Showing 18001 words to 21000 words out of 42826 words
shi cikin mutuntawa, Inna ta aikesu Jamail ya dage sai ya yi rakiya,
Dan jerawa ta yi da Aisha inda Lukman ya biyota da kalo da kalar tausayi,
Ko mai ya tausasa mata zuciya, ta juyo a hankali daidai da Lukman, murya a can ciki ta ce" Allah, ya dayaba, ya sa nufin da ka bayana alkhairi ne, ya nuna lokaci
Tana gama fadar haka ta daga kafarta sosai inda ta wuce su ta fada gida,
Da ido suka bita gaba dayansu, inda Lukman ya saki wani lalausan murmushi da ya bayanar da hakoransa waje, a fili ya furta Alhamdulilah, yanzu adu.arsa daya Allah ya sa mahaifin baban nasa ya yarda da wannan magana domin ya nace kan sai ya aura masa yar uwarsa Zuhra wace sam baya jinta a layin matan da yake sha.awar rayuwar aure da su
Haka suka karaso suka tarar da inna na ta tatar koko Wujdane na gefe tana gyara dambun shinkafar da zasu yi, ta zagine ta ce ita zata yi komai bayan Jamail ya nemi alfarmar a yi masa ya kaiwa yayansa dan yana da son dambu
Jefi jefi takan saci kallonsu da Aisha dake famar gyaran lemo na shan ruwa, a daidai wannan lokacin Abdul Fatah ya karaso cike da gajiya shi kan idan yana azumi akoy son jiki
Shima nan ya tile wajen su Aishar ana ta labari da Jamail wanda sosai a gidan ba wanda bai yi sabo da shi ba, tsananin yana son wannan zuri.a
Inna ce ta dan dago da kanta, ta yi ta yi ta hani kanta yi masa magana aman ta kasa, dan zama ta yi kafin ruwa ya tafasa tana kallonsa, a hankali ta ce" Jamail, ka yi hakuri, aman na kasa jurewa, shin Jamail wannan kayan abinci da ka kawo mai kennan?
Dago da kansa ya yi da sauri, daman ya san a rina shi ya sa yaki yarda ya zauna daga shi sai ita a gidan, wannan kayan kuwa yayansa ne ya bude yana talafawa talakawa shima yaje masa da bukatar a deba masa ya kawo gidan malan dake bada karatu a masalacinsa, hakan ya saka aka cika mota da su shinkafar gwomnati, hatsi, gero, macaroni, cuscus, kai harda su man kuli a babar jarka da su magi, kafin ya karaso sai da ya biya wajen malan ya fada masa da kuma fadin sakon yayan nasu na kar kowa ya tafi gida da wuri dan yana can baban shagonsa na abinci ana ta fitar da sadakar kafin ya karaso anguwar nasa, duda ba shine ke rabawar ba, domin a cikin masalacin mutane dadaya ne suka san shine mai taimakon nan, da yawa ba zasu shaida shi ba a boye yake
Kafin ya yi magana inna ta ci gaba da fadin" ina jin tsoron hakan Jamail, tunda aka haifeni har zuwa yau da furfurana a kai ban taba tara kayan abinci irin haka ba, Jamail ba wai ban yarda da kai bane ko wani abin, iyayenka basa tuhumarka da dawainiya da kake da gidan nan yau da kulun? Shin baka gannin ya yi yawa ne duda ka fadan cewa kai kana yi ne idan ka ga yin hakan ya dace, ka daukeni tamkar mahaifiyarka ne, malan mahaifinka, kana son talafawa mu, aman Jamail ya dace ka sasauta, ka ga da ba dan Wujdane na gidan nan yau ba da tuni layin nan sun cikani da kai kawo dan tsegumin mai ke faruwa a gidan nan, Jamail bana son abinda zai zo ya jagula kyakyawan zumuncin nan dan Allah
Jamail ya yi murmushi, a hankali ya juya wajen Abdul fatah ya ce" ni yaya a kasuwar sabon gari ma kana dan taba kasuwanci a can ko???
