Showing 99001 words to 102000 words out of 152888 words

Chapter 34 - Dama Ta

11 Oct 2024

8601

ba'a aureni na haifeka ta sameka ba nima wata na tarar duk da kai ma kanada naka lefin na boye mata musamman mu da ka gayamana ko da ka tashi daga saudia da kaitsaye gida ka iyoda ita da hakan bai faruba dan meza ka boyeta kace wani saita haifu gashi abinda ya janyo da wane ido zamu kalli Malam da Aisai mutumiyar arziki."
Nade Ummi tayi tayiwa Nabil fada

_Shiko hamdala yayi ganin koyau Fandau tafito zai mallake ta basai_ _asiri ya tonu_ _ba, yaran su zauna a yaran Hadim din kawai shide_ _yakasan ce da Fatin sa sai yaji wani karfin guiwar nemanta dan yasan Ummi zatayiwa Abban sa bayani yanda zai_ _gane._

Ummi ta sake cewa
"yanzu kenan tayiwa mutane asaran cikin wata 4."
"Ummi barni da ita na daga mata kafane dalilin cikin da yake jikinta ."

"amma inason ka janye kalman saki da kamata."

" shikenan yanda kikace haka za'ayi Ummina na maida da."

Ummi tace " yawwa sai kuma abuna 2 dole Malam da Aisa susani dan su tayamu adduan nemanta, sai kuma inason kai ma Baban ku yasani daga iya mu kar kowa yasani har sai an sameta kasan halin wanan Innar taku yanzu zata jakula komai." "to Ummi amma Ummi kimin alfarman koyawa Hadim hankali dan kiyaye gaba."

"Wane koyamata hankali zakayi bayan halin da take ciki ma ya isheta jiya wata kawar ta takawota ai bakaga yanda takoma ba ninan da niyar naci maka mutumci nazo sai na tadda lefinta yafi naka, saide ya fatime dole inaga itama tasani dan tananan tana fada baki da kunfa."

Mamar hadim kenan

"shikenan Ummi amma itama kartasan na maryar da Hadim din."

Ummi tace
"Bazata sani ba."


A ranan Ummi ta tasa Nabil a gaba suka koma. Alh Abubakar baban Nabil har marin sa yayi dan lefin shiya daurawa idan bashi yasakewa mace ba har ta isa tayi.

Shiko Malam lefin Fandau yagani dan a ganin sa Nabil taimakon ta yayi ma ai godiya dasa albarka ba irin wanda mama da Malam basuyiwa Nabil ba dan susan saboda su yayi.

Ko wacece wannan matar ta cucesu ta yaudari yarsu ta kaita har saudia.

Malam ya dukufa addua sosai duk dama yanayi dan yana mutukar son Fandau.

Itako maman Hadim cewa tayi kawai taji tayi lefi amma bai kamata ya dauki Fujjirat ya kaiwa uwar kishiya ba a karbo mata jikar ta, tayi akira mata Nabil kinzuwa yayi sai ita ta taka taje gidan Nabil din amma security suka hanata shiga dan waya suka yiwa Nabil yace kar abarta.

Aiko baki da kunfa tasa Sudais ya juya da ita gidan su Nabil ta samu Ummi ta mata tatas tace takira Nabil din
Nabil yana shiga ya gaida su "yace Mama ya mai jikin?

"lalle Nabil karena min hankali sai anan kake tabbayana ya mai jiki, aiko mutuwa tayi kaine sila tunda kai kamata duka ba kaga halin da take ciki ba yanzu tun yaushe tazo amma ko ajikin ka bakaje dubata ba."

"Mama inajin baki gama sanin abinda ita Hadim din tayi bane, ai gwara nida na daketa gashinan na bar miki ita kina kallon ta,
Itada ta tashi ba la'anta yar mutane tayi ba? ta kuma batar da ita, amma ina son idan kin koma ki gaya mata Wllh wllh darajan cikin da yake jikinta na kyaleta yanzu amma zata haifu zata ga yanda zanyi da ita, zuwa duba ta kuma karkiyi fatan wannan dan inhar zansa Hadim a idona to zan hallaka ta dan haka rashin zuwana rahama ne."
Kuka mama tasa tana nuna Ummi Hajara kina gani a gabanki dan da kika haifa a cikin ki yake gayamin wanan maganan?

