Showing 15001 words to 18000 words out of 42826 words

Chapter 6 - BANI DA ZABI COMPLETE HAUSA NOVEL

23 Aug 2025

643

hikima, idan bata tangarde wajen rikon xilon dansa ba, toh zata nemi fitina wajen gididige sannin waye shi hakan yake sakawa ya bale igiyar ya dauki wata


Yaro da shi auri saki ya mayar da shi tamkar a jininsa, abin nan na ciwa mahaifansa tuwo a kwarya, dan gujewa ya afka zina yake saka mahaifinsa nemamasa auren da anje an kwan biyu a gundule shi, domin zuciyarsa ta fi karfinsa ba zai yiwa wara banza uzuri ba

Wannan kennan,


Ci gaban labari



Haka ya fito da katon jirginsa na wasa ya mikawa Jamail ya ce" plz ka je da shi kawai, ya kwana wajenka aman karka yarda ka je da shi gida ( dan kar Khadija ta hadu da shi )

Daukansa ya yi yana ta yi masa dabara inda boy ya karkata hankalinsa gannin za.a fita yawo


Jamail na fita bai zame ko.ina ba sai gidan inna, dan ya je ya ci dambun da take domin ba karamin tafiya da imaninsa ya yi ba

Yana shigowa ya tarar da mutuniyar tasa tana yanyanka albasa, Aisha kuwa tana daka yaji,
Bayan ya gaisar da innar ya samu waje ya zauna Boy na lilike masa dan rashin sabo


Inna ta fito da kuli a leda baka tana fadin" yau ga miji yau ga miji, tana kokarin yiwa boy wasa aman ya lafe ya ki yarda ta dauke shi haka ma Aisha

Wannan ledar ta mikawa Jamail ta ce" yarona haka zamu fara da kai? Kul ka kiyayi fara hakan da ni sai na ji ba dadi


Cike da gannin girman tsohuwar yake kallonta, ya yi murmushi ya ce" inna, yaya ne ya fitar sadakar da yake bayarwa, shine na karbo maki naki, inna kennan idan Abdul fatah ya kawo ba zaki karba ba???

Wata kunya ce ta kamata, haka yake mata wannan wayon sai ya nuna kenan dan shi ne ya yi mata abu ba zata karba ba,

Mikewa ta yi dan zuba dambun tana adu.ar allah ya sa ya gama da duniya lafiya da shi da mahaifansa

Ihu boy ya saka wanda ya saka Wujdane saki wukar da take dan yanyanka albasa tana kallonsa


Fitsari yake ji sai ihu yake kuma ba zasu taba shi ba

Cike da jin haushi Jamail ya ce" zan fa wanwanka maka mari Boy meye hakan? Ka nutsu a cire maka wandon ka yi mana


Aa shi ya dage sai ihu yake shi jacuzzi jacuzzi,

Tsaki Wujdane ta ja ta mike ta nufo shi, cikin yaren turanci ta miko masa hannu tana fadin" zo nan boy dina na kai ka ka yi fitsarin na baka chocolate

Ai yana jin hakan ya dare gannunta yana sauke ajiyar zuciya ta yi bayi da shi

Gaba dayansu da ido suka bita na mamaki, duda sun san dan ya daina ihun nan ne ya daina damunta da ihu ya saka ta lalaba shi, domin itama ba wani onuwa daya take sha da yara ba, basa shiri da yara hakan ya matukar basu mamaki,

Jamail ya juyo wajen inna ya ce""::






........☹
[3/27, 9:59 AM] ‪+234 803 957 7698‬: 🦄🦄 *BANI DA ZABI*🦄🦄





*11*


WRINTING BY *SAJIDA*



Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,

*SAJIDARKU CE*


MARUBUCIYAR:

*YAR MAHAUKACIYA*

*DUK KARYAR KADA*

*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*

*NEMAN NA KAINA*

................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....





Jamail ya juyo wajen inna da mamaki fal a shinfide a fuskarsa ya ce" inna, daman kanwata tana shiri da yara?