Abdul Fatah ya ce" sosai ma, ai nan din yafi kwari kasuwancin domin a da soso nake kaiwa yanzu tsaron shago nake na siyar da irin turarukan nan na mata na shafawa
Jamail ya gyada kai ya ce" Masha Allah , Allah ya taimaka, aman yaya ka san wani da ake cewa Elhaj ALAIDINE MAI KAYA?
Abdul fatah ya ce" tap, ai wanda bai sanshi ba toh ka tabatar bako ne, domin tun daga kan hausawa da inyamurai dadaya ne basa bin reshen kasuwancinsa, suma dan basu samu ba, aman du yawancin haraka sai ka bi ta gefensa idan kana son ka ga komai ya je maka da sauki ga biyan bukata
Jamail ya ce" madallah, kuma ba tonan asiri ba, dan Allah yaya Abdul fatah, yana da tausayin na kasa da shi?
Abdul fatah ya ce" a kishin kishin din da ake yadawa wai ba wanda Allah ya cida haduwa da shi ba, aa, koda sako yake na bayar da zaka ko sadaka Allah ya sa ya biyo layin ka warke, yauma fa ana can store dinsa karka so ka ga layin jama.ar, ai sabko zan yi dan na samu gaba gaba, ba wani bambanci ko almajiri ko baba ko yaro ana sadaka ne da zuciya daya, aman ba wanda ya gansa ance yana ciki, mutane da yawa layin da suka yi dan su gansa ne da idannuwansu domin alkhairinsa ya jima da tardo su aman ka ga bawan Allahn nan ko mai yasa baya son a gansa
Sosai Abdul fatah ya dage yana bada labarin Alaidine, sai da ya koro da surutu ya dakata ya ce" aman kai ya aka yi ka tambayeni sunnansa? Ko ka sanshi ne??
Jamail ya saki murmushi, ya juyo wajen inna da Aisha da suke kallonsu sun rataba masu hankalinsu dan gane inda wannan labari ya nufa, Wujdane kuwa na daka tsidahu a zuciyarta tana aiyana mai kuwa zai hana shi banda girman kai irin na masu kudi,
Jamail ya ce" inna, kinga masalacin da malan ke bayar da karatun nan toh nasa ne, a wajensa na karbo kayayakin nan, ina fada masa a kawo na gidan Malan yace na je gidansa na fitar wai danma matarsa mugun hali ne da ita bata son kyauta wa wasu da ba yan gidansu ba, domin yan gidansu sun cika gidan tana ta fitarwa aman idan wani ya zo sai ka ga ranta ya baci, bata son ana rabar mata miji, ni na san da shine ya fitar ko yana tsaye aka fitar da bansan bama ya zamu kare da ku inna,
Inna ta dafe kuncinta ta ce" toh ikon Allah, shi kuwa wannan bawan Allah haka yake da sannin romon sadaka? Allah ubangiji ya jibanci lamuransa, ya bashi ladan sadakar da yake ta kasance masa haske a gobe kiyama, aman a anguwarku yake ko???
Jamail ya ce" shine mahaifin boy
Su duka sun cika da mamaki har wujdane dake daka sai da ta dan dago ta dan kale su, ta mayar da kanta sai ta tsinci kanta da cewa ai gwara da bai zama aku ba irinka(π€¦π»ββπ€£)
Haka sukai ta labari tsakaninsu, wanda Inna ta yi gum da mitar kayan nan sun yi yawa ta bi su da adu.a,
Abdul fatah da ya ji dambun nan shi za.a kaiwa sai ya lalubo dubunsa guda ya fice, bai dawo ba sai da sayaya niki niki ta su kifi da albasa yanda za.a yi yar jijibar miyar ci da dambun Aisha kuwa cike da murna ta karba ta shiga gyarawa
Konci tashi ba wuya, azumi har ya zo karshe wanda ake saka ran wayewar gari da sallah za.a tashi,
Idan ka shigo layin su Wujdane abin sai ya baka mamaki, duda karamar sallah ce aman cikin ikon Allah ko.ina ka wulga yara ne da yan mata da samari kowane na faman gyara kansa kunshi wa.inda basu samu yi a shekaran jiya da jiya ba
Aisha ce zaune ta gama hada sibkarta, tana bin Wujdane da kalo, ta san ita zata yi mata kunshin aman sai dan kai kawo take tana kara share gidan da baida dati ko kadan, su Mairo ma sun yi aiken dan girman Allah ta taimaka wannan salar ta dan yi masu komai kadan dinsa , fakat ta furta ba zata yi ba
Aisha ta kali ledar ta kuma dagowa ta shagwabe fuska ta ce" yanzu aunty ba za.a yi min ba kunshin nima Aishar ki?
