Showing 135001 words to 138000 words out of 200116 words

Chapter 46 - A RUBUCE TAKE (KADDARATA)

kadan,itakam halinta dabanne,duk da sun girmeta,bai taba jin hafsat ta aikesu tayi musu ko sannu ba bare godiya.

Tare suka fita a motar,shi ya doshi gate ba tare da yayi tunanin zuwa su gaida da hafsat ba,don sai suyi zuwa dari ba wanda ya kalli sashenta,sai dai idan sunga idanun abbas din,ko shi yace su shiga su gaisheta.

Kallon sashen hafsat din tayi,gabanta yadan fadi,ta tuna kiran data dinga mata bata dauka ba,wanda shine tun daga ranar bata sake kiranta ba,saita dauke kanta,ta doshi sashen abbas din da dan hanzari,tana Allah Allah ne ta shiga ta bashi ta fito ta wuce sassanta.

Tayi mamakin ganin wutar falon gaba daya a kashe,babu hasken komai sai na wutar bedroom dinsa,sarkin tsoro tsoron nata ya motsa,duk da bawai duhu can can yayi ba,don hasken fitilun waje suna ratsowa ta labulayen falon,ta fidda wayarta ta kunna torche sannan ta doshi dakin.

Da siririyar muryarta tayi sallama tana shiga dakin,bata lura dashi ba har sai daya dan motsa daga kwancen yana amsa mata sallamar,ta danja baya adan tsorace,sai ya koma rigingine yana kallonta da rinannu idanunsa

"Uncle.... Lafiya?" Ido ya lumshe sannan yayi qoqarin miqewa yazauna yana cije bakinsa kadan

"Lafiya lau,ina umar din?"

"Ya wuce,ga key din yace na kawo maka" ta qaraso gefansa ta duqa ta ajjiye,qamshinta ya huro masa har inda yake,sai ya maida idanunsa ya rufe

"Yunwa nakeji,zan samu abinci?" Da mamaki ta kalleshi

"Mommy hafsa fa?"

"Zan samu abinci?" Ya sake maimaita tambayar tasa ba tare da yabi takan maganarta ba,sai ta gyada kanta da sauri

"Okay,dafamin wani abun mai sauqi mai ruwa ruwa" sai a yanzun ta lura da yanayin fuskarsa,gaba daya ta nuna bashi da lafiya,jikinta yayi sanyi,ta matso sosai kusa dashi,tasa hannu tana dan taba fuskar tasa

"Uncle kamar baka da lafiya fa" ji yayi kamar ta zuba masa wani abu me sanyi a gangar jikinsa,ya rufe idanunsa ya budesu a kanta

"Bani da lafiya weedad" sosai fuskarta ta nuna damuwa qwarai,ta tsugunna gabansa tana ajjiye jakarta

"Amma uncle ne yasa ba zakasha magani ba?" Ido ya zuba mata sosai,yana ji a ransa inama zata iya dauke lalurarsa,inama tace zata zame masa maganin?,ya sani matarsa ce.....amma yasan halittar da Allah yayi masa a shekarunta yana ganin indai ya fuskanceta da wannan zai iya cutar da lafiyarta

"Zansha weedad......bani wani abun tukunna" da saurinta ta miqe ta zame mayafinta da jakarta duka ta aje a wajen,suman zaune ya kusayi,dogon sassalkan gashinta na kwance a bayanta,tunda ta shigo daman dankwalinta yana jakarta,ba kasafai take daura dankwali ba don basa shiri, skert din ya fidda shape dinta sosai,ta baya zata dauka takai shekaru ashirin da wani abu,sai a lokacin yaga girman da yaji 'yan uwansa na fadin tayi,ya koma da idanunsa luuuuu ya rufe yana kiran sunan Allah.

Faten dankali ta shirya masa,duk da yadda yayi dadi amma gaba daya baya gane taste dinsa akan harshensa,zamanta kusa dashi yafi komai dagula masa lissafi,ita kuwa ta zauna ne bilhaqqi tana matsa masa yaci

"ko baiyu dadi bane na sake maka wani uncle?" Ta fada a shagwabe saboda sam bata jin dadin yadda taga baya ci din sosai,kansa ya girgiza dankalin yana wuce masa wuya da qyar,sai ya aje plate din ya zuba mata idanunsa gaba daya yana mata wani mayunwacin kallo

"Maganin zaki bani" ya furta da wata birkitacciyar murya,itama shi take kallo,karon farko da taji kallonsa ya saukar mata da wani abu mai nauyi a jikinta da zuciyarta

"Ina maganin yake saina dauko maka" tayi masa tambayar tana janye qwayar idanunta daga kansa,saboda wani nauyi da taji ya saukar mata lokaci guda.