Inna ta yi dariya ta ce" kanwar taka a abin mamakinta baya karewa


Suna tsaka da maganar inna ta zuba masa dambun a plat dan madaidaici ta fito da Boy ta gyara masa wandonsa ta dawo ta zauna tana kallon kofa wani abu na fizgarta kan ta ficewarta


Wani yaro ne ya yi salama da naira goma a hannunsa, yana dan rakubewa ya ce" inna wai ana salama da MaMa,


Inna ta dago da kanta tana kallon yaron ta ce" wa ke salama da ita? Yama fa ya yi bana son fitar nan


Yaron yana dan bari da hannayensa ya ce" wai ya ce ace lukman ne


Firgigit ta dago da kanta daga kallon kasan da take a tare da Jamail, shima bai shirya ba ya dago cike da mamaki da karyata kunnayensa, Lukman? Waye lukman? Daman Wujdane na zance da saurayi???

Tunaninsa ne ya katse daidai lokacin da Inna ke fadin" to ai tana jin ka


Harara ta watsa masa ta ce" ka je ka ce ta yi baci


Tun kafin ta rufe bakinta yaron ya juya a guje yana maimaita maganar da zai fadi din dan kar ya manta


Tsam Jamail ya tsame hannunsa daga cikin abincin ya mike ya darwaye ya yi hanyar kofa

Da harara Wujdane ta bi shi ta ja tsaki ita kadai tana fadin natace


Yana fita ya tarar da Lukman na faman buga babur dinsa

Salama ya yi masa ya mika masa hannu suka yi musabaha

Lukman kallon Jamail yake, a yannayin girman jikinsa ba zaja bashi shekara 20 ba sai dai sama, ga cika ido

Murmushi Lukman ya saki ya juya a hankali a can kasan ransa yana ayana du da soyaya ba ruwanta da kyau mulki ko arziki ba, zab gwada nawa sa.ar ( toh fa )



Zaune yake cikin falonsa ya dafe kumatunsa da hannu bibiyu yana sauraron mahaifiyarsa hajiya Marwa, cike da hikima ta ci gaba" Haba Alaidine, ka ringa sasautawa zuciyarka, yanzu tsakani da Allah mahaifiyar boy na zaune ita ta ki ta sake suren wani, kai kuwa ka yi rantsuwar ka gama zaman aure da ita, du bama wannan yanzu dan tana gidan shikennan ba za kana leko mu ba? Ni yaya kake so nayi ne?


Cike da kaunar mahaifiyarsa wace bata taba nuna kyamarsa ba ya ce" Mom, idan ta yi aure ta bar gidan zan koma zuwa, mom


To kai ya maganar auren naka ne? Ta katse masa hanzari, ta ci gaba da fadin" ko na zaba maka ne???


Dago da kansa ya yi wannan karin, yana kallonta ya ce" Mom aa, bana so ki zaba min na dawo na kuma saka ki kunya, zan yi auren kwananan insha Allah


Kallonsa take tana jin ciwon irin rayuwar nan nasa, arziki dai na gidan duniya Allah ya malaka masa, wanda yana cikin mutanen da ake maganarsu a kasar, aman ka kasa zama cikeken mutun ta fannin ajiye iyali????

Ajiyar zuciya ta sauke ta shiga kiran layin mijinta dan jin a goben zai taso kuwa daga abujar wajen meeting?




Malan na shigowa d fara.a fiye da da cikin gidan,

Bayan sun gagaishe shi inna ta dauko kudin nan da ko kirgawa bata yi ba ta ajiye da niyar malan ya zo ta danka masa,

Kafin ta yi masa bayani ya karkace ya ciro kudi a aljihunsa yana ta aikin murmushi ya miko mata

Ido ta fitar waje bata karba ba ta ce" Malan wannan fa??