Ummi itama bata ji dadin abinda yayi ba amma tasan halin Nabil idan ransa ya baci zai iyayin fin hakama dan haka tace "tashi katafi kafin ka rufe muda duka."

Cikin kuka Maman Hadim tace ni yaje ya karbo min jikata ya karbota kawai."

Har zai fita Ummi tace "kaje ka karbo Fujjirat."

Juyowa yayi ya kalli mama yace jikar ki ya wuce na jikin yarki idan ta sauka idan macce ta haifa inason asa mata Fatima idan kuma Namiji ne Abba inusa amma fa Fatiman da na fada kar ki dauka sunan kine tunda kema Fatime sunaki."

Girgiza kai Ummi tayi tace "bance kafita ba."

Yafice yana cewa danme baza ta barni da masifar da yarta ta jamin ba sai tazo tana min masifa
Wllh in Hadim batayi furcin ba to wllh Fatima ta baiyana kafin haifuwar ta kai ko ta baiyana inde bata cikin haiyacen ta sai tayi zaman gidan yari baki koyawa yarki yand....... Ummi ce ta katse mishi maganan da jifansa dawani cup na glass sannan ya karasa ficewa "Yaya dan ALLAH kiyi hakuri ke kanki sheda ce akan yanda halin Nabil yake tun yana yaro idan ransa yana bace ba a masa magana bake ba koni idan na matsa wllh abin ba zaiyi kyauba."
"hajara ke sai ya miki ki kyale shi amma banda ni. A zaburi Hjy Fatime ta mike har da gudun ta tafita wajen a daidai inda zai shiga parlour Iya ta same shi ta baya ta fincikoshi "kazo ka gaya min matsayin y'ata awajen ka kuma ko a kotu sai na karbi dukka jikokina."

A hankali Nabil yasa hannu ya kwace a hannu ta idon sa fes cikin nata sai kace a gaban abokin sa yake yace "matsayin yarki bata dawani matsayi a wajena sai dai idan ragowan sakinta kikeso zan iya bin umarnin ki a masayin ki na uwa a gareni in baki sakinta.

"Sai kuma batun yara kema kince jikoki, jika ko ba d'a bane ki bari me yaran tace a bata da bakin ta" Iya ce ta fito tana "Subahanalla Nabil ya haka" Ummi mari tafara zu bawa Nabil shiko Nabil nade hannunsa yayi a kirjin sa yana jin yanda Ummi take zuba masa marin, kanne sa dukka suka fito sai kuka suke dakyar Iya ta ja Ummi itako Mama zubewa tayi tana rinjin kuka
Nabil ficewa yayi ya fada mota driver yaja motocin security dinshi suka rufa masa baya suka fita cewa yayi airport zasuje dan shi gani yake kamar ABUJA ne zai bashi Fatin sa.

*GIDAN DR MUKTAR*
"Aunty yanzu jibin zamu tafi kenan?
"habiba tace insha ALLAH kirki ta Ghana zamu tashi saboda ke Dr ya sara tafiyan ta can dan a wanan kasan bazai ykwu mu tashi dake ba yanzu haka Ghanan ma a mota zamu tafi saboda Shiddams ya tsanata bincike."

"Aunty yanzu haka zankoma banje naga su mama ba."
"Toni Fandau ya zanyi ne nayi nayi dashi yaki, nace idan munje dake kisa nikaf har mufito a kallah de kinga mama zakiji dadi, amma sai cewa yayi ai baki damu da ita ba da baki barta ba, saide idan kezaki gaya masa kiji."

Fandau tace"ni kema kinsan ban isa ba jiya haka yace wa maimu me aiki kar ta karayin komai a gidan nan nice sabowar me aiki ni zanyi."

Dariya Habiba tayi tace"wai dan kikoyi hankali ne yace ko amma da nake tambayar sa yace yana sone kina dan mosa jikin ki kinga cikin ki ya shiga wata 6 dan kisamu sauki wajen nakuda."

Ko da zasu tafi kaduna barin Fandau sukayi da meimu suka tafi.

