Showing 9001 words to 12000 words out of 73204 words
ko'ina ba ya sauka. Saboda Ramata ba kanwar lasa bace ba. Zama a gabansu sai ya zama kamar zama da wasu kishiyoyi ne, suka sako ni a gaba. Ni abin yana bani mamaki, ban tsarewa kowa komi ba, amma ni kuma ace na tsare? Shima din taso taga tayi dani, taga dai daga ita har Ramata din na jefa su a kwandon shara, sai ta saddakar, ta koma kan Ramata din.
Matsala ta farko a cikin wannan gida, ita ce rashin adalci. It was obvious Baba yafi son Ramata akan Alawiyya, zata iya yiwuwa so ne na tsakani da Allah, ko kuma wanda ta nemo a wajen malamai da yan tsibbu, koma dai wannene, amma kuma bai san ta yadda zai daidaita ko ya boye son nata ba domin samun adalci a cikin iyalansa, hakan yasa a kowane abu ne sai ya fifitata akan Alawiyya da 'ya'yansu. Ita da 'ya'yanta sun fi kowa kima da mutunci a idanun Baba.
A hakan ma kuma bata bar Alawiyya din ta zauna ba, ta hana ta zama lafiya da mijinta, ta hana ta sana'a. Kudi duk yawansu idan ta tarki sana'a dasu, zasu kare ne kafin a je ko'ina. Wani abu ne da naji suna kira wai 'mai rariya', duk yawan kudin da zasu shiga hannun mutum to zasu koma kamar an cinna musu wuta, nan da nan zasu kare ka rasa ta inda suka shiga. Abubuwa ne da ni na sha gani da idanuna. Wani lokaci na tashi cikin dare zan yi sallah inji ana kurumtu ko a bayan dakin Baba ko na Alawiyya, watarana shara zan shiga yi a dakin Baba in ga kulli-kulli na magani ko dami na layu da dai tarkace a lungu da sako na dakin, sai dai in daukesu in shiga wajen su Inna in kona su.
Bazamar da Alawiyya tayi wajen malaman Allah da Annabi domin neman kariya da kuma karyewar abubuwan dake kanta, itama ta fada cikin taskun bin malamai da yan tsibbun har ma da yan bori. Wannan masifa dana gani da idanu na, ta tsorata ni fiye da tunani na.
Duk sallar duniya idan nayi, sai na roki Allah ya raba ni da zama da kishiya. Ya zamana tunanin zama da kishiya kadai kan sa inji kamar zuciyata zata rabe biyu. A zamanin budurcina, saurayi yana zuwa daya, tambaya daya ce: kana da ra'ayin zama da mata biyu nan gaba? Idan yace eh, to sai in ce Allah ya kiyaye hanya tun ma kafin tafiya tayi nisa. To da yake ma ba kula samarin nake yi ba, saboda a lokacin hankalina yana kan in gama sakandire da sakamako mai kyau, in samu in shiga jami'a.
Allah Ya taimakeni sosai, gabadaya jarabobina na waec da neco suka yi matukar kyawu, sai dai kasancewar banyi jamb ba, -a cewar Baba in bari sai sakamakon jarabawar ya fita sannan-, yasa da Baban su Kulsum ya tashi sai mata form din makarantar SBRS, kasancewar ita bata ci jamb ba, yasa na roke shi akan ya nusar da Baba nima ya sai min. Allah Ya taimaka ya siya min, muka samu admission muka tafi.
*☆⋆03⋆☆*
A SBRS muka hadu da Janan. Haduwa irin ta wajen registration, daga tambayar zuwa wajen signing, sai kuma muka ji cewa ai duk dakinmu daya, nan muka hade. Ita Janan wanda yake auren Yayarta shine ya mata hanyar zuwa can, a lokacin shine DG din makarantar ma. Amma da yake irin mutane ko in ce iyayen nan ne na da, bai barta ta zauna a gida ta huta ba, da kanta tayi komi na registration.