Dan harare ta jefeta da shi, inna dake dakin malan tana ta faman gyara masa domin ana saka ran a ranar zai dawo daga masalaci da yayi kwana goma sha biyar , ta ce" ai fa sai ki zauna jiran ta yi maki, ba sai da na fada maki ba ki nemi mai kunshi mai neman na kanta wace ba zata wulakantaki ba tayi maki abinki tunda ke kin amince mace ce ke kina son gyara ki barta da shirmenta aman ke kin nace sai nata dan ta iya take yiwa mutane yanga, ita ta zauna a yi mata kitson ma ya gagara ta kunce dokar kuma ta daure gashin duda ba inda zaku ai ana samun baki, sai ka kimtsa kaima ka ji dadi irin na kowa, aman kiri kiri ta hade fuska ba damar yin wani abin na jin dadi
Kai wujdane ta dafe, ita dai ta rasa mai ya sa innarta komai ta yi sai ta ga rashin dacewar hakan
Bata shirya yiwa Aisha kunshi a lokacin ba aman dan ta rufe bakin innar ta zauna ta shiga zana mata
Aisha murna fal cikin ranta, a zahirin kuwa sai doka murmushi take, domin kunshin ya zanu, nima masha Allah na furta domin idan ba miskilancin Wujdane ba ta iya kunshi ashe har haka, tamkar wata amarya Aishar ta koma anyi mata kananuwan kitsonta ga yalwar gashi sosai, fuskarta ta jayu da kyau, ga kuma kunshi,
Inna na gamawa ta dora ruwan zafi a murhu, wanda yana yin zafin ta juye ta silka shi da ruwa ta zuba yodo a rabin, a sauran kuwa ta juye a buta, fir ta yiwa wujdane jan ido ta zo ta darje mata kan, wanda har wani zafi fatar kan nata ta fara, aman wata iska mai dadi na shiga kofa kofa na gashin nata, sosai ta ji dadin yanayin nata har innar ta gama daga nan wajen tun kafin ya bushe ta shafa mata mai mai maski maski ta hade shi ta daure mata shi a tsakiya sosai ta ja shi yanda fuskar zata dan fito, sannan ta tufke shi ta laulaye mata shi sosai
Zo ka ga wuwurga idannuwa wajen wujdane, kan nata ya dauki ciwo a lokacin wai anyi mata kitso, har wani lumshe shanyayun idannuwan magenta take tana cije lebenta dalilin hayaniyar anguwar
Wani yaro ne Saminu ya shigo a guje tun daga kofa ya kwala salama, yana shigowa ya ja ya tsaya,
Saminu ba dai firirita ba, akoy shi da taurin kai ,
Yana kale kalen gidan ya ce" wai aka ce ana magana da Wujdane
Ji tayi tamkar saukar aradu a kanta, kwal uba sunnana gatsal din nan ya kama dan uwarsa?