Fuskarsa wadace da murmushi ya ce" Masalacin da nake bayar da karatu, wato wanda yayan Jamail ya gina, a yau aka shigo aka nemi malaman dake bayar da karatu da masu kula aka bamu dubu ashirin ashirin, sannan a lokacin elhazen kamar hadin baki suka shiga bamu kyaututuka, kinga dai cikin ikon Allah yau a masalaci kinga abinda Allah ya bamu baki daya malaman na bada shawarar a hade kawai a raba domin akoy wa.inda yau basu samu halarta ba, su din ma ba masu karfin bane, sai aka bi shawarar nawa aka hade aka kasa kinga na tashi da wajen dubu arba.in da shida


Kallonsa kawai take a can kadan zuciyarta cike da tausayin mijin nasu da kuma godiya ga Allah, ta san dai ko ba komai a yau ya kara samu domin ma.aiki,

Murmushi ta yi ta mika masa na hannunta ta yi masa bayanin yanda suka yi da Jamail


Adu.a kawai yake yiwa bayin Allahn nan yana ta godewa Qllah kafin ya sake kallonta cike da fara.a ya ce" kin ga sai na kai kudin makarantar Wujdane, dubu bakwai ne da dari hudu da Malan din ya lisafa abinda ya dace sai na cike, sannan ku samu ku yi sabin dinki ku sayi su mai su dan turare sannan a sayo abinci ko???



Cike da murmushi take kallonsa tana amsa masa, da insha Allah, sannan ta gyara zamanta a dukan abinda ya zana bai sako kansa ba, domin cikin ikon Allah samarin gidan suna iya kokarinsu wajen yi masa sutura da su kansu, danma karatu na dauke hankin Abdul Fatah,

Mika masa gaba daya kudin ta yi, ta ce" malan du abinda Aka zana Allah ya idasa nufi,

Tana gama fada ta mike fan gabatar masa da shinfidarsa

Da ido ya bita, yana kara godewa Allah, matarsa, uwar yayansa, abin alfaharinsa, mai gane matsalarsa mai kula da fara.arsa, ita irin zumudin nan na ta ga kudi ma bata da shi, yana kara godewa Allah da du irin murdaden halayen Wujdane kudi baya gabanta, haka ya mike ya kara daura Alwallah ya shige dakinsa dan gabatar da salolinsa ya kuma kara godewa Allah da wannan budi da ya yi masa

Da sasafe kamar kulun, Wujdane ta fito daga wanka ta yi turus dalilin inna da ta ganni a dakin nasu zaune, dukawa ta yi har kasa ta kuma gaishe ta da kwana, innar na amsawa


Mikewa ta yi tana son saka kaya inna na binta da ido,

Dan murmushi inna ta yi a can kasan ranta take fadin kunyar karya irin ta wujdane, ita ba za.a ga tsiraicinta ba, gannin ta kasa saka wandon ya saka innar juyar da kanta tana kallon kofa

Aishama dariya take kasa kasa tana kokarin murza man kuli dake cikin wata yar farar roba a jikinta domin shine mansu idan man ya kare

Yan dari biyar biyar biyu ne a hannun innar, ta juyo ta mikawa Aisha sannan ta mikawa wujdane

Tsai suka yi suna kallonta, da alamun neman karin bayani

Zama ta yi ta ce" a jiya cikin ikon Allah sosai Allah ya yi budi a gidan nan, shine yau mahaifinku du irin kiye masa da nayi kan ba za.a baku hakan ba ya tirje min kan ai samu aka yi, shi ya sa ya bada wannan kudin ya ce na baku ku adanna idan bukatar sayen wani abin ya taso maku sai ku saya, ko dan saboda makaranta ma

Murmushi Aisha take ta saki, tana godewa Allah a fili ta ce" masha Allah, masha Allah, Allah mun gode maka, Allah ya kara budi , ya kara arziki mai anfanni


Amsawa inna take ta juyo wajen Wujdane, ta ga ta ajiye dari biyar din a nan kusan innar sannan tana kokarin saka hijabinta, inna ta ga yanda kitsonta ya tsufa sosai haka, to aman dan me bata dauki kudin ba ko ta raina ne? Inna ta ce" toh ke sarauniya, ya zaki jefar min da kudin a nan ne? Ko kin raina ne?