Kasancewarmu a daki daya yasa zumuntarmu gaba daya tayi karfi. Yayarta, Anty Sa'a anan cikin makarantar suke zaune ita da maigidanta da 'ya'yansu, duk da cewa suna da gida a Zaria, amma bata taba zuwa can ta kwana ba, wani abu da Anty Sa'a din da maigidanta suka ce wai zai sa ta dinga slacking akan karatunta.
Abotarmu tasa muka saba da danginsu sosai, har ma watarana Yayansu Bilal yazo ya daukar mana excuse, ya daukemu zuwa can gida Kaduna lokacin da aka yi bikinshi da Anty Ameerah. Yan'uwansu mutane ne masu mutunci kwarai, karimci da kyautatawa, jininmu ya hadu dasu sosai. Wannan shine ganina da Yaya Bilal na farko.
Mun gama makarantar da sakamako mai kyau, amma ba wanda zai shigar damu jami'ar Ahmadu Bello ba. Da yake Remedial Studies ne muka yi, idan Allah ya taimakeka ka fitar da sakamakon da ake so, za'a baka gurbin karatu a jami'ar Ahmadu Bello, matakin karatu na aji biyu, to mu Allah bai kaddara zamu samu ba. Amma mun sake rubuta jamb, mun kuma samu sakamako mai kyau both a jamb da kuma post-utme. Cikin ikon Allah duk suka bamu course din da muke so, nursing.
Nan muka koma gida muka fara shirin tafiya. Sai da muka tsaya aka yi bikin Kulsum. Kasancewar wanda zata aura ya dage akan yana bukatar ayi aurensu, yasa aka daura musu auren, da sharadin zata nemi gurbin karatu anan Umyuk, kuma zai barta tayi, yace ya amince.
Bayan bikin, muka je muka yi registration. Na koma gida na kara kimtsawa na sati daya, na tafi makaranta.
Mun shiga aji na uku muka hadu da Umar, ya raka kanwarshi registration lokacin. Shi NDA ta Kaduna yayi, ya samu ya gama, ya fara posting dinshi kenan muka hadu. Allah Ya taimake shi yana da hanya, shi yasa suka barshi a nan Zaria basu jefa shi waje mai nisa ba.
Babu bata lokaci muka fara soyayya ni da shi. A duk tsayin rayuwata, wannan shine karo na farko da na tsaya nayi wata soyayya da wani da namiji, ban taba ba kaina wannan damar ba.
Lokacin da ina gida da, na fara tsayawa da wasu. Sai dai, ban san dalili ba, duk wasu kalamai na so da zan ji sun fita daga bakinsu, sai inji ina karyata hakan. Wannan dalili yasa zancen ma baya yin nisa, ake watsewa. Daga karshe dai na fahimci cewa ban yarda da soyayyar bane. Duk lokacin da zan ji wani ya ambaci true love, to zan ce maka bata existing sai cikin littafan novels da fina-finai. Janan ta kan ce saboda ban samu wanda raina ya kwanta dashi bane, ko kuma ina jin tsoron commitment ne. Koma dai wannene, ban damu ba.
Shi kanshi Umar din, lokacin dana fara amincewa dashi, ba so bane, it was more like burgewa ko kuma abokantaka. A lokacin I was in a desperate situation, you know irin lokutan nan da zaka ji kana bukatar wani a kusa da kai, bayan abokai da yan uwa of course, sai kuma ya kasance na samu duk wani abu da ake bukata a wajen namiji a tattare dashi Tattali,kulawa da saukin kai. Irin free-spirited mutanen nan ne, duk inda zaku zauna dashi, in shaa Allah zaka ji ya shiga ranka. Sai dai rawar kai da ba'a rasa samarin yanzu da ita, wanda shima sai da muka yi nisa da haduwa dashi sannan na fara karantar hakan, amma nasan cewa lokaci ne, zai daina, tunda ina matukar yin kokari wajen ganin cewa duk lokacin da yayi kokarin yi min maganar banza na dakatar dashi. Hakan yasa lokuta da dama zamu yi fada burum-burum dashi, daga baya dai zai sake dawowa mu shirya.