Shiko Nabil abubuwa ya kacabe masa ga yan kungiya sun matsa masa wata 2 bashi har sauran kun giyoyin sun fara kawo farmaki ana ta yadawa wai Shiddams yabar Chelsea fans dinsa da sauran mutane sun damesa a media ga zaryar hospital yake ma dan ba shida cikakkiyar lafiya kullum ciwon kai dana kirji yake fama dashi, kowane dr idan ya duba shi sai yace yasa wani abu ne a ransa wanda yafi karfin zuciyar sa idan bai cireba to yana barazana ga rayuwar sa aiko yan club din su sunajin haka suka zo tafiya dashi ayi jinyar sa acan yace a'a abu har ya kaishi ga kwanciya sosai.

*HADIM*

Ko makiyinta ya ganta cikin wannan hali zai tausaya mata "Mama yanzu Nabil din bazai zoba bayan ance yana garinnan Ummi yasani a blacklist bana samun sa mama kibari naje London din mana na same sa tunda kince yakoma."
Mama cewa Hadim tayi Nabil ya koma dan ta kwantar mata da hankali amma kullum zancen ta Nabil da kuma a karbo mata Fuj yanzu dai Ummi ta sa ankawo Fuj sai Nabil da take ta ambata wanda acikin asbitin daya ma suke akwance bata sani ba dan ita ma sosai take akwance kullum Dr suna cikin yimata nasiyar ta kwantar da hankalin ta saboda kwata kwata BP dinta baya sauka zai iya janyo matsala idan watannin haifuwan ta yayi idan zamu mata aiki dan.......
"aiki kuma?
inji Ummi da mama
Dr Hafeez yace ba na rubuta muku bayanan acikin katin da na baku ba amma kubini office na karamu ku bayani."

Ummi da Maman Hadim zaune gaban Dr Hafeez
Yace " yaka mata ku kula da halin da yariyar nan take ciki, yanayin cikin ya kamata a kula da ita sosai tunda ba haifuwa zata iyayi da kanta ba aiki za amata dan mun duba mugani kugunta bazata iya haifuwa ba sai de aciro to alluran da zamu mata idan lokacin yayi ba ayiwa me hawan jini dan zai iya barazana ga rayuwar ta ita kuma BP mai makon ya sauka kullum kara hawa yake....

Mama kaseshi tayi da cewa aikin banza rashin sanin aikin kune na kasannan yaza ace bazata iya haifuwa ba itada ta haifi yan biyu ma lafiya haifuwa na 3 ace kugunta bazai iya haifuwa ba."
Dr yace" hjy a kugun akwai wani kashi a kugun kowani mutum mace ko namiji to dana maza ta na bata akwai ban banci na maza babu tsagu na mata da tsagu yanda idan mace tazo haifuwa wannan kashin shi zai bude shine zakiji nishi yazowa mace a daidai budewan tsagun na kashin bazai koma yarufe ba harsai d'a ya fado zai rufe, to ita Halima wanan kashin ba tsagu anata dan haka zan iya ja da kowane likita akan bazata iya haifuwa fa."
Mama tsabar haushima kin magana tayi Ummi "tace Dr dena fada duk haifuwan ta da kanta take haifan su Dr Hafeez yace"hjy kina nufin wannan ta taba haifuwa?

Ummi tace "Wanne irin tambaya ne wanan Dr muna cemaka haihuwa na uku zatayi na 2 ma yan 2 ta haifa yariyar da ka gani a gefin ta tana bacce itace yarta ta fari"

Dr Hafeez yace "Hjy ni a bincike na wanan mahaifan bai taba daukan ciki ba sai wannan asali ma shikan sa mahaifan cike yake da matsaloli dayawa da farko yana iy.......
"dakata inji Ummi dan itama yafara bata haushi itako Mama fuuu ta fice Ummi ma mara mata baya tayi.

Dr yace "niko idan matar na ta haifu da kanta daga ranan zan bar ai kina dan bai min amfani ba."

Sude basu saya bashi amsa ba suka fice.