Juyowa Wujdane ta yi da sauri tana kallon inna wai ta raina, ta dan girgiza kanta bata ce komai ba

Takaici ya cika inna , yau miskilancin na banza harda ita za.a yiwa, ai kuwa ta shiga fada inda take shiga ba ta nan take fita ba, Aisha du ranta ya bace gannin inna na yiwa yar uwarta fada da safiyar nan, ita kuwa ta sada kanta ta yi zuru tana sauraron fadan innar na rashin dalili a wajenta, bayan inna ta gama tana harararta ta dan dago, ta sanyaya muryarta ta dauko kudin ta mikawa innar ta ce" innata, ba wai rainawa na yi na, koda baba ya dage kan sai an bamu sai ki rike a wajen ki, cikin ikon Allah koda wata rana abinci ya dauke da ajiya ai za.a yi anfani da shi, mu ba kudin mota muke biya ba dan zuwa makaranta, ko a makaranta Aisha ke sayo min abincina, kenan inna na wajen Aishar ya ishe mu har ya yi yawa, insha Allah idan ta sayo manta na shafawa vaseline dari da hamsin sauran sai ta ajiye mana a wajenta tana sayo abincin a makaranta kinga sai ki huta da bamu kwana biyu ko??


Tana gama fadar haka ta sakawa inna kudin ta mike ta fice da ledarta ta mauludu da aka yi a anguwar aka raraba ita ce jakarsu ta makarantar ta saka litafinta da biro


Da ido inna ta bisu bayan fitar su, shar ta ji dumin hawaye a gefen idannuwanta, a hankali ta goge ta daga hannayenta sama ta shiga karanto adu.o.i wa yayanta baki daya



Malan kam yau fara.arsa ta ki ta yanke, bayan ya biya kudin makarantar Wujdane ya zarce masalaci dan akoy karatun safe da zai bayar,

Bayan ya gama ya yiwa mutane salama ya fito , ya shiga doka sauri dan zuwa kasuwa domin a lokacin har karfe biyu na rana ya yi,

Oda ya ji ana yi kamar da shi ake hakan ya saka ya dan waiga

Anwar ne da wani saurayi a cewar malan shima mai cikar kamala a gefen Anwar din sai dai wannan tamkar ya fi shi girma da isa, bakin gilas a fuskarsa da waya yana dan dadanawa


Malan barka da warhaka, za.a je gida ko na ga sai sauri ake, cewar Anwar yana gaisar da malan din cikin mutuntawa

Malan ya amsa yana mai dan sakin fara.a ,

Alaidine ya dago da kansa, sai ya samu kansa da cire glass din idannuwansa, a hankali shima ya furta" barka da rana Malan, ka shigo mu saukeka man na ga ana rana


Murmushi Malan ya saki ya ce" aa ba komai yaro, ai kasuwa ma zan je ba gida na yi ba

Anwar ya matsawa malan kan ya shiga ko kasuwar ce su sauke shi domin suma can suka nufa, hakan ya saka malan shiga motar tasu da ya karewa kallo sannan ya bada nutsuwarsa wa bakin titi yana kallon yanda motar ke gudu aman tamkar bata motsawa dan irin motocin nan ne da idan ba wani baban gargada aka shiga ba ba zaka san an shiga ba


Anwar ke dan jan Malan da zance inda Alaidine ya yi shiru yana mamakin surutun Anwar

Ni Malan ina Yar rikici ne take??? Cewar Anwar

Malan ya dago da kansa ya saki murmushi jin an ambaci Wujdane ya ce" ai fa ana nan, sun tafi makaranta da yar uwarta, Wujdane rigima ba, aman an dan kwana biyu ba.a yi ba mai yiyuwa adu.a ta ci karfinta


Anwar ya yi ta dariya abinsa,
Haka suka karaso suna dan labari da Anwar aman Alaidine yayi kif, tun gaisar da Malan din da ya yi bai kara komai ba

Daidai babar kofar suka sauke Malan inda suka juya dan karasawa shagonsa na atamfofi