Bayan wannan sai kuma daga baya da naji na zama very comfortable a tare dashi, ba kamar sauran samarin da nayi a baya ba. Ina jin shi kamar Janan, yadda zan zauna inyi hira da ita babu wani boye-boye, shima haka zan zauna inyi hira dashi. To ko bana son shi, a ganina wannan kadai ai zai ishi rayuwar aurenmu ko? Tunda mun fahimci juna sosai. Balle ma ina son shi. Duk da cewa maganar aurena dashi tana sa inji wani unsettling abu a cikina. Kodayake, har yau bai ma fara zancen auren namu ba, nafi tsammanin kila sai bayan mun gama karatu sannan, and I'm totally fine with that.
Shekararmu ta farko a makaranta babu sauki, yanayin karatunsu mai zafi ne, duk da cewa mun yi wanda yaci uban wannan a SBRS, still, yana mana wahala. Ni a cikin hostel din makaranta na zauna. Yayin da Janan take zaune tare da matar Yaya Bilal anan cikin samaru.
Yaya Bilal yana aiki da kamfanin jaridar daily trust ne. Kasancewar kamfanin yana Abuja ne, yasa yake tafiya can duk ranar lahdi da yamma ko litinin da safe, ya dawo ranar Juma'ah da yamma. Ban san dalilin da yasa bai tafi da amaryar shi ba, tunda naji Janan tace yana da gida acan Abujar. Ban kuma taba tambayarta ba koda wasa. Daga bakinta dai naji tace ashe ma gidan da suke zaune, mahaifin Ameerah ne ya sai musu gidan. Duk da abin ya daure min kai, ban tambayeta dalili ba shima.
Na sha jin korafin bata jin dadin zama da matar Yaya, ban taba fahimtar dalili ba sai da watarana daya da muka je gidan.
Muna cikin shirye-shiryen exams ne, Janan ta saba shigowa makarantar a ranakun weekends, muje library mu yi karatu. Ranar tana zuwa, Yaya Bilal ya kirata yana tambayar tana ina, ta fada mishi. Ba'a jima ba sai gashi yazo, ashe Anty Ameerah ce bata jin dadi, yace zai je ya dauko family doctor din su Ameerah din, muje mu tayata zama kafin ya dawo, a karo na barkatai, naji lamarin nasu ya daure min kai. Nan dai muka tarkata muka tafi.
A kofar gidan ya ajiye mu ko ciki bai shiga ba, ya juya, mu kuma muka shiga ciki. Gidan nasu dan madaidaici, mai kyau. A kalla mun dauki fiye da mintuna goma sha biyar muna doka kararrawar sanar da zuwan bako gidan. Ina tunanin ba wanda yake cikin gidan ba, hatta da wanda yake makotaka dasu, yaji wannan bugu da muka dinga yi. Yadda Janan tayi, very calm and collected, babu alamun wata damuwa a tattare da ita, yasa na gane cewa wannan ba shine karo na farko da irin haka ta faru ba.
Sai da aka kara kusan mintuna biyar sannan naji motsin taba kofa, aka bude kofar falau, cikin sanyin jiki duk muka shiga cikin falon. Ance wai shimfidar fuska tafi ta tabarma, duk da irin kayan alatun da suke cikin falon, hakan bai sa naji ni very welcomed ba a gidan. Ba'a bamu wajen zama ba, babu sannu da zuwa balle ga ruwan sha, haka aka barmu tsaye a tsakiyar falon dakin. Sai Janan ce ta min nuni da kujera, tace in zauna bari taje ta dauko min ruwa. Jiki a sanyaye na lalubi kujera na zauna, cikin nuna girmamawa na gaidata. Sai data gama shan kamshi sannan ta amsa, ya saukin jikin dana mata ma Allah bai bata ikon amsawa ba. Dama na gama shaka da ita, daga nan nima na maida kaina cikin wayata na cigaba da karatuna. A zuciyata kuma cike da mamakin wannan mata. Ita ba wata babba ba, saboda daga ganinta shekarun data bamu kadan ne, ita ba wata dangin sarauta ba balle ince ko jinin sarauta ne a jikinta, amma kice dole sai kin shimfida mulki? Duk da cewa yes, tana da kyawu Masha Allah, kuma daga yadda naji, mahaifinta mashahurin mai kudi ne, kila hakan ne yasa take dagawa. Na girgiza kai kawai.