Kanta ta daga sanda taga ya miqo mata hannunsa,ta kalli hannun ta kuma kalleshi,bata fahimci komai ba

"Zo na gaya miki inda yake" a mamakance ta miqa masa hannunta,bata kai ga tuna komai ba ta samu kyakkyawan masauki a jikinsa daya dauki dumi,cikin qirjinsa ya lullubeta gaba daya yana sauke wani irin numfashi a jejjere,komai ya fara koma masa sabo,tunaninsa ya fara nisa ya fara daina gane komai.

Yamutsa ta ya fara yi,abinda ya tsorata ta ta fara kiran sunanshi tare da qoqarin kama hannuwansa dake yawo a sassan jikinta,ko harafi daya bai gane ba cikin maganganunta,illa dai yana jin sautinta kamar mutumin daya sanya bakinsa cikin kofi yana magana(sama_sama),a yau ya ware dukka hannayensa a kanta,duk inda suka kai bai musu shamaki,haka nan bakinsa.

Sanda ya hade fatar jikinsu waje daya daukewa numfashinsa yayi cak na wucin gadi sannan ya samu ya qwatoshi da qyar,qasan da suke yaji tayi masa kadan,ya dagata zuwa tafkeken gadonsa ya shimfidar da ita,zuwa sannan tsoro ya kusa halakata,abinda bata taba gani ba,bata kuma taba zata ko tsammani ba.....yayin da abbas yayi nisa a wata duniya, duniyar da tunda yake bai taba tunanin ana kaiwa har can ba,tun daga tsarin lallausar fatarta zuwa daddadan qamshin jiki dana sumar kanta komai ya sake kwance masa,ya rasa ta inda zai juyata,ko ina ya juyatan sai yaji yayi masa kadan.

Kuka mai qarfi ta saki sanda taji ya soma rabata da sutturar jikinta,ta shiga roqonsa da kyau akan kada yayi mata komai......ummu ta hanata......idan yayi ummu zata kasheta,amma ina samm samm baiji ba,abu daya ne ya maidoshi duniyar sa,daukewar numfashi daga gangar jikinta bayan taja wani dogon numfashi sanda ya soma buda hanyarsa zuwa sabuwar rayuwa da sabuwar duniya.... dole ya zare jikinsa daga gareta ba tare da yakai ga cimma gaci ba,ya koma qoqarin ganin daidaituwar numfashinta.

Tun da safe ta tashi da sha'awar cin awara,sai da yaran sukayi bacci sannan ta fita da 200 zuwa bakin gate dinsu,ta bawa yaron gidansu ya siyo mata

"Ka riqemin kudi na da kyau,don idan ka yarmin sai ka biyani" kudin ya kalla sannan ya dubeta

"Hajiya dari biyu ce fa" ya fada qasan ransa fal mamaki,kaf unguwar kowa yasan waye ASP abbas din,amma ita sam bata jin kunyar yin aike da qaramin kudi

"Na sani,ko bani na baka ba?" Sai ya gyada kai

"Hakane" daga haka ya juya yana fita daga gidan,cikin ransa yana tur da irin halinta.

A hanyar dawowa ta kalli motarsa,har yanzu bataji motsinsa ba,wani sashen na zuciyarta yana mintsinarta kan ta shiga ta duboshi,wani sashen yana fadin ki shareshi,zai kawo kansa da kansa,kulawa ma yabawa ce ai.

Kamar giftawar iska taji fitar sautin qaramin ihu,wanda banda hankalinta dama akan sashen yake babu lallai taji,birki taja ta tsaya,gabanta yayi wani mugun faduwa,ta tsaya cak tana duban sashen nasa,muryar tayi mata kama da muryar widad,to amma yaushe ta shigo gidan?,tunda dai ita bata ji shigowar kowa ba,hakanan bataji fitar kowa ba,ta zubawa sashen idanun sosai ko zata sake jin wani motsi amma bata ji komai ba,sai hankalinta ya rabu biyu,wani sashen na zuciyarta na bata shawarar ta shiga ta duba,wani sashen kuma yana cewa tsarguwa ce kawai tayi,duk da haka saita kasa gamsuwa,ta dawo farfajiyar gidan ta zauna saman fararen kujerun da abbas din ya zuba a wajen saboda baqi,idanunta nakan sashen tana nazartarsa.