Ai kuwa tana dago da kai Saminu ya lura ashe ita ce a zaune da hijab dinta da ya jike da ruwa, ido ya zaro bazai manta dukan da ta yi masa ma wanda ko babansa bai taba yi masa irinsa ba duda dukansu da yake, ido ya kwalalo waje ya hade hannayensa waje guda
Ina ai gani ya yi hakan ba zata fishe shi ba, ganin irin yanda ta mike a zazafe ta nufo shi, daman a cike take da haushi tamkar ta fashe sai ga mai kan dauka ya tsokale ta,
Arcewa Saminu ya yi a guje yana ihun kiran sunnan mahaifiyarsa yana fadin" mama wujdane ce zata dake ni
Ai kuwa innna bata ankara ba sai giftawar Wujdane ta gani da gudu ta marawa yaron nan baya, da azuminta, da girmanta, da bakinta a kofa Lukman da abokinsa sun zo mata da kayan sallah
Kaka kara kaka wujdane nayi zaton kin nutsu ashe konto kika yi?π²π²π²π²π²π²π²π²π²π²π²
[3/27, 9:59 AM] βͺ+234 803 957 7698β¬: π¦π¦ *BANI DA ZABI*π¦π¦
*15*
WRINTING BY *SAJIDA*
Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,
*SAJIDARKU CE*
MARUBUCIYAR:
*YAR MAHAUKACIYA*
*DUK KARYAR KADA*
*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*
*NEMAN NA KAINA*
................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....
Yana zuwa masalaci jama.a sai harama ake ana mimika dabino ga gefe manyan jarkoki ne cike da su kunu ko tukudi masu sanyi wa.inda mutane ke kawowa sadaka, wasun kuwa daga can gefe suna ta kokarin gannin dan jaririn watan dake kokarin bacewa domin fitowar ranar ne
Nan da nan aka shiga musabaha ana godiya ga rabil izati, jama.a na neman yafiyar junnansu sannan ana ta buda baki
Shigewa ya yi cikin tarin mazan nan, ya zauna ana ta mimiko kunnu a kofuna
Karba ya yi yana hangen wasu tsofafi dake zaune gefensa, da alama dare duka yi har shan ruwa ya riske su,
Kansa ya juyo wajen MLan dake magana da Hamza, suna yar dariya da alama maganar mai dadi ce,
Haramar sallar da ladan yake maimaitawa a lasifika ya saka kowa mikewa masu kuskurar baki na yi, wa.inda a kuskuren suke har sun bi sahun sallah
Muryar Malan ne, wanda a ranar shi ya yi limanci yana jan sallar inda Alaidine yake ji gaba daya wata nutsuwa da tsoron Allah sun saukar masa, muryar malan ta saka shi nutsuwa fiye da tunanin mai karatu, haka ya samu kansa da zama bayan an gama sallar , almajirai sun bude karatu kamar kulun , wasun kuwa na zuwa kara daukan karatu qajen malan,
A hankali ya dauko alkur.ani shima, ya zauna har aka zo kansa ya je gaban malan, aka biya masa karatu wanda kwarai ya ji dadin hakan
Yana lure da malan sai da kowa ya watse kafin shima ya mike ya tafi bayan ya yiwa jama.a da dama salama, cike da fara.a ya fito ya kuwa dauki hanya yana doka sauri
Ajiyar zuciya Alaidine ya sauke, ga dukan alamu sun nuna mutumen kirki ne, aman zai kara nazartarsa, ya tabata idan har na gari ne matarsa ma haka toh zasu baiwa yaransu tarbiya, duda yanzu zamani ya zama na tir, domin kana tarbiyantar da yaron ne, a waje idan ya hadu da mugayen abokai suna warware maka tarbiyar yaro, shi dai abinda ya sani shine, bazai taba yarda irin rayuwar da yake ciki na rashi dacen macen aure ta kirki kanninsa ma ya fada a haka,
Shi dai adu.arsa shima ya samu mai dama damar kamar mayar anwar
Washe gari an tashi da sallah, inda cikin ikon Allah du jama.a sun ajiye azumi an tashi da sallah baki daya,
Zo ka ga yanda mutane ke shigo da fici,
