Showing 51001 words to 54000 words out of 73204 words
faranti da cokali. Sai data ajiye sannan ta kalleni, "taso ki ci abinci, ki sha magani".
Sai da tayi maganar abinci sannan naji cikina yana juyawa, ba musu na tashi na cire hijabin jikina na ninke ta da abin sallar. Tun kafin in zauna kamshin kifi ya cika min hanci, naji yawun bakina ya guda. A kasa na zauna muna fuskantar juna, ta turo min plate cike da faten doya. Anyi garnishing dinshi da green beans, peas, alayyahu, hanta da aka yanka kanana, ga kifi da dafaffen kwai a gefe. Ina yin loma daya na lumshe idanuna, kai na hau girgizawa, "ramgwadi! Gaskiya yau ba karamin baje basira kika yi wajen girkin nan ba, meye sirrin?".
Ta kalleni, "ke yanzu nace miki ni na dafa wannan abincin yarda zaki yi? Yanzu na amsa shi wajen Anty Sarah".
Na bude baki cikin mamaki, watakila lokacin da yan kirki suke kan Anty Sarah bamu taba sa'ar cin karo dasu ba sai a wannan lokacin. Iyaka sanina da ita, wannan baya daga cikin halayen dana santa dashi. Amma zata iya yiwuwa dama can hakan take, kila sanin hakan ne bamu taba yi ba.
Nace "ta kyauta sosai, nagode".
Ta kai cokali daya bakinta, "ta shigo ne taga yanayin jikina fa sai ta ganki da drip a hannu. Dazu kuma sai ta turo Mimah tace in je in amsar mana abinci". Na gyada mata kai. Har muka gama cin abincin babu wanda ya sake yin magana. Bayan mun gama, Janan ta kauda kayan can gefe, ta dauko magungunan ta fara balla tana miko min. Da kyar na iya watsa su a baki na hadiye. Wannan yana daga cikin dalilan da suka sa naki tashi dazu da safe zuwa asibiti yana nufin allura da magunguna, ni kuma bana son allura da magunguna.
Janan ta harareni lokacin dana hadiye kwayar maganin karshe da kyar, na fara kakari. Tace "dazu ai da ana tsira miki allura a jiki ko a jikinki".
Nace "kema kin san saboda bana cikin hankalin kaina ne, amma ina ji ina gani in zauna a tsira min allura? hauka nake?".
Ta kwashe da dariya, na harareta, "muguwa kawai!". Gwalo ta min kamar wata karamar yarinya.
Tashi tayi ta dauki kwanukan ta fita. Na lallaba na lalubo wayata daga bayan katifa inda na jefata jiya. Nasan anyi ta nemana babu kakkautawa, musamman ma Muhammad. Na kunna wayar na tsaya tayi loading kafin na bude ta, nayi gaskiya kuwa. Sakonni daga Muhammad sun fi cikin kwando, tambayarshi daya, lafiya? Na hade fuska lokacin dana kula daga cikin sakonnin akwai na Umar, ko kara kallonsu ban yi ba na goge su gabadaya. Na tafi dungurungum nayi blocking dinshi daga wayata.
Komawa nayi daya bayan daya ina karanta sakonnin shi. Duk karantawar da zan yi, zuciyata kara narkewa take yi cike da begen shi, Allah ya sani, a kullum kaunar bawan Allahn nan kara yado take yi a sassan zuciyata. Ban sani hakan ko abu mai kyau bane ko kuma akasinsa. Kafin in gama karantawa jikina yayi wani irin sanyi, daga cikin kalaman shi kawai, babu tantama zaka karanci tsananin kulawa, tsantsar so, da kauna mara iyaka a cikinsu. Jikina yayi sanyi saboda babu mahalukin daya taba nuna min kwatankwacin irin wannan so, kauna da kulawar da wannan bawan Allahn yake nuna min. A duniya yanzu waye yake damuwa kawai don ya kira wayar wani daga dare zuwa safe ya ji a kashe? Sai Muhammad. Sai daya kai ga tambayar ko dai wani laifi yayi min ne, a cikin sakon. Ina gama karanta shi na lalubo lambar shi na danna kira, ban ma san me zan ce mishi ba. Sai dai cewa aka yi line busy, alamun yana waya. Don haka naci gaba da karanta sauran sakonninshi, nasan idan yaga missed call dina zai kira.