Babu ma alamun haske gaba daya,wanda wannan sign din da take gane abbas din yayi bacci,don baya kwanciya da haske a kanshi,sai taji zuciyar dake gaya mata tsarguwa ce tafi rinjaye,amma duk da haka zata jira dawowar yaron,tasan zaiyi wuya wani ya shigo ko ya fita baya wajen.

Bai jima ba ya dawo da awarar a farar leda karrr kana hangota quru quru,tasa hannu ta karba tana dubansa

"Babansu mimi ya fita ne dazu?" Kai ya girgiza

"Anya?,tunda ya dawo dai banga ya fita ba"

"Bayan shi fa ba wadda ta shigo gidan nan?" Kai ya jinjina

"Babu gaskiya" saita gyada kai tana sauke ajiyar zuciya

"Shikenan jeka" sai data qara wasu sakanni sannan ta miqe ta koma ciki,tana tafe tana waigen sashen, zuciyarta taqi gamsuwa,amma ranta ya aminta da abinda yaron ya fada,tsaki taja daga qarshe,ta maida qofa ta rufe sashenta.


*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks: Huguma*

Page 70


Duk da cewa baikai ga cimma gaci ba,duk da cewa buri da muradinsa bai cika ba......amma ta kaishi wata duniya data sake haukata tunaninshi,ta sake ninka burinsa......ta sake kwadaita masa ita,ta kuma haifar da wani yanayi da kai tsaye zaka kirashi da ZAZZAFAR K'AUNA a karon farko,cikin jininsa ya dinga ji cewa eh weedad din ta dabance,zata iya zamowa ta musamman cikin mata..... za'a iya kiranta da 'yar baiwa,ya samu wani irin nutsuwa da tarin ni'imomin dake hutar da zuciya su kuma sanya ma ruhi nutsuwa tattare duka a iya jikinta kadai,tun baikai ga afkawa waccar duniyar ba.

Wani irin ciwo yakeji har cikin zuciyarsa sanda take rera wani irin kuka,ciwo ciwo takeji daga can qasanta duk da baiyi yawa ba,saidai hankalinta a mugun tashe yake,me ya aikata mata kenan?,da wanne fuska zata kalli mutane?.

Yayi lallashi yayi ban bakin amma a banza,har sai da bacci ya taimakeshi ya dauketa,sai ya zareta daga jikinsa a hankali ya shimfidar da ita,ya kunna bedside lamp ya matso da ita kusa da fuskarta sosai.

Kallo na haqiqa ya zauna yana qare mata,baisan da wanne suna zai kirata ba,baisan kuma a wanne matsayi zata iya tsayawa cikin zuciyarsa ba daga ranar da ya maidata tashi,a yanzun Allah ne kadai yasan me yakeji a kanta,qauna soyayya tausayi da kuma shauqi gaba daya, mintuna qalilan amma sun canza matsayinta daga wani bigire zuwa wani bigiren na daban.

Ya jima zaune kamar mai karanta littafi yana kallon baby face dinta da tayi jazur da ita,sannan ya sauke ajiyar zuciya,ya zura qafafunsa ya sauka daga saman gadon ya shige bandaki.

Tsarkake kansa yayi sannan yayi wanka,ya fito ya tsane jikinsa da kyau ya sauya kaya sannan ya koma saman gadon,bai jishi dai dai ba har sai daya jawota jikinsa,tunane tunane ne masu tarin yawa ke masa yawo a kai,shi kansa idan yace ga dai dai lokacin data ma zuciyarsa wannan muguwar illar yayi qarya,wani abu mai qarfi akanta ya dinga shigarsa,sai ya dinga jin gaba daya duniyarsa ta ta'allaqa da ita.

Kiran sallar asuba ne ya tasheshi,har ya gama shirinsa na fita masallaci bata ko motsa ba,bacci take sosai tana kuma sauke ajiyar zuciya lokaci bayan lokaci,har sunkuya saman kanta zai tasheta yaji ya kasa tashin nata,yaja mata bargon ya rufeta bayan yayi kissing goshinta,ya fita yana waiwayawa kamar wanda akace za'a dauketa kafin ya dawo.