Malan ya yi masu sayaya daidai gwargwado harda su macaroni ta zamani, da fulawa da shinkafa da su magi mai gishiri , sosai ya yi masu tsince tsince sannan ya karasa shagon masu sayar da kaya
Nan ya sayawa inna atamfa da hijabi biyu, ya sayawa su Wujdane hijabai suma da atamfar kala biyu ,shine harda abaya yar dubu da dari biyun nan da yan takalma plate masu kyau da turare da mai na shafawa, rigi rigi almajiri ke binsa da kaya har ya zo fita ya ga yan abubuwan hannu, ya dakata ya sayowa Wujdane da Aisha sannan ya sayi sabulu sinki guda,
Malan dai ya yi sayaya ya kashe kudi bai fi dubu shida a aljihunsa ba ya nemi adaidaita ya yi shata har gidansa



Zaune suke Inna na tsefe mata dokar kanta da ta tsufa sosai har sai ta laluba take jin tufkar kitson tana yi tana mitar gaskiya Wujdane sai kin canza hali, ke daki yi tsaftar ko ina aman bakya so a taba maki kai??



Idannuwanta a rintse, jin taba kan nan nata take tamkar inna na yankan naman jikinta

Malan ne ya shigo da ledoji Aisha ta tashi ta tarbo shi, ya koma dan dauko sauran kayan

Yana daukowa Motar Jamail na tsayawa daga dan nesa da gidan kadan








(Talauci ba zai hana yin walwala a cikin gida ba idan har an gina rayuwar gidan a kan tubali mai kyau)
[3/27, 9:59 AM] ‪+234 803 957 7698‬: 🦄🦄 *BANI DA ZABI*🦄🦄





*13*


WRINTING BY *SAJIDA*



Da sunnan Allah mai rahama mai jin kai,

*SAJIDARKU CE*


MARUBUCIYAR:

*YAR MAHAUKACIYA*

*DUK KARYAR KADA*

*DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA*

*NEMAN NA KAINA*

................... *BANI DA ZABI* INSHA ALLAH....





Mom dake sama ta lumshe idannuwanta ta shiga yiwa yaronta adu.ar shiriya bayan komai da ya faru a idannuwanta duda bata ji takamaiman mai ya bata amsa ba ta san dai ba maganar dadi bace, tana adu.ar Allah ya sa wannan auren ya kasance ya shiga ransa, ya sota tamkar ransa, sannan ya shinfida shakuwa a tsakaninsu, tana adu.ar ta samu sarakuwar da zata zamo tamkar yarta, matar Anwar akoy mutunci da mutunta su, damuwar nesa ga yara sai ya kasance weekend kawai suke samun yi
Gaisuwarsa ta katse mata tunanin da take ta bada hankalinta kacokam kansa




Wujdane, Wujdane, ki saurareni mana, haba Wujdane ya dace a ce na samu karbuwa a wajenki daidai wannan lokacin, ki tuna fa a kala na kwashe wata biyu na bin bayanki, haba Wujdane dan adam daraja gare shi, ki saurare ni


Juyowa Wujdane ta yi, tana dan dubansa ta cikin nikab dinta, a can kasar zuciyarta tana aiyana" ya salam, yanzu Baba da ya fitar da maganar wani ta tsayar da miji wai ya yake so ta yi ne? Ko dai Lukman din nan kawai zata fadawa idan har yana son nata kawai ta aureshi ta huta da wannan rayuwar,


Ki ban amsa mana Wujdane, cewar Lukman yana kalar tausayi

Kanta ta dan dafe hango su Jamail sai a lokacin suka shigo kwanar shi da Aisha, ta juyo wajensa ta ce" ka ga dai azumi ne, ba.a sha ruwa ba ya zaka tare ni da azumina kanai min wasu maganganun soyaya? Na fada maka ni ban santa ba, ni ban iya ba, sannan ai ba ni na takuraka kan sai ka bi ni dole ba ko???


Tausasa muryarsa ya yi , ya ce" kwarai na san da azumi a bakin mu , aman maganar da nake miki na neman aure ne, kinga dai da dare ba samun ganninki zan yi ba, ki taimaka ki lamunce min na turo iyayena bayan sallah insha Allah da sannu zaki so ni Wujdane


Ido ta dan zaro gabanta na faduwa, daidai su Aisha sun karaso inda Aisharma ke gaishe

Join Our Groups

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login