Janan ta dawo dakin da waya a kunnenta, daga yanayin yadda take maganar da Yaya Bilal take wayar. Hankalina yana kan sakonnin M.B da nake ta nanatawa, kamar wani karatu. Don haka sama-sama nake jin muryarta a kaina. Bayan ta gama ta zauna a gefena, tace "Yaya ne ya kira yana tambayar ko kin tashi nace eh. Yana Funtua shi da Anty Ameerah, wai ya kaita wajen sunan kawarta," ta fada tana tabe baki, ni kuma na dan murmusa saboda yadda ta bani dariya, "yace a duba ki da jiki dai kafin ya dawo".
Nace "babu komi wallahi, ai na warware".
Tace "yauwa, na ma tuna! Ummah tace tana so ta duba ki itama". Ta ciro wayarta ta kirata, bayan sun gaisa sun yi yar hira, Janan ta miko min wayar na amsa, na gaisheta cike da girmamawa kamar tana gabana. Tace "Janan dai ta goga miki, daga zuwa jinya sai kema ki buge da jinya?", ni da Janan muka yi dariya sosai. Mun jima muna hira da ita, Ummahn su Janan ta iya bi da mutum cikin sanyin kalami kaji ka saki da ita, akwai lokuta da dama da zamu fara hira da ita cikin dari-dari ko rashin sakin jiki, amma cikin dan kankanin lokaci zan ji na saki da ita sosai, inji na hau hira da ita sosai. Wasu lokutan sai daga baya zan zauna ina mamakin hakan. Munyi sallama da ita tana ta zuba mana addu'o'i kamar yadda ta saba, na kashe wayar na mikawa Janan.
Kwanciya tayi rigingine tana kallon ceiling din dakin, ni kuma na lalubo game din candy crush a wayata ina bugawa. Shiru ya ratsa dakin na dan wani lokaci, can naji tace "Nan da sati biyu Yaya zai tafi umarah shima".
Na kalleta cikin mamakin dalilin da yasa ta fada min, nace "and?".
Ta kalleni tana wani yin kasa-kasa da idanu, "don Allah kizo ki taya ni zama kafin ya dawo!".
Na zaro ido, "wa? Ni?? Ki rufa min asiri in mutu maza su kaini ba mata ba! Ana zaman lafiya, da hankalin kaina, anya kina ma so na kuwa?".
Ta harareni, "yo meye na wani zaro ido? Wuta nace ki zo ki taya ni zama?".
Na koma na kwanta ina dariya, "lallai ma, zama a gidan nan naku ai sai wanda ya shirya, ni kuma ban shirya ba. Jira nake goben nan tayi, idan na cira kafa na bar nan gidan sai kuma baba ya gani. Idan da son rai na ne ma, har in bar Zaria ba zan kara zuwa nan ba!".
Tace "inaa, kema kin san wasa kike yi coz you are stuck with me babe, babu yadda zaki yi dani. Sannan gobe babu inda zamu je sai jikinki ya kara yin kwari sannan, maybe zuwa talata?".
Na kalleta ina dan murmushi cike da jindadi, "babu wani hutu da nake bukata don ni nan garas nake ji na, amma kuma wa zai ki hutu koda na kwana daya ne musamman daga wannan asibitin?". Itama tayi murmushi.
Karan da wayata tayi ne yasa na kalli hannuna duk da kida na musamman ne, na riga nasan mai kiran. Na turo baki cikin shagwaba, ban san dalili ba, duk lokacin da nake tare da Muhammad, na kan ji ni kamar wata yarinya karama, kamar wata sabuwar halitta.
Cikin shagwabar na daga, yana ta magana nayi shiru, yace "haba baby na, come on, talk to me mana. Nayi laifi ko? Am sorry!". Nayi shiru ina jinshi ya cigaba da cewa "haba baby na, baki so in ji daddadar muryar nan taki ne? Come on...".