Sanda ya fita sallar yayi mamakin ganin cunkoson jama'a a layin nasu,ya qarasa a hankali ya fara musabaha da mutanen dake wajen

"Munyi tunanin baka gari ai yallabai" daya daga cikin dattawan layin ya fada yana duban abbas

"Me yake faruwa alhaji audu?" Abbas din ya tambaya yana dubansa

"Wallahi daren jiya 'yan fashi suka shigo gidan maqocina alhaji isah"

"Subhanallah" ya fada cikin alhini

"Kusan kowa yaji abun,don tun wajen karfe daya na dare suka shigo unguwar,basu fita sai qarfe uku"

"Ya salam,Allah bai sa naji ba,amma aka rasa wanda zaiyi kiran koda wayata?"

"Wallahi Allah ya daukewa kowa wannan tunanin" matsawa gaba ya fara yi zuwa gidan alhj isah din,inda mutane suka fara dandazo

"Badai wanda suka raunata ko?"

"Eh to,sun harbi yarinyar sa,suna hanyar kaita asibiti"

"Kun kira jami'an tsaron?" Cikin alhini alhj audu ya girgiza kai

"Kusan awa guda kenan amma babu su ba dalilinsu" sosai ran abbas din ya baci,ya tambayi police din wanne area dinne alhaj audu ya gaya masa,sai ya fidda wayarsa yayi kiran dabai wuce na minti uku ba cikin bacin rai

"you must be there before thirty minutes" abinda ya fada kenan ya kashe wayar ya mayar aljihu

"Kada kowa ya shiga cikin gidan,sannan suma mutanen gidan a gaya musu su nisanci inda abun ya faru.... alhaji muje muyi sallah tukunna" tare suka rankaya da alhaji audu zuwa masallacin suna sake tattauna yadda abun ya faru,bashi da nauyin bacci sam,kamar yadda bai saba dogon bacci ba,amma yayi mamakin yadda jiya har akayi aka gama abun baiji ba,lallai da gasken gaske 'yar qaramar yarinyar ta gigita masa rayuwa da kyau a jiyan,ta kuma shirya janshi zuwa wata rayuwa ta daban,baisan sanda wani siririn murmushi ya kubce masa ba.

Wannan case daya faru a unguwarsu ya hanashi komawa gida da wuri,sunata bincike kan abun har sai da suka samu nasarar tracking barayin cikin taimakon Allah da kuma qwarewar da yake da ita,sai wajen qarfe daya na rana sanann ya gama nasa aikin,ya danqawa wadanda alhakin kula da area din yake a hannunsu,ya zare safar hannunsa ya miqawa daya daga cikin police din,gaba daya hankalinsa yana kanta tun dazun,dauriya kawai yakeyi.

Sama sama ya amsa gaisuwar yaron gidan nashi ya wuce zuwa cikin gidan,kai tsaye sashensa ya wuce,ya tura qofar falon ya shiga,bata falon bata bedroom din,sannan bata toilet,sai zuciyarsa ta raya masa ko tana sashenta,don haka ya juya akalarsa zuwa can.

Kaf ya gama dubawa bai ganta ba,sai abun ya shiga bashi mamaki,baya da niyyar shiga sashen hafsat din yau gaba daya,amma dole ya shiga ya gani ko tana can.

Dukkansu suna falo ita da yaran,tuni falon ya koma 'yar gidan jiya,tana saman k????      

                  ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? ujera zaune abinta,ta cika tayi fam da fushi,daga abbas din har widad din kowanne da nasa laifin a wajenta,donme yarinyar zata tafi gidan hajiya tayi zamanta?,uban waye zaiyi mata aikin da tafi kowa sanin itace zata yishi?,sannan abbas din me yake nufi da ita?,har azahar tayi amma ya kasa leqowa yaga lafiyarsu?,jikinta ya soma sanyi amma wani sashen na zuciyarta yana qarfafa mata gwiwa,tare da sake kambama mata laifukansa,duk da haka ta soma rasa qwarin gwiwarta,tasanshi....yana da danne zuciyarsa da hanata saurin fushi,amma kuma idan yayi fushin bashi da dadi sam.