Ko kallon ruwan da Janan ta kawo min ban yi ba, Allah-Allah nake Yaya Bilal ya dawo, in narko wani excuse din in karawa bujena iska don ba zan iya zama a haka ba Allah ya sani.
Muna zaune mu duka ukun, babu wanda yake cewa wani ci kanka, har rana ta daga sosai babu alamun Yaya. Gashi ko TV ba'a kunna ba a falon balle mu ce zata dauke mana hankali. Gabadaya naji na takura, ban iya dogon zama irin haka babu hira ko wani abu to discuss ba. Rawar kai na da tsokanata basa barina zama waje daya.
Janan ce ta katse dogon shirun daya mamaye dakin ta hanyar tambayar ta, 'Anty ko za'a dora abinci yanzu ne?'.
Budar bakinta sai cewa tayi, 'daga gida za'a kawo mata abinci yau, bata son jin kamshin gas ko risho', da dai na samu na hana kaina daga kama baki in ce to?!, sai na bame bakina na kara tura kaina cikin wayata.
Allah ya taimakemu Yaya ya zabi daidai wannan lokacin ya fado falon kamar an jefo shi daga sama.
Tayi tsalle ta afka jikinshi, mu da muka dago da niyar yi mishi sannu da zuwa sai kasa muka yi da kanmu a rikice saboda ta'asar dake gudana. To ta'asa mana! Ba kullum bane kake ganin irin wannan 'intimate moment' a gabanka ba. Sai daya gama tsotse mata baki da fuska, sannan muka jiyo alamun tashin muryarsu kasa-kasa, hakuri ya dinga bata kan cewa bai samu ganin likitan nasu ba, kuma har gidanshi yaje, amma ko zata daure su tafi asibiti yanzu? Ta wani lankwashe murya kamar wata yarinya karama, tana cewa ai ita so tayi ya zauna kusa da ita kawai, bata wani bukatar likita.
Nayi kokari na danne dariyar data kusa kamo ni, irin wadannan 'cheesy lines' din ai nayi zaton a films kadai suke amfani da novels, ba a ainihin rayuwarmu ba.
Yaya ko kallon mu bai kara yi ba, ya dai jefo mana "ku zauna ku jira ni, ina zuwa!", bai jira jin ta bakinmu ba, ya ciccibi amaryarshi suka shige daki. Na kama baki na bi bayansu da kallo, a zuciyata ina kara tausayawa Janan. Idan har haka ake treating dinta a gidan Yayanta, Allah kadai yasan halin da take ciki gaskiya.
Ta ja ni zuwa dakinta inda yake can cikin falon, can karshe kusa da wani karamin daki da suka mayar dashi kamar store. A gefen katifa duk muka zauna, na titsiyeta sai data bani labarin abinda yake faruwa a gidan, tun daga farko har karshe.
Matar Yayanta irin matannan ne da idan Allah ya hada ka kishi dasu, taka ta kare. Babu boka babu malam, zasu dafa ka cikin ruwan sanyi ka kankare. Irin matannan ne masu dan banzan kissa.
Tace a bayan idon Yaya Bilal, ita, Janan din da sauran dangin shi har ma da Ummansu, basu maraba da kayan wanki a wajenta, amma idan a gabanshi ne sai tayi ta tattalinsu tana ririta su.