Na turo baki kamar yana gabana, "ba kai bane ka ki daga wayata dazu ba?".
Ya saki murmushi mai sauti, "tuba nake gimbiyata, ina amsa wata waya mai muhimmanci ne. And you are the one to talk, idan maganar gaskiya ake yi ai nine ma yakamata ace nayi fushi. Na ga tun jiya nake kiran wayarki a kashe. Baki ji warin kunar da zuciyata ta dinga yi bane?!".
Ban san lokacin dana kwashe da dariya ba, nace "oohh, da gaske?".
Yace "sosai ma, da yadda nayi ta kiran sunanki. Duk baki ji ba?".
Na sake yin wata dariyar ina girgiza kai cikin wani irin matsanancin farinciki, nace "ban ji ba gaskiya!".
Yace "nayi tunanin gabadaya mutanen Zaria sun ji!". Na cigaba da kyalkyala mishi dariya.
Mun jima sosai muna kwasar hirar soyayyarmu, har na rasa tracing din lokaci. Lokacin da muka yi sallama dashi, bakinshi yana furta I miss you's da I love you's. Zuciyata fara kal, kamar farar takarda.
Janan da tunda na fara wayar take kallona baki a dage, ta kalleni tana murmushi, "anyi nisa a lambun soyayya!!".
Nayi dariya ina birgima a tsakiyar dakin, "baki san komi ba Jan... You've no idea. Ya Allah, I love that man!!".
Dariya ta saki, ta taso ta rungume ni, ban san dalili ba, amma nima rungumeta din nayi. Tace "na taya ki murna, dear. Congratulations!". Nayi murmushi.
#F.W.A
[23/03 9:40 AM] Jiddah Lawal: 🌟 *⋆☆A ZATO NA...!☆⋆* 🌟
*⋆©Jeedderh Lawals⋆*
*☆⋆18⋆☆*
Yinin ranar a daki muka yi shi. Bayan munyi sallar la'asar, Janan ta kunna mana film din X-Men a wayarta muka fara shi tun daga farko. Babu abinda ya dinga tada mu sai sallah da cin abinci.
Bayan isha'i, Janan ta tado ni muka fita waje, a cewarta kafa zamu dan wasa musamman ni da babu inda na fita tun yau. Ban damu ba, na dauki hijabi ta na saka muka tafi. Garin tun da yamma tayi yayi alamun hadari, ga wani irin zafi da aka yi kamar zai kona mutane. Sai dai zuwa yanzu ya dan yi sanyi, iska mai sanyi yake bugawa a hankali.
Muka taka ni da ita har bayan layin su, can wajen irin masu suyar wara da doya da fulawa dinnan don Janan tace abinda take son ci kenan yanzu.
Matar inyamura ce, sana'ar hannu take yi tun karfinta, safe, rana, dare, babu hutu balle kakkautawa. Shi yasa wajenta kullum cike yake da kwastomomi da kuma ma'aikatan da suke kama mata aiki.
Saboda yawan mutane yasa bamu samu mun siya da wuri ba, lokacin da muka tsaya a gabanta, ta kallemu cikin murmushi. Ba laifi mun dan saba da ita, saboda a yawancin lokuta a wajenta muke sayen buns da eggroll da rana. Ta kalli Janan tace "kwana biyu kun dauke mana kafa!".
Ni da Janan murmushi kawai muka yi muka gaisa da ita. Ta kulla mana wanda muka saya a cikin leda, muka amsa muka mata sallama muka juya.
Cikin rashin sa'a kafin mu karasa gida ruwan sama ya sauka mai karfi, muka daga kafa cikin sassarfa muka kara sauri. Duk da haka kafin mu karasa gida, jikinmu ya jike sharkaf! Har digar ruwa muke yi. Da sauri muka karasa cikin falo, a dan corridor dinsu kafin a shiga falo muka tsaya domin mu dan kafe kada mu bata musu carpet din falo da lema.
Muna tsaye anan sai karan turo kofa muka ji, muka juya muna kallon Yaya daya shigo shima yana linke umbrella din daya shigo da ita. Muka zaro idanu mu duka a tsorace muna kallonshi, nayi zaton a gidan Anty Ameerah yake yau, ko kuwa ba acan yake ba? Aka fara kallon-kallo tsakaninmu dashi.