Boyayyar ajiyar zuciya ta sauke sanda taga shigowarsa,ya tsugunnawa yaran suka haye bayansa,fuskarsa na fidda murmushi,zuciyarsa dauke da tausayinsu,da babu alamun an musu wanka

"Ina antynku?"

"Daddy ta dawo?,ka kaini wajenta" mimi ta fada,abinda ya tabbatar masa kenan bata shigo ba kwata kwata

"Ina kwana?" Ta fada ganin yana niyyar miqewa ba tare daya kalleta ba

"Lafiya"

"Ga breakfast dinka har ya huce baka ci ba"

"Na qoshi" ya amsa mata yana ficewa riqe da yaran.

Hankalinsa yadan tashi,ina ta tafi to?,ya tambayi kansa,sai ya jawo wayarsa ya kira layinta,a kashe layin yake,ya sauke wayar yana fidda iska daga bakinsa,gidan hajiya ta koma?,wata zuciyar ta gaya masa,har ya danna kiran layin hajiya sai ya kashe,idan ta tuhumeshi dalilin komawarta baisan me zaice mata ba,don haka ya kira layin umar.

"Kana gida ne?"

"Eh hajiya za'a baka?"

"Weedad tazo?"

"A'ah yaaya,tun jiya dai dana kawota gida"

"Okay,karka cewa hajiya ga abinda na tambayeka"

"To yaaya" umar din ya fada ,kafin ma ya qarasa abbas din ya katse kiran,sai yaji hankalinsa ya sake tashi.

Muhsin ne ya fado masa,baiyi qasa a gwiwa ba yayi kiransa bayan sun gaisa kafin abbas dinma yace komai ya rigashi magana

"Jiya jiya muke zancanku,inajin madam fa gobe ko jibi zata shigo ganin diyarta,nace ban da tabbacin kunxo weekend wannan satin"

"Jiya mukazo,amma kuma banajin zamu jima zamu koma,yanzun ban fiya sakewa a bauchi ba,ayyuka sunyi yawa a kaduna" hira kadan suka taba sukayi sallama,don shima muhsin din fitowarsa kenan daga gida yana kan hanya yana driving.

Wayar ya ajjiye,ya koma gefen gadon ya zauna hannuwansa cikin sumarsa yana murzata a hankali,yanason qwaqwalwarsa ta hasaso masa mutum na gaba da zai kira ya bincika ko can taje,ya akayi ta iya fita daga gidan har ta fita ba tare da wani ya ganta ba?.

Kasa zama yayi,sai kawai ya miqe ya dauki key din motarsa,tsoronsa daya kada yarinyar mutane ta bata cikin garin daba nasu ba,don yana da tabbacin zaiyi wuya ace shigowa akayi aka dauketa,don ya duba duk wani abu da zai iya bada alamun hakan bai gani ba,sai ya fita da yaran ya zubasu a motar suka fice daga gidan.

Layi layi titi titi ya dinga bi yana dubata amma sam babu ita ba alamarta,har wajen azahar,ya tsaya a wani restaurant ya siyama yaran takeaway,ya dawo cikin mota ya zauna kenan wayarsa ta dauki tsuwwa,ya duba me kiran sai yaga muhsin ne

"Kasan matarka ta tafi kano?"

"Kano?" Ya tambayi muhsin din cikin mamaki qwarai,duk da dama yana cikin dimuwar son sanin ina tayi

"Eh,yanzu muka gama waya da ummu,ta kirani tace na shaida maka,don tafiyar batayi mata kama data nutsuwa ba" qatotuwar ajiyar zuciya ya sauke yana jin wata nutsuwa na saukar masa

"Alhamdulillah" ya fada a fili

"Ka ganni a gefan hanya,tun dazun nake checking ko batayi nisa ba,ina shirin kira headquarter ma su bani mutane muyi aikin tare"

"Subhanallah.......wanne irin sakarci ne wannan?,halan bata gaya maka ba bakasan da tafiyar tata ba" qaramin murmushi ya subuce masa,yasan sarai muhsin ba wasa,yanzun nan idan yace zai gaya masa gaskiya sai yace zai taba masa mata,shi kam a yanzun a yadda widad takai har cikin ruhinsa,baya jin ko ruwan sama zai lamunce masa ya taba masa ita

"Me na tone tone?, tunda ka isar da saqon ummu shikenan,zan kirata"

"Please abbas......kada kace zakayi kawaici,ka gayamin gaskiya"

"Amma

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login