda bana miki shi,ci sha suttura,kudin kashewa,hatta da lighter da za'a kunna gas a gidan nan alhmdlh ban bari ko yarda ki siya ba,me kika rasa hafsat?,amma kin kasa tsaida hankalinki ki tsaftace gidanki,ki kula da yaranki,ki sauke hakkina dake kanki,zaki iya tuna when last da kika kawo kanki gareni?" Ys jefa tambaya mafi girma da taketa tsoron yayi mata ita

"Don Allah kada ka kawo wannan zancan,ka san dai ina iya bakin qoqarina ai......" Wani miskilin murmushin takaici ya saki

"Well......am listen to you" da qyar ta tattaro dukka jarumta da qwarin gwiwar ta,duk da cikin ranta har yanzu bata jin kanta a matsayin mai laifi

"Ina fa kwatantawa,ina qoqarina dear,aikin gida fa ba is not easy at all,sauqinta ma ace ina da 'yar aiki,amma yanzun komai fa ni nakeyin abina,ga yara,ga makarantar mimi,dole wania abun fa sai ana haquri" ta fada tana dan tsuke girarta fuskarta qasa qasa,ita ala dole bataji dadin gyaran da yakeson mata ba.

Shuru yayi kawai yana kallon fuskarta, reaction din da ta nuna saman fuskarta ya isa ya gamsar dashi cewa bata dauki kanta a tana aikata wani abu na ba dai dai ba,an dade hakan tana faruwa a tsakaninsu

"Idan aiki ya hanaki gyara muhallin mijinki dana yaranki.....shi kuma kitchen da kika tara kwanukan wanke wanke fa?, harda na tuwon jiya?"

"Yau ai fita nayi,kuma ka sani dear,ban zauna gaba daya a gidan ba,amma gobe in sha Allah da aikinsu zan tashi,idan na gyara gobe zaka ga kamar ba'ayi ba,ba shikenan ba?" A hankali ya lumshe idanuwansa gaba daya yana kiran sunan Allah,mata nawa ne keda nauyin da yafi nata amma zaka samesu su da gidansu da iyalinsu tsaf?,wannan muguwar qazantar baisan ta yaya zai raba hafsat din da ita ba,tafi komai ci masa tuwo a qwarya,ya yiwa qazanta wani mugu tsana da har baisan iyakarsa ba,abinda hafsat din har kwanan gobe ta kasa ganowa,mai aiki dai mai aiki dai.....shikam ba sakaran namiji bane da zai daukoma hafsat mai aiki,ya tabbatar daga qarshe ita zata koma yin komai.na gidan,qarshe harda abincinsa da zaya ci.

Miqewa kawai yayi,ya zura hannayensa a aljihunsa

"Duk abinda ya kamata nayi miki na miki shi,ya kamata ki canza for now.....yaranki suna girma,zasu kuma dauki jalar kowacce dabi'a daga wajenki,dama sau daya tak take zuwa ma mutum a rayuwa" yayi maganar yana daga yatsansa guda daya,sanann ya juya yana barin dakin.

Gabanta ya fadi,binsa tayi da kallo har ya fice,to me yake nufi?,abbas din yana da wuyar fahimta wani lokacin,ta janye idanunta daga kallon qofar da tuni ya jima da wucewa,ta dawo

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login