Ba Janan kadai ba, ni kaina sai da naji zuciyata tana tseren tashin hankali.
Ya hade fuska kamar yaga wasu mala'ikun daukar rai, "daga ina kuke?!". Ya tambaya murya a cune.
Janan ta fara kokarin ja da baya a tsorace, cikin in'ina ta fara cewa "um... nan.. ne baya!".
Ya daga murya, "ina ne nan bayan exactly?! Ba na hana ki fita waje da dare ba? Ban da rashin hankali kawai sai ku kama kafa ku fita daga gida da dare babu tunanin komi, kuna ganin hadari kuma! Ku duba yanda ruwa yazo ya muku duka, musamman ke da kike rashin lafiya! Karatun da kuke yi kenan dama? Idan fa jikin ki ya kara rikicewa?". Ya maido tambayar kaina. Na dan yi tsalle a tsorace, na koma bayan Janan na lafe kamar ita zata kare ni daga fadan shi.
Allah ne ya bata kwarin gwiwar iya daga baki don ni gabadaya jikina rawa yake yi, tace "kayi hakuri Yaya, abinci muka fita muka sayo".
Yace "abincin waje a gidana? An hana ku dafa abincin ne? Waye ya hana ku?!".
Janan tayi saurin girgiza kai, "babu ko daya wallahi, kawai mun ji marmarin awara ne, shine muka fita muka sayo. Bamu yi zaton ruwan zai same mu a hanya bane amma kayi hakuri...".
Ya dan sauke ajiyar zuciya alamun ya dan sauko, yace "to shikenan, amma kada ku kara". Muka hau gyada kawuna kamar wasu kadangaru.
Yace "to ku wuce kuje ku canza kaya kafin wani abin ya kama ku". Bamu jira ya sake cewa komi ba, muka bar wajen a sukwane.
Sai da muka shiga daki muka maida kofar muka rufe, sannan muka sauke wata nannauyiyar ajiyar zuciya, kafin muka kalli juna muka kwashe da dariya.
Bayan mun canza kayan jikinmu, mun shanya wadanda muka cire, muka cigaba da kallonmu muna cin awarar.
*
Washegari bamu tashi da wuri ba saboda mun san cewa ba asibiti zamu je ba. Da muka yi sallar asuba, Janan ta wa wata sister Mairo matron dinmu text akan cewa ba zamu samu damar shigowa ba saboda rashin lafiya, bayan ta turo mata da amsa akan babu damuwa Allah ya bamu lafiya, muka koma gefe muna dariya kafin muka koma barci. Sai wajen karfe tara na safe muka tashi. Janan ta fita kicin zata dora mana abinda zamu ci, ni kuma nayi amfani da wannan damar na shiga bandaki na watsa ruwa.
Kafin in fito ta dafo mana indomie, muka zauna muka ci ta sake daukar kayan ta fita dasu. Ta dawo ta zauna a kusa dani ina duba wasu textbooks dinta, zuwa yanzu naji na warware sosai, kamar ban taba yin wata rashin lafiya ba, amma duk da haka sai da Janan ta takura min ba sha magani.
Tace "ki zo muje ki taya ni in yiwa Yaya doughnut da cin-cin don Allah".
Nace "nayi zaton ya tafi?".
Ta girgiza kai, "sai gobe. Abin azumin da za'a fara gobe, yana can babban gida, jiya da yau yayi rabon azumi".
Na ajiye textbook din ina kallonta, "amma banda abinki Jan, saboda Allah me zai yi da doughnut da cin-cin da azumi?".
Tace "ya dinga sahur ko shan ruwa mana!".
Na fashe da dariya ina girgiza kai, "gaskiya Ummah tana da sauran aiki a gabanta wallahi, haka zaki yi aure kije ki dinga soyawa miji cin-cin da azumi?".
Ta mintsileni a gefen cinya tana dariya, "bana son iskanci wallahi, zaki taya ni ne ko yaya?".