Ameerah irin sangartattun yaran masu kudin nan ne. A wannan shekarar ta gama karatunta. Bata aikin komi a gidan wannan sai zama, kallo da nanikewa miji. Tana da yan aiki kala-kala, don ma dai ba kwana suke yi a gidan ba. Da masu girki, masu sharar waje, masu wanki, har da masu gyaran daki, kuma duk mahaifinta yake biyansu. Tace yanzu haka garar da aka kawota da ita tana cike da store, ko alamun tabata ba ayi ba, saboda bata yin girki. Watarana ma daga gidansu takanas ake dafo abincin a kawo mata. Kai hatta da wutar amfani wannan ta gidan, mahaifinta ne yake biya. Yayan yayi magana game da hakan, amma mahaifanta suka nuna duk cikin son da suke yiwa diyarsu ne.
Tunda Janan taje gidan, take gasa mata aya a tafin hannu cikin ruwan sanyi. Bata da bakin korafi saboda koda wasa bata bar hanyar da Yaya zai yi suspecting dinta ba. Spare makullin gidan da Yaya ya bata, ta amshe, kullum sai ta buga mata gida idan ta dawo daga makaranta, kuma sai ta wulakantata kafin ta bude mata gidan, store din abinci a kulle yake, wani lokacin sai dai ta saka kudinta ta sayi abinci. Idan Yaya baya gidan to ita da babu duk daya suke, duk kokarin Janan akan su daidaita abin yaci tura. Ita cewa ma tayi gwanda ace fada suke yi akan wannan zaman doya da manja din.
Ita kuma tayi-tayi dashi akan ya bari ta koma wajen Anty Sa'a tunda suna Zaria yanzu, ko basa nan akwai kanwar mijinta da suke zaune tare a gidan sai ta zauna dasu, ko kuma ya kama mata gida a samaru, ko ma dai a ina ne, amma yayi fir ya ki. Ita kuma bata so ta takura mishi da maganar kada yace ko bata son zama da matar shi ne ko wani abu.
Sai a ranar naji cewa ashe ba mahaifinsu daya da Yaya Bilal ba. Mahaifinsu Yayan ya jima da rasuwa, bayan nan ne ta auri wani mutum a Kaduna, shine mahaifin Janan din. Sai lokacin na fahimci komi, ina ta mamakin dalilin da yasa Ummarsu take zaune a Kaduna bayan duk danginsu suna Zaria, nayi zaton ko aikine ya kai baban su Janan din Kaduna. Amma nayi mamaki, koda wasa basu taba nuna mata banbanci ba, ita ko su Harira diyar kishiyar Umma, basu taba nuna mata wani ki ko kyama ba.
Janan kuka take yi sosai lokacin da take bani labarin wannan, na rungumeta ina bata hakuri, don shine kadai abinda zan iya yi a lokacin, har ta gama kukan. Daga nan muka fito da littafanmu muka cigaba da karatu har aka kira sallah muka tashi muka yi, muka koma muka cigaba da karatunmu. Muna nan sai ga Anty Ameerah ta leko, tace muje mu debi abinci, Janan ta fita zata zubo mana abincin, sai gata ta dawo wai Yayan yace muje muci tare dasu. Tace haka yake, in dai yana gidan tare suke cin abinci. Na dauki hijabita na saka muka fita.
A falon sai na daga baki ina kallon ikon Allah, gabadaya mata ta rikide, ta koma kamar wata salihar kirki, kamar ba wannan matar da take amsa mana magana da dai-daya ba.
Sai nan-nan take yi damu, abinci kamar zata zuba mana a baki yadda take ta turo mana plates na varieties din abinci gaban mu. Tsabar mamaki ma ni kasa yin magana nayi. Lallai an saka Janan a cikin tsaka mai wuya. Idan har haka take mata, to lallai kuwa babu wanda zai yarda da cewa idan an saka mata yatsa a baki zata ciza, sai dai idan har tayi hakan a gabanka.
Muna gama cin abincin muka koma daki. Muna shiga na fara zuba magana, tsananin mamakin matar ya hana ni hada maganganu masu ma'ana ma, Janan sai