Suna fita wajen dakin da aka kwantar da Nabil sukace karo da su Jidda sai runjin kuka suke suna ambaton Ya Shid kar kamana haka wllh kaine gatanmu shi kawai suke mai maitawa Ummi ji tayi bata iya daga kafanta dan dama tabar Nabil cikin wani hali yana aman jini dasauri wani Dr yafito yace"wacece Ummi? Da sauri Kamal ya kamo hannun ta yace" gatanan ya farfado ne? ni nasan dama suma yayi ai
Nabil yana gani Ummi yayi wa Dr alaman ya cire masa roban jawo nufashin da yake hancin sa dan baya iya daga hannun sa Ummi tana karanta duk addu'an da yazo bakin ta takara sa inda take kamo hannun sa tayi dakyar ya bude bakin yace "ba'a ganta ba Ummi an nemeta an rasata bansan hanyan da zanbi na samota ba Hadim ta hallakamin ita naso ALLAH ya barni naga haifuwan Hadim na daukarwa Fatima fansa bakin cikina Ummi tasha cewa nace ina son ta amma ban taba furta mata ba ina ma zan ganta ko a mafarki da nace inason ta inason ta ba a dadi, Ummi zan barmiki wasiya idan ta baiyana kice ina sonta har na rasa raina akanta karki damu da yanda take na rashin hankalin ta kigaya mata nina sani ni da ita zuciyar mu ahade yake Ummi me na yiwa Hadim ta lalata rayuwa ta bayan ni namata duk yanda take so ita fatasa na auri yariyar dan.................



*Tofa Nabil Allah ya baka lfy amma kar ka tona asiri*😭😭😭

*Ya Hadim zasu kare da Dr Hafeez me tonan silili mai gani har hanji da gaske ne kashin kugunta irin na maza ne wato ba zai iya budewa ba idan tazo haifuwa wane irin matsaloline a mahaifarta*

*Ya Aisa maman Fandau taji da taji yanda rayuwa ya juya da yarta*


*B JATTKO*

*DAMATA*





*NA*





*BATUL ADAM JATTKO*

*Phareedah umar sokon ki ya iso gareni kuma na gdy da kauna ki zanduba bukatun ku na insamu ina muku typing koda (2days ) ne*

*Haeeza Murtal*
Banman tadake ba
Dakeda duk kan masoyan damata

*ME ZOGALE*
*kema muna mugun tare*


*Gaskiya kina mutukar godiya agareku masoya ina mamakin yanda kuke nuna soyyyyan ga* ```DAMATA```
*Ina baku hakuri wanda suka min magana ban samu na amsa musu ba wllh abubuwa ne suka min yawa amma ina dare da masoyana aduk inda kuke karfin guiwan ku da addua anku yake kara karfafanin guiwa musamman JATTKO GROUP kuna sani nishadi wllh 🤣🤣🤣🤣ina tare daku*


( editing mzz daddy)


*40*


*K*asa k'arasawa yayi dan yanda dan tumfashin da yake ja yagagare shi yaja idonuwan sa suka kakkafe atake da sauri Dr yabayar masa oxygen ahankali nunfashin yafara sauka

Ummi kuka take sosai Kamal ya kamata yafita da ita yana kwantar mata da hankali

Wani sadeden gaye nagani shida familyn disa badan karnayi karyaba zan iya cewa wane Nabil akomai da sauri saurin yake takawa haryabar ss dinshi da family shi su Jidda suka meke kai Ya BilAL BilAL Maina kangeya kenan d'aga Ahj Maina kange millions wanda ya dauki dauyin karatun Nabil shine yake takawa har gaban su Ummi ya durkusa ya gaida su Kamal cikin girmamawa yamasa jagora har gaban gadonda Nabil yake kwance Bilal yasa abokin nasa agaba yana mamakin wai Nabil da mata suke tsoron tunkara yakoma haka akan macce

Yakalli Kamal yace kamal "kiramin Dr din ."
kamal yafita suka shigo da Dr tare
Bilal yace"Dr kuhada mana kwararun doctor wanda zasu ina control din matsalan sa acikin jiri har kukara sa England."

Dr yace ok sir yaushene tafiyan? yace "yanzu."