Na mike ina laluben abinda zan sakaya jikina dashi, "kin san ni bana wuce tayin kayan zaki dangin fulawa". Muka fita daga dakin muna dariya bayan na dauki karamar hijabi data tsaya a ruwan cikina na sa.
Gidan shiru, haka falon babu kowa hatta da TV a kashe take. Na san kila sun tafi makaranta, wannan ko kuma suna daki suna barci. Muka fada kicin muka fara aikin daya kaimu.
Bamu yi minti talatin cikakke ba, muka ji an bude daki an fito. Ba'a jima ba Salama da Haleemo suka shigo kicin din cikin kayan barci, na kallesu na kauda kai cikin girgiza kai. Haka suke yawo wani lokacin a gidan cikin kaya masu bayyana jiki, a ganina duk da a gidan Yayarsu suke ai hakan bai kamata ba. Ba fa kowane mutum bane na Allah.
Haleemo ta dan dakata data ganmu a kicin din, sai kuma ta maze ta kallemu, wai "sannunku!". Muka yi banza ni da Janan muka kyaleta kamar ba damu take ba. Salama tayi dariyar mugunta tana bude firjin, tace "Allah ya kara, uwar sanabe da neman gindin zama!". Ta dauki abinda zata dauka ta fita daga kicin din ta bar Haleemo a tsaye.
Kame-kame ta fara, "uhmn, Na'ilah nace., ni fa ban san wannan gayen saurayinki bane! Shi ya fara zuwa wajena, kuma sai daya ne, na rantse da Allah...".
Na katseta ta hanyar juyawa ina watsa mata harara, nace "ni fa kinga Haleemo, idan na raina kasuwa ko sako bana badawa cikinta. Ban tambayeki alakar ki da tsohon saurayi ba ba, ko kallon banza ban miki ba, saboda baki kai matsayin da zan zauna ina cacar baki dake akan wani saurayi ba wallahi. Alfarma kika min babba da kika lallaba kika hillace shi, godiya ma yakamata in miki, don haka ki kwashi jikinki ki bar nan wajen wallahi, duk abinda mutum yayi dai ai kansa ya yiwa, walau mai kyau ko marar kyau!".
Ta saki baki tana kallona, sai kuma ta juya ta bar kicin din da sauri. Naja dan siririn tsaki.
Da yake kwabin doughnut din da muka yi babu yawa, nan da nan muka gama soya shi. Muka fara na cin-cin din, zuwa lokacin rana ta fara yi.
Ni kadai ce a kicin din lokacin da Raheemah ta fado kicin din kamar wata kububuwa, Janan ta leka waje zata samu wani yaro ta suka can bakin titi.
Na gaidata a kaikaice, hankalina yana kan fulawar da nake murzawa.
Maimakon ta amsa, sai naji ta ja dan tsaki, "uhumm, ihunka a banza kenan! Ina amfanin wadda za'a kwace saurayi a hannunta tana zaune? Hakan yana nuna aikin banza ne, kuma abu mai wahala ace za'a iya kwace miji! Don ma dai mutum yaji ya sani, idan ma saboda mijina ne ake min zarya ana min shige da fice a gida, to wallahi mijina yafi karfin haka. Nima kuma nafi karfinshi!".
Allah sarki, naji maganganunta sun bani takaici sun kuma bani dariya, na girgiza kai a hankali ina dan murmushi. Banda tsabar hauka da rashin tunani, har ta wani kalleni tace wai zanyi kwacen miji? Tsakanin ni da ita ko wa yayi kama da wanda zai yi kwace? Na sake girgiza kai.
Ta kama kugu tana wani jijjiga jika ganin ban tanka ta ba, tace "ke Baiwar Allah dake nake, aha! Ni dai na fada na sake fada miki, mijina yafi karfinki!".
Na juya na kalleta ina murmushi, "ai na fiki sanin haka, saboda haka ki kwantar da hankalinki, mijinki naki ne ke kadai, ban iya snatching ba wallahi!".
Sai ta hau wasu tsalle-tsalle cikin masifa, "dariya ma kike min kenan? Ke wallahi na ga alamun iskancin ki yawa yake yi fa! Ke har kin isa ki zauna kina min