Malan ya sha sabon farin yadinsa da Hamza ya dinka masa, ya dora sabuwar hularsa da takalminsa da Abdul Fatah ya kawo masa, sai sabon carbi da turare, fuskarsa na fitar da annuri
Yana fitowa ya tarar inna sai gyaran kayan miyarta take, da zabi biyu a gefe wa.inda ya saka aka kawo mata, sai aikinta take cikin nutsuwa, ta sha sabuwar atamparta ta saka kwali a idannuwanta, sai ta fito radam da ita sai sheki jikinta ke yi na mai da ta shafa vaseline dinsu sabo, ga turare da ta fesa yau ranar sallah kowa kwaliya yake
Cike da fara.a malan yake amsa gaisuwar yayansa, kyam kuwa yana karewa matarsa kallo wace ta fitp masa a yarinyarta, masha Allah shi kam ya godewa Allah da ya bashi innar yara a matsayin matarsa malakinsa
Haka samarin suka fice wajen idi , inda yan matan suka shiga taya inna aikin cikin gida da zabin nan da ake shirin tsantsara masu dafuwar cire kuneπ€£
Yau sallah kwana uku kenan, Jamail bai samu lekowa gidan malan sai a ranar nan domin hidomomin sallah gidansu a cike yake da yaya da jikoki ana ta shagali ana ta murnar sallah, harda Alawiya ma kanta ta zo bisa umarnin Alaidine wace take taku daidaiya tana yabawa khadija magana, itama tana ramawa
Shiru ya yi yana sauraron inna na yiwa Wujdane fada kan tace ba zata bi su yawon sallah ba shi da Aisha dake shiryawa da yayan ysyunsa da ya dauko yaran wajen Anwar da Boy, du sun sha shigarsu ta manyan kaya kamar ka sace su ka gudu
Mikewa Wujdane ta yi ta fito ranta a bace ta fada wanka, ko maganar ma yau bai samu ba domin sai take ganin ai laifinsa ne shi ya jaza aka takurata wani yawon sallah
Fitows ta yi ta shige dakinsu, tana sauraron yanda yaren suka cika gidan da surutu
Mai ta shafa, ta dauko bakar abayar da Malan ya kawo masu ta walwale tana niyar sakawa
A hankali Aisha ta rike hannunta ta ce" Aunty, ki yi hakuri dan Allah na dan gyara maki fuskar ki, kin ji auntyna dan Allah ba dan ni ba
Yatsina fuska ta yi ta zauna , Aisha taa dan samu ta dan gyara mata fuskar duda kwali ne kawai sai girarta da ta caje mata ta daidaitata, fir ta ki a saka mata jan baki a pink din lebenta sai dan lips aka dan goga mata,
Abayar ta saka bayan ta daura zani daga ciki don karta like mata a jiki,
Gashin kanta take faman sai ta dunkule waje guda dan ta daure aman idan ta gwada nada mayafin abayar sai gashin ya cunkushe,
Tsaki ta ja da ta saki gashin ta nanada ta ga ya yi dan cicif a jikin nata tana ayana wannan ai sallon iskanci ne
Kallonta kawai Aisha take, sam kalar Wujdane ba ta bahaushiya bace, ba ta yan africa bace, tamkar wata balaraba haka ta fito ga kalar adon jikin abayar duwatsu ne blue da fari sai suka haskaka idannuwanta masu kwayar ido blue
Dan takalminta plat ta saka, suna yiwa inna salama wace ta yi masu gargadi sosai , ta kara kawa Wujdane kune banda fada,
Haka suka fito inda Jamail ya kasa daina kallonta, a kasan zuciyarsa yana ayana daman haka take ? A hankali ya lumshe idannuwansa bayan ya bude mata gaba ta shiga da Boy a hannunta ta zauna a kasan zuciyarsa ya furta" ya Allah, idan har inna da rabon auren wannan baiwa taka , Allah ka kadara min shi kafin nayi kaura gareka
Haka ya zagaya ya shige ya ja motar ya fara nufar gidansu domin can zai fara kaisu kafin su karasa park
Yana zuwa mamaki ya kashe shi irin yanda gidan yayo tsit, tamkar ba mutane bayan a fitarsa ma ya barsu a barbaje suna ta shalakwalinsu harda yayan kawayen Mom dinsu
Juyawa ya yi sai ya hango motar yayansa, wace