Kamal dadi yaji dan bayanda ba ayi da Nabil afita da shi amma yace shibawan da ya isa yasa shibarin Nigeria dan Fatin sa tanaciki sunrasa wacece Wata Fatin dansu har yanzu ba agaya musuba yanzu koyasan bai isa hana BilAL fita dashi ba

dasauri doc yafita

daidai da shigowan malam da Baban Nabil da Bunu dan gidan Malam
Addua malam yamasa yace Bunu da Baba su daga shi abashi rubutun Baba
Yace
"akkaramakalha da anbar rubutun nan tunda kace na dan ganane kar kuma wata rana matar sa ta baiyana yakita azo ana nadama."

Murmushi Malam yayi yace" Abukar abashi."

Bunu da kamal suka daga shi kuka Nabil yasa daker yabude bakin sa yace"Malam kar abani abinda zan manta Matata."

Matsawa Malam yayi inda yake yakama hannun sa yace"baza ka manta ta ba wannan na samun saukine acikin cunci ko bakaso Fatin naka ta sameka da lafiya ne?
" ina somana Malam
Yaushe zanganta?
"kakusa ganinta kasha rubutun komai zai zomaka da sauki."
ai dasauri
Yace"idan nasha za aganta?
Malam yace "insha ALLAH."

Ai da sauri ya daga kansa duk da bazai iya tashiba alaman abashi Bunu ne yakara masa roban abaki yadan sha sosai sai da yaji cikin sa yana murdawa yabari shiko kashi zai iya ci inde za asamu Fatin sa
Kamal ya kwantar masa kan a filo
Bilal ya durkusa ya gaida su Baba yace "Malam waifa BilAL soyake ya fitar da abokin nashi."
"ai ba lefi saide aikin da zan masa na kwana 3 addua idan angama sai su tafi."

Cikin kwantar da murya BilAL yace"gafurta sai atafi da kai ai inde badamuwa."

Malam yace "badamuwa zanso hakan saide gobe akwai meeting namu na hakimai wanda yazama dole na halarci taron da safene da yanma sai muwuce."
Baba yace "da yau da goben duk dayane ai."

Haka washe gari aka tarkata Nabil da har yafara samun sauki dallin aduar da ake masa aka fita da shi yan club din Chelsea su sunji dadin hakan su suka dauki nauyin komai

Maman Fandau danne watayi agaban su Malam amma hankalin ta bakaramin tashi yayi ba harya fi na sanda Fandau ta tafi tashi yanzu shikenan anmata alluran da ta banta da komai arayuwan ta bazan iya yafewa matar da ta dauketa ta kaita saudia dan ta nema mata kudiba ALLAH sarki Fatima na da taji labarin zan warke shine aka yaudare ta da dashi dama nasan yanda kike sona da kishina komai zaki iyayi akaina saide yarinta daya hana baki gane illar kina macce me karancin shikaru barin ki gida da hatsarine ba bakiyin tunani ba gashi har kin fada halinda kwara makantata so dubu amma nasan Halima bata san ke y'ata bane da bata gwada wanan zalincin akanki ba dan kina kishiyar ta
Koda ta gayawa Bagana haka bagana taci kukanta tace "mama wllh dawannan labari kwara ace ta mutu."

Mama tace "ina zaki hada dama ai mutuwa kowa zaman jiranta yake."

"mama ALLAH ya isa tsakanin muda Hadim."

Mama tace "kai dena fadan haka kiyafe mata dan nasan ba lefinta bane lefin mesunan Malam ne daya gaya mata yarmu ci danasan halin kirkin Halima da bazata mata ba."

"mama wllh da lefinta ai kishi ba hauka bane koma yar wacece yaka mata tayi hakane jiyan nan fa naje naduba ta baga yada taba ni tausayin ba bata da lafiya abin dausayi tunda nazo nakecewa abban Tajjudeen anty Hadim ta zama abin tausayi ashe ita ta jefa min yar uwa cikin wani hali ban sani ba sake fashiwa tayi da kuka tana cewa YaFandau ina zanganki."

Dakyar mama ta lallasheta
tace" keda kike hakin haifuwa yau ko gobe bai kamata kijefa kanki cikin damuwa ba shima Nabil din yana iya kokarin sa wajen nemanta
Mama ta dauki Tajuddin tace "dashi zan tafi dama an dauke Hajara."

Bagana tace

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login